الجمعة، 24 أغسطس 2018

BARKAN KU ALHAZAI


Hudubar Juma'a  na Masllacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sheikh Abdullah bin Abdurrahman Al-Buaijan 13-12-1439
HUDUBAR FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda da ni'imarsa ne ayyuka nagari ke cika, ina gode mishi tsarki ya tabbata a gare shi,ina neman taimakonsa bisa abin da ya shude da abin da zai zo, na shaida, ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, ya yi wa Alhazai baiwan kammala hajjinsu,  bayan sun tsaya a farfajiyan  arfa.
Na shaida Annabi Muhammadu  bawan sa  ne kuma manzon sa ne    Ubangijin shi ya turo shi da shiriya  da hujjoji bayyanannu  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da iyalan shi da sahabban shi  da  gaisuwa mafi tsarki.
   BAYAN HAKA:
Ina muku wasiyya ya ku bayin Allah da kuji tsoron Allah , domin tsoron shi shi ne mafi alherin tufafi kuma  shi ne mafi alherin guzuri  kuma shi ne mafificin hanya zuwa ga yardan Ubangijin bayi   ( Ya ku wadanda suka yi  imani in  kun ji tsoron Allah  zai sanya muku  haske da zai banbance tsakanin karya da gaskiya   zai kankare muku miyagun ayyukan ku zai gafarta muku zunuban ku  Ubangiji ma'aboci falala ne  mai girma ).
    Maziyarta dakin Allah mai alfarma
Albishir ga wanda ya amsa kira kuma * ya nufi ta bigiren  wurare masu tsarki ,yana mai hailala yana neman rahama.
Barkanku Alhazai maziyarta dakin Allah mai alfarma tun da Allah ya shiryar da ku ya karrama ku,ya muku baiwa na saukake muku hajji wanda da yawa daga cikin mutane basu samu iko ba.
Barkan ku  da kuka  samu  datarwa  don sauke ayukan haji daya daga cikin rukunnai  guda biyar  na musulunci  kuka amsa kira kuka kyautata sauke nauyi .
    Barkan ku  an daga darajojinku  an gafarta muku zunuban ku  an kankare muku kusakuran ku  an sitirce muku laifukan ku da izinin Allah Masanin gaibi .
   Barkan ku  kun ciyar da dukiya kun bada lokaci  kun bada karfi da kokari kun kutsa cikin wahala da gajiya   kun bada kyautan abubuwa mafi tsada na ku .
   Kun bar iyalai  da  kasashe  kun amsa kiran mai girma da daukaka  kun zo kun hallara a gu mafi daraja   da daukaka kun tsiraita daga  adon ku da tufafin ku     kun fiskanci Allah  da kura kuna masu talbiya  kuna kai bici-bici  kuma kuna masu talbiya kuna masu kankan da kai  kuna marairaicewa  kuka nemi mafaka a gare shi shi kadan shi  kuna masu ikilasi  to albishirin ku –albishirin ku to,  Allah shi ne mafakan masu jinkan masu yin jinkai  shi ne mafi karamcin masu karamci,  ba ranar  da Allah ya fi 'yanta bayi daga wuta  kamar ranar Arfa kuma lallai yana kusantowa  sannan ya yi alfahari da ku ga mala'iku, sai ya ce wadannan bayi na ne sun zo min suna  bici - bici da kura,  daga kowani sako mai zurfi, suna neman rahama ta suna tsoron azaba ta, ina kuma ace da sun ganni?  Da zunubanku sun  kai adadin turbaya ko tudun kumfan kogi da na gafarta muku, ku tafi ya ku bayi na na gafarta muku,
Albishirinku ya ku mutanen Arfa  wanda   ***  da shi  Allah ke gafarta zunubai ya yi rahama.
'yantattu nawa ne aka kammala 'yanta su a ciki***  Wasu kuma suna can suna ta kokarin  aikin, kuma  Ubangijin shi ne mafi  rahama
YA KU MUSULMAI:
Masu ziyartan dakin Allah mai alfarma  a wadan nan ranaku  a aikace kamar cewa suke yi ,   ga mu mun  dawo mun kuma komo masu tuba muna masu  godiya  ga Ubangijin mu .
       Farin ciki na lullube da su  suna masu komawa kasashen su da garuruwan su  a halin sun kammala ayukan su na hajji sun sauke nauyin su ,  ( Ka ce da falalan Allah da rahamar sa  sabo da haka su yi farin ciki shi ya fi  alheri  daga abin da suke tarawa .)
   To ta iya yiwuwa su koma  kasashen su kamar yanda mahaifiyar su ta haife su , za su koma da ganima  da ke sanya  yabo da godiya  an gafarta zunubai zan suturce aibi an kankare kusakurai  .
    To dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah  bisa kamalar sa da daukakar sa  ,  kuma dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah  da  ya shiryar da mu zuwa ga wannan  kuma ba mu kasance da mu shiryu ba , ba don Allah ya shiryar da mu ba.
YA TAWAGAN ALHAZAI :
     Lallai ko wani  fiskantowa na da juyawa  haka nan ko wani haduwa  na da rabuwa da kuma abin labartawa,  bayan mun ga alhazai suna tahowa daga ko wani sako mai zurfi da gari na nesa don su halarci abubuwa masu amfani a gare su  runduna-runduna masu yawa da gangami daban-daban  a wurare masu tsarki na ibada , wanda hakika harsunan su ya saba da juna  da launukan su da garuruwan su  da kuma jinsin su  da kuma shekarun su  sai dai musulunci  ya  hade su   ya maida alkiblan su daya  da ayukan  hajjin  su suna masu ihrami da tufafi iri guda  suna masu talbiya da kira iri guda sun taru a farfajiya guda  hakika Allah ya hada zukatan su   da ka ciyar da abin da yake doron kasa gaba daya da ba ka hada zukatan su ba amma Allah ya hada zukatan su  .
    Bayan kammala ayukan haji   sai ga tarun jama'a masu yawa da adadi masu dumbin yawa  suna bankwanawa wuraren ibadan da  suke tsananin shauki a zuciyar su  da gabban su, yana nuni da cewa:-
 Gidajen mu kuna da matsayi a cikin zukatan mu
  Taron nan na al'uma suna ta  rabuwa  cikin    yanayi da za ka gani a ido na ban tsoro kuma mai tasiri,   wani abu ne na daukan darasi mai girma da jama'a suka shaida .
   Lallai wanna rabuwa din bayan haduwa na wani lokaci  kankani  yana tunatar da mu rabuwa irin na duniya  da kuma  sauyin al'uma bayan al'uma  karni bayan karni  a haifi wannan al'uma a yi barka da su a fiskance  su  a yi bankwana da wancan al'uma a jajanta musu  a kaurar da su , ( Dukkan wanda ke kanta zai kare   fiskan Ubangijin ka ne zai wanzu ma'aboci daukaka  da girmamawa ).
YA TAWAGAN ALHAZAI :
Lallai a hajji akwai abin wa'azi ga me  wa'azantuwa  kuma lallai da'a tana da wani amfani da tasiri a cikin zuciya ,  salla tana hani da alfasha da abin ki  amma ambaton Allah ya fi girma ,  hajji kuma wani mashaya ne na kwankwadan tsorn Allah (Ku yi guzuri mafi alherin guzuri shi ne tsoron Allah  ).
To ita ibada idan bata kusantar da mutum zuwa ga Allah ba  tana nisatar da shi ga abin da Allah ya haramta ba ,  to fa lallai wannan ibada mai algus ce ko kuma wacce ta sabawa addini,  Allah madaukakin sarki ya ce :-(Lallai Allah na karba ne kawai daga masu takawa).
YA KAI  ALHAJI:
Abin da ke kan ka na farilla ka rama shi  abin da kuma ke doron kasa na wani abokin jayayya to ka yardar da shi abin da ke kanka na hakki kuma ka bayar da shi   ka tsaida farillun Allah kuma ka yi kokari a sha'anin su   ka lizimci sunnan Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a  gare shi   a dimance shi  ka nemi  tsira da kubuta  ka sabunta  alkawari tsakaninka da Allah da azama da cika alkawari da ikhlasi, .
   YA KU ALHAZAI:
 Lallai Allah mai shaida ne akan dukkan komai ( ba ya fada daga wata magana face mai zaman dirshan yana nan gare shi ) Makogoron ku ya shake kuna ta fadin kalmar tauhidi duwatsun makka na amsa  kuwwan talbiyar ku har zuwa ranar idi  Allah mun amsa kiran ka  kuma Allah mun amsa kiran ka , mun amsa kiran ka ba ka da abokin tarayya ,  dukkan yabo da godiya  sun tabbata gare shi   da mulki duka na ka ne  ba ka da abokin tarayya ,
To a yi bara'a daga shirka to a yi bara'a daga shirka  domin Allah bai karbar aikin da akwai kwatankwacin kwayar zarra  na shirka a ciki,  hakika kuma ya ce  ( Ni na wadatu daga abokan tarayya duk wanda ya yi wani aiki  ya hada ni da wani a ciki na barshi da  shirkar sa) muslim ne ya rawaito.
(To ku bautawa Allah kar ku hada shi da wani ),  to ku lizimci shari'ar ku ku kiyaye addinin ku .
BAYAN HAKA:
YA KU MUTANE:- Lallai Ubangijin ku daya ne mahaifinku guda ne   ku saurara ba fifiko tsakanin balarabe  akan ba'ajame ,    ko ba'ajame akan balarabe  ko ja akan baki ko baki akan ja sai da tsoron Allah   , to lallai Allah ya haramta a gare ku jinannakin ku da dukiyoyin ku ,  da mutuncin ku , kamar   alfarmar ranar suka  a watan zulhijja a garin makka,  ku saurara kar ku koma a baya na kafurai sashi na dukan  wuyan sashi .
     YA  KU ALHAZAI :
Wannan shari'ar Ubangijin ku ne    kuma wasiyyar Annabinku ne to ku lizimce ta  hakan shi ya fi alheri a gare ku a wurin Mahaliccin ku ,.
HUDUBA TA BIYU  
 Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kamalan addini da cikan ni'ima  da bayyanar hanya  da bullowar hujja  da kammalan aikin hajji  godiya wanda zai cika  ni'imomin sa  mabanbanta  tsira da amincin Allah su tabbata   ga Manzannin sa da Annabawan sa .
       Maziyarta dakin Allah mai alfarma  lallai na daga cikin alamomin karban da'a  akwai daidaituwa  akan tafarki da kuma tabbatuwa da dukufa akan shi ,  da kuma yiwa  rai hisabi   bisa ga gajartawa da sakaci da  take yi   wadannan  su ne sifofin masu tsoron Allah masu kushu'i  da ikhlasi (Allah na tabbatar da wadanda suka yi imani da  tabbataccen zance a rayuwar duniya da ma lahira  kuma Allah na batar da azzalumai  ).
    Ku saurara lallai daidaituwa akan tafarki  shi ne hakikanin  mika wuya  da tabbatuwa akan addini da gaskiya da wafa'i .
   An karbo daga Sufyan dan Abdullah Assakafi  Allah ya kara yarda a gare shi  ya ce : na ce ya Manzon Allah  ka fada min wata ,magana a cikin  musulunci wanda bazan tambayi wani ba koma bayanka  sai ya ce: ( ka  ce na yi imani da Allah sannan ka daidaitu ) Muslim ne ya rawaito .
     Daidaituwa akan tafarki shi ne   kubuta daga tsoro  da  aminta daga   kwadayi da bacin rai  , kuma albishir ne mai girma( Lallai wadanda suka ce Ubangijin mu Allah ne   sannan suka daidaita mala'iku na sauka a gare su:- kada ku ji tsoro, kada ku yi  bakin ciki   kuma ana muku albishir da aljanna wadda aka kasance ana muku alkawari da ita 0) 
Tsayuwa a kan tafarki   yana daga cikin darajoji na kamala ba wanda zai samu haka sai ma'abota himma da dabi'u  hakika mai izza da daukaka ya ce:-( ku cika alkawarin Allah  idan kun yi alkawari kada ku warware rantse-rantse bayan karfafata alhali kun sanya Ubangiji wakili akan ku hakika Ubangiji  ya san abin da kuke aikatawa  ,      Kada ku kasance kamar matar nan da ta warware kadin ta bayan inganta shi   , a warware) .
    Maziyarta dakin Allah mai alfarma  :  lallai na daga cikin wajibi akan ko wani musulmi  ya godewa Allah mabuwayi da daukaka  bisa ga abin da yayi  na ni'ima na aminci , da zaman lafiya ,ga wannan kasa mai albarka,     wacce take karban wadannan adadi mai yawa na daga musulmai daga sassa daban-daban  na duniya  take tashi da karban bakuncin su  da kimtsa musu wuraren ibada   cikin mafi kyaun  mutsayi kuma ta gabatar musu da hidimomi mafi daukaka  gwargwadon iyawa  wanda ke fitowa kai tsaye karkashin kulawan mai hidima ga Masallatayya biyu masu Alfarma,  da mataimakin sa amintacce   Allah ya kiyaye su, to godiya da kimantawa  da jagororin mu masu tsayuwa akan hidimawa musulunci  da musulmai  godiyar Allah ga kokarin su, kuma Allah ya karbi ayukan su ya rubuta hakan cikin ma'aunin  kyawawan su.
  

YA KU ALHAZAI:
Ku lizimci bin doka da oda da tsari  wanda ke taimakawa wurin sauke hidima  kuma  ya saukaka a gare ku  hanyoyi na gudanarwa  sa'annan kuma yana bada kaso mai yawa wurin kawo aminci da zaman lafya a rayuwa   ku tausayawa kawunan ku, ku nisanci sabawa doka da oda  .
 Allah ya sanya hajjinku abin da'a ne kokarin ku kuma abin godewa ne zunuban ku kuma abin gafartawa ne ya mai da ku zuwa ga iyalanku da gidajen ku cikin aminci   kuma cikin ganima kuna masu samun lada da farin ciki da annashuwa.
 Muna mikawa Allah ajiyar addinin ku da amanar ku da karshen ayukan ku Allah ya muku guzuri da tsoro Allah , ya gafarta muku zunuban ku ya tabbatar muku gurace-guracen ku , ya riskar da ku zuwa ga cimma muradan ku  da fatan ku , lallai shi mai ji ne kuma mai amsawa.
  Wannan kenan to, ku yi salati da aminci ,- Allah ya muku rahama- bisa ga mafificin halittu.
      
      
  
  












ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق