Hudubar Idi na
Masllacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sheikh Salah bin
Muhammad Al-Budair 10-12-1439
HUDUBAR FARKO
( ALLAHU AKBAR
ALLAHU AKBAR ALLAHU
AKBAR ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR
ALLAHU AKBAR ) Allah mai girma Allah mai girma Allah mai girma Allah mai girma Allah mai girma Allah mai
girma. Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
( WALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR WA
LILLAHIL HAMDU) kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya na shi ne , (ALLAHU
AKBAR KABIRAN WALHAMDULILLAHI KASIRAN WA
SUBHANALLAHI BUKRATAN WA ASILA ) Allah mai girma kuma babba dukkan yabo da godiya masu tarin yawa na shi ne , kuma
tsarki ya tabbata ga Allah safiya da
maraice .
Allah mai girma safiya da maraice *** Zuciya mai kauna kuma mai yarda na wayan gari da shi
Allah mai girma
hasken duhu idan ya yi duhu *** wata ya
bayyana gare mu mai haske mai kaye
Allah mai girma da
safiya idan *** haske idan ya sulale
zuwa ga zukat masu kyau
Allah shi ne mafi girman wanda za a kira kuma shi ne mafi
darajan wanda za a yi fata a gare shi
kuma shi ne mafi daukakan wanda ke bada kyauta Allah mai girma cikin kauna
da kankan da kai da
girmamawa da daukaka .
Allah mai girma Allah mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan
yabo da godiya na shi ne.
Dukkan yabo da godiya na shi ne ,
dukkan yabo da godiya na shi ne bana bukatan canza wani da shi , godiya wanda zai kai da yardan sa mafi
cika , ina gode mishi godewa na kololuwa kuma mafi cika da kamala kuma mafi girma
mafi gamewa.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
shi kadai yake ba shi da abokin tarayya ya yalwata mana ni'imomin sa masu
yawa da kuma ladufan sa masu girma
, na shaida cewa Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad bawan
sa ne kuma Manzon sa ne tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi da kuma dukkan
Annabawa da dukkan iyalan su da mabiyan
su masu daraja tsira da amincin
Allah abin ribanyawa masu tsarki na
dindindin ba tare da yankewa ba .
BAYAN HAKA:-
TO YA KU MUSULMAI:-
Ku ji tsoron Ubangijin
ku hakika mai tsoron Allah ya rabauta
mabarnaci kuma shakiyyi ya yi hasara .
(Ya ku wadan da suka
yi imanin ku ji tsoron Allah cancancin tsoron sa kar ku mutu face kuna musulmai ).
YA KU MUSULMAI
:-
Ina tayya ku murna a
gare ku bisa ga wannan rana mai girma , ina taya ku murna ga wannan rana
na idi mai sa'ida .
Ina taya ku murna da wannan ranar Hajji mafi
girma.
ina taya
ku murna da wannan rana na yanka
mai kayatarwa.
Ina taya ku murna da
wannan rana na gangami mai girma
Iska ya kada sai ya
bada kyauta na shauki mai yawa ga zuciya *** Ya koro zuwa gare ni
na daga farin cikin abin da ya koro
An karbo daga Abdullahi dan Kurad Allah ya kara yarda
a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (LallaiMafi
girman ranaku a wurin Allah madaukin sarki
shi ne ranar yanka sannan kuma sai ranar shanya ). ABU DAUDA
NE YA RAWAITO SHI .
Tsayuwa a daren shi jifa da suka
da dawafi a safiyan shi to abun mamaki da irin girman wannan rana abin mamaki kuma da irin taruwan da ake yi a
cikin shi .
Allah mai girma Allah
mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai
Allah , kuma Allah mai girma Allah mai girma
dukkan yabo da godiya na shi ne .
YA
KU MUSULMAI :-
Tun lokacin da aka kafa
wannan addinin aka dasa ginshikanta musulunci ya daukaka da darajan shi :- Shugaban hanifai baba ga Annabawa wanda ya gina ka'aba abin
girmamawa Ibrahim Alkhalil tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi
sai ga muminai tawaga –tawaga suna shauki zuwa ga daki abin girmamawa , kuma gari mai alfarma bukatu ba sa yankewa daga gare shi aba a kare
bauta a cikin shi da tunani da dubi .
Tsarki ya tabbata ga Allah abin bauta wanda ya shar'anta a gare mu wadannan ibadodi
masu girma kuma ya shiryar da mu zuwa gare
su wadannan alamomi na addini da dalilai
ya kawata mu da wadannan manyan alamomi
da tutoci .
Tsarki ya tabbata
gare shi sa'annan kuma tsarki ya tabbata gare shi wanda zai koma zuwa gare shi
*** Kafin mu dutsen judiyyi sun yi tasbihi da sandararrun abubuwa
Allah mai girma Allah
mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai
girma dukkan yabo da godiya sun tabbata
gare shi
YA
KU MUSULMAI :-
Na daga ni'imomi
bayyanannu da falaloli
na zahiri kuma wannan shi ne mafi
girman abin alfahari na zamani kuma mafi
daraja , daga cikin alamomin shi shi ne Allah ya kebance wannan kasa mai
albarka da hidimawa wadan nan garuruwa
biyu masu alfarma madaukaka da wuraren ibadodi masu tsarki da kulawa da ayukan haji da kuma alhazai sai ya bata daukakanta , ya damka mata jagorancin ta ya mika mata jan ragamar su kai madalla da
wannan girmamawa na wannan ni'ima da wannan kyauta abin mamaki da girman wannan kyauta abin
mamaki da girman wannan kyauta sannan abin mamaki da girman wannan kyauta .
Sarakunan wannan kasa ta sunna da gommnonin
ta da mazajenta sun yi alwashin ba da kawunan su don hidimawa aikin hajji da alhazai.
Sai suka jagoranci
al'amura na hajji * Allah da musulunci da Addini na godiya gare su.
Cikin mu akwai masu
daukaka addinin Allah da ba shi kariya * cikin mu akwai masu zare tokobi don taimaka
addinin Allah.
Amma shi makiyi idan ya
ga ni'ima sai ya yi kus, idan ya ga kuskure sai ya yi murna, idan ya ga wata
falala sai ya yi shuru
Yana boye gaba
alhali bata boyuwa *makiyi
yana fadin abin da ya gani na abin da ya mishi dadi
Masoyi yana da wani ido na bayyane ***game da abin kiyayya shi kauna na da wasu alamomi
Yin kiyayya ga wannan
kasa mai albarka da kokarin taba amincinta da zaman lafiyanta shi ne kiyayya ga alkiblan musulmai da
wuraren su masu tsarki da
hurmomin su da hajjin su da ibadodin su
da kuma gaba ga musulmai kwatankwacin fadin mai fadi :-
Kai dinnan ba mai
mulki ne kawai don tunkude wanin shi ba sai dai tauhidi ne don rushe shirka Allah
mai girma Allah mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai
girma Allah mai girma dukkan yabo da
godiya sun tabbata gare shi.
YA KU MUSULMAI:-
Yana daga cikin
tushe na ma'abota imani ma'abota hadisi da sunna masu kiyaye addini da taskace shi da kuma kundin ilimi da kuma masu daukan shi girmamawa ne ga littafin Allah da sunna, littafi shi ne shirin su sunna kuma ita ce
hujjar su Manzon Allah shi ne abin koyin su
suna koyar da tauhidi da akida
suna kuma karfafan shari'a kuma suna rusa bidi'a abin muni
suna kin kungiyanci abin
kaskanci ba su da wani abin bi wanda suke ta'assubanci sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
, suna neman sanin halayen shi kuma suna girmama fadin shi suna kuduri da shi suna dogaro da shi suna gaskata shi suna karban
shi suna mika wuya gare shi ba sa
jayayya da shi .
Allah mai girma Allah mai girma ba abin
bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya sun tabbata gare shi
YA KU MUSULMAI :-
Lallai kuna rayuwa a
cikin farfajiya na aminci mai yalwa da arzikin bajinta na jin dadi mai yawa ,
mutane a kewayen ku ana musu kwace ana kashe su a kama su a matsayin kamanmun
yaki da kuma bayi da kuyangu suna dandanan bala'I da
annoba kuma suna jin jiki a wurin tsada da kore su a gidajen su da karar
da su ku kiyaye amincin ku da kasar ku
da zaman lafiyan ku .
Gari nawa
ne aka samu sabanin kalma kuma
aka warware wilayan da aka kulla sai ga shi kwarjinin hukunci ya zube babu jagora
babu hadin kan jama'a to ga
mutanen cikin ta sai yakan junansu suke yi suna rarraba kawunan su suka rasa
aminci da zaman lafiya sai ga shi da
suka rasa shi ya zama rashin na su ya musu muni, dawo da shi ya gagara . Amru Dan As ya ce a cikin wasiyyan da ya yiwa dan shi sai ga
shi ya ce : ( Ya dana shugaba adili ya fi alheri akan ruwan sama mai yawan
zuba ).
Jagora mai yawan zalunci ya fi alheri akan
fitinan da za ta dauwama Abdullahi Dan
mubarak Allah ya mishi rahama ya ce :-
Lallai jama'a igiyan
Allah ne to ku yi riko da ita ita ce***
igiya mai karfi ga wanda ya yi
hisabi .
Allah yana tunkudewa da shugaba abubuwa masu
wahala *** game da addinin mu bisa rahama gare shi da yarda
Ba don jagorori ba
da ba mu samu aminci a hanyoyin mu ba *** kuma zai kasance masu raunin mu abin
kwata ne ga masu karfin mu
Idan hayaniya ta yawaita kara ta daukaka aka tada zanga-zanga to to farkon wanda zai
tsaya a bayan ta ya ruruta wutanta su ne makiya
musulunci , wanda siyasar su ta tsaya ne
akan yin ko oho da hakkin musulmai da kuma halatta dukiyoyin su da kuma lalata garuruwan su da rusa tattalin arzikin su , da fada da addinin su, kuma musulunci idan
sun yake shi sai ya yi karfi
idan suka barshi sai ya yadu , wanda
baya cutuwa don wani ya saba
mishi ko ya yi ridda daga gare shi, kuma
bai cutar da shi wanda ya tsananta
wurin gaba da shi ba zai cutar da shi ba , sanin Allah game da makiya addinin sa ba a
maida shi .
Duk wanda ya nemi shiriya a wanin
musulunci to ya bata , duk wanda kuma ya
nemi kawo gyara ba tare da musulunci ba to zai zame, wanda ya nemi daukaka a
wajen musulunci to zai kaskanta, duk
wanda ya nemi aminci da wanin musulunci
to amincin shi zai saraya ya ma rasa shi .
(
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR ) Allah
mai girma Allah mai girma Allah mai
girma Allah mai girma Allah mai girma
Allah mai girma. Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah .
YA KU MUSULMAI:
Zage –zage shi ke kunna
fitina ,
zagi baya dawo da wanda ya guje baya kuma janyo mai musu
sai ma ya shuka gaba a tsakani da tsanan juna shi kuma abokin fada sai ya kara dogewa da
musu abubuwa na ta faruwa cikin
al'uma mutane ba za su ji wata
kara ko
wani abu ba da ya faru na kusa ko na nesa face sun garzaya ga yanar
giza suna rikar wannan abin da ya
faru suna masu zagin junan su da
shi suna gaggawa zuwa ga shafin sada
zumunta na facebook tsakanin mai jifa da
mai kazafi da mai suka da mai
tsinuwa da mai zagi da mai cin zarafi sai
wanda Allah ya jikan shi wadanda ba su
da yawa 'yan kadan ne .
Ya wadanda suke zana tsinuwa da zagi suke jefa tuhumce-tuhumce da hukunce-hukunce to fa lallai za a tambaye ku game da abin da
kuke rubutawa a ranar da halittu za su taru a cikin shi a kuma auna ayuka a cikin shi har abubuwa
da suke kanana ko wani rayi za ta
zo tare da ita akwai mai shaida da mai
korawa.
Ya wanda yake fakewa a bayan gilashin na'urarsa , ya wanda yake buya da sunan aro ya yi nesa daga idanuwa ya rinka auna zagi da cin zarafi ga wanin sa !
Shin ka manta cewa Allah yana ganin ka ne ?! Kuma shi yana tsinkayan sirrinka da
ganawarka .
Mumini bai zama mai yawan suka ko
tsinuwa ko mai alfasha ko mai batsa ba .
To ka tuba daga abin da
hannayen ka suka rubuta ka share zagin
ka da cutarwarka ka tuna da fadin
mahaliccin ka kuma majibincin ta ( KA
CE DA BAYI NA SU FADA ABIN DA TAKE KEKKEWA LALLAI SHAIDAN SHAIDAN YA KASANCE YANA BARNA A TSAKANIN SU
KUMA HAKIKA SHAIDAN YA KASANCE MABAYYANIN
KIYAYYA NE GA MUTUM ).
Allah mai girma Allah mai girma ba abin
bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya sun tabbata gare shi
YA KU MUSULMAI :
Ku rayu da musulunci da aminci da kauna da hadin kai kar ku warware
cakudedeniya face da kekkewan
mu'amala da sauke hakkoki na mu'ashara da kuma tabbatar da adalci awurin mu'amala wanda ya cika
wani abu da ya kasance na mu'amala a kan shi , haka shi ma za a kiyaye mishi abin da ya
kasance na shi a kan wani to wanda ya yi
haka ya yi adalci a alkalanci ya yi
hukunci kuma na dai-dai neman
kwalkwalewa cikin hakkoki yana
haifar da bijirewa, haka tsanantawa na bata zamantakewa,
Wanda ya kuskuren
hanyar kauda kai da kawaici da yafiya to
makiyansa zasu yawaita, wadanda zasu yi zaman lafiya da shi 'yan kadan ne. Masoyan sa za su kaurace mi shi masu mu'amala da shi za su guje shi wanda ya jahilci guraben shiriyar sa wanda ya tsunduma cikin kogin jahilci to zai haura jirgin fajirci da kiraye – kiraye da cece ku ce da karya a wurin koke – koke da musu sai ya zabi jafa'i akan 'yan uwantaka da
kiyayya a kan soyayya da kaushi akan
taushi in aka yi mu'amala da shi sai ya
yi tsanani in an kusanto shi sai ya yi
fada da mutum idan ka nemi ku game da shi sai ya saba kana neman riskan shi yana neman darewa ya zo a cikin sahihul muslim Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce : ( Kada ku yankewa juna
kar ku juya baya wa juna kada ku
yi gaba kada ku yi hasada ku kasance bayin Allah 'yan uwan juna ).
Duk wanda ya shimfidawa mutane taburman
girmamawa ya fadada musu shimfidi na
kimantawa ya nema musu hujjoji da
uzurori , ko da ya musguna a gare shi ya gajarta :- To zai rayu ne a cikin
zukata abin girmamawa kuma a harshe abin
mutuntawa .
Na kasance idan na kulla alaka da mutane*** sai na abokance su kuma dabi'una shi ne wafa'i
to ka kyautatawa
lokacin da masu kyautatawansu suka kyautata***
to ku nisaci munanawa in sun musguna
ina son sabanin abin da suke so amma sai na zo
*** Da abin da suke so na bar abin da nake so
'' Hakika ance cikin kauda kanka akwai hutu ga gabbanka'' ''kuma
ance mai ladabi mai hankali shi ne mai wayo mai kawaici '' to ku yi
yafiya a tskanin ku ku dauke kai daga wanda ya musguna muku ku fita daga kunci na tattaunawa zuwa ga
hutu na yafiya , ku fita daga
tsanani na tsauri zuawa ga saukin mu'amala
ku nade tabarmar yankewa a tsakanin
ku da kewa ku sada
zumunci na 'yan uwantaka da
kauna ku karbi uzuri , domin karban uzuri na daga cikin kyawawan halaye idan kun iya
, idan ku ka samu iko akan mai musgunawa
to ku sanya yafiya a gare shi godiya ga
Allah sabo da kudura da kuka samu akan
shi .
Allah mai girma Allah mai girma ba abin
bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya sun tabbata gare shi
YA KU MUSULMAI :-
Babu dauwama a duniya ga wanda yake fata hakanan babu wanzuwa a cikinta ga mai
fata kuma mutane ba kowa ba ne sai
matafiyi dan matafiyi zamani kuma ba
wani abu ba ne face daci ne na yini da
dare mutuwa kuma ba wani abu bane face
mai saukowa makusanci ba wani numfashi
face yana nisatar da haifaffe kuma yana
kusanto da mutuwa zuwa ga zukata don su fita
abin mamaki da irin saurin ranaku wurin nadewa tana tafiya gare mu sannan ta tafiyar da mu , to, ku farkar da zukata daga bacci irin
na gafalanta ku kauda zukata daga guraben sha'awe-sha'awen
ta , ku kiyaye salloli biyar na wajibabbu da aka farlanta kada ku yi sakaci wurin farillu da
wajibabbu kar ku rena haramtattun abubuwa kar ku bayyana munanan
abubuwa, ku sani cewa kuna cikin ranaku
da ana muku daku bayan su akwai lokaci , gaggawa na ingiza su duk wanda
yau din shi bai amfanar da shi ba
to kuma abun da bai tare da shi ,
shi ya fi wahala a gare shi , wanda baya kusa da shi kuma shi ne zai gagare shi
kuma lallai babu baccin da ya fi nauyi
kaman na
gafala , babu kuma bauta irin na gafala
babu bauta da yafi mallaka irin na sha'awa babu musiba kuma da takai mutuwan zuciya babu abu mai gargadi da ya kai kololuwa sama da hurhura babu
makoma mafi muni da ya kai wuta .
Allah mai girma Allah mai girma ba abin
bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya sun tabbata gare shi
Ina fadin abin da kuke
ji ina neman gafaran Allah to ku nemi gafarar sa lallai shi ya kasance mai gafara ne ga masu
komawa gare shi.
HUDUBA TA BIYU
(
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR ALLAH MAI GIRMA ALLAH MAI GIRMA ALLAH MAI GIRMA WALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR WA LILLAHIL HAMDU )
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah madaukaki mai girma
mai tausayi goni na shaida ba
abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya ya halicci dukkan komai ya kyautata kaddara
shi ya gudanar da halittu ya kyutata
gudanarwa na shada Annabin mu kuma
shugaban mu Muhammadu bawan sa ne kuma
manzon sa ne mai albishir mai
gargadi kuma fitila ne mai haske tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
da iyalan shi da sahabban shi tsira
abun ribanyawa na madauwamiya har
zuwa ranar sakayya .
BAYAN HAKA:-
YA KU MUSULMAI:
Ku ji tsoron Allah ku yi murakabar sa kuma ku yi mishi
biyayya kar ku saba mishi ,(Yaku wadan da suka yi imani ku ji tsoron Allah ku kasance tare da masu gaskiya
)
YA KU MUSULMAI :
Laiha kusanci ne madauwami kuma
ibada ce mai girma kuma wani alama ne daga cikin manyan alamomi na addini ita laiha sunna ce mai karfi ba wajiba ba, ba kuma mustahabbi ba ne barin ta ga wanda ke
da iko baya isarwa ga laiha sai dabbobin gida mafificin su shi ne rakumi sai tumaki sannan sai tarayya a rakumi sai kuma tarayya a saniya shi kuma tarayya a rakumi da tarayya a saniya da tinkiya guda yana isar ma duk wani mutum guda da iyalan
gidan shi baya isarwa ga laiha sai jaza'in rago koma bayan shi kuma dan shekara biyu rakumi shekara biyar saniya shekara biyu
akuya shekara guda rago wata shida mafificin su
shi ne wanda ya fi kyau kuma ya fi kiba
mafi girman su kuma mafi cika mafi dadi
kuma wanda ya fi tsada , ku kiyaye laifuka da suke hana isarwa ga laiha mai aibi bayyananne ba zai isar ba na daga rashin lafiya ne ko ido daya ko gurguntaka
ko rama ko makanci na ido .
ku
lura da idanuwa, da kunnuwa , kar ku yi laiha da laiha da mai kececcen kunne ko mai tsagaggen kunne ko mukabila ko mudabara wato su ne masu
aibi a kunnuwan su ta hanyar kecewa ko
buli ko tsagu ku kyautata yanka ku wasa
abin yanka don ya kasance ya kai kuma
ya yi sauki .
Ku fiskantar da abin yankan ku zuwa ga alkibla
ku ambaci Allah ku yi kabbara ku
ci ku yi kyauta ku yi sadaka wanda ya yi
yanka kafin sallah to ya sake laihar
sa wanda ba haka ba kuma to ya yi yanka
bisa sunan Allah .
Allah ya karbi laihan
ku ya yarda da ku kuma ya yardar da ku ya tabbatar muku cikin alheri bukatun ku
kuma ya sanya ku walwala kar ya sanya ku cikin tsiya sannan kuma ya sake maimaita muku sa'ada
, muddin idi ya sake maimaitowa, itaciya kuma ta yi koriya
Allah mai girma Allah mai girma
ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai girma dukkan yabo da godiya sun tabbata gare shi
YA KU MUSULMI:-
Wannan rana ce na
yafiya da rangwami ku yi rangwami ku yi
yafiya ku yi rahama ku kasance bayin
Allah 'yan uwan juna wanda ya sammaka ya bi ta wata hanya to ya dawo ta wata hanyar
ba ita ba in hakan ta yiwu a gare shi
don koyi da sunnan shugaban
manzonni tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi .
Allah ya maimaita mana da ku wadan nan
ranaku masu albarka na shekaru masu
yawa da zamuna daban-daban
masu yawa a hali muna cikin
koshin lafiya da daddadan rayuwa .
Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai
ka kaskantar da shirka da mushrikai ka rusa
makiya addini ka sanya kasan mu cikin
aminci da natsuwa da sauran garuruwan musulmai .
Ya Allah ka datar da jagoran mu kuma
shugaban mu shi mai hidima wa harami
biyu masu alfarma da daukaka cikin abin da kake so kuma ka yarda da shi kuma ka riki makwarkwadan sa zuwa ga da'a da takawa ,
Ya Allah ka datar da mataimakin shi cikin
abinda akwai daukakan musulunci da
gyaruwan musulmai ya Ubangijin talikai .
Ya Allah ka taimaki sojojin mu masu dako a
bakin daga da iyakoki ya Ubangijin talikai ya Allah ka kiyaye jami'an tsaron mu ka saka
musu da alheri mafi cika ya Ubangijin
talikai .
Ya Allah ka warkar da mara lafiyan mu ka bada lafiya ga wanda ka jarabce shi a cikin mu
ka tausayawa matattun mu ka
taimake mu akan wanda ya yi gaba da mu .
Mafificin salati da
aminci *** Bisa ga Annabi Musdafa mai girma .
Muhammadu mafi
alherin talikai al akibu *** kuma lallai shi dinnan shi ne mai haske a goshi ma'aboci falaloli.
Da sahabbansa masu
girma masu da'a *** manya zababbu
Ya Allah ka yi dadin
tsira da aminci bisa ga Annabin mu kuma shugaban mu Muhammadu da iyalan sa da sahabban sa salatin da za ta wanzu da aminci da zai
bibiyi juna har zuwa ranar sakayya .
Allah mai girma Allah
mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah mai girma Allah mai
girma dukkan yabo da godiya sun tabbata
gare shi .
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق