الجمعة، 27 سبتمبر 2019

NEMAN MAFAKA WURIN UBANGIJI DA TUNKUDE BALA'I


Hudubar Masallacin Annabi 28-1-1441AH na shaikh Husain Al-Assheikh.
HUDUBAR FARKO
Duniya ba ta tabbatuwa a hali guda, sai an samu wasu lokuta wani yanayi na kunci da bakinciki kan gitta wa mutum, har ma da bacin rai a wasu lokuta,sabo da wasu sabuba ta fiskoki mabanbanta.
To ku saurara ! lalle komawa zuwa ga Allah bisa gaskiya ita ce hanya guda kadai da zata kubutar ta kuma bada kariya daga dukkan bakinciki da bacin rai.tare da kankan da kai  ga Majibinci Allah Tabaraka wa Ta'ala.
Allah Madaukakin sarki ya ce :"kuma lalle ne, Hakika, muna sanin cewa lalle kai,kirjinka yana yin kunci game da abin da suke fada(na izgili). Sabo da haka ka yi tasbihi game da gode wa Ubangijinka, kuma ka kasance cikin masu sujada. Kuma ka bautawa Ubangijinka har mutuwa ta zo maka."
Biyayya ga Allah abu ne na farinciki kamar yadda Takawa kuma abu ne mai sanya annashawa da walwala,to ka lazimci da'a ga Ubangijinka zai yaye ma dukkan bakinciki da ka shiga ya cire maka duk wani kunci. Allah Madaukakin sarki ya ce :"Duk wanda ya ji tsoron Allah to zai sanya mishi mafita kuma ya azurta shi daga ta inda bai tsammani" Allah Mai tsarki da daukaka ya ce :"Lalle masu biyayya na cikin ni'ima"
Kuma wannan ni'imar ta hada da jin dadin zuciya da farincikinta a nan duniya.
Idan ka shiga kunci  ka fada cikin duhun bacin rai to ka lazimci littafin Allah ta hanyar karanta shi da lura da ma'anoninSa tare da amsa kiranSa da aiki da shi, domin haske ne da waraka daga dukkan wahalhalu. Allah Madaukakin sarki ya ce : "ya ku mutane hakika waazi ya zo muku daga Ubanginku da waraka daga abin da yake cikin kiraza da shiriya da rahama ga muminai"
 Allah Madaukakin sarki ya ce : "ka ce shi (Alkur'ani) shiriya ne da waraka ga wadanda suka yi imani"
To duk wanda ya lizimtawa kansa maganar UbangijinSa, hasken sa ya haskaka masa zuciya to zai yaye mar duk wani bakinciki da bacin rai.
Ya Dan'uwa na musulmi:
Idan bakinciki da bacin rai ya dame ka to ka marairaice gaba ga Ubangijinka, ka nuna bukatuwarka zuwa gare shi,ka kankan da kai zuwa ga Mahaliccinka ka rusuna da adu'a, Allah  Madaukakin sarki ya ce : "kuma da Ayyuba a sa'ad da ya yi kiran UbangijinSa, (yace,) lalle ni, cuta ta shafe ni, alhali kuwa kai ne mafi rahamar masu rahama.Sai muka amsa masa, sa'anan muka yaye mishi abin da ke gare shi na cuta, kuma muka kawo masa mutanensa da kwatankwacinsu tare da su, sabo da rahama daga wurinMu da tunatarwa ga masu ibada."
     ka kankan da kai zuwa ga Mai iko ga kowani abu kankan da kai na gaskiya ka roke shi da harshe da gabbai cikin khushu'i ciki da waje, tare da cikakken marairaicewa irin na bawa ga Mahaliccinsa, da bawa ga Majibincinsa, tare da sakankancewa ba tsira da mafaka sai a gare shi Allah  Madaukakin sarki ya ce : "kuma mai kifi a sa'ad da ya tafi yana mai fushi, sai yayi zaton cewa ba za mu kuntata masa ba, sai ya yi kira a cikin duffai cewa ,: Babu abin bautawa face kai. Tsarki ya tabbata a gare ka.Lalle ne ni, na kasance daga azzalumai.sai muka amsa masa, kuma muka tsiratar da shi daga bakin ciki, kamar haka ne muke tsiratar da masu imani."
 Ya tabbata a sunna kwadaitarwa bisa ga wannan Adu'a, kuma ba wani musulmi da zai roki Allah da shi face Allah ya amsa masa, kuma yana cikin adu'o'in yaye bakin ciki da kwaranye bala'i sabo da abin da ya kumsa na ma'ana mai girma na kadaita Allah da girmama shi ta tsarkake shi da bayyana gajartawa da gazawa,na dan-Adam  da zaluntar kai wajen cika alkawari na hakkokin Mahalicci tsarki ya tabbata a gare shi, ba wata ni'ima ga zuciya ko jin dadi ga rai face da cikar tauhidi da tsaida hakki na imani.
Sabo da haka ne ya zo a cikin Bukhari da Muslim Daga Abdullahi dan Abbas  Manzon Allah (tsira da amincin Alllah su tabbata a garshi) ya kasance yana yin wannan addu'ar a lokacinda yaji kansa a yanayin damuwa:
La ilaaha ill-Allaah al-‘Azeem ul-Haleem, Laa
ilaaha ill-Allaah Rabb il-‘arshil-‘azeem, Laa ilaaha
ill-Allaah Rabbis- samawaati wa Rabb il-ard wa
Rabbil-‘arsh il-kareem
Ma'ana :(Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Mai girma Mahakurci, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Ubangijin Al'arshi Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Ubangijin sammai da kassai Ubangijin Al'arshi mai girma".

Na daga cikin Aduo'in yaye bakinciki da bacin rai wanda ya kumshi rusuna wa Allah  Mabuwayi da daukaka da tawassuli da sunayenSa kyawawa da sifofinSa Madaukaka  akwai : "Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Mahakurci Mai girma.Tsarki ya tabbata ga Allah,Albarka ta tabbata ga Ubangijin Al'arshi Mai girma. Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai."
Ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :"Ba wata musiba da zata samu wani mutum sai ya ce :

"Ya Ubangiji ni Bawanka ne dan bawanka dan baiwarka, makwankwadar kaina tana hannunka, kuma duk abinda ka Hukunta akaina, kuma Adalci ne Hukuncinka a gareni, ina rokonka da dukkan suna da yake naka wanda ka kira kanka da shi, ko ka saukar da shi a cikin littafinka, ko ka sanar da wani daga cikin bayinka, ko ka fifita saninsa akankin kanka, kasanya Alkur'ani Kakar zuciya ta, da hasken zuciya ta, da kuma yayewar bakin ciki na, da tafiyar damuwa." Face Allah ya tafiyar masa da damuwarsa da bacin ransa ya sauya masa su da farinciki kamar yadda ya zo a nassin Hadisin sabo da haka Annabi yayi umarni da a koye shi (An ce ya Manzon Allah ba za mu koye shi ba sai ya ce : "Ya dace duk wanda ya ji ya koya"
  Na daga cikin adu'o'i  na neman tunkude bakinciki da bacin rai :
 "Ya Ubangiji lallai ni ina neman tsari da kai daga Bacin rai da kuma damuwa, da gajiyawa da Kasala, da rowa da tsoro, da dabaibayewar bashi da galabar Mutane''
Daga ciki akwai (Allah Ubangiji na ba zan hada ka da wani ba   .) daga ciki akwai ya hayyu ya kayyum ; ya rayayye tsayayye  ina neman agaji da rahamar ka.
Ya kai musulmi:

Na daga cikin sabuba mafi girma na farin ciki da jin dadi da walwala  da annashuwa ;  shi ne ka tsaya gaba ga Ubangijin ka  da sallan farilla ko nafila  a lokutan da ba na hani ba kana mai kushu'i  tare da marairaicewa da nuna bukatuwa  ga Ubangiji mabuwayi  kasaitacce  Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Ku nemi taimako da hakuri da salla )

Buhari ya rawaito daga Ummu salama Allah ya kara yarda a gare ta  ta ce wata rana  Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya farka cikin dare   sai ya ce '' tsarki ya tabbata ga Allah , me aka saukar na fitintinu a wannan dare me aka bude na taskoki ? ku tada ma'abota dakuna  sau da yawa  wata za ta zama tana cikin tufafi a duniya amma a cikin tsiraici a lahira .)
 A wata ruwayan kuma (har su samu su yi salla)
Ibn Hajar ya ce;  a wannan hadisi  akwai mustahabbancin gaggautawa zuwa ga salla yayin da aka tsoraci wani sharri , a wurin Muslim kuma fadin sa   tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Idan dayan ku ya ga abin da ya tsana (a cikin bacci) to ya tashi ya yi sallah)  A kan haka aikin magabata ya kasance kamar yadda Ibnu Abbas da waninSa suka rawaito.

Huduba ta biyu

Ya ku Bayin Allah!

Kyautatawa da nau'ukanSa na da tasiri na ban mamaki wurin tunkude naui daban –daban na bala'i musamman sadaka. Allah madaukakin sarki ya ce:- (Allah na saka wa masu sadaka). Allah madaukakin sarki ya ce:- (Ku kyautata Allah na son masu kyautatawa).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Aikata ayyukan alheri na kare fadawa bala'i, sadakar boye na dushe fushin Ubangiji, sada zumunta na karan tsawon kwana.) Dabarani ya fito da shi a littafinsa Alkabir, Imamul Baihaki da Munziri suka ce isnadinsa hasan ne yana da hanyoyi masu yawa da zasu karfafe shi.
Ya 'yan Uwa a Musulunci:
Samun farinciki da walwala na cikin daa ga Allah da da'a ga ManzonSa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da aiki na kwarai da gaggawa zuwa ga ayyukan alheri, da lizimtar wajibabbu, da sauran ayyukan da'a,
  Allah madaukakin sarki ya ce:- (wanda ya yi aiki na kwarai namiji ne ko mace a halin yana mumini to zamu raya shi daddadan rayuwa kuma mu saka masa da lada fiye da abin da suka kasance suna aikatawa.)


الأربعاء، 25 سبتمبر 2019

Girman Allah da girmamawanSa ga bawanSa


Hudubar Masallacin Annabi 14-1-1441AH na shaikh Aliyu Bin Abdurrahman Alhuzaifi.
HUDUBAR FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mabuwayi mai yawan gafara, yana juya dare akan wuni kuma yana juya yini a kan dare, lalle akwai abin lura a hakan ga masu basira,ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi bisa ni'imominSa da ba mai iya kididdige su sai shi, daga wadanda muka sani da wadanda ba mu san su ba,sunayen Ubangijinmu sun tsarkaka, siffofinsa sun kasaita, ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Tilo Mai rinjaye,na shaida Annabinmu shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne mai Albishir da rahamar Allah da AljannarSa, mai gargadi da ukubar duniya da azabar wuta, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka ga bawanka kuma Manzonka Muhammad da iyalansa da sahabbansa ma'abota biyayya. Bayan haka ku ji tsoron Allah Madaukaki ta hanyar neman yardarSa da tsoracewa fushinSa da ukubarSa,Allah Tsarki ya tabbata a gare shi yace " Kuma Ubangijinka yake halitta abin da ya so ya kuma zaba, zabi bai kasance na su ba, tsarki ya tabbata ga Allah Madaukaki daga  abin da suke yi na shirka"
Lalle Ubangiji Mabuwayi da daukaka ya halicci halittu da kudurarsa da iliminSa da hikimarSa da rahamarSa ya samar da wannan duniya da ake gani, ya sanya mata wani ajali da zata kare zuwa gare shi ba zata wuce shi ba,ya halicci wannan duniya da muke ciki tare da sababi, ya halicci abin da ke zamewa da sababi kuma shine ke halitta sababi da abin da ke kawo sababin: To duk abin da Allah ya so zai kasance duk abin da bai so ba kuma ba zai kasance ba.Allah Madaukakin sarki ya ce: Allah ne Mahaliccin dukkan komai kuma shine wakili akan kome. Shi ke da mabudan sammai da kasa kuma wadanda suka kafirta da ayoyin Allah, wadannan su ne masu hasara.     Kuma ya ce: "To shine da halittar kuma da umarnin Albarkar Allah Ubangijin halittu ta bayyana! ".
Mutum halitta ne daga cikin halittun Allah na ban mamaki, Allah ya hada mishi sifofi na ban al'ajabi, wdanda ke rarrabe ga wasu halittu da ba shi ba. Allah ya ce : "Lalle ne Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa".Allah Madaukakin sarki ya ce: kuma a cikin rayukan ku (akwai ayoyi) kuma ba za ku duba ba?"
Ya kuma ce : "kuma akwai daga ayoyinSa ya halitta ku daga turbaya sai ga ku kun zama mutum kuna watsuwa" kuma Allah ya yi baiwa ga bani adam bisa karrama su sai yace "kuma Lalle ne Mun girmama 'yan Adam kuma muka dauke su a cikin kasa da teku kuma muka azurta su daga abubuwa masu dadi, kuma muka fifita su a kan mafiya yawa daga cikin wadanda muka halitta, fifitawa."
Kuma girmamawa da Allah ya yi wa bani Adam girmama wa ne na gaba daya ga mai biyayya da mai fajirci a nan duniya da ni'imomi, amma kebantacciyar girmama wa a lahira da yardarSa da Aljanna ta ni'ima ga muminai ne kawai, kafuri bai da rabo a lahira, kuma Ubangijinka ba ya zaluntar kowa, amma a lahira Ubangiji bai girmamawa sai ga wanda ya mishi biyayya cikin Mutane da Aljanu.
Ibnu Asakir ya rawaito daga Hadisin Anas dan Malik Allah ya kara yarda a gare shi"Daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Lalle mala'iku sun ce : ya Ubangijinmu ka halicce mu ka halicci bani Adam sai ka sanya su suna cin abinci kuma suna shan abin sha,suna sanya tufafi kuma suna auren mata, kuma suna hawan dabbobi,suna barci suna hutawa, amma mu baka sanya mana wani abu na daga wannan ba, to ka sanya musu a duniya mu kuma ka sanya mana a lahira sai Allah Mabuwayi da daukaka ya ce: Ba zan sanya wanda na halita da hanu na na kuma busa mishi rayi na ba tamkar wadda na ce da shi kasance ! sai ya kasance"
akwai wani hadisin da zai karfafe shi daga hadisin Abdullahi dan Amr wanda Dabrani ya rawaito.
Na daga cikin ni'imomi masu girma da aka yi wa bani Adam akwai hore masa abubuwa masu amfani da maslahohi da ni'imomi, Allah Madaukakin sarki ya ce: "Ase baku ga yadda Allah ya hore muku abin da ke cikin sammai da kasa ba ya kuma yalwata muku ni'imominSa na zahiri da badini " Allah Madaukakin sarki ya ce: ya hore muku abin da ke cikin sammai da kasa baki daya, daga gare shi, lalle cikin haka akwai ayoyi ga mutanen da suke masu tunani."
  Hikima na yalwata ni'imomi ga bani Adam ita ce :don su mika wuya ta hanyar da'a ga Allah Madaukaki su kuma gode masa, kada kuma su hada shi da wani a cikin bauta, Allah Madaukakin sarki ya ce:"kamar wancan ne Allah ya ke cika ni'imarSa a gare ku ko zaku mika wuya.
Ibnu kasir Allah ya mishi rahama ya ce a tafsirinsa:"Ai haka zai sanya muku abin da zaku taimaki kanku cikin al'amuranku da abin da za ku bukace shi don ya zme muku abin da za agaza muku wurin bin Allah da bauta masa"
Allah bai yi nuni ga ambaton dan Adam ba tun da ya halicci Adam da hanunSa da abin da ya ke tsakanin marhala zuwa wata marhala na mutum  face don ya bayyana mishi nauyin da ke kan shi a wannan rayuwa ta duniya kuma ya sanar da shi aikin da ke kan shi, da hikimar da ya sa aka halitta shi, kuma an kallafa mishi umarni da hani kuma yana mai dauke da wannan sharia da kuma daukakaka na bautawa Ubangijinsa Allah Madaukakin sarki ya ce:   " yanzu mutum na zaton zaa bar shi haka kawai ne " Imamusshafi'I Allah ya mishi rahama yace : wato ba za a umarce shi ba ko a hana shi,
Allah Madaukakin sarki ya ce: " To kuna zaton cewa mun halicce ku don wasa ne kuma ba za ku dawo zuwa gare mu ba?
Na daga cikin abin da Allah ya tsara wannan duniya  da abin da ya halitta na sabuba da ke tasiri a samuwar wadannan abubuwa, lalle Allah ya bayyana mana daga cikin sunnoninSa a rayuwa cewa ayyukan dan Adam na inganta rayuwa ta yi dadi idan ayyukan sun yi kyau a nan duniya, haka kuma rayuwa kan baci idan ayyuka suka lalace, kuma ayyukan dan Adam na shiga har cikin dabbobi da tsirrai ya yi tasiri wurin gyaruwansu ko bacin su, bisa rahamar Allah da adalcinsa, don ya lazimtawa mutum da'a kuma ya kauracrwa abubuwan da aka haramta.   Allah Madaukakin sarki ya ce game da albarkar rayuwa da alherinta na ga kyautatuwan ayyukan mutum :- (Da mutanen  alkarya za su yi imani su yi takawa da mun bude mu su  albarkatu daga sama da kasa  sai dai sun karyata sai muka rike su da abin da suka kasance suna aikatawa )

Kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :-  (Da ma'abota littafi za su yi imani  su yi takawa da mun kankare musu laifukan su  kuma da mun shigar da su aljanna na ni'ima .  Kuma da a ce sun tsaida attaura da linjila  da abin da aka saukar musu daga Ubangijin su  da sun ci daga saman su da kuma karkashin kafan su )
Kuma Alkur'ani shi ne abin da Allah ya saukar ga musulmai da ahlul kitabi  ba wanda  ya sanja shi sabo da kiyaye shi , kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Wadanda suka yi imani basu chakuda imanin su da zalunci ba wadannan suna da aminci kuma su ne shiryayyu)
Wato basu churkuda imanin su da shirka ba , kamar  inda annabin shi ya  fassara shi kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Ya ku wadan da suka yi imani in za ku taimaki Allah Allah zai gtaimake ku). Wato in za ku taimaki addinin Allah to zai taimake ku.
 Kuma Allah mabuwayi da daukaka ya ce :- ( Wadan da in mun basu matsayi a doron kasa sai su tsaida salla kuma su bada zakka su yi umarni da kyakkyawa su yi hani da mummuna  , kuma lallai akibar al'amura na wurin Allah ).
Ibn Kasir Allah  ya mishi rahama  ya ce a tafsiri  : ''Umar Dan Abdul-aziz ya yi huduba sai ya karaanta wannan aya sai ya ce : 'ku saurara wannan aya bata tsaya akan jagora kadai ba sai dai ta kunci shugaba da talakawa  a sai  ba zan baku labari ba  da abin da yake hakkin ku ne akan shugaba da kuma abin da ya ke hakkin shi ne akan ku:- na daga  ciki , shi ne ya rike ku da hakkokin Allah da ke kan ku  kuma ya karbi hakkokin wasun ku da ke kan wasu  kuma ya shirye ku zuwa ga abinda yake dacewa iya'iyawan shi  , to, ku kuma ya wajaba a gare Ku ,  ku mishi da'a'' . Afadin Allah (kuma lallai akibar al'amura na wurin Allah ).
Akwai aminci ga wanda ya tashi da wadannan al'amura guda hudu :  Na daga wani da kuma kaidi na makiya  kamar yanda Allah Madaukakin sarki ya ce:- (muddin kuka yi hakuri kuka yi takawa to kaidin su ba zai cutar da ku ba da wani abu  lallai Allah ya iyakance abin da suke aikatawa).
Kuma kamar yanda gyaruwan aikin mutum  yakan game da alheri  to haka namma yake shafi shi mai aikin shi kan shi ,  kamar yanda Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Duk wanda ya yi aiki na kwarai  na miji ko mace a halin yana mumini to za mu raya shi rayuwa daddada  kuma za mu sakanya mu su  da ladan su da mafi kyaun abin da suka kasance suna aikatawa).
Ta daya bangaren kuma  da ke kishiyantan wannan  shi kan shi barna na aikin mutum yana cutar da shi kan shi mutum din   kuma ya shigar da shi  barnan a cikin rayuwa ,  Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Da a ce gaskiya zai bi soye-soyen rayukan su da sammai da ksa sun   lalace da abin da ke cikin su )  

 Kuma Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Barna ta bayyana a doron kasa da taiku  sakamakon abinda hannayen mutane ya aikata  don ya dandana musu wani sashi na abinda suka aikata  ko za su dawo ). Kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Duk wani abin da ya same ku na musiba to sakamakon abin da hannayen ku suka aikata ne  kuma yana yafiya ga mafi yawa)

To ka yi lura ya kai mutum halin wadannan da suka munana aiki  abin da ya sauka a gare su  Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Sau dayawa muka halaka daga alkaryu wanda sun kasance azzalumai   bayan su muka tada wasu mutane daban)
An karbo daga Abdullahi Dan Umar  Allah ya kara yarda a gare su ya ce :-(  Abubuwa biyar na tare da wasu abub uwa biyar : Alfahasha ba zata bayyana ba a cikin mutane har kuma su bayyana ta karara  face annoba ta bayyana a cikin su da cututtuka irin wanda ba a samu ba daga wadanda suka gabace su.kuma muddin jagororinsu ba su yi hukunci da littafin Allah ba face Allah ya sanya yakinsu a tsakaninsu, kuma ba wasu mutane da zasu hana zakkan dukiyar su face an damke su da fari a kuma hana su ruwan sama ba don dabbobi da ba a saukar musu da ruwa ba, kuma zasu tawaye kilo ba face an rike su fari da zalunci shugaba, baza su warware alkawarin Allah da Manzo ba face Allah ya dora musu makiya akan su, su rika kwace wani sashi na abin da ke hanun su) Ibnu Maja ya rawaito

  Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Kuma dan adam bai da wani abu sai abin da ya aikata . Kuma aikin sa da sannu za a gani ). Allah ya sa min albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma

 HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah mabuwayi mai yawan gafara mai hakuri mai yawan godiya , ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi  ina tuba zuwa gare shi kuma ina neman gafarar sa ,  to lallai godiya ta tabbata ga Ubangijina a duniya da lahira  bisa falalar sa  da baiwar sa cikin abin da muka sani da wadda ba mu sani  na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya masani da abinda ke cikin zukata  ,  na shaida Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad    bawan sa ne kuma Manzon sa ne  wanda aka turo shi  da shiriya da haske Allah ka yi dadin tsira  da aminci da Albarka  bisa ga bawan ka kuma Manzon ka Muhammad  da iyalan sa da sahabban sa  wanda suka yi fintinkau zuwa ga dukkan aiki na da'a .

Bayan haka  ku ji tsoron Allah Madaukaki don ku riki tafarki  zuwa ga Allah wanda zai shigar da ku cikin aljannar sa  ku rabauta da yardan sa   ya kai dan adam yi dubi zuwa ga ni'imomin  Allah a gare ka  da ya ni'imtar kai wanda ba wanda ke da kudura na iyakance su sai Allah kuma ka tashi da godiya gare shi game da su  da zai kwace mafi karancin ni'ima to ba wanda ya isa ya dawo ma da ita sai shi  .
A cikin ni'imar Allah ba wani abu kankani   a halin kuma ga ka ya kai mutum ta hanyar daidaiton ka da gyaruwan ka  da yadawan ka ga alheri  da kuma kamewan ka daga sharri   za ka kasance ka taimaka wurin kiyaye muhallin ka na zama(matattara)  da kuma tseratar da kanka daga sharrace-sharrace , da ukubobi , ka sani lallai kai abin tambaya ne game da ayukan ka a rayuwar ka  da kuma bayan mutuwar ka   to ka yi dubi me za ka gayawa Ubangijin ka Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Ya kai  mutum lallai ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijin ka , wahala mai tsanani to, kai mai haduwa da shi ne.  To amma wanda aka baiwa littafin sa da damarsa .  To za a yi masa hisabi mai sauki . Kuma ya juya zuwa ga iyalan sa (a cikin aljanna) yana mai raha. Kuma amma wanda aka baiwa littafin sa daga wajen bayan sa .  To za shi dinga kiran halaka kuma ya shiga (wutar) sa'ira .

    
Ya zo a hadisi:- (Kafan bawa baza su gushe ba har sai an tambaye shi game da abubuwa guda hudu;  game da rayuwan sa   cikin abin da ya karar da su da samrtan sa   a cikin me ya tafiyar da , da dukiyar sa  daga ina ya same su kuma a me ya ciyar da su,    da kuma aikin sa  mai ya aiwatar da shi ).
Ka sani ya kai mutum lallai gidan ka da ke wanzuwa na dindindi ita ce take gaban ka bayan mutuwa, to dadi ya tabbata a gare ka in ka rayata da ayuka na kwarai  , kuma azaba ya tabbata a gare ka in ka yarda da wannan duniya taka ka manta lahirar ka ,  duniyar ka za ta juya ma baya ne in ka kaunace ta ko  ka ki ta , lahira kuma za ta fiskanto ka  bisa ga abin da ka kaddamar  kuma ita  ta har abada ce .

Ya ku bayin Allah ! lalle Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce.

 














   

الثلاثاء، 3 سبتمبر 2019

wasiyya ga dalibai


Hudubar Masallacin Annabi na sheikh Salah Dan Muhammad AlBudair.29 zulhajji 1440AH

Hudubar Farko

Ya ku musulmai
Kokari zuwa ga halaye na mutunci da kyawawan dabi'u dabi'a ce na masu juriya kuma al'ada ce na masu kokari, ilimi shi ne daukaka mai daga darajan mai nemansa kuma aga kiman ma'abocinsa a ido , duk wanda ya so ilimi to falalolin shi kuwa zai kewaye shi abubuwan adonsa su sauka a farfajiyansa. Almuzani ya ce : "na ji shafi'I Allah ya yarda da shi yana cewa duk wanda ya nemi ilimin alkura'ani to kimarsa za ta kara girma duk kuma wanda ya yi nazarin ilimin fikihu matsayinsa zai yi kyau, duk wanda ya rubuta hadisi zai zama yanada karfin hujja duk wanda ya yi nazari a ilimin lugga dabi'arsa za ta tausasa, duk wanda yayi nazari a ilimin hisabi ra'ayin shi zai yawaita duk wanda bai kare kansa ba to iliminsa ba zai mishi amfani ba" .
Al'umma na samun karfi ne ta hanyan ilimi ###  hukunci a cikin zamani ana danganta shi ne zuwa ga alkalami ###sau da yawa tokuba na zubar da jini #### alkaluma kuma na zubo da hikimomi ###da mutane za su yi a'adalci ### da falala a tsakaninsu zata kasance ne  ### ta hanyar digon tawada ba ta hanyar zubar da jini ba ### ka dukufa wurin neman ilimi #### za ka kai kololuwa a matsayi ### a falala  wanda yana kumshe da daukaka da karamci.
ilimi a lokacin fitina ya na baka kariya, a lokacinci  kadaici yana dauke ma kewa yana sanya daukaka a cikin iyalai 
ya ku musulmai:
ga sabuwar shekarar karatu ta kunno kai nan ba da jimawa ba za a bude makarantu da jami'o'i za a karbi dalibai da kauna da maraba to saboda haka ga wasu wasiyyoyi ga dalibai maza da dalibai mata game da wannan munasabar:
Ya kai dalibi to ka koma makaranta tare da kwadayin karatu da farinciki da annashuwa da himma da kokari ka cire mutuwan jiki da jin tawaya da sakaci da kasala .
samun daukaka na ga kokari ### rasawa kuma na ga kasala  ### to ka kafu za ka samu cimma burinka nan kusa  ### lallai matashi wanda ya siffantu da himma irin na mutanen farko ### kuma bai saba rage zance ko aiki ba duk wanda ya sarayarda himma to ba zai cimma bukatunsa ba ### duk wanda ya yi jifa da kifiyoyi na ji ji da kai to ba zai samu ba .
Hakika mai himma ma'aboci hankali za iya cimma gaci ta hanyar da'a ga himmarsa da kuma sabawa son rai.
ya ku dalibai : ku yi sammako ku gaggauto zuwa ga ajin karatu, na horeku da ku nesaci  jinkiri da ja da baya  domin a cikin sammako akwai albarka da samun arziki da najahi da kuma dace,  Tirmizi ya rawaito daga sakr dan gamidi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (ya Allah ka sa albarka ga alummata a cikin sammakonta , sai ya ce ya kuma kasance  idan ya tura mayaka ko kuma runduna yana turasu ne a farkon wuni sakru ya kasance mutun ne dan kasuwa ya kasance kuma idan ya tura kasuwanci yana tura su ne da jijjifi sai ya zama hanshakin mai kudi dukiyarsa ta yawaita)   
Samun albarkan rana baya tabbatuwa sai da riskan sallan asubahi domin lallai sallan asubahi tamkar wata iska ce mai kamshi da wani yanayi mai dadi ku sammaka kuma ku yi katanga da adu'oyi  na neman kariya da azkar da suka zo daga annabi wadanda suke jefa debe kewa a cikin rayi da farin ciki a cikin zuciya su kara karfi da nashadi a jiki da kariya da kiyayewa ,duk wanda ya bawa ransa rabonta na more rayuwa da mutuwan jikin da sabo da jinkiri da bacci daga barin aikin shi da makarantan shi da hissarsa na karatu to hakika zai rasa  manufarsa danashinar sa zata yi girma, duk wanda ya yawaita kwanciya to zai rasa biyan bukata wanda ya lizimci kasala to zai yi asaran fatarsa shi mutun sakali mai kasala yana rayuwa ne matsiyaci zai zama yayi nesa amma duk wanda ya yi hakuri  to zai rabauta, da hakuri ne ake bude kofofin da suke rufe kuma ayi dace.
Baccin safiya wato yin bacci baya sallar asuba ya halatta sai dai idan zai kai ga sarayar da wajibi, kuma baccin kailula wato baccin azahar mustshabbi ne saboda hadisin Anas Allah ya kara yarda  a gare shi ya ce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce (ku yi baccin kailula saboda shaidanu basa yin baccin kailula ) abu nua'im ne ya fitar dashi 
 saboda kailula yana maida nashadi ga kwakwalwa da kuma jiki yana taimaka wa wurin bita da sauke nauyin da ya wajaba akan mutun da kuzari da kuma karfi da nashadi.
ku kiyaye kashe dare da hira domin yana haifar da wahala da kuma sa nauyin jiki kuma bala'i ne da ke bata yanayi, mutun ya kasa sakewa ya kashe mishi kuzari ya jefa mishi gajiya na zuciya da jiki kada  ka fi karfin idanunka ka hana shi barci idan barci ya zo, ka yi barci a farkon dare ka hutar da idanuwanka biyu, kada ka cutar da iyayenka,  a ko wani safiya sau da yawa mun ga wanda ya sarayar da aikin shi ko ya bar karatun shi ko kuma yayi sakaci da iyayen shi da iyalan shi sakamakon bata dare kan abin da ya ke na haram abun zargi tare da wasu abokan banza masu batarwa masu lalatarwa. ya kai dalibi ka yi kwadayin samun ladabi da tsabta da tsarkin zuciya da girmama malami da  lazimtan tsari da kiyaye abin da aka dora ma na karatu, da kiyaye wurin karatu da kuma abin da aka dora ma na karatu na makaranta, ka ji tsoron Allah domin Allah ba abin da ke boyuwa  a gare shi na zuciya ba wani kwayan zarra ko kwayan hancin dibino da zai shiga wa Allah duhu, ka sanya ilim shi ne babban tattalinka ladabi ya zama shi ne tufafinka ka kasance mafi cikan mutane ladabi, mafi tsananinsu wurin kankan da kai, kuma ka zama ka fi su tsarkaka da kuma addini ka zama ka fi su karancin shirme da kuma yawan fushi, ka abokanci mutanen kwarai ka yi nesa daga mutanen sharri, kar ka kusance su kar ka aminta da su kar ka yi cakudedeniya da su ko ka zauna da su, kada ka zauna zuwa ga mutanen banza domin halayen wawaye yana raba  mafi sharrin mutane shi ne wanda bai damu mutane su gan shi ba yana mummunan abu, duk wanda ya so yayi ababan mutunci to zai nesaci abubuwa na haramun kar ka saki ganinka kada ka kafa ganinka zuwa ga waninka domin idanuwa tarkon shaidan ne duk wanda ya saki ganin shi zai hadu da ajalin shi, na horeka kar ka kai kanka wuraren abin tuhuma da  abin da zai haifar da shakku na horeka da kar ka yi abin daza ka zo kana bada uzuri ka dauki izina daga waninka duk mutumin da luran shi ya yi yawa to kusakuren shi za su karanta, lallai rabautacce mai samun sa'ada yana da abin wa'azi ga wanin shi kuma yana mai daukan gogewa a matsayin abin da zai yi mishi hukunci  abin da zai rika lura da shi, na gargade ka da dukkan wani wasa wanda zai haifar da kiyayya ko ya zubar da kwarjini,  ba daukaka shi ne a kyakkyawan tufafi ba sai dai daukaka na nan ga ilimi ne da ladabi da addini, harshe waziri ne na mutun idan baka iya fadan magana wanda ya ke na daidai ba to ka yi shuru daga abin da yake ba daidai ba shi kanshi shi ne daidai, kada ka kasance cikin wanda ya ke aibata wa sannan ya na yawaita zagi yana yawaita suka ga abokai kada ka bankado laifukan mutane muddin sun boye sai Allah ya tona asirinka na daga laifuka, ka ambaci kyawawan abin da ka gani a cikinsu a duk lokacin da aka ambace su  kar ka aibata wani cikinsu a abin da kai ma kana da shi kar ka yi abokantaka da mai kasala, Abubakar alkawarizmi ya na cewa :" kar ka abokanci mai kasala a duk halayensa## sau da yawa mutun na kwarai kan lalace sakamakon bacin wani## raban wawa zuwa ga mai wayo abu ne da yake cikin sauri## baka ganin gaushi da ake dora shi a cikin toka shi ke nan sai gaushin ya mutu ?
A tarbiyantar da al'uma su taso kan kyawawan laduba wajibi ne da ya rataya ne a kan iyaye da majibinta al'amura,  wani daga cikin masu hikima ya ce : "ku yi gaggawa ta hanyan ladabtar da yaranku kafin shungulla su rarraba tsakaninku"
Ya ku dalibai : ku yi gaugawa zuwa ga ilimi wanda  dage mishi  ya dace agare ku, ku kiyayi hayaniya da kuma gajiya da kosawa da kasawa da yankewa .
Ka nema kada ka yi hayaniya wurin neman, laifin dalibi shi ne ya yi hayaniya ku nemi ilimi duk wanda ya nemi ilimi zai mikar da shi tun yana karami kuma zai gabatar da shi idan ya girma.
 Urwa dan zubair ya ce :" 'ya'ya na 'ya'ya na ku nemi ilimi in kun kasance kanana ba a bukatanku, to ya wuci ku zame manya  ba za a wadatu da ku ba."
ku yi kwadayi bisa makarantu domin  makarantu su ne wurin dashe, duk wanda darasi ya kwace mishi to dashe ya baci mishi, ku dimanci kallo a cikin littafi kada ku gaji daga leke leke a littafi da bincike da karatu da kuma daukan rubutu da bita da kuma mudarasa a tsakani da hadda.
Ibnul jauzi Allah ya mishi rahama ya ce : da zan ce lallai ni din nan na tsinkayi littafi littafi da ya kai mujalladi dubu ashirin kai dama sai na ce ma ya kasance ya fi haka a lokacin da na ke nema,
Ya ku dalibai  kokari kokari a tsakanin alkaluma da kuma litttatafai da tawada da abun rubutu har ku riski burinku, wasunsu suka ce na yi kura shekara arba'in ban yi kailula ba ban kwanta ba face littafi na dore akan kirji na an tambayi Imamu Ahmad bin Hanbal Allah ya mishi rahama zuwa yaushe ne mutun zai nemi ilimi sai ya ce "tare da kurtun tawada har zuwa akai shi makabarta" ya kai dalibi kasa natsuwa da bi a hankali da kaifin hankali na horeka da kar kayi gaggawa a wurin tafiya da hauka da nuna danyen kai da yaranta, wanda ke koro sharri ya jefa mutun cikin nadama hakika wanda ya bi a tsanaki zai iya riskan hajarsa wanda ya yi gaggawa kuma zai iya fadawa cikin kuskure, duk wanda ya yi amfani da wayar salula a yayin da yake tuki to hakika ya kai kansa ga hatsarin mutuwa ya kai kansa zuwa ga bakin halaka da abin da ya ke makruhi saboda waya yana dauke hankali da ji ya sa mutun ya rasa kulawa da halartowa da hankali duk mutuninda idonsa ya kafu akan waya ya saki kunnuwarsa ya sunkuyar da kansa da kafadunsa ya shagalta da tattaunawa da ture ture da yada tagrida da ababan kallo  a halin yana tafiya to hakika ya zo da wani babban laifi da wani abin da aka ki, to ka sanya tunanika ka tattaro da hankalinka zuwa ga inda ka nufa da abin da ka fiskanta da tukinka idan wani abu ya zo ma na tunani ko na sada wani zumunci ta wayarka to ka fita daga kan hanya ka tsaida abin hawanka to ka kare bukatarka da wayarka ka kame kanka daga cutar da musulmai da kuma shi kanshi sharrinka kafin wani abin ki ya faru har ya sanyaka ka yi bakinciki da nadama da hasara da kaji radadi ka ce wayane ya mantar da ni ya makantar da ni ya shagaltar da ni a wannan lokacin kuma nadama ba zata yi amfani ba bayan kafarka ta riga ta zame.
Kuyi salati da aminci bisa ga Ahmadu mai shiryarwa mai   
mai ceto ga halittu gaba daya .                       

 

Huduba ta biyu

Ya ku dalibai : girmama malami fa wajibi ne mutunta shi da kimanta shi da kankan da kai  a gare shi farilla ne na tilas, sanin falalan ilimi da gode wa mai kyau aiki ne daga cikin abubuwa na kyawawan dabi'u masu daraja dalibi na siffantuwa da ladabi a ajinsa hakama tare da abokan karatunsa domin wannan shi ne girmama ilimi da kuma ma'abotansa Umar dan kaddabi Allah ya kara  yarda agareshui ya ce : (ku nemi ilimi kuma ku ilmantar da mutane shi ku nemi ilimin mutuntawa da kuma nitsuwa ku yi tawaliu ga wanda kuka koya daga gareshi da kuma wanda kuke koyarda shi kar ku kasance masu jiji da kai na daga malammai shi malami yana cikin manyanmu ne abun girmamawa cikin manya kuma girmama manya yana cikin abnda aka samo daga hadisi)
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda  a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce (Duk mutuminda bai tausaya wa karaminmu ba kuma bai san kiman ko hakkin babbanmu ba to baya tare da mu)
Tashi don malami ka girmamashi ###
                                      malami ya kusa ya zama manzo .
yanzu ka san wanda yafi daukaka ###
fiye da wanda yake gina kuma ya tada rayuka da hankula ?!.
tsarki ya tabbata a gare ka mafi aherin masu ilmantarwa ### ka ilmantar da alkalami karnonin da suka shude na farko
.ka fidda wannan hankalin daga duhunsa ### ka shiryar da shi zuwa ga hanya na haske bayyananne .
katuro Annabi Musa da attaura yana mai shiryarwa ### dan batulu kuma ya ilmantar da injila .
sai ka bubbugo da mabubbuga na bayani ## sai ya shayar da hadisi kuma ya bada alkura'ani (tanzila).


الأحد، 18 أغسطس 2019

TSAYUWA A KAN TAFARKI


Hudubar Masallacin Annabi na sheikh Husain Al- Ashaikh 15-12-1440AH

Hudubar Farko
Ya ku musulmai!
Na daga cikin ni'imar Allah a gare mu da ya shiryar da mu ga wannan Addini,ya kuma sanya mu musulmai: (Ku tuna ni'imar Allah a gare ku da Alkawari mai karfi da ya yi da ku a yayin da kuka ce mun ji mun bi, ku ji tsoron Allah, lalle Allah masani ne ga abin da ke cikin zukata.)
 Ya ku wadanda Allah ya musu ni'ima da kammala hajjinsu, ya wadanda aka musu baiwan ayyukan da'a a lokutan alheri to ku gode wa Allah Mai tsarki ku tsayu a kan lazimtar addininSa. Da shari'ar sa da nisatar saba mishi  da kuma ketare iyakoki Allah madaukakin sarki ya ce ;-  ( Sai  ka daidaita  kamar yadda aka umurce ka kai da wadan da suka  tuba  tare da kai  kuma ba  masu kyatara haddi ba lallai shi mai gani ne ga abin da kuke aikatawa )
(An karbo daga Abu Sufyan Dan Abdallah As-sakafi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ;- Na ce ya manzon Allah  ka fada mini wani fadi a musulunci wanda ba sai na tambayi wanin ka a bayan ka  ba sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce;- '' ka ce na yi imani da Allah sannan ka daidaita  ) muslim ne ya rawaito
 Lallai aikin musulmi a wannan rayuwa shi ne daidaituwa akan  kadaita Allah mai tsarki da daukaka  da dayanta bauta gaba daya a gare shi , shi kadai  adu'a ne, roko ne, fata ne , tsoro ne  da kuma kwadayi da firgici  fadi da aiki  cikin da waje  a bayyane da boye  Allah madaukakin sarki ya ce :- (ka ce lallai ne sallata  da ibada na  da rayuwata da mutuwa ta na Allah ne Ubangijin talikai babu abokin tarayya gare shi kuma da wancan aka umarce ni  kuma ni ne farkon masu sallamawa )    
Lallai ita ce daidaito wadda take sanya ka  mai tsananin kauna  ga mahaliccin ka   tsarki ya tabbata a gare shi  tare da cikan kankan da kai a gare shi wanda sha'anin sa ya buwaya  da girmamawa,  lallai girmamawa ne wanda ya kunshi kadaita Allah  wanda  yabon sa ya girmama sunayen sa sun tsarkaka  da abin da ya kebanta da shi , mai tsarki na daga  rububiyya  da uluhiyya da sunaye da siffofi  Allah madaukakin  sarki ya ce ;- (ku bi abin da aka saukar zuwa  gare ku daga Ubangijin ku , kuma kada ku rinka bin wasu majibinta baicin sa)
(Kuma (ance mini) ka tsyar da fuskarka  ga addini kana karkata zuwa ga gaskiya, kuma kada ka kasance daga masu shirka   kuma kada ka kirayi baicin Allah abinda baya anfaninka kuma baya cutarka to idan ka aikata haka saannan lalle kai a lokacin kana daga masu zalunci kuma idan Allah ya shafeka da wata cuta to ba mai yaye maka ita sai shi kuma idan yana nufinka da wani alheri to ba mai mayarda falalansa yana samun wanda yake so daga cikin bayinsa da shi kuma shi ne mai gafara  mai jin kai )
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (ka kiyaye Allah sai Allah ya kiyayeka ka kiyaye Allah za ka sameshi gaba gareka idan za ka roka ka roki Allah idan za ka nemi taimako ka nemi taimakon Allah ) tirmizine ya rawaito kuma ya ce hadisi hasan sahihi
Daidaituwa akan tafarki mai tsiratar da bayi ita ce take sanya bawa ya zama mai kushuii gaba da girman Allah  ko wace girma ke kankanta gaba da girmansa shi halitta  duk yadda ya kai ga masayi ko duk yadda ya kai ga martabansa ya daukaka to shi halattace ne kuma abin raino ne wanda ake gudanar da shi abin mallaka. Allah Madaukakin Sarki ya ce game da AnnabinSa: (Ka ce ba ni mallaka wa raina wani amfani kuma haka ban tunkude wata cuta face abin da Allah ya so, kuma da na kasance ina sanin gaibi da lalle ne da na yawaita daga alheri kuma cuta ba za ta shafe ni ba.ni ban zama ba face mai gargadi kuma mai bayar da bishara ga mutane wadanda suke yin imani).
Ya kai bawan Allah ka kwadaita daga Allah kuma ka roke shi shi kadai ba shi da abokin tarayya, ya yaye cutarka ya kawo ma amfani ya yaye ma bakin cikinka, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Idan Allah ya shafe ka da wata cuta to babu mai kuranyewa gare ta face shi, kuma idan ya shafe ka da wani alheri to shi ne akan komi mai ikon yi )  kuma Allah mabuwayi mai girma ya ce : (ko wane ne yake karba wa mai bukata  idan ya kira shi kuma ya sanya ku mamayan kasa shin akwai wani abin bautawa tare da Allah?.kadan kwarai kuke yin tuna
lalle babbar manufa na samuwarka -ya kai halitta a wannan rayuwa- shine don ka tsayu bisa tafarkin Allah mikakke akan manhaji wanda yake na rayuwarka da kuma dabi'unka da halayenka a cikin kai-komonka wahayin da aka saukar da shi yayi hukunci akanka da kuma tarihin Annabi wanda aka turo amincin Allah su tabbata agare shi, Allah madaukakin sarki ya ce: (kuma lalle wannan ne tafarkina yana madaidaici sai ku bi shi kuma kada ku bi wasu hanyoyi su rarrabu da ku daga barin hanyata wannan ne Allah yayi muku wasiyya da shi tsammaninku kuna yin takawa )
Ya bawan Allah  ka tsayu bisa ga aiki da alkura'ni mai girma da halaye kan sunnan shugaban annabawa da manzanni zahiri da badini kana mai kuduri kuma kana aiki da shi kana mai hukunci da shi kuma kana mai nema ama hukunci da shi, Allah Ubangiji tsarki da daukaka su tabbata a gare shi ya ce: (kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gareka kuma ka yi hakuri har Allah ya yi hukunci kuma shi ne mafi alherin masu hukunci)
 Allah Mai tsarki da daukaka ya ce :(saboda haka sai ka yi kira kuma ka daidaita kamar yadda aka umarce ka kuma kada ka bi son zuciyarsu kuma ka ce na yi imani da abin da Allah ya saukar na littafi)
Ya kai mumini ka lazimci kiyaye  dokokin Allah kuma ka tsarkake aikinka gareshi shi kadanshi ta hanyan nufatanshi da kuma nema, za ka kasance cikin walwala na har abada  da kuma aminci  cikakke da rabauta mai girma   duniya da lahira za ka zama mafi tsarkakan mutane a rayuwa  kuma za ka kasance mafi cikan ni'ima kuma za ka zama mafi jin dadin rayuwa a cikin mutane da hali mafi dadi Allah madaukakin sarki ya ce :(lalle ne wadanda suka ce Ubangijinmu Allah ne sa'an nan suka daidaitu to babu wani tsoro a kansu kuma ba za su yi bakin ciki ba)(wadannan 'yan Aljanna ne suna madawwama a cikinta a kan sakamako ga abin da suka kasance suna aikatawa )
 Ya wanda ya sarayar da lokutan alheri ya barnatawa kansa ta hanyar aikata zunubai da abubuwa masu halakarwa to ka koma zuwa ga majibincinka Allah ka saurara zuwa ga abin da zai jefa maka fatan alheri a cikin zuciyarka to ka kasa kunnuwarka tare da sauraro daga gareka wanda zai ratsa cikin zuciyarka domin shi din nan kira ne daga wurin Ubangiji wanda ke turo rahamarsa da kaunarsa ga bayinsa, lalle yekuwa ne daga gurin Ubangiji Mai tausayi ga bayinsa duk yanda zunubi ya yi girma munanan laifuka suka daukaka Allah madaukakin sarki yana cewa (ka ce (Allah ya ce) ya ku bayina wadan da suka yi barna akan rayuwarsu kada ku yanke kauna daga rahamar Allah, lalle Allah na gafarta zunubai gabadaya lalle shi, shi ne mai gafara mai jin kai )
sannan ya kwadaitar da bayinSa zuwa ga maida al'amari ga Allah da komawa gare shi kafin tserewan lokaci da sarayar da zamani domin kar a fada cikin hasara da nadama game da sakacin yin da'a ga Allah Mai rahama. Allah Madaukakin sarki yace : (kuma ku mayarda al'mari zuwa ga ubangijinku kuma ku sallama masa a gabanin azaba ta zo muku sa'nan kuwa ba za a taimake ku ba)
(kuma ku bi mafi kyaun abin da aka saukar zuwa gare ku daga ubangijinku a gabanin azaba ta zo muku bisa auke kuma ku ba ku sani ba)

Huduba ta Biyu
Ya ku bayin Allah ku tsayu kan da'a ga Allah za ku rabauta, ku lazimci koyarwar Alkur'ani da sunna zaku samu walwala, samun daukaka da shugabanci na ga lizimtar addinin Allah da bin sunnar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma kyakkyawan karshe na ga tabbatar da tauhidi da tsoron Allah Mabuwayi abin girmamawa.   
Allah Madaukakin sarki yace : (wadanda suka yi imani kuma basu gauraya imaninsu da zalunci ba wadannan suna da aminci kuma sune shiryayyu)
Kuma kaskanci da walakanci da tabewa da hasara na cikin sabawa Allah da munanan laifuka da sabawa umarni da hani.
 Allah Madaukakin sarki yace : (kuma wanda ya sabawa Allah da ManzonSa kuma ya ketare iyakokinSa zai shigar da shi wuta yana madawwami a cikinta kuma yana da wata azaba mai walakantarwa).


   

السبت، 27 يوليو 2019

Alhurmar Aikin Haji


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Abdullahi dan Abdurrahman Albuaijan 23/11/1440AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya tattaro zuwa gare shi wanda ya nemi mafaka, Ya tanadi Aljannar ma'awa ga wanda ya nufe shi.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, ya daidaita bisa al'arshi, kuma ya yi hukunci,lalle kowani mutum da abin da ya nufa, na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne,bai bata ba kuma bai kauce hanya ba, kuma bai furuci bisa son rai face wahayi da ake yi masa, ya isar da sako ya bada amana ya yi wa Al'uma nasiha kuma ya yi umarni da takawa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa, da wanda ya bi su da kyautatawa ya hana rai ga soye soye rai,
 Bayan haka lalle mafi alherin zance shine maganar Allah,wanda aka saukar, kuma maga mafi gaskiya ita ce :
Ku saurara dukkan kome abin da ya ke ba Allah ba bata ne, kuma mafi alherin shiriya shi ne shiryarwar Annabi Muhammad dan Abdullah abin fifitawa, kuma mafi sharrin zance shi ne fararrun  mai kirkirare da ya zama bidiah, ko jahili mai wauta mai batarwa,ya ku bayin Allah, ina muku wasiyya da ni kai na da ku ji tsoron Allah don ita ce wasiyar Allah ga mutanen farko da na karshe, ( Hakika mun yi wasiya ga wadanda aka bawa littafi gabanninku da ku kan ku da ku ji tsoron Allah)
 Ya ku musulmai! Lalle Allah na halittan abin da ya so ya kuma yi zabi, hakika ya zaba cikin mala'iku manzanni da kuma cikin mutane.
Ya fifita ramadan bisa sauran watanni na lokaci, ya zabi Daki mai alfarma ya sanya shi dakin farko da aka sanya wa mutane,ya fifita shi ya sanya shi mazauni ya sanya shi gun samun lada da aminci ga mutane,da aminci ya albarkace shi ya sanya shi Alkibla,ya tattale shi ya ba shi alhurma,ya girmama shi ya sanya shi wurin ibada na tushe, (Allah ya sanya kaba daki tsararre ma'aunin Addini ga mutane)
Ya sanya Alhurma ga shingensa, ya sanya shi daki dadadde ya kira zuwa ga a nufe shi,Ibrahim ya ce : (ka  shelanta ga mutane a hajji za su zo ma a tafe da akan abin hawa zasu zo daga kowane sako)
             Ya ku musulmai! Ku amsa kiran Allah " mun amsa kiranka ya Allah kuma mun amsa kiranka ya Allah! Mun amsa kiranka ba ka da abokin tarayya ya Allah mun amsa kiranka! Lalle dukkan godiya da ni'ima naka ne kuma mulki ma naka ne baka da abokin tarayya.
Ya ku bayin Allah! Lalle musulunci Akida ne da Ibadoji da dabiu da halayya an gina shi akan abubuwa guda biyar, ; rukunnai wadanda sune tushe :Ta An karbo daga Ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi da mahaifinsa ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : "An gina musulunci a kan abubuwa guda biyar; Akan su kadaita Allah da tsaida sallah da bada zakka da Azumin watan ramadan da hajji"Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
  
 Ya ku mutane!Lalle Allah ya wajabta hajji  a gare ku, to ku yi hajji,  Allah Madaukakin sarki yace (kuma akwai hajjin Dakin domin Allah, akan mutane ga wanda ya samu ikon zuwa gare shi)
Hajji ibada ce ta rayuwa, kuma karshen al'amari da cikan rukunan musulunci, a ciki ne Allah Mabuwayi da daukaka ya saukar da
(A yau na kammala muku Addininku,kuma na cika ni'ima ta a gare ku, kuma na yard da musulunci ya zama addini a gare ku)
An karbo daga Abu Said Alkudri cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :; Allah Madaukakin sarki ya ce;Lalle bawa na na bashi lafiyan jikin shi, kuma na yalwata mishi a rayuwa, shekaru biyar bai zo gare ni to lalle hasrarre ne) Ibnu Hibban ne ya fitar da shi a sahihinsa.
   Ku sauke farillun Allah, ku nufi dakin Allah (kuma ku cika hajji da umara domin Allah!)
Ya ku bayin Allah!
Hajji rukuni ne na wajibi kuma farilla ne na dole Alkur'ani mai girma ya yi nuni ga hakan da muhimmin labari mai girma, Hajji na cikin ibadoji mafi daraja, da ayyuka mafi girma  na neman kusancin Allah, da masa biyayya, yana daga darajoji yana goge kusakurai yana kankare munanan laifuka har da manyan su.An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: Duk wanda ya yi hajji don Allah bai yi jima'i ba kuma bai yi fasikanci ba zai koma kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi) Bukhari ne ya rawaito.
 Kuma Tirmizi ya rawaito a littafinsa Assunan ya ku inganta shi daga Abdullahi dan Mas'ud Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ;Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ku biyar da hajji da umara domin suna gusar da talauci da zunubai kamar yadda zuga zugi ke tafiyar da dottin karfe da zinari da azurfa.Hajji mabrur bai da sakayya sai Aljanna)
Ya zo cikin sahihu Muslim daga Abu Huraira an tambayi Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ko wani aiki ne ya fi falala? Sai ya ce :Imani da Allah:aka ce sa'anan sai me? Sai yace : jahadi a tafarkin Allah sai aka ce sai me? Sai ya ce : Hajji Mabruri)

Ya ku jama'ar musulmai!
Lalle Allah mai tsarki ne bai karba sai mai tsarki, to duk wanda ya nufi aikin hajji to ya kame daga Haram, to ya zabo daga dukiyarsa halal, An karbo daga Abu Huraira yace Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :( Lalle Allah Mai tsarki ne bai karba sai mai tsarki, lalle Allah ya umarci muminai da abin da ya umarci Manzannai sai ya ce (ya ku Manzannai ku ci daga tsarki kuma ku yi aiki na kwarai lalle ni masani ne ga abin da ku ke aikatawa) kuma ya ce: ( ya ku wadanda suka yi imani ku ci daga mai tsarkin abin da muka azurta ku) . sai ya ambaci wani mutum yana tsawaita tafiya mai gashi a tsatsaye da kura yana daga hannayen shi sama yna cewa : Ya Ubangiji na ya Ubangiji na a halin abincinsa na haramun ne, abin shansa na haramun ne, kuma tufafinsa na haramun ne kuma an ciyar da shi abin kalace na haramun.
Allah ya sanya ni da ku cikin wadanda suke jin magana su bi mafi kyansa, wadannan su  Allah ya shiryar wadannan su ne ma'abota hankula.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya bada kuma ya ni'imta, ya kuma shiryar zuwa ga shiriya kuma ya yi ilhama, ya bayyana daidai ya kuma fahimtar,ya sanya hajji mafi darajan aiki kuma mafi girma,
 Ya ku musulmai!
Lalle kuna wata mai alfarma da Allah ya shar'anta alfarmanta ya girmama shaninta ya yi gargadi game da zalunci a cikinta sai ya ce:( Lalle kidayan watanni a gurin Allah guda shabiyu ne a littafin Allah a ranar da ya halicci sammai da kasa, daga cikinsu akrajab da muwai guda hudu nasu alfarma) uku daga cikin su a jere suke Zulka'ada da zulhajji da Muharram da rajab,na mudar. Sannan ya ce wannan wani wata muke ciki sai muka ce Allah da ManzonSa ne suka fi sani sai ya yi
Shuru har sai da muka tsammaci zai ambace shi da wani sunan ne, sai yace ase ba zulhajji ba ne sai mka ce : E sai yace wani gari ne wannan sai muka ce Allah da ManzonSa ne suka fi sani sai ya yi shuru har muka zaci zai ambace shi da wani suna da ba shi ba sai yace Ase ba wannan bane gari mai alhurma? Sai suka ce e shine.sai yace to a wace rana muke?sai suka ce Allah da Manzonsa ne suka fi sani. sai ya yi
Shuru har sai da muka tsammaci zai ambace shi da wani sunan ne, sai yace ase ba a ranar suka muke ba? Sai suka ce: E   haka ne sai ya ce : To lallai jininku da dukiyanku da mutunci a gare ku haramun ne, kamar alhurma wannan ranar taku a wannan gari naku a wannan wata taku., za ku hadu da Ubangijinku zai tambaye ku game da Ayyukanku, ku saurara : kada ku koma a baya na kafurai sashinku na dukan wuyan sashi, to ku saurara wanda ya ke nan ya sanar da wanda bai nan, don ta iya yiwuwa wanda za a isar zuwa gare shi ya kiyaye fiye da wanda ya jiyo.ku saurara! Shin ko na isar da sako, shin ko na isar da sako) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
Lalle watan zulkida shine watan farko cikin watanni masu alfarma da suke hade, a cikinsa ne Annabi ya kasance ya yayin da mushrikai suka hana shi shiga,da umaran da ya yi a shekaran da ta kewayo a zulkida ne ya yi ta a lokacin da ya yi sulhu da su, azulkada a yayin da ya yi sulhu da su, da umarar ji'irrana wanda ya raba ganimar hunain,da umara da ya yi da hajjinsa.  Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Ya ku bayin Allah !
lokaci na hajji lokaci ne na biyayya da da'a da kyauta, kuma karama ce  samun kyautar,
ya kasance a jahiliyya abin alfahari ne shayarwa ga Alhazai da suturce kaba da bata kulawa.suna munafasa a cikinta, da musulunci ya zo sai ya tabbatar da haka, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shiya yiwa Abbas izini da ya kwana a makka a dararrakin kwanan mina don shi,ya zo gurin da ake shayarwa  da ya nemi da a shayar da shi kuma ya sha ya tafi ta gun masu zamzam a halin suna shayarwa suna aiki sai yace (ku yi aiki lallai kuna kan aiki na kwarai,)  yace (Ba don kar a yi galaba a kanku ba da na sauka har na sa igiya a nan fa ya yi nuni ga kafadansa) Bukhari ne ya rawaito.
Allah ya yi gyadan dogo ga kasar Saudiya cikin hidima da ta ke yi na wurare masu tsarki, da amintar da shi ga masu dawafi da masu itikafi da masu rukui da sujada, ya mata baiwa na hidima da karbar bakuncin Alhazai da 'yan umara da masu ziyara ko shige da fice, tare da tausaya musu da gabatar da hidima da ta dace a gare su, da agaza musu wurin sake nauyin ibadojinsu,da shinfida musu dukan wata hanya ta aminci da zaman lafiya gare su, to Allah ya saka wa jagororinmu da shugabanninmu da sakayya mafi  alheri da cika da kamala da kyau da tsarki, bisa abin da suke tashi da shi na hidima ga masallatayya biyu masu alfarma da daukaka da masu tahowa gare su.
Ya ku bayin Allah! Ku kuna guri ne da ya fi soyuwa a gurin Allah, to ku bada hadin kai wurin ganin ku taimakawa ma'aikata masu tsare tsare da hidima, Allah ya karba mana ni da ku, ya mana gamon katar.
Alhazai ga daki mai alfarma,…
Hakika kun yi kokari kun yi dace na amsa kiran Allah na haji wajibi, to ku dage wurin yinta da cikata bisa yadda zaa karbe ta, ku nemi sanin hukunce – hukuncenta, na gargade ku da ku nesaci jima'I da fasikanci da jayayya (Haji watanni ne sanannu to duk wanda ya shiga aikin haji cikinsu babu batsa ko fasikanci ba musu a hajji)
   Ku sa nitsuwa da tsanaki, ku yi aikin jinkai idan an samu cunkoso, ku yi nesa da turereniya, ku tausayawa masu rauninku,domin a dalilinsu ne ake azurta ku a baku nasara.
 An karbo daga jabir yace Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya goyi Usama abayansa ya taso daga Arfa yana matse linzami dabbarsa Alkaswa kanta na taba tankin dabbar ya na nuni da hanunsa na dama da (ya ku mutane Natsuwa natsuwa) a duk lokacin da ya zo wani dutse daga cikin duwatsu sai ya dan saki linzami gareta har ta haura har ya iso muzdalifa) .Muslim ne ya rawaito