الثلاثاء، 3 سبتمبر 2019

wasiyya ga dalibai


Hudubar Masallacin Annabi na sheikh Salah Dan Muhammad AlBudair.29 zulhajji 1440AH

Hudubar Farko

Ya ku musulmai
Kokari zuwa ga halaye na mutunci da kyawawan dabi'u dabi'a ce na masu juriya kuma al'ada ce na masu kokari, ilimi shi ne daukaka mai daga darajan mai nemansa kuma aga kiman ma'abocinsa a ido , duk wanda ya so ilimi to falalolin shi kuwa zai kewaye shi abubuwan adonsa su sauka a farfajiyansa. Almuzani ya ce : "na ji shafi'I Allah ya yarda da shi yana cewa duk wanda ya nemi ilimin alkura'ani to kimarsa za ta kara girma duk kuma wanda ya yi nazarin ilimin fikihu matsayinsa zai yi kyau, duk wanda ya rubuta hadisi zai zama yanada karfin hujja duk wanda ya yi nazari a ilimin lugga dabi'arsa za ta tausasa, duk wanda yayi nazari a ilimin hisabi ra'ayin shi zai yawaita duk wanda bai kare kansa ba to iliminsa ba zai mishi amfani ba" .
Al'umma na samun karfi ne ta hanyan ilimi ###  hukunci a cikin zamani ana danganta shi ne zuwa ga alkalami ###sau da yawa tokuba na zubar da jini #### alkaluma kuma na zubo da hikimomi ###da mutane za su yi a'adalci ### da falala a tsakaninsu zata kasance ne  ### ta hanyar digon tawada ba ta hanyar zubar da jini ba ### ka dukufa wurin neman ilimi #### za ka kai kololuwa a matsayi ### a falala  wanda yana kumshe da daukaka da karamci.
ilimi a lokacin fitina ya na baka kariya, a lokacinci  kadaici yana dauke ma kewa yana sanya daukaka a cikin iyalai 
ya ku musulmai:
ga sabuwar shekarar karatu ta kunno kai nan ba da jimawa ba za a bude makarantu da jami'o'i za a karbi dalibai da kauna da maraba to saboda haka ga wasu wasiyyoyi ga dalibai maza da dalibai mata game da wannan munasabar:
Ya kai dalibi to ka koma makaranta tare da kwadayin karatu da farinciki da annashuwa da himma da kokari ka cire mutuwan jiki da jin tawaya da sakaci da kasala .
samun daukaka na ga kokari ### rasawa kuma na ga kasala  ### to ka kafu za ka samu cimma burinka nan kusa  ### lallai matashi wanda ya siffantu da himma irin na mutanen farko ### kuma bai saba rage zance ko aiki ba duk wanda ya sarayarda himma to ba zai cimma bukatunsa ba ### duk wanda ya yi jifa da kifiyoyi na ji ji da kai to ba zai samu ba .
Hakika mai himma ma'aboci hankali za iya cimma gaci ta hanyar da'a ga himmarsa da kuma sabawa son rai.
ya ku dalibai : ku yi sammako ku gaggauto zuwa ga ajin karatu, na horeku da ku nesaci  jinkiri da ja da baya  domin a cikin sammako akwai albarka da samun arziki da najahi da kuma dace,  Tirmizi ya rawaito daga sakr dan gamidi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (ya Allah ka sa albarka ga alummata a cikin sammakonta , sai ya ce ya kuma kasance  idan ya tura mayaka ko kuma runduna yana turasu ne a farkon wuni sakru ya kasance mutun ne dan kasuwa ya kasance kuma idan ya tura kasuwanci yana tura su ne da jijjifi sai ya zama hanshakin mai kudi dukiyarsa ta yawaita)   
Samun albarkan rana baya tabbatuwa sai da riskan sallan asubahi domin lallai sallan asubahi tamkar wata iska ce mai kamshi da wani yanayi mai dadi ku sammaka kuma ku yi katanga da adu'oyi  na neman kariya da azkar da suka zo daga annabi wadanda suke jefa debe kewa a cikin rayi da farin ciki a cikin zuciya su kara karfi da nashadi a jiki da kariya da kiyayewa ,duk wanda ya bawa ransa rabonta na more rayuwa da mutuwan jikin da sabo da jinkiri da bacci daga barin aikin shi da makarantan shi da hissarsa na karatu to hakika zai rasa  manufarsa danashinar sa zata yi girma, duk wanda ya yawaita kwanciya to zai rasa biyan bukata wanda ya lizimci kasala to zai yi asaran fatarsa shi mutun sakali mai kasala yana rayuwa ne matsiyaci zai zama yayi nesa amma duk wanda ya yi hakuri  to zai rabauta, da hakuri ne ake bude kofofin da suke rufe kuma ayi dace.
Baccin safiya wato yin bacci baya sallar asuba ya halatta sai dai idan zai kai ga sarayar da wajibi, kuma baccin kailula wato baccin azahar mustshabbi ne saboda hadisin Anas Allah ya kara yarda  a gare shi ya ce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce (ku yi baccin kailula saboda shaidanu basa yin baccin kailula ) abu nua'im ne ya fitar dashi 
 saboda kailula yana maida nashadi ga kwakwalwa da kuma jiki yana taimaka wa wurin bita da sauke nauyin da ya wajaba akan mutun da kuzari da kuma karfi da nashadi.
ku kiyaye kashe dare da hira domin yana haifar da wahala da kuma sa nauyin jiki kuma bala'i ne da ke bata yanayi, mutun ya kasa sakewa ya kashe mishi kuzari ya jefa mishi gajiya na zuciya da jiki kada  ka fi karfin idanunka ka hana shi barci idan barci ya zo, ka yi barci a farkon dare ka hutar da idanuwanka biyu, kada ka cutar da iyayenka,  a ko wani safiya sau da yawa mun ga wanda ya sarayar da aikin shi ko ya bar karatun shi ko kuma yayi sakaci da iyayen shi da iyalan shi sakamakon bata dare kan abin da ya ke na haram abun zargi tare da wasu abokan banza masu batarwa masu lalatarwa. ya kai dalibi ka yi kwadayin samun ladabi da tsabta da tsarkin zuciya da girmama malami da  lazimtan tsari da kiyaye abin da aka dora ma na karatu, da kiyaye wurin karatu da kuma abin da aka dora ma na karatu na makaranta, ka ji tsoron Allah domin Allah ba abin da ke boyuwa  a gare shi na zuciya ba wani kwayan zarra ko kwayan hancin dibino da zai shiga wa Allah duhu, ka sanya ilim shi ne babban tattalinka ladabi ya zama shi ne tufafinka ka kasance mafi cikan mutane ladabi, mafi tsananinsu wurin kankan da kai, kuma ka zama ka fi su tsarkaka da kuma addini ka zama ka fi su karancin shirme da kuma yawan fushi, ka abokanci mutanen kwarai ka yi nesa daga mutanen sharri, kar ka kusance su kar ka aminta da su kar ka yi cakudedeniya da su ko ka zauna da su, kada ka zauna zuwa ga mutanen banza domin halayen wawaye yana raba  mafi sharrin mutane shi ne wanda bai damu mutane su gan shi ba yana mummunan abu, duk wanda ya so yayi ababan mutunci to zai nesaci abubuwa na haramun kar ka saki ganinka kada ka kafa ganinka zuwa ga waninka domin idanuwa tarkon shaidan ne duk wanda ya saki ganin shi zai hadu da ajalin shi, na horeka kar ka kai kanka wuraren abin tuhuma da  abin da zai haifar da shakku na horeka da kar ka yi abin daza ka zo kana bada uzuri ka dauki izina daga waninka duk mutumin da luran shi ya yi yawa to kusakuren shi za su karanta, lallai rabautacce mai samun sa'ada yana da abin wa'azi ga wanin shi kuma yana mai daukan gogewa a matsayin abin da zai yi mishi hukunci  abin da zai rika lura da shi, na gargade ka da dukkan wani wasa wanda zai haifar da kiyayya ko ya zubar da kwarjini,  ba daukaka shi ne a kyakkyawan tufafi ba sai dai daukaka na nan ga ilimi ne da ladabi da addini, harshe waziri ne na mutun idan baka iya fadan magana wanda ya ke na daidai ba to ka yi shuru daga abin da yake ba daidai ba shi kanshi shi ne daidai, kada ka kasance cikin wanda ya ke aibata wa sannan ya na yawaita zagi yana yawaita suka ga abokai kada ka bankado laifukan mutane muddin sun boye sai Allah ya tona asirinka na daga laifuka, ka ambaci kyawawan abin da ka gani a cikinsu a duk lokacin da aka ambace su  kar ka aibata wani cikinsu a abin da kai ma kana da shi kar ka yi abokantaka da mai kasala, Abubakar alkawarizmi ya na cewa :" kar ka abokanci mai kasala a duk halayensa## sau da yawa mutun na kwarai kan lalace sakamakon bacin wani## raban wawa zuwa ga mai wayo abu ne da yake cikin sauri## baka ganin gaushi da ake dora shi a cikin toka shi ke nan sai gaushin ya mutu ?
A tarbiyantar da al'uma su taso kan kyawawan laduba wajibi ne da ya rataya ne a kan iyaye da majibinta al'amura,  wani daga cikin masu hikima ya ce : "ku yi gaggawa ta hanyan ladabtar da yaranku kafin shungulla su rarraba tsakaninku"
Ya ku dalibai : ku yi gaugawa zuwa ga ilimi wanda  dage mishi  ya dace agare ku, ku kiyayi hayaniya da kuma gajiya da kosawa da kasawa da yankewa .
Ka nema kada ka yi hayaniya wurin neman, laifin dalibi shi ne ya yi hayaniya ku nemi ilimi duk wanda ya nemi ilimi zai mikar da shi tun yana karami kuma zai gabatar da shi idan ya girma.
 Urwa dan zubair ya ce :" 'ya'ya na 'ya'ya na ku nemi ilimi in kun kasance kanana ba a bukatanku, to ya wuci ku zame manya  ba za a wadatu da ku ba."
ku yi kwadayi bisa makarantu domin  makarantu su ne wurin dashe, duk wanda darasi ya kwace mishi to dashe ya baci mishi, ku dimanci kallo a cikin littafi kada ku gaji daga leke leke a littafi da bincike da karatu da kuma daukan rubutu da bita da kuma mudarasa a tsakani da hadda.
Ibnul jauzi Allah ya mishi rahama ya ce : da zan ce lallai ni din nan na tsinkayi littafi littafi da ya kai mujalladi dubu ashirin kai dama sai na ce ma ya kasance ya fi haka a lokacin da na ke nema,
Ya ku dalibai  kokari kokari a tsakanin alkaluma da kuma litttatafai da tawada da abun rubutu har ku riski burinku, wasunsu suka ce na yi kura shekara arba'in ban yi kailula ba ban kwanta ba face littafi na dore akan kirji na an tambayi Imamu Ahmad bin Hanbal Allah ya mishi rahama zuwa yaushe ne mutun zai nemi ilimi sai ya ce "tare da kurtun tawada har zuwa akai shi makabarta" ya kai dalibi kasa natsuwa da bi a hankali da kaifin hankali na horeka da kar kayi gaggawa a wurin tafiya da hauka da nuna danyen kai da yaranta, wanda ke koro sharri ya jefa mutun cikin nadama hakika wanda ya bi a tsanaki zai iya riskan hajarsa wanda ya yi gaggawa kuma zai iya fadawa cikin kuskure, duk wanda ya yi amfani da wayar salula a yayin da yake tuki to hakika ya kai kansa ga hatsarin mutuwa ya kai kansa zuwa ga bakin halaka da abin da ya ke makruhi saboda waya yana dauke hankali da ji ya sa mutun ya rasa kulawa da halartowa da hankali duk mutuninda idonsa ya kafu akan waya ya saki kunnuwarsa ya sunkuyar da kansa da kafadunsa ya shagalta da tattaunawa da ture ture da yada tagrida da ababan kallo  a halin yana tafiya to hakika ya zo da wani babban laifi da wani abin da aka ki, to ka sanya tunanika ka tattaro da hankalinka zuwa ga inda ka nufa da abin da ka fiskanta da tukinka idan wani abu ya zo ma na tunani ko na sada wani zumunci ta wayarka to ka fita daga kan hanya ka tsaida abin hawanka to ka kare bukatarka da wayarka ka kame kanka daga cutar da musulmai da kuma shi kanshi sharrinka kafin wani abin ki ya faru har ya sanyaka ka yi bakinciki da nadama da hasara da kaji radadi ka ce wayane ya mantar da ni ya makantar da ni ya shagaltar da ni a wannan lokacin kuma nadama ba zata yi amfani ba bayan kafarka ta riga ta zame.
Kuyi salati da aminci bisa ga Ahmadu mai shiryarwa mai   
mai ceto ga halittu gaba daya .                       

 

Huduba ta biyu

Ya ku dalibai : girmama malami fa wajibi ne mutunta shi da kimanta shi da kankan da kai  a gare shi farilla ne na tilas, sanin falalan ilimi da gode wa mai kyau aiki ne daga cikin abubuwa na kyawawan dabi'u masu daraja dalibi na siffantuwa da ladabi a ajinsa hakama tare da abokan karatunsa domin wannan shi ne girmama ilimi da kuma ma'abotansa Umar dan kaddabi Allah ya kara  yarda agareshui ya ce : (ku nemi ilimi kuma ku ilmantar da mutane shi ku nemi ilimin mutuntawa da kuma nitsuwa ku yi tawaliu ga wanda kuka koya daga gareshi da kuma wanda kuke koyarda shi kar ku kasance masu jiji da kai na daga malammai shi malami yana cikin manyanmu ne abun girmamawa cikin manya kuma girmama manya yana cikin abnda aka samo daga hadisi)
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda  a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce (Duk mutuminda bai tausaya wa karaminmu ba kuma bai san kiman ko hakkin babbanmu ba to baya tare da mu)
Tashi don malami ka girmamashi ###
                                      malami ya kusa ya zama manzo .
yanzu ka san wanda yafi daukaka ###
fiye da wanda yake gina kuma ya tada rayuka da hankula ?!.
tsarki ya tabbata a gare ka mafi aherin masu ilmantarwa ### ka ilmantar da alkalami karnonin da suka shude na farko
.ka fidda wannan hankalin daga duhunsa ### ka shiryar da shi zuwa ga hanya na haske bayyananne .
katuro Annabi Musa da attaura yana mai shiryarwa ### dan batulu kuma ya ilmantar da injila .
sai ka bubbugo da mabubbuga na bayani ## sai ya shayar da hadisi kuma ya bada alkura'ani (tanzila).


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق