HUDUBAR
FARKO
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah Mabuwayi mai yawan gafara, yana juya dare akan wuni kuma yana
juya yini a kan dare, lalle akwai abin lura a hakan ga masu basira,ina kyautata
yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi bisa ni'imominSa da ba mai iya
kididdige su sai shi, daga wadanda muka sani da wadanda ba mu san su ba,sunayen
Ubangijinmu sun tsarkaka, siffofinsa sun kasaita, ba abin bautawa da gaskiya
sai Allah Tilo Mai rinjaye,na shaida Annabinmu shugabanmu Muhammad bawanSa ne
kuma manzonSa ne mai Albishir da rahamar Allah da AljannarSa, mai gargadi da
ukubar duniya da azabar wuta, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka
ga bawanka kuma Manzonka Muhammad da iyalansa da sahabbansa ma'abota biyayya.
Bayan haka ku ji tsoron Allah Madaukaki ta hanyar neman yardarSa da tsoracewa
fushinSa da ukubarSa,Allah Tsarki ya tabbata a gare shi yace " Kuma Ubangijinka yake halitta abin da ya so ya kuma zaba,
zabi bai kasance na su ba, tsarki ya tabbata ga Allah Madaukaki daga abin da suke yi na shirka"
Lalle Ubangiji Mabuwayi da
daukaka ya halicci halittu da kudurarsa da iliminSa da hikimarSa da rahamarSa ya
samar da wannan duniya da ake gani, ya sanya mata wani ajali da zata kare zuwa
gare shi ba zata wuce shi ba,ya halicci wannan duniya da muke ciki tare da
sababi, ya halicci abin da ke zamewa da sababi kuma shine ke halitta sababi da
abin da ke kawo sababin: To duk abin da Allah ya so zai kasance duk abin da bai
so ba kuma ba zai kasance ba.Allah Madaukakin sarki ya ce: Allah ne Mahaliccin dukkan komai kuma shine wakili akan
kome. Shi ke da mabudan sammai da kasa kuma wadanda suka kafirta da ayoyin
Allah, wadannan su ne masu hasara. Kuma
ya ce: "To shine da halittar kuma da
umarnin Albarkar Allah Ubangijin halittu ta bayyana! ".
Mutum halitta ne daga cikin
halittun Allah na ban mamaki, Allah ya hada mishi sifofi na ban al'ajabi,
wdanda ke rarrabe ga wasu halittu da ba shi ba. Allah ya ce : "Lalle ne Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon
tsayuwa".Allah Madaukakin sarki ya ce: kuma a cikin rayukan ku (akwai ayoyi) kuma ba za ku duba
ba?"
Ya kuma ce : "kuma akwai daga ayoyinSa ya halitta ku daga
turbaya sai ga ku kun zama mutum kuna watsuwa" kuma Allah ya yi
baiwa ga bani adam bisa karrama su sai yace "kuma
Lalle ne Mun girmama 'yan Adam kuma muka dauke su a cikin kasa da teku kuma
muka azurta su daga abubuwa masu dadi, kuma muka fifita su a kan mafiya yawa
daga cikin wadanda muka halitta, fifitawa."
Kuma girmamawa da Allah ya yi
wa bani Adam girmama wa ne na gaba daya ga mai biyayya da mai fajirci a nan
duniya da ni'imomi, amma kebantacciyar girmama wa a lahira da yardarSa da
Aljanna ta ni'ima ga muminai ne kawai, kafuri bai da rabo a lahira, kuma
Ubangijinka ba ya zaluntar kowa, amma a lahira Ubangiji bai girmamawa sai ga
wanda ya mishi biyayya cikin Mutane da Aljanu.
Ibnu Asakir ya rawaito daga
Hadisin Anas dan Malik Allah ya kara yarda a gare shi"Daga
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Lalle mala'iku
sun ce : ya Ubangijinmu ka halicce mu ka halicci bani Adam sai ka sanya su suna
cin abinci kuma suna shan abin sha,suna sanya tufafi kuma suna auren mata, kuma
suna hawan dabbobi,suna barci suna hutawa, amma mu baka sanya mana wani abu na
daga wannan ba, to ka sanya musu a duniya mu kuma ka sanya mana a lahira sai
Allah Mabuwayi da daukaka ya ce: Ba zan sanya wanda na halita da hanu na na
kuma busa mishi rayi na ba tamkar wadda na ce da shi kasance ! sai ya
kasance"
akwai wani hadisin da zai
karfafe shi daga hadisin Abdullahi dan Amr wanda Dabrani ya rawaito.
Na daga cikin ni'imomi masu
girma da aka yi wa bani Adam akwai hore masa abubuwa masu amfani da maslahohi
da ni'imomi, Allah Madaukakin sarki ya ce: "Ase
baku ga yadda Allah ya hore muku abin da ke cikin sammai da kasa ba ya kuma
yalwata muku ni'imominSa na zahiri da badini " Allah Madaukakin
sarki ya ce: ya hore muku abin da ke cikin sammai
da kasa baki daya, daga gare shi, lalle cikin haka akwai ayoyi ga mutanen da
suke masu tunani."
Hikima
na yalwata ni'imomi ga bani Adam ita ce :don su mika wuya ta hanyar da'a ga
Allah Madaukaki su kuma gode masa, kada kuma su hada shi da wani a cikin bauta, Allah Madaukakin sarki ya ce:"kamar wancan ne Allah ya ke cika ni'imarSa a gare
ku ko zaku mika wuya.
Ibnu kasir
Allah ya mishi rahama ya ce a tafsirinsa:"Ai haka zai sanya muku abin da zaku taimaki kanku cikin
al'amuranku da abin da za ku bukace shi don ya zme muku abin da za agaza muku
wurin bin Allah da bauta masa"
Allah bai yi
nuni ga ambaton dan Adam ba tun da ya halicci Adam da hanunSa da abin da ya ke
tsakanin marhala zuwa wata marhala na mutum face don ya bayyana mishi nauyin da ke kan shi
a wannan rayuwa ta duniya kuma ya sanar da shi aikin da ke kan shi, da hikimar
da ya sa aka halitta shi, kuma an kallafa mishi umarni da hani kuma yana mai
dauke da wannan sharia da kuma daukakaka na bautawa Ubangijinsa Allah Madaukakin
sarki ya ce: "
yanzu mutum na zaton zaa bar shi haka kawai ne " Imamusshafi'I
Allah ya mishi rahama yace : wato ba za a umarce shi ba ko a hana shi,
Allah Madaukakin
sarki ya ce: " To kuna zaton cewa mun
halicce ku don wasa ne kuma ba za ku dawo zuwa gare mu ba?
Na daga cikin
abin da Allah ya tsara wannan duniya da
abin da ya halitta na sabuba da ke tasiri a samuwar wadannan abubuwa, lalle
Allah ya bayyana mana daga cikin sunnoninSa a rayuwa cewa ayyukan dan Adam na
inganta rayuwa ta yi dadi idan ayyukan sun yi kyau a nan duniya, haka kuma
rayuwa kan baci idan ayyuka suka lalace, kuma ayyukan dan Adam na shiga har cikin
dabbobi da tsirrai ya yi tasiri wurin gyaruwansu ko bacin su, bisa rahamar
Allah da adalcinsa, don ya lazimtawa mutum da'a kuma ya kauracrwa abubuwan da
aka haramta. Allah Madaukakin sarki ya ce game da albarkar
rayuwa da alherinta na ga kyautatuwan ayyukan mutum :- (Da mutanen
alkarya za su yi imani su yi takawa da mun bude mu su albarkatu daga sama da kasa sai dai sun karyata sai muka rike su da abin
da suka kasance suna aikatawa )
Kuma Allah Madaukakin
sarki ya ce :- (Da ma'abota littafi za su yi imani su yi takawa da mun kankare musu laifukan su kuma da mun shigar da su aljanna na ni'ima . Kuma da a ce
sun tsaida attaura da linjila da abin da
aka saukar musu daga Ubangijin su da sun
ci daga saman su da kuma karkashin kafan su )
Kuma Alkur'ani
shi ne abin da Allah ya saukar ga musulmai da ahlul kitabi ba wanda
ya sanja shi sabo da kiyaye shi , kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Wadanda suka yi imani basu chakuda imanin su da zalunci
ba wadannan suna da aminci kuma su ne shiryayyu)
Wato basu
churkuda imanin su da shirka ba , kamar
inda annabin shi ya fassara shi
kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Ya ku
wadan da suka yi imani in za ku taimaki Allah Allah zai gtaimake ku). Wato
in za ku taimaki addinin Allah to zai taimake ku.
Kuma Allah mabuwayi da daukaka ya ce :- ( Wadan da in mun basu matsayi a doron kasa sai su
tsaida salla kuma su bada zakka su yi umarni da kyakkyawa su yi hani da
mummuna , kuma lallai akibar al'amura na
wurin Allah ).
Ibn Kasir Allah ya
mishi rahama ya ce a tafsiri : ''Umar Dan Abdul-aziz ya yi huduba sai ya
karaanta wannan aya sai ya ce : 'ku
saurara wannan aya bata tsaya akan jagora kadai ba sai dai ta kunci shugaba da
talakawa a sai ba zan baku labari ba da abin da yake hakkin ku ne akan shugaba da
kuma abin da ya ke hakkin shi ne akan ku:- na daga ciki , shi ne ya rike ku da hakkokin Allah da
ke kan ku kuma ya karbi hakkokin wasun
ku da ke kan wasu kuma ya shirye ku zuwa
ga abinda yake dacewa iya'iyawan shi ,
to, ku kuma ya wajaba a gare Ku , ku mishi
da'a'' . Afadin Allah (kuma lallai akibar
al'amura na wurin Allah ).
Akwai aminci ga wanda
ya tashi da wadannan al'amura guda hudu :
Na daga wani da kuma kaidi na makiya
kamar yanda Allah Madaukakin sarki ya ce:-
(muddin kuka yi hakuri kuka yi takawa to kaidin su ba zai cutar da ku ba da
wani abu lallai Allah ya iyakance abin
da suke aikatawa).
Kuma kamar yanda gyaruwan aikin mutum yakan game da alheri to haka namma yake shafi shi mai aikin shi
kan shi , kamar yanda Allah Madaukakin
sarki ya ce :- (Duk wanda ya yi aiki na
kwarai na miji ko mace a halin yana
mumini to za mu raya shi rayuwa daddada
kuma za mu sakanya mu su da ladan
su da mafi kyaun abin da suka kasance suna aikatawa).
Ta daya bangaren kuma
da ke kishiyantan wannan shi kan
shi barna na aikin mutum yana cutar da shi kan shi mutum din kuma ya shigar da shi barnan a cikin rayuwa , Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Da a ce gaskiya zai bi soye-soyen rayukan su da sammai
da ksa sun lalace da abin da ke cikin
su )
Kuma Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Barna ta bayyana a doron kasa da taiku sakamakon abinda hannayen mutane ya
aikata don ya dandana musu wani sashi na
abinda suka aikata ko za su dawo ). Kuma Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Duk wani abin da ya same ku na musiba to sakamakon abin
da hannayen ku suka aikata ne kuma yana
yafiya ga mafi yawa)
To ka yi lura ya kai mutum halin wadannan da suka munana
aiki abin da ya sauka a gare su Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Sau dayawa muka halaka daga alkaryu wanda sun kasance
azzalumai bayan su muka tada wasu
mutane daban)
An karbo daga Abdullahi Dan Umar Allah ya kara yarda a gare su ya ce :-( Abubuwa biyar na tare da wasu abub uwa biyar : Alfahasha
ba zata bayyana ba a cikin mutane har kuma su bayyana ta karara face annoba ta bayyana a cikin su da
cututtuka irin wanda ba a samu ba daga wadanda suka gabace su.kuma muddin jagororinsu ba su
yi hukunci da littafin Allah ba face Allah ya sanya yakinsu a tsakaninsu, kuma
ba wasu mutane da zasu hana zakkan dukiyar su face an damke su da fari a kuma
hana su ruwan sama ba don dabbobi da ba a saukar musu da ruwa ba, kuma zasu
tawaye kilo ba face an rike su fari da zalunci shugaba, baza su warware
alkawarin Allah da Manzo ba face Allah ya dora musu makiya akan su, su rika
kwace wani sashi na abin da ke hanun su) Ibnu Maja ya rawaito
Allah Madaukakin sarki ya ce :- (Kuma dan adam bai da wani abu sai abin da ya aikata .
Kuma aikin sa da sannu za a gani ). Allah
ya sa min albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah mabuwayi mai
yawan gafara mai hakuri mai yawan godiya , ina kyautata yabo ga Ubangiji na
kuma ina gode mishi ina tuba zuwa gare
shi kuma ina neman gafarar sa , to
lallai godiya ta tabbata ga Ubangijina a duniya da lahira bisa falalar sa da baiwar sa cikin abin da muka sani da wadda
ba mu sani na shaida ba abin bautawa da
gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya masani da abinda ke
cikin zukata , na shaida Annabin mu kuma shugaban mu Muhammad bawan sa ne kuma Manzon sa ne wanda aka turo shi da shiriya da haske Allah ka yi dadin tsira da aminci da Albarka bisa ga bawan ka kuma Manzon ka Muhammad da iyalan sa da sahabban sa wanda suka yi fintinkau zuwa ga dukkan aiki
na da'a .
Bayan haka ku ji
tsoron Allah Madaukaki don ku riki tafarki
zuwa ga Allah wanda zai shigar da ku cikin aljannar sa ku rabauta da yardan sa ya kai dan adam yi dubi zuwa ga ni'imomin Allah a gare ka da ya ni'imtar kai wanda ba wanda ke da
kudura na iyakance su sai Allah kuma ka tashi da godiya gare shi game da su da zai kwace mafi karancin ni'ima to ba wanda ya isa ya
dawo ma da ita sai shi .
A cikin ni'imar Allah ba wani abu kankani a halin kuma ga ka ya kai mutum ta hanyar
daidaiton ka da gyaruwan ka da yadawan
ka ga alheri da kuma kamewan ka daga
sharri za ka kasance ka taimaka wurin kiyaye muhallin
ka na zama(matattara) da kuma tseratar
da kanka daga sharrace-sharrace , da ukubobi , ka sani lallai kai abin tambaya
ne game da ayukan ka a rayuwar ka da
kuma bayan mutuwar ka to ka yi dubi me
za ka gayawa Ubangijin ka Allah Madaukakin sarki ya ce:- (Ya kai mutum
lallai ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijin ka , wahala mai
tsanani to, kai mai haduwa da shi ne. To
amma wanda aka baiwa littafin sa da damarsa .
To za a yi masa hisabi mai sauki . Kuma ya juya zuwa ga iyalan sa (a
cikin aljanna) yana mai raha. Kuma amma wanda aka baiwa littafin sa daga wajen
bayan sa . To za shi dinga kiran halaka
kuma ya shiga (wutar) sa'ira .
Ya zo a hadisi:- (Kafan
bawa baza su gushe ba har sai an tambaye shi game da abubuwa guda hudu; game da rayuwan sa cikin abin da ya karar da su da samrtan
sa a cikin me ya tafiyar da , da
dukiyar sa daga ina ya same su kuma a me
ya ciyar da su, da kuma aikin sa mai ya aiwatar da shi ).
Ka sani ya kai mutum lallai gidan ka da ke wanzuwa na
dindindi ita ce take gaban ka bayan mutuwa, to dadi ya tabbata a gare ka in ka
rayata da ayuka na kwarai , kuma azaba
ya tabbata a gare ka in ka yarda da wannan duniya taka ka manta lahirar ka
, duniyar ka za ta juya ma baya ne in ka
kaunace ta ko ka ki ta , lahira kuma za
ta fiskanto ka bisa ga abin da ka
kaddamar kuma ita ta har abada ce .
Ya ku bayin Allah ! lalle Allah da mala'ikunSa suna salati
ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci
tabbatacce.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق