الأربعاء، 27 مايو 2020

HUDUBAR KARAMAR SALLAR IDI NA MASALLACIN ANNABI 1441AH

Hudubar idi na masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi 1-10-1441Ah /24/5/2020Ad

    Na Shaikh Abdullahi dan Abdurrahman Al-Buaijan

Huduba ta farko

Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne, Allah ne Mafi girma Mai girma, dukkan yabo  da godiya masu yawa sun tabbata ga Allah, Tsarki ya tabbata ga Allah safiya da maraice godiya sun tabbata ga Allah bisa datarwanShi da kyautatawanShi , godiya bisa ga yalwan kyautanSa da baiwarSa dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah wanda ya shiryar da mu zuwa ga musulunci ya kuma datar da mu zuwa ga azumi kuma da tsayuwan dare dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya kwararamana daga cikin taskokin kyautanSa , abinda ba ya iyakantuwa shi ne wanda ya fi dacewa a bauta wa kuma shi ne yafi dacewa da a ambata kuma shi ne wanda ya fi cancanta da a godewa kuma Allah mai girma ya shar'anta mana shari'o'I da hukunce hukunce kuma ya sa sauki a ciki dukkan yabo da godiya sun tabbata ga wanda ya fara kuma ya ke maidawa , Ma'aboci al'arshi Madaukaki , mai yafiya kuma mai yawan gafara mawadaci abun godiya mai aykata duk abinda ya so , wanda ya shiryar da shi ne zai samu walwala kuma shi ne wanda ke kan daidai wanda kuma ya baar to shi ne tsinanne daga rahama abun korewa wanda ya shiryar da shi zuwa ga hanyan tsira to shi ne shiryayye .

Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allahshi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya ga dukkan komai mai sheda ne shi yayi ni'ma a gare mu da shedawa na tauhidi da kuma shaidawa cewa Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne zababbe cikin bayinSa Ma'boci manhaji shiryayye da kuma abin bi wanda ya ke na daidai tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalanSa da sahabbanSa salati na din din din har zuwa ranan alkawari

 Bayan haka :

Muna muku barka da ranan idi, Allah ya sa muku albarka a cikin dukkan wani abu sabo ya sa ku walwala da bushara ya sa muku kari, Allah mafi girma Allah mafi girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Allah shi ne mafi girma dukkan yabo da godiya naShi ne.

Ya ku musulmai , ban kwana irin na ramadana kafin 'yan kwanaki ne mu ke fiskantan watan ramadana gashi a yau kuma muna mishi ban kwana yana kokarin shudewa ya zama cikin zamani abin tarihi haka nan ne kuma lokacin ya ke tafiya rayuwa shekaru na mutum su kare wata mai daraja ya tafi dararrakinsa da abun rayawa da wuninsa abun dulmuya a cikin bauta gajiyansa ya tafi wahalansa ya kare ladansa kuma ya tabbata in Allah ya so wata ne mai albarka da falala da kuma alheri da kuma da'a wanda ranakunsa sun kare an kuma nade ayyukansa masu rabauta sun ci riba sun masu kokari  kuma sun  samu ganima, ina ma da mu san wadanda aka karma musu mu taya su murna, mu kuma san wadanda aka maida musu jajanta musu!

Ya farin cikin wadanda suka rabauta! Hakika Allah ya musu ilhama na tuba, ya datar da su ga da'a, muna rokon Allah ya karba musu kuma ya basu daidaituwa a kan tafarki.

Ya kaiton wanda ya yi hasara, hakika sun rasa alheri, an musu shamaki daga Ubangijinsu, damammaki na rayuwa sun kwace musu, da lokuta na alheri basu ribace shi ba sai hasara da nadama, sai dai kofofin tuba basu gushe ba suna bude ba a rufe su bayan ramadana,kuma Ubangijinmu Mai daukaka da buwaya yana karbar tuba daga bayinSa a dukkan lokaci da wuri,

(Kace ya ku bayi na wadanda suka barnata ma kawunansu!kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah, lalle Allah na gafarta zunubai gaba daya kuma shi Mai gafara ne Mai jinkai).

      Ya ku musulmai!

Lallai na daga cikin alamu na karbar ayyuka akwai sauyawa daga wani hali zuwa hali mafi kyau, to ku roki Allah tabbatuwa akan daa har zuwa mutuwa, ku nemi tsarin Allah daga juyawar zuciya, da kuma lalacewa bayan gyaruwa, abin mamaki da dabbancin kaskancin sabo bayan daukaka na da'a, ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,(Lalle dayanku zai yi aiki irin na 'yan aljanna har sai ya kasance tsakaninsa da ita zira'i sai littafinsa ya rigaya sai ya yi aiki irin na 'yan wuta sai ya shigeta, kuma lalle dayanku zai yi aiki irin na 'yan wuta har sai ya kasance tsakaninta da shi saura zira'i sai ya yi aiki irin na 'yan aljanna si ya shige ta.)

 

Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

Ya jama'ar musulmai… [ fiskantar karamar idi da farinciki da taya murna]

Muna muku murna da idin karamar sallah, hakika Allah ya rubuta muku lada kuma ya yafe muku laifukan ku, ya gafarta muku zunubai ya daga darajojinku kuma ya kankare muku kurakurai, ku godewa Allah ku roke shi karbar ayyuka da tabbatuwa. Muna taya ku murna da kuka fifita yardar Allah bisa ga jin dadi na duniya da sha'awe sha'awe, kuka kyautata kuma kuka cika kuka yi abin da ya dace na ibada, kuka samu mafi girman sakayya in sha Allahu, barkanku da samun yin azumi kuma barkanku da samun tsayuwa, barkanku da yawaita ayyuka na da'a, barkanku da farin ciki na idi da kawa na idi da walwala, ku ji dadi da duk wani abu da ya ke sabo.

 

Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

Ya ku bayin Allah! Yafiya da rangwami.

Lalle Allah ya cikamake azumi da idi karama mai albarka kuma ya sanya ta cikin manyan alamomi na addini, na daga cikin sunnar mafificin Annabawa da Manzanni a bayyana farinciki a tsakanin musulmai da bayyana jin dadi da walwala da annashawa da kawa, to ku yada abubuwa na kauna  kyawawa, da kalamai masu dadi, ku jefa duk kayan kamshi da dadadawa.

 ku yada walwala  a doron kasa da  ku  yi dariya da sifa ta murmushi mai ban kaye, ku yi gaishe gaishe na idi domin yana kara kauna ta kuma karfafi soyayya da 'yan uwantaka,

ku shigar da farinciki a zukata, ku binne kyashi da bakinciki, ku shigar da farinciki ga iyalai da makusanta da makwabta, ku yi wasici ga juna da gaskiya da rahama, ku tausayawa wanda ke doron kasa sai wanda ke sama ya tausaya muku.

Yau rana ne na afuwa da kauda kai da rangwami, wanda ke son afuwa da gafara daga Allah to ya yafe ya ya kuma yi afuwa ga mutane, domin sakayya na kasancrwa ne da irin nau'in aikin da mutum yayi, Allah Madaukakin sarki ya ce (su yi rangwame su yi afuwa, shin ba ku son Allah ya gafarta muku)

(kuma lalle ne wanda ya yi hakuri ya gafarta to shi wancan aiki haki yana daga manyan al'amura).

      Ku yi afuwa ga wanda ya yi zalunci ku dauke kai daga wanda ya muzguna.

(kuma ku yi gaggawa zuwa ga neman gafara daga Ubangijinku da wata Aljanna fadinta sammai da kasa ne)

Yau rana ne na biyayya da kyautatawa,to ku kyautata kamar yadda Allah ya kyautata zuwa gare ku Allah yana son masu kyautatawa , a yau rana ne na sada zumunci , da kauna , ku sada zumuncin wanda ya yanke muku ku bawa wanda ya hana ku , ku yafe wa wanda ya zalunce ku ba wai mai sadarwa shi ne wanda mai rama abinda aka mishi ba na alheri , a yau rana ne na sanin yakamata to ku yi wasici wa junan ku da masu rauninku ku yi musu wasici da alheri ku tausayawa kananan ku , kuma ku girmama manyan ku , ku kyautata zuwa ga talakawan ku , ku shigar da farin ciki a cikin zukatansu da annashawa ku yaye musu bakin ciki da bacin rai kuma ku magance musu ciwonda suka ji ku ji tsoron Allah ku kyautata ku sulhunta tsakanin ku kada shaidan ya fitineku ku yi sulhu tsakanin 'yan uwanku .

An karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(ana bude kofofin Aljanna ranan litini da alhamis sai a gafartawa dukkan wani bawa wanda ba ya hada Allah da wani sai mutumin da kawai ya kasance tsakaninshi da dan uwan shi akwai gaba sai a ce da shi a sararawa wadannan har lokacin da suka yi sulhu ku jira wadannan mutane biyu sai sun yi sulhu ku jira wadannan mutane biyu har sai sun gyara tsakanin su) Muslim ne ya rawaito .

To ku gyara kawunanku ya ku bayin Allah bisa ga tsarkake zukatan ku da kuma aminci zukata ku jaddada alaka na kauna da soyayya tsakaninku da tausayi imanin dayan ku ba zai cika ba har sai ya so ma dan uwan shi abinda ya so ma kanshi kuma ku yi kyauta za ku so juna .

Allah mai girma , Allah mai girma , Allah mai girma ba abin bautawa da gaskiya sai Allah , Allah mai girma Allah mai girma dukkan godiya nashi ne .

Bayin Allah :

Lallai ku din nan 'yan uwa ne daga uba da uwa (A'adam da Hawwa'u) sai dai shaidan yana iya rarraba tsakaninku ya jirkita zaman lafiyan tsakanin ku da 'yan uwantakan ku hakika ya fidda mahaifan ku biyu daga Aljanna ta hanyan rudi, ya byyana tsakaninku kuma adawa da kiyayya to ku yi riko da igiyan Allah ku yi sulhu tsakanin 'yan uwanku ku jo tsoron Allah kada ku rarraba kada ku cece ku ce sai ku dare karfinku ya tafi.

An karbo daga Abu huraira ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (kada ku yanke zumunci kada ku juya wa juna baya kada ku yi gaba kada ku yi hasada kada ku yi tajassusi (leken asiri) kuma kada ku yi bincike,kada ku yi munajasha ku kasance bayin Allah 'yan uwan juna, ku kasance 'yan uwa kamar yadda Allah ya umarce ku)Muslim ne ya rawaito.

   Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

Ya jama'ar musulmai… [Tasirin akida a tarbiya]

Lalle Allah ya zaba muku musulunci, to kada ku mutu face kuna musulmi, to ku kiyaye tushen shi da rukunan shi, ''An gina musulunci akan abubuwa guda biyar , shaidawa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Annabi Muhammadu Manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakkah, da azumin ramadana da yin Hajjin dakin Allah''.

Ku kiyaye imani domin shine tushe kuma a kan shi a ke gini, shine tsagoron addini da dalakin shi, shine (Imani da Allah da mala'ikunSa da littatafanSa da MazanninSa da ranar lahira da imani da kaddara na alheri da sharri).

Ku yi kokari wurin murakabar Allah a kowani zamani da kowani wuri, don shine hakikanin ihsani wato (ka bautawa Allah kamar kana ganinSa to in ba ka ganinSa shi yana ganinka)

Ya ku bayin Allah Tauhidi shine tushen addini kuma abin rikon shi mai karfi, kuma shine asali da ake gini a kan shi, da kuma hukunce hukunce, bisa shi ne ake karbar ibada kuma ya inganta ko akasin haka,  da ayyukan da'a  da shi ne ake samun tsira na duniya da lahira kuma shine hakkin Allah a kan bayi, An karbo daga Mu'azu dan Jabal ya ce na kasance goye akan jaki da ake kira Ufairu a bayan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace : sai yace ya Mu'azu ko ka san hakkin Allah akan bayi da hakkin bayi a kan Allah? Sai na ce  : a'a Allah da ManzonSa suka fi sani, sai yace : (Hakkin Allah akan bayi shine su bauta masa kada su hada shi da wani, hakkin bayi kuma a kan Allah shine kada ya azabtar da wanda ba ya hada shi da wani.yace sai nace ya manzon Allah ba zan yi wa mutane albishir ba? Sai yace a'a kada ka musu albishir su saki jiki) Buhari ne ya rawaito.

Lalle tauhidi shine mabubbuga na hadin kai da fahimtan juna da 'yan uwantaka. Da shi ne ake samun haduwar kalma kuma al'uma ke zama tsintsiya madaurinki daya. Da shi ne ake zartar da alakoki ko a kulla wani abu. Da shi ne al'uma ke iya tsayawa a kan kafanta a samu zaman lafiya.

Ku godewa Allah bisa ga shiryarwa kuma ku roke shi tabbatuwa a kanta.

  Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

      Ya ku musulmai! [Tasirin ibada da muamaloli]

Ku maida hakkoki zuwa ga ma'abotanta, ku sauke abin da ke kan ku nauyi, ku bada amana ga ma'abotanta, ku bawa dan kodago hakkinsa kafin zufansa ya bushe,

An karbo daga Abu Huraira Allah kara yarda a gare shi ya ce : (Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( wanda ya kasance yana da wani abu na zalunci da ya ci wa dan'uwansa na mutunci ne ko waninsa to ya warware daga gare shi  tun a yau kafin ya kasance dinari ko dirhami  in ya kasance yana da aiki na kwarai sai a dauka daga gare shi gwargwadon abin da ya zalunta, in kuma bai da kyawawa sai a dauka daga laifukan sahibin nasa sai a dora masa.) Buhari ne ya rawaito.

Ya ku bayin Allah! Ku cika alkawura da kuma yarjejeniya a hakkoki da muamala da suran abubuwa na cinikayya cikin hukunce hukunce da aka dora muku na hakkoki (Duk wanda ya cika abin da ya yi wa Allah alkawari to zai bashi lada mai girma).

 Domin hakan na cikin abin da ke karfafa zumunci da alaka, kuma ya kara kauna da soyayya, ya kuma kara aminci da tausayawa juna,

An karbo daga nu'uman dan Bashir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Lalle halal a bayyane ya ke kuma haram a bayyane ya ke a tsakanin su akwai wasu al'amura masu rikitarwa, da yawa daga cikin mutane basu san su ba, duk wanda ya tsoraci shubhohi to ya kubutar da addininsa da mutuncinsa, to duk wanda ya fada cikin shubhohi to ya auka cikin haram, kaman mai kiwo ne yana kiwo ne a bakin iyaka yana kusa da ya fada a ciki, ku saurara ! lalle kowane sarki na da iyakansa,ku saurara iyakan Allah shine abin da ya haramta, ku saurara lalle a cikin jiki akwai wata tsoka idan ta gyaru to dukkan jiki ya gyaru, idan ta baci to dukkan jiki ya baci, ku saurara ita ce zuciya).

Ku bi umarnin Allah, ku kame daga abin da ya haramta,ku nesaci shubhohi ku gyara niyoyi, ku sabonta zumunci da kauna da soyayya da alakoki.

Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

 

Huduba ta biyu

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya yalwata ni'imomi, ya kiyaye mu daga azaba, ya tula mana mamako na karamci.

Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

Ya ku bayin Allah ! ku ji tsoron Allah a sirrace da bayyane, ku lazimci Alkur'ani da sunnoni, ku nesaci alfahasha wanda ya bayyana da abin da ya boyu, ku nesaci shubuhohi, Da shubuhohi da sabuba na fitintinu ko Allah zai dauke muku bala'i da jarrabawa.

Allah Mai girma Allah Mai girma, Allah Mai girma,  Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

 

 Ya jama'ar musulmai! [ Ayyukan idi karama]

Allah ya shar'antawa bayinSa da su cike azumin ramadan da zakkan fidda kai, da sallar idi da kabarbari da ambato, girmamawa da godiya ga Allah bisa ni'imar cikan azumi da tsayuwa, hakika sharia ta wajabta zakkan fidda kai ga musulmai wanda tsarkaka ne ga mai azumi daga wass, da batsa kuma abinci ne ga miskinai, lokacinta shine kafin fita zuwa sallar idi, duk wanda ya jinkirtata to ya wajaba a gare shi ya gaggauta fitar da ita, duk wanda ya fitar kafin sallah to zakka ce a gare shi ,karbabba, wanda kuma ya fitar bayan idi to ita sadaka ce daga cikin sadakoki, An karbo daga dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi shi da mahaifin shi ya ce :(Manzon Allah ya wajabta zakkan fidda kai sa'i guda na dabino ko kuma sa'i guda na sha'iri bisa ga bawa da da na miji da mace da kuma yaro da babba na daga musulmai). Buhari ne ya rawaito.

Na daga cikin manyan alamomi na addini ga musulmai a ranar idi kabbarori, kuma sunna ne ga maza da mata, tun daga faduwan ranan karshe na ramadana Allah Madaukakin sarki ya ce ; (Kuma don ku kammala adadi kuma ku girmama Allah bisa shiryar da ku da yayi ko za ku gode)

Allah Mai girma Allah Mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

Allah Mai girma Allah Mai girma,  Allahu mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

 Ya ku musulmai!

Hakika uzuri ya killace ku a wannan yanayida aka samu kai a ciki da naku sa rashin halartar idi, to ku yi kwadayin yin ta a gidajenku, kuma lokacinta na farawa ne tum daga dagowar rana  har zuwa zawali, zai yi kabbarori bakwai araka'ar farko, a raka'a ta biyu kabbarori biyar, sai ya karanta suratul q wal kurani majid  ko sabihisma rabbika a raka'ar farko, a raka'a iktarabatissaatu wan shakkal kamar ko hal'ataka hadisul gashiya,ko da abin da ya sauwaka na daga kur'ani.

Allah Mai girma Allah Mai girma,  Allahu mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Allah Mai girma kuma Allah Mai girma kuma dukkan yabo  da godiya na Allah ne.

Ya taron mata!

 Lalle Allah Mai hikima ne a cikin gudanarwarsa, Masani ne cikinhalittunsa da mulkinsa, adalci ne al'amarinSa da hukuncinSa. Ya tura sako da bayani ya saukar littafi don mutane su tsaida gaskiya da mizani ta ti umarni da adalci  yin adalci  ya yi hani ga zalunci da tawaye hakki sai ya ce : (lalle na umartanku da ku maida amana zuwa ga ma'abotanta, idan kuka yi hukunci tsakanin mutane to ku yi hukunci da adalci.)  

Hakika Allah ya yi adalci tskanin maza ga mata a shariarSa da hukunce hukuncenSa ya kuma kebance kowannensu da abinda ya dace da halittarsa da kudurarSa da karfinsa ya daidaita tsakaninsu a komabayan haka na daga magana da karramawa da alkawarin lada da azaba da kuma dora nauyi na sharia.

Hakika musulunci ya bada kariya ga mace ya shar'anta hakkokinta ya daukaka matsayinta ya yi umarni da a bata kulawa a kuma ciyar da ita a mutunta tam a gyara a katange ta, hakika Annabi ya yi wasiya ga mace a Hajji bankwana, na daga cikin abin da ya ambata (Ku saurara ku yi wasiyya ta alheri game da mata, lalle su mataimaka ne a gre ku,, ku saurara lalle kuna da hakki a kan matayenku, su ma suna da hakki a kan ku,

Hakkinsu mata a kan ku  ku kyautata zuwa gare su cikin tufatar da su , Tirmiz ne ya rawaito.

Ya ku taron mataAllah!

Gudumawar da mace za ta bada ranar idi kamar gudumawar da na miji zai bada ne, zata yi tarayya wurin yada farinciki da karfafan dankon zumunci da afuwa da rangwami da gyara, da tsarkake zukata da karfafan alakoki da hamaka kauna da sada zumunci da yin ziyzrce ziyarce, da taimakawa talakawa da miskinai da marasa galihu da yin ma'arufi. (ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijinku  wanda ya halicce ku daga rai guda ya halitta masa matarsa daga gare shi ya kuma yada daga gare su maza masu yawa da mata, ku ji tsoron Allah da ku ke magiya da shi ku ji tsoron mahaifa, lalle Allah ya kasance a gare ku mai tsaro).

 

 


الجمعة، 22 مايو 2020

BANKWANA DA WATAN RAMADANA

Hudubar masallacin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na 29/9/1441

 

Hudubar farko:

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah tsira da amincin Allah su tabbata ga manzonSa

Bayan haka :

watan ramadana ya kare , wanda Allah ya bamu labari cewa wasu 'yan kwanaki ne kididdigaggu sai gashi ya wuce kaman kyabtawan ido, ya wuce kaman hasken walkiya, hakika zukata sun kasance sun yi shaukin zuwan shi, ga shi a yau kuma yana shelanta tafiya kuma yana juyawa yana mai ban kwana, ba abin mamaki ba ne a samu zuciya ta samu nau'uka daban daban na abin da ta ke ji na daga cikin labaran zuciya, muna jin falalan Allah a gare mu da ya shiryar da mu zuwa ga musulunci kuma ya sanar da mu alkur'ani, kuma ya riskar da mu ramadana ya taimake mu zuwa ga azumi da kuma tsayuwa, shi ne mai ni'imtarwa mai yawan kyauta, Allah Madaukakin sarki ya ke cewa:(suna goranta maka don sun musulunta ka ce kar ku min gori bisa musuluncin ku sai dai Allah Shi ne zai goranta muku saboda ya shiryar da ku zuwa ga imani) wan nan shi ne halin masu tafiya zuwa ga Allah suna shelantawa da dukkan ladabi mai girma da daukaka da rusunawa da jingina ni'ma zuwa ga ma'bocinta (sai ya ce wannan falala ne na Ubangijina) wan nan shi ne abin da ya dace duk wasu ayyukan kwarai a rufe da su, a fiskanci ayyukan girmamawa da su (Dukkan godiya a gare shi ta ke a duniya da kuma lahira hukunci  ma naShi ne kuma gare shi za ku koma) lallai Shi Madaukaki mai falala na hakika da dukkan wani abu mai kyau ga halittunSa ,

An karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ba wani ni'ma da Allah zai yiwa bawa sai bawan ya ce godiya ta tabbata ga Allah face sai abin da aka bashi zai fi abin da ya rika) wan nan shi ne yanayin halin 'yan aljanna a lokacin da suka kai kololuwa gurin buri da samun yardan Allah sannan suka shiga aljanna harsunan su na daga murya da godiyan Allah Madaukaki suna cikamake adu'arsu da shi da ayyuka na kwarai , Allah Madaukakin sarki ya ke cewa (sai suka ce dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya tafiyar mana da bakin ciki lallai Ubangijin mu mai yawan gafara ne kuma mai yawan godiya)(wanda ya bamu masauki a gidan dawwama daga cikin falalanSa , ba wani gajiya ko wahala da zai shafe mu)

Gaggautawa zuwa ga godiyan Allah da kyautata yabo bisa ga ni'mominsa a yayin kammala wannan watan falala shi ne manhaji na musulunci da kuma taujihin alkura'ani , Allah Madaukakin sarki ya ce: (Domin ku cike adadin kuma ku girmama Allah bisa ga abin da ya shiryar da ku ko za ku gode) ya zo a hadisi wanda Bukari da Muslim suka rawaito shi daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Mai azumi nada farin ciki guda biyu , farin ciki guda yayin shan ruwansa farin ciki guda kuma yayin haduwa da Ubangijinsa )

 Tabbatar da ma'ana ta yabo da godiya ta watan ramadana alama ce ta kyautata zaton bawa ga Allah da kuma fatansa cewa Allah ya karba mishi abin da ya yi na da'a kuma ya kankare mishi tawaya da aka samu a aiki da kuma gafala na daga halaka da kuma jahilci , yayin sauke nauyi , hakika ya zo a hadisul kudusi (Ni ina inda bawa na ya zaceNi) idan bawa ya kyautata zato ga Ubangijin shi to ya lizimta a gare shi da ya yawaita addu'a don Allah ya karba mishi da'an shi yana mai ladabi tare da Allah da neman tabbatar da zaton shi da gaskiyan fatan shi.

Hakikanin godiya a karshen watan ramadan shi ne gyaruwan aikin bawa da lazimtan shi ga da'a ga Ubangijin shi da gaggautawa zuwa ga wurin samun yardar Allah , Allah Mabuwayi da daukaka ya ke cewa(ku yi aikin godiya ya ku mutanen Dauda , kadan ne daga cikin bayi Na su ke masu godiya) Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kan yi tsayuwan dare har kafafuwarsa su kumbura sai a ce da shi kai da Allah ya gafarta maka abin da ya gabata na daga zunubanka da abin da ya jinkirta? Sai ya ce : (Ashe ba zan zama bawa mai yawan godiya ba ?).

Musulmi wanda Allah ya haskaka zuciyarsa a cikin watan ramadana ya kara fadada da imani ya sha daga mabubbuganSa, ya koshi daga tabkinSa, ya yi tsayuwan daren Sa , ya azumci wuninSa , to ba zai gushe ba yana tsere zuwa ga ayyuka na da'a har bayan watan ramadana, ba zai yi sakaci ba wurin neman ayyuka na ganima wanda ya ci daga dadinta a cikin azumin shi da kuma sallarsa da biyayyarsa, duk wanda ya dandani dadin ganawa da Allah ya kuma dandani dadin imani a ramadana natsuwa da kwanciyar hankali ya kwararo a cikin zuciyarsa to ba zai  yi sakaci ba wurin barin wannan sa'ada din ya tsere mishi, zai zame ne zuciyarsa  na ta'allake da Ubangijin shi kuma zai zame yana ta debe kewa da Ubangijin shi, kuma tare da Allah kuma zuwa ga Allah, idan lokacin ramadana ya kare lallai lokuta na alheri na bibiyan juna falaloli na Mai rahama ba a'a iya iyakance su lokuta na da fifiko wurin kima da kuma lada a duk lokacin da aka samu nunfasawa na wani lokaci da  dama ta samu to mai hankali zai yi gaggawa ne ya tashi zuwa gare ta, mai komawa zuwa ga Ubangijin shi zai ribace ta, Allah Madaukakin sarki ya ce: (ka yi sujada ka kusanto)

A dukkan safiya da gari zai waye fage ne na yin hailala da kuma godiya da kabarbari da kuma istigfari.

 A dukka yammaci in ya sake duhun shi  to lokaci ne na ganima wanda zai  farauce shi, wanda ya san kimanta shi ne masu yawan ibada a cikin dare wanda sassan su ke nesatan makwanci suna rokon Ubangijinsu suna bisa halin tsoro da  kuma tsammani.

 Wadanda suka san hakikanin rayuwa da kuma kimanta suna da iko lokutan su su zama duka lokuta ne na ayyukan alheri, za su kuma rika  kai komo cikin nau'uka na mubadara ta hanyan ayyuka na kwarai da, yada ilimi da taimaka wa mabukaci da girmama bako da kuma shafa kan maraya da kuma gyara da gina masallaci da kuma yalwata nasiha da karfafan tsangayoyi  na alkur'ani  da tarayya wurin gidauniya  na alheri da kuma aiki bisa habaka kasa da kuma daga al'uma, Allah Madaukakin sarki ya ce: (Duk wanda ya ke son lahira kuma ya yi aiki don ita irin aikinta a halin yana mumini to wadan nan ayyukan su za su zama abin godiya).

Musulmi ya kan hadu da wani nau'i na bala'i ko annoba a zuciyansa ko iyalansa idan ya godewa Allah kuma ya nemi ladan musiban a wurin Allah ya yi imani da abin da Allah ya hukunta ya kaddara to Allah sai ya girmama mishi ladan shi, ya maida mishi da mafi alheri kuma ya rubuta masa rahama da gafara da shiriya Allah Madaukakin sarki ya ce:( lallai za mu  jarabe ku da wani abu na tsoro da yunwa da tawaya na daga dukiya da rayuka da 'ya'yan itace, ka yi albishir ga masu hakuri wadanda idan musiba ta same su sai su ce : ga Allah muke kuma gare shi za mu koma, wadan nan suna da wani kyakkyawan ambato daga Ubangijinsu da kuma rahama kuma lallai wadan nan su ne shiryayyu)

Haka na zuwa ne a wani yanayi na annoba wanda ya sanya abu mai motsi ya zama ya natsu ya mosta kuma abin da ya ke zaune gu daya, ya yi yawo a doron kasa ya sanya zukata cikin tsoro da  idanuwa kuru kuru na daga abin da jiki ke kwanta dama, da abubuwa da ke faruwa na kamuwa da cututtuka daya bayan daya da ake gani a wan nan yanayi na kunci mai tsanani akan fiskanci ludufin Allah boyayye  rahamomin Allah su kewaye mu sai Allah ya kiyaye bayi daga wan nan annoba mai ragargazawa ya katange kasa daga rashin lafiya mai halakarwa ya dauke bakin ciki daga al'uma tasirin shi a doron kasa ya zamana dan kadan ne san nan ya tunkude shi da falalanSa ga Ubangiji wani abu ne da ba mai wahala ba.

wannan shi ne yaye bakin ciki mai girma, zai sanya idin mu ya zama zai zo gare mu nan kusa cikin mafi kyan idi kuma wanda ya fi farin ciki da kuma jin dadi domin tufafin da za mu sa sabo a cikin idi shi ne na tsoron Allah da kuma lafiya, abin hawa mai laushi da za mu hau shi ne na aminci da zaman lafiya shakatawa da walwala shi ne mu shaki tacecciyar iska wacce ta kubuta daga wan nan annoba da kuma farin ciki na haduwan iyalai da 'yan uwa da makusanta da kuma makwabta, shi ne a samu labarin suna cikin koshin lafiya suna cikin ni'ma, shin bayan wannan ganima akwai wani abu kuma na nema ? ku tafi a doron kasa ku yi dubi zuwa ga halin da wadan su su ke ciki, domin ku san kaye na hali da daukaka da ni'ima a kuma kima na ludufi, abin mamaki da girman Allah da rahamarSa Mahalicci, lallai  halarto da ni'ima da gode wa Allah da harshe da zuciya yana sanya karin samun rahama da ludufi .

Huduba ta biyu:

Musulmi yana cika watan ramadana ne yana mai godiya da farin ciki saboda riskan cikan shi yana lullube da rahamar Allah yayin shan ruwan shi ni'man Allah da falalanSa yana mai gaggawa zuwa ga jefa farin ciki a al'umansa, sai ya fitar da zakkan fidda kansa domin tsarkakewa ga mai azumi daga kazanta da wasa kuma ya farantawa talakawa rayi ya wajaba ga musulmi haka kuma ga duk wanda musulmi ke daukan nauyin shi, mikdarin shi shi ne sa'i daga cikin abincin gari.

An karbo daga dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi shi da mahaifin shi ya ce :(Manzon Allah ya wajabta zakkan fidda kai sa'i guda na dabino ko kuma sa'i guda na sha'iri bisa ga bawa da da na miji da mace da kuma yaro da babba na daga musulmai kuma ya umarni da a fitar da shi kafin fitan mutane zuwa sallah). Ya halatta gabatar da shi da rana daya ko rana biyu saboda abin da aka rawaito daga ibnu Umar cewa sun kasance suna badawa kafun fita eidi da rana daya ko rana biyu.

Tare da dakatar da sallah da aka yi a masallatai da kuma wuraren sallah na idi saboda wannan annoban an shar'antawa musulmai sallan idi a gidajensu a jama'a ko kuma a daidaiku, kuma za a fara kabarbari ne tun daga faduwan ranar daren idi sannan idan aka sallace ta a gida to sai a yanke kabarbarin tare da shiga salla. Ana sallatanta sifanta ne rak'a biyu ba tare da huduba ba za a yi kabbaran harama a farko sannan a yi kabarbari guda shida bayanta, a rak'a ta biyu kuma za a yi kabbara na tashi sannan kuma a yi kabarbari guda biyar bayanta , lokacin sallar idi na fara shigowa ne tun daga bayan hudowar rana da kuma bullowanta da mikidarin mashi biyu ko kuma da mikidarin abin da bai gaza minti ashirin ba kuma zai ci gaba lokacin nata har zuwa lokacin sallan walaha kafin shigan lokacin sallan azahar da kusan sulusin sa'a, hakika hani ya zo daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na hani ga sallah a lokacin da rana ke hudowa. 

Allah ya karba mana ayyukanmu na kwarai da ayyukan ku na kwarai.            

      

 


الأربعاء، 20 مايو 2020

FALALAR SALLAR DARE DA KARATUN ALKUR'ANI

 

اللغة : الهوسا

التاريخ 8/9/1441هـ

Hudubar masallacin Annabi  na shaikh Abdullah Bin Abdurrahman Albuaijan

8/9/1441 AH 1/5/2020 AD

 

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya sanya da'a gare shi ya zama dalili ne na samun yardarSa, ya sanya yardarSa kuma a matsayin dalili ne na rabauta da AljannarSa ya kuma datar da mumunai zuwa ga bauta masa, sai suka kauracewa ababan jindadi da sha'awe sha'awensu suka fifita samun yardarSa.

Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya abin godiya abin girmamawa, shaidawar da zan hadu da Allah  da ita a halin ina ni kadai na tilo. Na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne Allah ya isa Mai shaida. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci abin kari mai yawa.

Bayan haka, lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabinmu Muhammad dan Abdullah, kuma sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta,

ya ku bayin Allah ina muku wasiya da ni kai na da tsoron Allah Mabuwayi da daukaka, to ita ce wasiyar Allah ga mutanen farko da na karshe, (Hakika mun yi wasiyya ga wadanda muka baiwa littafi kafin ku da ku kan ku da ku ji tsoron Allah).

    Ya ku bayin Allah! Biyayya ga Allah ita ce mafi alherin ganima da abin ribata, kuma yardarSa ita ce mafi alherin riba da abin nema, Aljanna an kewaye ta da abubuwan ki, wuta kuma an rufe ta da abubuwan sha'awa, abin sani za ku samu ladan ku cike a ranar alkiyama, to duk wanda a ka nesatar daga wuta aka shigar Aljanna to hakika ya rabauta.

Ya ku masu azumi!

Allah ya karbi biyayyarku, ya gyara halayenku, ya datar da ku cikin abin da ya rage a wannan wata, ya kuma rubuta muku tabbatuwa  bisa da'a a gare shi a tsawon ranakun zamani.

Ya ku jama'ar musulmi!

Ramadan wata ne na ibada da tuba, watan neman kusanci ne da komawa ga Allah, wata ne  na tuba da dawowa ga Allah da ikhlasi da khushu'i da sujudi da ruku'i, wata ne na azumi da tsayuwa, wata ne na biyayya  da kyautatawa da karatun Alkur'ani.

Ya ku masu azumi!

Karbabbiyar ibada na da tasiri a imani, tasirinta na ga zuciya da rai , gyara niyya da tsarkake rayuka da takawa da ikhlasi da khushu'i  ga Allah Mafi daukaka.

Tasirinta da ke gabbai da jiki; kamewa daga ayyukan sabo da abin da aka haramta da jurewa gun aikata ayyukan alheri da da'a.

To ku sa Allah a idanuwanku cikin ayyukanku, to shi Allah bai dubi ga surorinku ko jikunanku sai dai yana dubi ne ga zukatanku ne da ayyukanku , so da yawa wani mai azumin baida wani abu a azuminshi sai kishin ruwa da yunwa da gajiya sau da yawa wani mai tsayuwan dare bai da wani abu na daga tsayuwan shi sai hana ido barci da wahala.

Ya jama'ar musulmai :

Lallai Allah ya saukar da Alkur'ani a watan azumi  sai yace: (watan ramadana ne wanda aka saukar da Alku'ani yana shiriya ga mutane da hujjoji bayyanannu daga shiriya da rarrabewa) kuma Allah ya ce : (lallai mu muka saukar da shi a daren lailatulkadri ) (wa ya sanar da kai menene lailatulkadri)(lailatul kadri mafi alheri ne  daga wasu watanni dubu) (Mala'iku da Ruhi suna sauka a cikinsa da izinin Ubangijinsu saboda kowane umurni) (sallama ne shi daren har fitar alfajiri) kur'ani ya sauka a daren lailatul kadari na  ramadana zuwa baitul izza a sama ta duniya san nan ya sauka zuwa doron kasa a rarrabe cikin shekaru ashirin da uku  gorgodon abubuwan da ke faruwa da kuma sabuban sauka, to karatun kur'ni a watan da aka saukar da shi , na daga cikin mafificin ayyukan kusanci  saboda haka ne Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana fiskantan karatun kur'ani a cikin watan ramadan Jibrilu ya kasance yana zuwa mishi a ko wani dare a cikin watan ya yi bitan kur'ani da shi .

An karbo daga Ibnu Abbas Allah ya kara yarda a gare su ya ke  cewa:( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance mafi kyauta cikin mutane kuma kyautansa ya  fi kasancewa ne a watan azumi a yayinda ya ke haduwa da Jibril , jibrilu ya kasance yana haduwa da shi a ko wani dare na ramadan sai ya yi bitan Alkur'ani da shi to Annabi na da yawan kyautan alheri a yayin da ya hadu da shi sama da iska da ake turowa) .

To ya ku bayin Allah ku riki karatun Alkur'ani  ku karanta shi da tajwidin shi kuma ku nemi fahimtar ma'anoninsa ku yi tadabburinsa  , to an karbo daga abdullahi dan Mas'ud Allah ya yarda da shia ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbat a a gare shi ya ce:(Duk wanda ya karanta harafi  yana da kyakkyawa , kuma kyakkyawa na da kwatan kwacinta guda goma, ba zan ce alif lal mim harafi ne sai dai alif harafi ne lam harafi ne mim harafi ne) Tirmizi ne ya rawaito shi kuma ya inganta shi , kuma aga gare shi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(lallai wan nan alkur'ani wani abin ci ne to ku koya daga wan nan abincin iya iyawan ku lallai wan nan alkur'ani igiyan Allah ne kuma haske ne mai bbayyanawa  komin kuma waraka ne mai amfani kuma kariya ne ga wanda ya yi riko da shi da kuma tsira ga wanda ya bishi ba zai zame ba har ya zama abin zargi, ba zai kuma karkace ba har ya zama abin mikarwa ,kuma abubuwan mamakinsa ba za su kare ba kuma yawan maimaita shi ba zai tsufar da shi ba to ku yi tilawarsa , don lallai Allah zai ba ku lada bisa ga tilawarsa kyakyawa goma ga ko wani harafi amma ni ba zan ce alif lam mim sai de da: alif, da lam, da mim …. )  Dabrani ne ya rawaito .

An karbo daga Abdullahi dan Umar Allah ya kara yarda a gare su ya ce : Mazon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Ana cewa ga ma'abocin Alkur'ani a ranar alkiyama , ka karanta ka haura kuma ka yi tilawa kamar  yanda ka kasance kana tilawa a duniya domin matsayinka tana a'ayan karshe da ka karantata) Tirmizi ne ya rawaito .

To ku karanta Alkur'ani bayin Allah kar ku kaurace masa , na hore ku da kar  ku da yankewa  alkur'ani, na hore ku kada manta  Alkur'ani don hakan hasara ne da nadama, da juyawan hankali ne da abin zargi.

Muna neman tsarin Allah  da mu kasance  cikin wadan da  Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  zai kai karan    su wurin Allah ,   sabo da kauracewa kur'ani da suka yi :-  (kuma Manzo ya ce : Ya Ubangijina! Lalle mutanena sun riki wannan Alkur'ani abin kauracewa).

Ya ku bayin Allah ! Mafi girman ambaton Allah Mabuwayi da Daukaka shine Alkur'ani,  barin karanta shi kaura ce masa ne  da kuma juya masa baya Allah madaukakin sari ya ce :- (Duk wanda ya  kauda kai daga ambato na  (Alkur'ani) , to lallai ne rayuwa mai kunci ta tabbata a gare shi  ,kuma  muna tayar da shi a ranar kiyama yana makaho.   Ya ce  Ubangiji '' don me aka tayar da ni makaho , alhali kuwa na kasance mai gani ?  . Y a ce '' kamar wancan ne ayoyin mu suka je maka  sai ka mance su ,  kuma kamar haka a yau ake mance ka.

An karbo daga Abu Musa Al-ash'ari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce:- Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-    (misalin muminin da ya ke karanta kur'ani  kamar misalin tanjarin ne kamshin shi na da dadi dandanon shi ma na da dadi ,   kuma misalin muminin da baya karanta kur'ani  kamar misalin dabino ne, bai da kamshi kuma dandanon sa na da dadi , kuma misalin munafiki da yake karanta kur'ani kamar turaren wuta ne  kamshin shi na da dadi kuma dandanon shi na da dadi) Buhari da Muslum ne suka rawaito .Hakika Magabata sun kasance suna kwadayin karanta kur'ani  da lura da ma'anonin shi  suna da wuridin da suke yi ko wani rana  ba sa yankewa daga gare ta musamman a wannan watan. 

Watan  ramadana da aka saukar da alkur'ani a cikin ta , to ku kwadaici yawaita tilawar sa kada  na'urori na zamani da shirye-shirye masu shagaltarwa su yi gogayya da shi  

  YA KU BAYIN ALLAH:

A halin kuna wannan yanayi to ku nemi magani da waraka   da karatun alkur'ani  domin shi waraka ne da rahama ga muminai .

 Ku dukufa a kan shi a gidajen ku, a lokacin da ku ke kadaicen ku ko a bayyanen ku , ku karanta shi kuma  ku saurare shi a sauran lokutan ku .

Kuma wanda hakan ya mi shi nauyi ,  ko karanta kur'anin ya gagara a gare shi  to, ya saurari tilawar sa , domin shi ma mai sauraron abokin tarayyan mai karantawa ne a lada da sakayya .

Allah yana cewa : (Idan an karanta Alkur'ani to ku  saurare shi  ku yi shuru ko za ku samu rahama)

 

 

HUDUBA TA BIYU

Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah Masanin gaibi Mai yafe zunubai da sauran kusakurai da laifuka , kuma Mai yaye bakin ciki yana  shimfida hanunSa da dare don mai laifin yini ya tuba ,  kuma yana shimfida hanunSa da rana don mai laifin dare ya tuba .

 

 

YA KU BAYIN ALLAH:

Ku yiwa kanku hisabi kafin a mu ku  hisabi , kuma ku auna ayyukanku  kafin a aunaku  kuma kafin ayi kira gare ku : lallai su dinnan ayyukanku ne muke  kididdige  mu ku , sa'annan mu cika muku ita  duk wanda ya samu alheri to, ya godewa Allah , kuma wanda ya samu koma bayan haka to, kada ya zargi kowa sai kansa.   

(Duk wanda ya aikata  wani aiki kyakkyawa kwatankwacin kwayar  zarra zai gani, haka  kuma duk wanda ya aikata mummuna kwatankwacin kwayar zarra zai gani) 

 

 

YA KU BAYIN ALLAH:

Tsayuwar dare kusanta ne ga Allah  ba mai kiyaye ta sai muminai , haka kuma sunna ce da ba mai juriya  a kanta sai masu tsoron Allah ,   (Wadan da suke kwana don Ubangijinsu  suna  masu sujada da tsayuwa )  

Wadan da Allah ya ce  game da su :- (sasannin su  na nisanta daga wuraren  kwanciya ,  suna  kiran  Ubangijin su bisa ga tsoro da tsammani,  kuma suna  ciyarwa daga abin da muka azurta su . )

Sabo da haka  wani rai  bai san  abin da  aka boye  musu ba , na sanyin idanu , domin  sakamako  ga abin da suka kasance  suna aikatawa .

Wadan da Allah ya daukaka su (Lalle masu takawa suna a cikin lambunan ita ce  da maremari. Suna masu karbar abin da Ubangijinsu ya ba su ,  sun kasance  masu kyautatawa  a gabanin  haka (a duniya).  Sun kasance a lokaci kadan na dare suke yin barci . Kuma a lokutan asuba suna ta  yin istigfari)

Bayin Allah lokacin yin Tahajjud cikin dare  shi ya fi sabo da lokuta irin na kusanci Allah Madaukakin sarki ya  ce :- (Lalle ne tashin dare  shi ne  mafi  tsananin natsuwa ,  kuma mafi daidaituwa  ga magana )

Kuma lokaci ne da a cikin shi  Allah yake saukowa zuwa  saman duniya yana kira; shin akwai mai

roko na amsa mishi, shin akwai mai neman gafara na gafarta masa ? shin akwai mai tuba na karbi tubansa ? , kuma lokaci ne wanda ake bude kofofin sama ana amsa adu'a.

 karatun kur'ani shi ne mafi girman kusanci da munini zai  nemi kusanci da shi a wan nan lokaci, maganan Allah da kuma salla, mafi lokacin da kuma bawa ya fi kusa da UbangijinSa shi ne a lokacin da yake sujada (shin, wanda  ya ke mai tawali'u sa'o'in dare , yana mai sujada kuma yana mai tsayi ga sallah yana tsoron  lahira kuma yana fatan rahamar ubangijinSa  ).

Mafificin tsayuwa shi ne tsayuwan dare (sallar nafila) na ramadana, shi ne ya fi karfi a cikin sunnoni kuma na daga cikin mafificin nafilfilu, to an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Duk wanda ya yi tsayuwan ramadana yana mai imani kuma da neman lada za a gafarta mishi abin da ya gabata na daga zunuban shi kuma wanda ya yi tsayuwan lailatul kadri yana mai imani da neman lada za a gafarta mishi abin da ya gabata na daga zunubansa) ya zo a ckin sahihu muslim daga Urwatu dan Zubair cewa Ummul mu'minina A'isha Allah ya kara yarda a gare ta ta bashi labarin cewa:( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fita cikin dare sai ya yi salla a masallaci , sai wasu mutane su ka bi sallansa suka yi koyi da shi sai  da aka wayi gari sai mutane suka bada labarin hakan sai mutane suka hallara   sama da wadancan sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fito a dare na biyu sai mutane suka yi koyi da sallanSa sai mutane suka wayi gari suna ambaton hakan sai mutane suka cika masallaci a wannan dare na ukun sai Annabi  ya fito ya yi sallah sai mutane suka yi koyi da sallan shi yayin da aka zo dare na hudu masallacin ya kasa daukan jama'a Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai bai fito ba har zuwa lokacin da aka fita zuwa sallan asubahi yayin da aka kare sallan asuba sai ya juyo ya fiskanci mutane san nan ya yi Tashahhudi (Ashhadu alla ilaha illaallah wa ashhadu anna muhammadarrasulullah) sai ya ce : bayan haka lallai bai boyu mini ba sha'aninku na daren jiya sai de na tsoraci kar a farlanta muku sallan dare ne ku gagara yinta).

Mutane sun kasance bayan haka suna sallatanta  jama'a kashi –kashi, kuma  a daidaiku har zuwa lokacin da Umar dan kaddabi Allah ya kara yarda a gare shi ya hada su a mai karatu guda daya ,

An karbo daga Abdurrahman dan Abdu Alkari cewa ya ce : na fita tare da Umar dan kaddabi a cikin watan ramadana zuwa masallaci sai ga mutane su na warwatse a rarrabe wan nan na salla shi kadansa wasu jama'a  na  koyi da sallan sa , sai Umar ya ke cewa wallahi ; ni ina ganin da kun hada wadan nan mutanen bisa ga makaranci guda daya da zai fi dacewa sai ya hada su ga Ubayya dan ka'ab .

Bayan haka ya ku bayin Allah duk wanda niyarsa ta kasance ta gaskiya gurin azama ga yin salla a daya daga cikin masallatayya biyu masu alfarma,  ko wasunsu na daga masallatayya , amma ; hakan ya gagara yiwuwa a gare shi ko wani abu ya yi shamaki tsakanin shi da hakan sai ya yi salla a gidan sa to lallai ladansa na nan cikakke a rubuce insha Allahu ; domin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa:( lallai abin sani kawai ga ko wani mutum yana da abin da ya nufa ) kuma ya ke cewa :(Duk mutumin da ya himmatu da aikata wata kyakkyawa bai samu aikatata ba to za a rubuta mishi kyakkyawa guda) Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa : (Idan bawa ya yi tafiya ko ya yi rashin lafiya to za a rubuta mishi kwatankwacin abin da ya kasance yana aikatawa a halin yana mazaunin gida mai lafiya) .

Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa yayin da ya kusanto Madina yana dawowa daga yakin tabuka( lallai a garin Madina akwai wasu mutane da ba ku tafi wata tafiya ba ko kuma kuka keta wani kwari ba face kun yi tarayya da su a lada sai suka ce: ya Manzon Allah ahalin suna Madina ? sai ya ce : E, suna Madina uzuri ne ya hana su )

 to ku yi albishir     

 

  

  

   

ABUBUWAN MAMAKI GUDA 4

 

 
الوصف: cbc250ed-6a0e-4037-8d54-a9eb3d0a0577                                                                                                                           

ترجمة الخطبة

اسم المترجم :أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاريخ : 15-9-1441هـ

 

Hudubar Masallacin Annabi Na shaikh Ahmad Dalib 15/9/1441AH/7/5/ 2020AC

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne. tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da aminci tabbatacce.

(Ya ku wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face kuna musulmai)

(ya ku mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji tsoron Allah da ku ke roko da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance mai tsaro ne a kan ku.)

(ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta mai girma.)

 

Bayan haka, lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabinmu Muhammad, kuma sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta.

Ku sani ya ku bayin Allah lallai ba makawa bin hanyar zuwa lahira dole sai da ilimi wanda ke yaye wa zuciya makanci, da kuma aiki wanda zai dauke wa mutun shamaki na basira da iklasi wanda zai kubutar da mutun daga hasara na faduwa da kuma tsoro wanda zai sa mutun ya kiyaye bala'o'i na rudi.

 Dukkan halittu matattu ne sai malamai, malamai kuma dukkansu masu bacci ne sai masu aiki, masu aiki kuma dukkansu rudaddu ne sai wanda suke masu  iklasi, su kuma masu iklasi suna cikin wani hadari mai girma (shin , kuma wanda ya kasance matacce, sa'an nan Muka rayar da shi Muka sanya wani haske dominsa, yana tafiya da shi , yana zama kamar wanda misalinsa yana cikin duffai , shi shi kuma ba mai fita ba daga gare su ? kamar wancan ne aka kawata wa kafirai abin da suka kasance suna aikatawa).

Abin mamaki dukkan mamaki ga mutumin da ya ke aiki amma bai damu da sanin abin da ke gaba gare shi ba na daga al'amari ko labari, ko kuma ya nemi sanin abin da zai zo bayan mutuwa gaba gare shi ta hanyar nazari da dubi ga dalilai da kuma wa'azuzzuka da ayoyi da kuma gargadi ba. (shin ba su yi dubi ba a cikin mulkin sammai da kasa, da kuma abin da Allah ya halitta daga kome kuma akwai tsammani kasancewar ajalin su, hakika ya kusanta? to da wani labari a bayansa su ke yin imani) ( wanda Allah ya batar, to babu mai shiryarwa a gare shi kuma yana barin su a cikin batarsu suna dimuwa) abin mamaki ya kaiton makanci irin na zuciyarsa (shin to, ba su yi tafiya ba a cikin kasa domin zukata wadanda za su yi hankali da su da kunnuwa da za su yi saurare da su, su kasance a gare su ? domin lallai ne idanu ba su makanta, amma zukata wadanda ke a cikin kiraza su ke makanta).

Abin mamaki dukkan mamaki ga malamin da ba ya wa'azantuwa da abin da ya sani na yakini sai abin da ya ke gaba gare shi na daga musibu masu girma da kuma abubuwa na cikas da ke gaba masu fadi ya tsorata daga kasala ya gargadu zuwa ga jahadi da kuma aiki (ka ce, shi (Alkur'ani) babban labari ne mai girma. ku, masu bijirewa ne daga gare shi) ya kaiton hijabin idanuwansa (Bone ya tabbata ga masu nakkasawa) (wadanda su ke idan su ka auna daga mutane suna cika mudu)(kuma idan sun auna musu , da zakka , ko da sikeli , suna ragewa)(shin wadancan ba su tabbata cewa lallai su , ana tayar da su ba?) (domin yini mai girma) (yinin da mutane ke tashi zuwa ga Ubangijin halitta).

Abin mamaki dukkan mamaki, ga mai aiki wanda ya sarayar da iklasi ya sarayar da mabudin samun kubuta ta hanyar lalata zuciyarsa  (ka ce, ''Ni mutum ne kawai kamarku, ana yin wahayi zuwa gare ni cewa : lallai ne abin bautawarku Abin bautawa guda daya ne, saboda haka wanda ya kasance ya na fatan haduwa da Ubangijinsa, to sai ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bautawa Ubangijinsa.) kaito da hasaran faduwan mutum ya rasa riba! (kuma aka halaka dukkan 'yayan itacensa, sai ya wayi gari yana juyar da tafunansa biyu , saboda abin da ya kashe a cikinta , alhali ita tana kwance a rassanta, kuma yana cewa , kaitona dadai ban tara wani da Ubangijina ba!) (kuma wata jama'a ba ta kasance a gare shi ba, wadanda ke taimakon sa baicin Allah, kuma bai kasance mai taimakon kansa ba) abin mamaki dukkan mamaki ga mai iklasi wanda ba ya duba zuwa ga mua'amalar Allah Madaukaki tare da masoyanSa da ManzanninSa wadanda su ne masu nusar da halittu daga wurin Allah sai ya halarto da tsoronsu, ga masoyi na farko yana cewa (kuma a lokacin da Ibrahim ya ce ,''ya Ubangijina! Ka sanya wannan gari amintacce, kuma ka nisata ni ni da 'ya'yana daga bautawa gumakai) ya na shaida tsoron su masoyi cikakke yana ce da shi (kuma an yi wahayi zuwa gare ka da kuma zuwa ga wadanda su ke gabaninka , ''lallai idan ka yi shirka hakika, aikinka zai baci ,kuma lallai za ka kasance daga masu hasara.)

To ya kai mai rudin kansa (To, a yau ba za a karbi fansa daga gare ku ba . kuma ba za a karba daga wadanda su ke kafirai ba makomarku wuta ce , ita ce mai dacewa da ku kuma makomarku din nan ta munana ) (shin, lokaci bai yi ba ga wadanda su ka yi imani zukatansu su yi tawaliu ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya ? kada su kasance kamar wadanda aka baiwa littafi a gabanin haka sai zamani ya  yi tsawo a kansu , saboda haka zukatansu su ka kekashe, kuma masu yawa daga cikinsu fasikai ne) .

Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin Alkura'ani mai girma .

Huduba ta biyu

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya isa, tsira da aminci su tabbata ga Annabi zababbe da alayenSa da sahabbanSa ma'abota da'a da kuma cika alkawari, da kuma wanda ya bi su da kyautatawa kuma ya bi sawu, lallai Allah ya kira ku da sunan imani kuma da tsoronsa ya kira ku Ya gargade ku game da faduwa irin na mantuwa da kuma radadi irin na hasara ya kuma sanar da ku tserewan yanayi da halaye a ranan komawa, girman tasirin Alkura'ani da an saukar da shi ne a kan duwatsu , ya kuma sanar da ku da kamalan sunayenSa Madaukaki da kyawawa.

(ya ku wadanda su ka yi imani ! ku bi Allah da takawa , kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da takawa lallai Allah , Mai kididdigewa ne ga abin da kuke aikatawa) (kuma kada ku kasance kamar wadanda suka manta Allah shi kuma Ya mantar da su rayukansu, wadannan su ne fasikai) ('yan wuta da 'yan Aljanna ba su daidaita . 'Yan Aljanna su ne masu babban rabo) (Da Mun saukar da wannan Alkura'ani a kan dutse, da lallai ka ga dutsen yana mai tawali'u, mai tsatsagewa saboda tsoron Allahh , kuma wadancan misalai Muna bayyana su ne ga mutane, da fatan za su yi tunani) (wanda ya saukar da Alkur'ani shi ne Allah, wanda babu wani abin bautawa face shi, masanin fake da bayyane, Shi ne Mai rahama Mai jin kai) (Shi ne Allah, wanda babu abin bautawa face Shi Mai mulki Mai tsarki, aminci Mai amintarwa , Mai tsarewa , Mabuwayi , Mai tilastawa, Mai kamun kai, tsarki ya tabbata a gare shi daga abin da suke yi na shirka da shi) (Shi ne Allah, Mai halitta Mai ginawa, Mai surantawa, yana da sunaye masu kyau, abin da ke a cikin sammai da kasa suna tsarkake Shi , kuma Shi ne Mabuwayi , Mai hikima).

Tsarki ya tabbata gare Shi Madaukaki bai halicce ku don wasa ko kuma don kazanta ba sai dai kawai domin ku nemi gafaran Shi kuma domin a muku  rahama (shin, to kun yi zaton cewa Mun halitta ku ne da wasa, kuma lallai ku zuwa gare mu ba za ku koma ba?) (Allah Mamallaki, Gaskiya, Ya daukaka babu abin bautawa face Shi, Shi ne Ubangijin Al'arshi , mai daraja) (kuma wanda ya kira tare da Allah wadansu abubuwan bautawa na daban , ba yana da wani dalili game da shi (kiran) ba , to hisabinsa yana wurin Ubangijinsa kawai lallai ne kafirai ba su cin nasara) (kuma ka ce, ''Ya Ubangijina ! Ka yi gafara Ka yi rahama kuma Kai ne Mafi alherin masu rahama).