|


التاريخ
:1/9/1441هـ
اللغة :
الهوسا
Hudubar Masallacin Annabi 1/9/1441AH 24/4/2020 AD shaikh Salah Bin Muhammad Al budair
Hudubar farko
Dukkan
yabo da godiya sun tabbata ga Allah,bisa ga riskan watan ramadan, godiyan da
zata cika ni'imarSa da kyautarSa, ina gode masa bisa abin da ya kwararo ya
yalwata na alheri, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya
ke, ba shi da abokin tarayya, ba wani abin bauta bisa cancanci koma bayanSa,
kuma na shaida Annabinmu kuma shugabanmu
Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne. Kuma AnnabinSa kuma zababbe ne, abokin ganawarsa masoyinSa
kuma yardajjenSa, kuma zababbenSa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
da iyalan shi da sahabbansa, har abada muddin safiya na bayyana haske na fitowa.
Bayan
haka
Ya ku
masu azumi!
Ku ji
tsoron Allah ta hanyar yin aiki zuwa ga neman yardarSa, da nesatan saba masa, (Ya ku wadanda suka bada gaskiya an wajabta muku azumi kamar
yadda aka wajabtawa wadanda suka gabace ku ko zaku samu takawa).
Wannan
watan ramadana ne ga ta ta kunno, wata ne na busowan alheri ga ta ta bullo, ga haske mai ban kaye ya sauka, ga shaidan
abin jefewa ya kaskanta, An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare
shi ya ce, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Idan ramadan ya shigo sai a bude kofofin Aljanna, a rufe
kofofin jahannama a kuma daure shaidanu) Buhari da muslim ne suka rawaito. A
riwayar Muslim (a bude kofofin rahama) a riwayar Tirmizi ( sai a rufe kofofin
wuta ba za a bude ko kofa guda ba, a kuma bude kofofin aljanna ba zaa rufe ko
da kofa guda ba daga cikin su).
Allah Mai girma wani irin abin
farinciki ne wannan ! wani irin abun kaye ne wannan! Wani irin kyauta ce
wannan! Wani irin kawa ne wannan! Wani irin daukaka ce wannan!
Ya ku
musulmai !
Barkan
ku da watan ramadana da ke cike da
kamshi, mai kore gurbacewa, dukufaffen annoba ko dare mai saibi ba zai iya
gurbata hasken shi da kayen shi da daukakan shi ba, kada ku ji a ranku kamar
wasu 'yan fursina da ke kulle cikin bakinciki wadanda suka hadu da jarabawa, to
alfijir zai bayyana ka zama kana da aminta, domin kyakkyawan fata na ga wanda
ke da aminta, fatan ka na alheri na bakin ka, yin sika da Allah ya isanmaka,
Zamu
rayu cikin yanayi mai dadi tamkar kaka bayan bakinciki *
Kai ka
ce bamu dandani daci a jiya ba.
Ku yi
fatan alheri duk da samuwar annoba da
firgicinta, to zaa kashe wutanta da giragizai,
Ku yi fatan alheri da sannu zaa yaye mana
bakinciki, jamaa da ke shaukin masallaci su dawo,
Ku yi
fatan alheri Allah zai hada mu mu ji dadi da abokai da sa'anni.
Bushara
zata zo sai mu samu sa'ada da aminci yayin safiya mai fara'a da iska mai dadi.
Ku
taho zuwa ga kofofinku an bude su, duk matafiyi mai yawo garuruwa ya fire zuwa
inda ya ke so.
Ku
kankan da kai,Allah shine Mafi karamcin wanda aka roka, yana warkar da musibu
duka da falalarSa.
Ku
kankan da kai da adu'a don ba mai daukewa ko tunkudewa ko gusarwa, kuma ba mai yaye wannan annoba sai Allah wanda ke
mallakar cutarwa da amfanarwa,
wanda ke tasarrufi a cikin halittun sa da abin da ya so wanda halittu suka rusunawa kasaitarSa da daukakarSa , kuma dukkan halittu suka zama ba komai ba a gaba gare shi , suka tsananta roko suna maimaitawa ya Ubangijinmu ya Ubangijinmu, Hasanul Basari yake cewa a fadin sa :-(Sai Ubangijinsu ya
amsa musu) , ba su
gushe ba suna cewa ya Ubabngijin mu ya Ubangijin mu har aka amsa musu .
Ya mai yaye damuwa da bakin ciki £ Gare ka
muke guduwa don neman mafaka
To
ya Ubangijin mu wannan annoban ya illan
ta kuma ya boye wasu abokai ya Allah ka
janye shi kar ka tsawaita wani tsanani
akan mu a hannun ka ne yayewa ya ke, ya Allah
kar ka nuna mana cikin wanda muke
kauna sai abin da muke so , ya wanda
muke so ya mafi rahamar ma su rahama.
YA KU MUSULMAI:
Ku
sanya Alkur'ani a gidajen ku kamar kukan zuma
ku sanya ambaton Allah a watan ku abin maimaitawa , ku yi mudarasan Alkur'ani
tare da iyalanku da 'ya'yan ku tun
daga farkon sa zuwa karshensa ku kamsasa
lebban ku da shi, ku turara bakunan ku da alkur'ani , ku raya mazaunin ku ,
da unguwannin ku da
gidajen ku da tilawa da
tarawihi da kunuti.
Ku yi
sallan tarawihi a gidajen ku a daidaiku
ko a jam'i ko da ya ke haduwan ya
fi sa nashadi ga
iyalai kuma ya fi kwadaitarwa, kuma ya fi zamewa abin koyi idan har mutum bai da karfin yin ta sai ta
hanyar koyin din kuma ya ji tsoron barin ta in har a shi kadai zai yi to a sallace
ta jam'i din shi ya fi dacewa
kuma shi ya fi falala wurin
ribatan dararraki masu daukaka, idan
kuma mutum yana da karfin himma na yi
shi kadai kuma ya himmatu da haka , ya kwadaitu da ya sallace
ta shi kadai don neman kushu'i ko tsawaita karatu da ruku'u da sujjada ,
to zai iya yin hakan , al'amarin a cikin shi akwai yalwa .
Baya
inganta mace ta limanci maza ko da a tarawihi ne ko ga dangin ta a cikin
zance mafi inganci , amma za ta iya limantan mata a gidan ta .
YA
KU MUSULMAI:
Idan
larura ta saka killacewa mataki ne na kariya
da ya hana ku yawo da shawagi , da kaura daga nan zuwa can to, lallai
kuna da wani fage na rahama a watan azumi
da ba haramtattu ba da kuma wasu alheri dake busowa wanda ba a iya
killace su , kada ku kasance cikin wadan
da za su shagalta da abubuwa masu shagaltarwa, suka gafala daga watan alheri da rahama , wayoyi na cikin abubuwan da aka kirkira aka sana'anta
wanda abubuwan ban mamaki a cikin
su na da yawa ababen nema a cikin su sun
yawaita , faratunan su sun ta'allaka da mu,
abubuwan da ake shiga a cikin su sun sha bamban to ku kiyaye kar ku bar
waya ya cinye mu ku lokutan wata mai albarka , wanda ba da jimawa ba zai zo ya
wuce .
Ya kai
wanda ke jin radadi da bakin ciki bisa rufe masallatayya ya rasa haduwa da
gamayya a sahu, da haduwa a juma'a da jam'i da tarawihi, kar ku yawaita
abubuwan na makoki kamar wake, kada kuma
kururuwa ta musiba ta dauke ku domin
haka bai da wanin amafani, ku yawaita
ambaton Allah da tasbihi a gare shi da
girmama shi da tunani cikin ayoyinSa da daukan izna ku yawaita nuna bukatuwar
ku zuwa ga Allah da istigfari , da bada
hanzari da lura da wa'azantuwa .
Duk
wanda bai ba da hanzari ba a yau to yaushe ne zai bada hanzari
Abin da Ubangiji na ya so ya kasance sai ya kasance * mutum ya kan kai
kan shi ga halaka wasu lokuta
Rana ba ta bullowa ko ta bace fa
ce da umarnin wanda sha'anin sa abin
mamaki
Muna da sarki mai kyautatawa a gare mu * mu su wane ne in ba falalar sa
a gare mu ba , tsarki ya tabbata a gare ka ya Allah
Ka yi aminci ka yi aminci ka cika
ni'imomi a gare mu kuma ka cika
Allah ne Ubangiji na kuma shi ne
mai mulki ba yi da abokin tarayya cikin
mulkin sa
YA KU MUSULMAI:
Mai
yawan dauwama da dogewa akan da'a wanda
ba ta gushe ba tana cikin dabi'arsa da halin sa , bai datse ba daga gare su
sannan wannan annoba ya yi shamaki ya killace tsakanin shi da su tare da son sa na yanke zuwa aikata su , da
an kadarta a gare shi , to ana sa ran
Allah zai rubuta mishi ladan shi cikakke , to, ana muku albishir ya ku wadan da
kuka kasance kuna raya masallatayya da salla
da tsayuwa da tarawihi da karatun alkur'ani albishirin ku ya ku wadan da kuka kasance kuna shimfida sufura don shayar da masu azumi Ubangijin ku Ma'abocin
da'a ne da tausayi da karamci.
An
karbo daga Jabir Allah kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Lallai
a cikin madina akwai wasu mutane, ba wata tafiya da za ku yi ko ku keta wani kori face sun kasance tare da ku, '' rashin
lafiya ne ya tsare su'') a wata riwaya face sun yi tarayya da ku a lada,) Muslim ne ya rawaito. A BUHARI kuma a
riwayar Anas. Allah kara yarda a gare shi (uzuri ne ya kange su).
Ibnul Munzir Allah ya masa rahama yace : (wanda bai samu zuwa ba sabo da uzuri to yana daidai da
wanda ya je)
Muna kwadaitar da masu kyautatawa, masu abin hanu, da su
yi tarayya a wannan hobbasa na aikin gidauniyar ramadan na madina wanda ke nufin ciyar da talakawa da miskinai wadanda dalilin hana fita ya musu illa
da tsayawar ayyuka , mafi alherin sadaka shi ne sadakan cikin
watan ramadana , (Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya
kasance mafi kyautan mutane kuma kyautan
sa ya fi yin sa cikin azumi)
Wanda ya shayar da mai azumi yana da kwatankwacin ladan
shi ba tare da an tawaye wani abu ba na
daga ladan mai azumin ba, . shekul islam Ibn Taimiya Allah ya mishi rahama yana
cewa :- (''Abun da ake
nufi da shayar da shi ; shi ne kosar da shi ''
An karbo daga salt Dan Basdam ya ce:- ''Hammad
Dan Abi Sulaiman yana shayar da mai azumi hamsin a ko wani rana a ramadan , to idan kuma daren salla ya zo sai ya
tufatar da ko wannen su tufafi –tufafi''.
Ku tausayawa
masu rauni da talakawa da gajiyayyu, to duk wanda baya tausayawa ba za a
tausaya mi shi ba , ku sada zumunci da sadakoki .
Ba wata dukiya da za ta saraya
idan ta haifar da godiya ga ma'abotan ta * sa dai dukiyan marowaci ita take saraya , ina fadin abin da kuke ji kuma ina neman gafaran
Allah to ku nemi gafarar sa domin lallai
shi ya kasance mai yawan gafara ne ga ma su komawa gare shi .
HUDUBA TA BIYU
Ya kai dan uwa na dan uwa na wanda aka shafe shi da
wannan bala'i, aka hada shi da wannan annoba
aka killace shi aka yi nesa da shi aka
killace shi daga mutane kada ka kuntata abu mai fadi mai yalwa.
Duniya bata yi kunci
ba gare ka da fadinta*
Ba a
rufe ma kofar yafiyar Allah ba
Ku yi bushara da waraka da lafiya, ku bazama zuwa ga
sallah, ku kyautata zato ga Allah, ku debe kewa da ambaton Allah, da karatun
Alkur'ani, kada ka yanke tsammani kada ka yanke kauna daga rahamar Allah, ku
dogara ga rayayye wanda bai mutuwa.
Kada ka kashe kan ka da damuwa da bakinciki, domin
damuwa ne dafi mafi hadari, ka nemi tsarin Allah daga damuwa da bakinciki, ba
wani abu ba ne face wata musiba da ta sauka
kuma za ta gushe, kuma abin da iska ya dauko sannan kuma zai bace yarda da kaddara kamar wata ganima ce na yammaci kuma babbar itaciya ce ga maras lafiya , wannan firgici na tsorata mara fasalin bayi da wani fa'ida kuma ba a bada lada ga wannan cutan , lallai
mafi girman sakayya na ga mafi girman
bala'i kuma idan Allah ya so mutane sai ya jarrabe su , duk wanda ya yarda to
yana da yarda, duk wanda ya yi fushi to,
yana da fushi .
Muna
mika jajen mu ga duk wani wanda ya rasa dansa da kuma wacce
ta rasa dan ta , abun kaunarsu mai kima , muna fatan shahada ga wanda ya mutu cikin musulmai a dalilin wannan annoba.
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda
a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- (Shaihidai guda biyar ne ; wanda annoba ta kashe shi, da
wanda ya mutu ta sababin ciwon ciki da
kuma wanda ya mutu a ruwa da kuma wanda gini ya fadi a kansa , da kuma
wanda ya mutu a tafarkin Allah ) Buhari da Muslim ne suka rawaito
An karbo daga Rashid Dan Hubaish
Allah ya kara yarda a gare shi ,cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya shiga ga Ubadatu Dan Samid yana ziyartan shi a rashin
lafiyan sa , sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya ce :-ko kun san shahidi a cikin al'uma ta? sai Ubadata dan samid ya ce ya
Manzon Allah :- shi ne mahakurci mai neman lada a wurin Allah , sai Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- '' lallai shahidai a cikin al'umata in dai haka
ne to, dan kadan ne wanda aka kashe su a
tafarkin Allah sun yi shahada , da wanda ya yi mutuwar annoba shi ma ya yi shahada,
da kuma mutuwa a ruwa shi ma shahada ne
da mutuwa dalilin ciwon ciki shi ma shahada ne , da mutuwa ta dalilin haihuwa dan na ta zai ja ta
da cibiyar sa zuwa Aljanna
Abul Auwam ya kara da cewa '' da gobara da kuma ambaliya '' Ahmad ne ya
fitar da shi
YA KU MUSULMAI :-
Ku
lazimci matakan kariya da nusarwa da fiskantarwa , wanda ke hana yaduwan
korona ku kiyaye taruwa a wurin buda
baki da sahur a cikin ramadana .
Da kukan
mutuwa gara killacewa a gida , ku yi
salati da aminci bisa ga Ahmadu mai shiryarwa mai ceton bayi gaba daya
Duk wanda ya yi mar salati guda to Allah zai mar
salati guda goma.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق