17-8-1441ه، الهوسا
Hudubar
Juma'a a Masallacin Annabi 17-8-1441AH / 10-4-2020AD na shaikh Ali Bin Abdurrahman Alhuzaifi
Hudubar
farko
Da sunan
Allah Mai rahama Mai jinkai
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah Mai yawan gafara Mai karamci, Mai yawan godiya
Mai hakuri, Mai gudanar da halittunSa da mashi'arSa da rahamarSa da kudurarSa,
kuma Shi Masani ne ga dukkan komai.
Ina kyautata
yabo ga Ubangiji na kuma ina gode masa, bisa ni'imominSa da ba mai iya
kididdige su sai Shi, wadanda muka sani da wadanda bamu sani ba, Allah
Ma'abocin falala ne mai girma.
Na shaida ba abin bautawa da
gaskiya sai Allah Shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, Ubangijin al'arshi
mai girma, kuma na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa
ne, ma'aboci halaye masu girma, ya Allah ka yi salati da aminci da albarka ga
bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalansa da sahbbansa ma'abota tafarki
mikakke, Bayan haka, ku ji tsoron Allah ta hanyar tashi da wajibabbu, da nesatan haramtattu, za
ku rabauta da alheri a rayuwa da bayan mutuwa, kuma zaku zauna a gidajenku a
cikin aljanna, Allah Madaukakin Sarki ya ce : ((Wanda
ya ji tsoron Allah zai kankare masa laifukansa kuma ya girmama ladansa.)
Ya ku
mutane, wanda ya kasance yana son lahira to lahira na hanun Allah ne shi
kadai ba shi da abokin tarayya, Allah ya bayyana Mabuwayi da daukaka ayyukan da
zaa yi don ita kafin mutuwa, to madallah da aiki kuma madalla da ladan, wanda ya ke son duniya ya manta da lahira to
wanda ya mallaki duniya shine Ubangijin
talikai,Allah zai bashi wani rabo daga ciki kuma bai da rabo a lahira Allah Madaukakin
Sarki ya ce :(Wanda ya kasance yana nufin duniya sai
mu gaggauta masa a cikinta,abin da muke so ga wanda muke nufi, sa'anan mu sanya
masa jahannama ya konu da ita yana abin zargi abin tunkudewa. Kuma wanda ya
nufi lahira, kuma ya yi aiki saboda ita, irin aikinta alhali kuwa yana mumini
to wadannan aikinsu ya kasance abin godewa. Dukansu muna taimakon wadannan da
wadancan daga kyautar UbangijinKa kuma kyautar UbangijinKa bata kasance abin
hanawa ba),
Allah Mabuwayi da
daukaka ya ce : ((Wanda ya kasance yana nufin noman lahira zamu kara masa a
cikin nomansa, kuma wanda ya kasance yana noman duniya zamu tsammasa daga gare
ta alhali kuwa ba shi da wani rabo a cikin lahira)
Allah Madaukakin Sarki ya ce
: (Kuma lalle gare mu lahira take da duniya) To
duk wanda zai neme su to kar ya neme su a gun wani ba Allah ba, to musulmi yana
jin dadi ne da abin da Allah ya hore mishi a nan duniya jin dadi mai kyau, ba
zai tsallaka abubuwa na halal zuwa haram ba. Ya lizimci tsakaitawa ya nesaci almubazzaranci da alfahari, ya gyara a
rayuwa abin da Allah ya bashi, ya habaka alheri cikin arzikin Allah ya sanya
abin da Allah ya bashi na kaso a nan duniya guzuri ne don lahira gidan ni'ima, Allah Madaukakin
Sarki ya ce : (To daga cikin mutane akwai wanda yake
cewa : ya Ubangijinmu ka ba mu a cikin duniya, kuma bai da wani rabo a cikin
lahira, kuma daga cikin su akwai wanda ya ke cewa : Ya Ubangijin ka bamu mai
kyau a duniya da mai kyau a lahira kuma ka tsare mu daga azabar wuta.kuma
wadannan suna da rabo daga abin da suka sana'anta. Kuma Allah Mai gaggawar
sakamako da yawa ne.)
Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma ka bida a cikin abin da Allah ya baka gidan lahira
kuma kada ka manta da rabonka daga duniya, kuma ka kyautata kamar yadda Allah
ya kyautata a gare ka, kuma kada ka nemi barna a doron kasa lallai ne Allah ba
ya son masu barna).
Ya
ku mutane ! Lalle ba a riskan abin da ke hanun Allah sai ta hanyar yi masa
biyayya, kuma ba a tunkude sharri daga mutum sai da falalar Allah da rahamarSa,
Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma idan Allah ya
shafe ka da wata cuta to babu mai yaye ta face shi, kuma idan ya nufe ka da
wani alheri to babu mai mayar da falalarSa, yana samun wanda ya ke so daga
cikin bayinSa da shi, kuma shi ne Mai gafara Mai jinkai).
Ina fadakarwa da hakikanin da
ko wani mutun zai yi kokari ya yi aiki don shi, shine dukkan ko wani mutun yana
aiki ne ya yi kokari domin ya riski alheru kuma ya rabauta da abubuwa na falaloli
da abubuwan karramawa kuma ya tsira ya kubuta daga sharrori da abubuwa masu
halakarwa , sai dai wan rabauta mai girma ba a'a riskan shi kuma ba ya tabbatuwa face ta
hanyar bin Manzanni tsira da amincin Allah su tabbata a gare su, kuma cikiamakinsu shi ne Annabinmu kuma
shugabanmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi duk wanda ya bi shi zai
rabauta da alherin duniya da lahira ko da wani abu ya same shi da ya ki na daga
cikin musibu, an karbo daga Suhaibu dan Sinan Allah ya kara yarda a gare shi ya
ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Abin mamaki da al'amarin mumini, dukkan al'amarin shi
alheri ne hakan ba ya kasancewa ga wani face mumini idan abin farin ciki ya same shi sai ya yi godiya sai ya
zama alheri a gare shi idan kuma cuta ta same shi sai ya yi hakuri, hakan sai
ya zama alheri a gare shi) Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya kuskure hanya ya
haramtu daga imani to hakika ya yi hasaran duniyarsa da
lahirarsa ba zai amfane shi ba duk abin da ya riska ko abin da ya samu a nan
duniya, don jin dadin duniya wani abu ne mai gushewa mai kaucewa, kuma jin dadi
ne wanda ya ke cakude da bakin ciki da kuma abubuwa na bacin rai Allah ta'ala
ya ke cewa ; (kuma rayuwar duniya ba wani abu ba ne
face jin dadi na rudi) , ya kai mutun ka yi kwadayi zuwa ga UbangijinKa
ka dawwama bisa ga addu'a da rokon Allah Madaukakin sarki dukkan alheri da kuma
neman tsarin shi daga dukkan sharri, Ubangijin mu Mai rahama ne Mai jinkai ya
na so a roke shi abubuwa mafi daukaka Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisul
kudusi (Ya ku bayi Na, da na farkonku da na
karshenku da mutanenku da aljanunku za su hadu su hallara a kan kasa guda suka
roke ni sa'an nan na basu na bawa ko wanne bukatarsa to ba abin da zai rage na
daga abin da ke gare Ni face kamar abin da zai rage ne idan aka sa allura aka
kamfata daga cikin kogi) Muslim ne ya rawaito daga Abu Zarri.
Na daga cikin adu'o'i mai
amfani na kiyaye addini da kuma lafiyan jiki da kiyaye maslahohin duniya da
kuma lahira rokon Allah Madaukakin sarki
waraka musamman a irin wadan nan musibu da su ke sauka na gamagari da 'irin bala'u
masu girma, An karbo daga Abbas dan Abdulmuddalib Allah ya kara yarda a gare
shi ya ce : na ce ya Manzon Allah ka sanar da ni adu'an da zan roki Allah da
shi , sai ya ce : (ka roki Ubangijinka lafiya
sai na zauna wasu ranaku sannan na zo mishi , sai na ce ya Manzon Allah ka
sanar da ni wani abu da zan roki Allah da shi sai ya ce ya Abbas ya baffan
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ka roki Allah waraka
a duniya da lahira) Tirmizi ne ya rawaito ya ce wan nan hadisi ne
sahihi.
(Hakika Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi yana girmama Abbas kuma ya na son shi kuma
ya na bashi matsayi matsayin mahaifi ya kasance yana cewa ya baffa ka yawaita
adu'a na neman waraka). Dabarani ne ya rawaito , sahabbai sun kasance su na
girmama Abbas sayyidina Umar da sayyidina Usman Allah ya kara yarda a gare su
idan su ka zo wucewa wurin Abbas sai su sauka daga kan abin hawan su domin girmama shi, Imamul kurra'a da
muhaddisai na zamanin shi Muhammad dan Aljazari Allah ya mar rahama ya ke cewa
mai hankali ya yi dubi ga mikidarin wan nan kalma wanda Manzon Allah ya zabe ta ga baffan shi domin duk mutumin da aka ba shi
waraka to ya rabauta da abin da ya ke fata kuma da abin da ya ke so ciki da
waje duniya da addini kuma za a kare shi daga abin da ya ke tsoro a duniya da
lahira.
Ilimi na yakini hakika ya zo
ta hanya mutawatiri daga gare shi Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi adu'arSa ta neman waraka ko lafiya ya zo daga gare shi
lafazin da ma'anan duka ta fiskoki da za su kai kaman hanyoyi hamsin, wannan
hakika shi da an gafarta mishi abin da ya gabata na daga zunuban shi da abin da
ya jinkirta kuma yana katangagge hakikatan to ta yaya kuma mu wadanda mu a ko
yaushe mu na kai kan mu ga kifiyoyi na kaddara ma'ana zunubai da kuma abubuwa
da su ke na tsakanin rayi da kuma shaidan da son rai ) maganan shi ya kare.
An karbo daga Abubakar Allah
ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : (ku nemi Allah waraka ta
lafiya lallai wani ba a ba shi wani abu ba bayan yakini da ya fi alheri akan
waraka) Tirmizi ne ya rawaito da Ibnu Hibban da Hakim kuma ya ce
isnadin shi ingantacce ne.
Yakini shi ne imani da Allah
da mala'ikunSa da littatafanSa da ManzanninSa da lahi da ranar lahira da imani
da kaddara na alheri da na sharri, da gaskatawa gaskatawa na yanke da abin da
Annabi ya zo da shi na Alkur'ani da sunna wanda ba wani abu da zai cakudu da
shi na shakku a cikin haka da kuma karkata zuwa ga Allah a dukkan komai da
maida al'amari gaba daya zuwa gare shi, An karbo daga Anas Allah ya kara yarda
a gare shi cewa wani mutumi ya zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : ya Manzon Allah wani adu'a ne ya fi? sai ya ce (ka roki Ubangijinka lafiya da waraka a duniya da lahira)
san nan ya zo
mishi a rana ta biyu, sai ya ce : ya Manzon Allah wani adu'a ne ya fi? , sai
fada mishi kwatankwacin haka , sannan ya zo shi a rana ta uku , sai ya ce da
shi kwatankwacin wancan ya ce: ( Idan an baka
waraka na duniya to an baka ita a lahira
hakika ka rabauta )Tirmizi ne ya rawaito.
An karbo daga
Ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :(
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bai kasance ya kan
bar wadan nan adu'o'in ba a lokacin da ya ke yammaci haka nan lokacin da ya ke
wayan gari: ya Allah ina rokoKa lafiya a duniya da lahira ya Allah ina rokonka
afuwa da kuma waraka a addini na da duniya ta da iyalaina da dukiya ta, ya
Allah ka suturce al'aura ta ka amintar da tsoro na, ya Allah ka kiyaye ni ta
daga gaba gareni haka nan daga bayana haka nan daga dama ta haka nan daga
haguna haka nan daga sama ta kuma ina neman tsarinKa da kasaitanKa da a
min kisan gilla ta kasa ta ) Hadisi
ne ingantacce Abu Dauda ya rawaito shi da Ibnu Majah da Hakim da Ibnu Hibban, Da
adu'a Allah yake tunkude wan nan annoba da waninsa, An karbo daga Salman Allah
ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce (Ba abin da ya ke maida kaddara
sai adu'a, ba abin da ke kara tsawon rai sai biyayya) Tirmizi ne ya
rawaito da Hakin da Ibnu Hibban.
Ambaton Allah da nau'ukansa duk gaba daya
addu'a ne na ibada, Allah na tunkude bala'i da shi, ka yi lura da fadin Annabi
tsira amincin Allah su tabbata a gare shi ga Abu Musa Al'ash'ari , ya ce ka ce:
(Ba dabara ko karfi sai ga Allah , domin ita
taska ce daga cikin taskokin aljanna) Buhari da Muslim ne suka
rawaito, da hadisin Abu huraira Allah ya
kara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce: (La haula wa la kuwwata illa
billahi waraka ce daga casa'in da tara na daga cututtuka, mafi saukin shi shi
ne damuwa) Dabarani ne ya rawaito a cikin littafinsa Al'ausat haka
nan Hakim ma a cikin littafin sa Almustadrak kuma ya ce sahihin isnadi ne,
cikan amfani a zikiri akwai bukatan halarto da zuciya da kuma yakini wato
sakankancewa, Hakika Allah Ta'ala ya umarci musulmai da adu'a da neman alheri
da tunkude dukkan wani abu ya yi umarni da dogaro bisa ga Allah Madaukaki da
kuma gaskiyar komawa zuwa gare shi da
dogaro na zuciya a gare shi , sai ya ke cewa:( ka
dogara ga rayin da ba ya mutuwa) Allah ya ce (ka bauta mishi ka dogara a gare shi) Allah kuma ya
lamuncewa duk mutumin da ya dogara a gare shi dogaro na gaskiya ya nemi mafaka
zuwa gare shi da gaskiya Allah ya lamunce mishi isarwa , sai Allah subhanahu wa
ta'ala ya ke cewa (Dukkan wanda ya dogara ga Allah
to shi ne zai isam masa) kuma shari'a ta yi umarni da rungumar
abubuwa na sababi tare da dogaro ga Mahaliccinta.
An karbo daga Usama dan Sharik ya ce : Na
kasance a wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai
larabawan kauye suka zo suka ce : ya Manzon Allah shin muna yin magani ? sai ya
ce ( ya ku bayin Allah ku yi magani lallai Allah
Mabuwayi bai saukar da wata cuta ba face ya sanya mata waraka banda cuta guda
daya , sai suka ce menene ita ? sai ya ce tsufa) Ahmad ne ya rawaito
da Tirmizi ya ce wan nan hadisi ne ingantacce.
Addu'a da
neman tsarin Allah daga sharrace - sharrace dukkaninta na gaba daya da kuma na
kebe na daga cikin sabuba wanda su ke abin da ya ke mukaddari wanda Ubangijinmu
ya umarce mu da mu yi aiki da su tare da
magunguna, An karbo daga Abdullahi dan khubaib Allah ya kara yarda a gare shi ya
ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (kul a'uzai biyu ka
fade su yayin da ka yi yammaci haka nan yayin da ka wayi gari ka karanta su sau
uku za su isam maka daga dukkan komai) Abu Dauda ya rawaito shi da Tirmizi .
Ka karanta kul
huwallahu Ahad ka yi tawassuli
da sunayen shi Madaukaki da kuma muawwizai guda biyu; Neman tsarin
Allah ne daga sharrace - sharrace na gaba daya da kuma na kebe na daga cikin
sabuba na sharri dukkanin su da kuma dukkan wasu sabuba na sharri dukkaninsu ,
ya zo a hadisi ba wanda zai roki Allah da kwatankwacin su.
Na daga cikin abin da ya dace
maimaita tunatar da shi, shi ne; taimakekeniya bisa ga daukan mataki na kariya
ta hanyan bin nusarwan bangaren lafiya domin a samu daga kowa da kowa a tsallake
wan nan musiba mai tsanani da kuma wannan tsanani wanda ke mai ban wahala,
Allah ya saka da alheri ga jagorori
shuwagabanni - Allah ya kiyaye su - bisa ga kokarin da su ke yi na a yaba wurin
fiskantar wannan annoba mai dauke jama'a da kuma kwadayin su mai tsanani wurin
ingancin samun lafiyan 'yan kasa da kuma mazauna to lallai kiyaye koyarwansu da
ka'idodin su zai karanta daga wan nan cutan na wan nan fairos din kuma Allah
zai daga wan nan bala'i da izinin Shi, to rahamar Allah tana da yalwa kuma
farin ciki na kusa Allah Madaukakin sarki yace : (Allah
Ubangijinku ya ce ku roke Ni zan amsa muku lallai wadanda su ke girman kai bisa
ga roko na za su shiga jahannama suna masu kaskanci) Allah ya sa
mana albarka bisa alkur'ani mai girma .
Huduba ta biyu
Dukkan yabo
da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya halicci dukkan komai ya kaddara shi
kaddarawa, kuma ya yalwaci dukkan komai a ilimi ya iyakance dukkan komai a
adadi , Allah ya kasance Mai ji kuma Mai gani ina kyautata yabo ga Ubangijina
kuma ina gode masa bisa ga ni'imomi da ba mai iyakance su sai shi, da abin da
muka sani cikinsu da wanda ba mu sani ba, na shaida ba bu abin bautawa da
gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya ba abin da zai
gagare shi a kasa ne ko a sama na daga bada agaji da shi kuma duk wanda ya nemi
agaji na gaggawa a wurin Allah to Allah zai tsirar da shi wanda kuma ya roki
Allah kariyarSa to Allah zai kare shi wanda ya nemi taimakon Allah to Allah zai
shiryar da shi ya bashi mafaka, haka nan kuma UbangijinKa ya isa mai shiryarwa
kuma mai taimako na shaida Annabinmu kuma shugaban mu Muhammad bawanSa ne kuma
ManzonSa ne, Allah ya turo shi da albishir kuma da gargadi, ya Allah ka yi
dadin tsira da albarka ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalanSa da
sahabbanSa dadin tsira da aminci mai yawa bayan haka ; ku ji tsoron Allah Mabuwayi
da daukaka domin da tsoron Allah ne Allah ya ke bada kyautan lada kuma ya
tsiratar daga azaba.
Ya ku mutane
lallai ku kuna ji kuma kuna gani abin da ya faru a doron kasa na daga bakin
ciki mai tsanani lallai annoba bala'i na
gamagari ba mai dauke shi sai Ubangijin talikai , na daga cikin sabuba na dauke
shi shi ne taimakekeniya wurin daukan sabuba na shari'a da kuma na ilimin rayuwa da su ke na halal mafi girman sabuban
da su ke sa a dauke shi shi ne tuba na gaba daya daga al'umma dukkansu, Allah Mabuwayi da daukaka
ya na tausayawa ta hanyar tuba da adu'a,
abin da bayin shi ba za su iya dauke shi ba Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce :(Halal a bayyane ya ke
kuma haram a bayyane ya ke) Allah ya bamu kissa na dauke azaba daga
mutanen Yunus ta hanyan tuba sai Allah ya ke cewa : (Ba don wata alkarya ta kasance imaninta ya mata amfani ba face mutanen
Annabi Yunusa yayin da su ka yi imani mu ka yaye musu azaban walakanci a rayuwan
duniya mu ka jiyar da su dadi zuwa wani
lokaci) .
Ibnu kasir Allah ya mishi
rahama ya ke cewa: yayin da su ka rasa Annabinsu suka zaci cewa lallai azaba fa
ya kusa zuwa gare su sai Allah ya jefa a cikin zukatansu tuba suka sanya rigar
masu ibada Su ka rarraba tsakanin dukkan dabbobi da 'ya'yayensu san nan su ka
yi ta ambaton Allah suna komawa zuwa gare shi har dare arba'in, yayin da Allah
ya ga haka daga gare su da gaskiyan zukatan su da tubansu da nadama bisa ga abin
da ya shude sai Allah ya yaye musu wannan azaba bayan an zuro azaban kusa gare
su.
Ya ku bayin Allah lallai
Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi
salati a gare shi da aminci tabbatacce.