الجمعة، 24 أبريل 2020

ROKON ALLAH WARAKA


أمين سعد عبد الله
17-8-1441ه، الهوسا

Hudubar Juma'a a Masallacin Annabi 17-8-1441AH / 10-4-2020AD  na shaikh Ali Bin Abdurrahman Alhuzaifi

Hudubar farko
Da sunan Allah Mai rahama Mai jinkai
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mai yawan gafara Mai karamci, Mai yawan godiya Mai hakuri, Mai gudanar da halittunSa da mashi'arSa da rahamarSa da kudurarSa, kuma Shi Masani ne ga dukkan komai.
Ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode masa, bisa ni'imominSa da ba mai iya kididdige su sai Shi, wadanda muka sani da wadanda bamu sani ba, Allah Ma'abocin falala ne mai girma.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, Ubangijin al'arshi mai girma, kuma na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, ma'aboci halaye masu girma, ya Allah ka yi salati da aminci da albarka ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalansa da sahbbansa ma'abota tafarki mikakke, Bayan haka, ku ji tsoron Allah ta hanyar  tashi da wajibabbu, da nesatan haramtattu, za ku rabauta da alheri a rayuwa da bayan mutuwa, kuma zaku zauna a gidajenku a cikin aljanna, Allah Madaukakin Sarki ya ce : ((Wanda ya ji tsoron Allah zai kankare masa laifukansa kuma ya girmama ladansa.)
Ya ku mutane, wanda ya kasance yana son lahira to lahira na hanun Allah ne shi kadai ba shi da abokin tarayya, Allah ya bayyana Mabuwayi da daukaka ayyukan da zaa yi don ita kafin mutuwa, to madallah da aiki kuma madalla da ladan,  wanda ya ke son duniya ya manta da lahira to wanda ya mallaki duniya  shine Ubangijin talikai,Allah zai bashi wani rabo daga ciki kuma bai da rabo a lahira Allah Madaukakin Sarki ya ce :(Wanda ya kasance yana nufin duniya sai mu gaggauta masa a cikinta,abin da muke so ga wanda muke nufi, sa'anan mu sanya masa jahannama ya konu da ita yana abin zargi abin tunkudewa. Kuma wanda ya nufi lahira, kuma ya yi aiki saboda ita, irin aikinta alhali kuwa yana mumini to wadannan aikinsu ya kasance abin godewa. Dukansu muna taimakon wadannan da wadancan daga kyautar UbangijinKa kuma kyautar UbangijinKa bata kasance abin hanawa ba),    
Allah Mabuwayi da daukaka  ya ce : ((Wanda ya kasance yana nufin noman lahira zamu kara masa a cikin nomansa, kuma wanda ya kasance yana noman duniya zamu tsammasa daga gare ta alhali kuwa ba shi da wani rabo a cikin lahira)
Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Kuma lalle gare mu lahira take da duniya) To duk wanda zai neme su to kar ya neme su a gun wani ba Allah ba, to musulmi yana jin dadi ne da abin da Allah ya hore mishi a nan duniya jin dadi mai kyau, ba zai tsallaka abubuwa na halal zuwa haram ba. Ya lizimci tsakaitawa ya  nesaci almubazzaranci da alfahari, ya gyara a rayuwa abin da Allah ya bashi, ya habaka alheri cikin arzikin Allah ya sanya abin da Allah ya bashi na kaso a nan duniya guzuri ne don lahira gidan ni'ima,  Allah Madaukakin Sarki ya ce : (To daga cikin mutane akwai wanda yake cewa : ya Ubangijinmu ka ba mu a cikin duniya, kuma bai da wani rabo a cikin lahira, kuma daga cikin su akwai wanda ya ke cewa : Ya Ubangijin ka bamu mai kyau a duniya da mai kyau a lahira kuma ka tsare mu daga azabar wuta.kuma wadannan suna da rabo daga abin da suka sana'anta. Kuma Allah Mai gaggawar sakamako da yawa ne.)
 Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma ka bida a cikin abin da Allah ya baka gidan lahira kuma kada ka manta da rabonka daga duniya, kuma ka kyautata kamar yadda Allah ya kyautata a gare ka, kuma kada ka nemi barna a doron kasa lallai ne Allah ba ya son masu barna).
  Ya ku mutane ! Lalle ba a riskan abin da ke hanun Allah sai ta hanyar yi masa biyayya, kuma ba a tunkude sharri daga mutum sai da falalar Allah da rahamarSa, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma idan Allah ya shafe ka da wata cuta to babu mai yaye ta face shi, kuma idan ya nufe ka da wani alheri to babu mai mayar da falalarSa, yana samun wanda ya ke so daga cikin bayinSa da shi, kuma shi ne Mai gafara Mai jinkai).  
Ina fadakarwa da hakikanin da ko wani mutun zai yi kokari ya yi aiki don shi, shine dukkan ko wani mutun yana aiki ne ya yi kokari domin ya riski alheru kuma ya rabauta da abubuwa na falaloli da abubuwan karramawa kuma ya tsira ya kubuta daga sharrori da abubuwa masu halakarwa , sai dai wan rabauta mai girma  ba a'a riskan shi kuma ba ya tabbatuwa face ta hanyar bin Manzanni tsira da amincin Allah su tabbata a gare su,  kuma cikiamakinsu shi ne Annabinmu kuma shugabanmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi duk wanda ya bi shi zai rabauta da alherin duniya da lahira ko da wani abu ya same shi da ya ki na daga cikin musibu, an karbo daga Suhaibu dan Sinan Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Abin mamaki da al'amarin mumini, dukkan al'amarin shi alheri ne hakan ba ya kasancewa ga wani face mumini idan abin  farin ciki ya same shi sai ya yi godiya sai ya zama alheri a gare shi idan kuma cuta ta same shi sai ya yi hakuri, hakan sai ya zama alheri a gare shi) Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya kuskure hanya ya haramtu daga  imani  to hakika ya yi hasaran duniyarsa da lahirarsa ba zai amfane shi ba duk abin da ya riska ko abin da ya samu a nan duniya, don jin dadin duniya wani abu ne mai gushewa mai kaucewa, kuma jin dadi ne wanda ya ke cakude da bakin ciki da kuma abubuwa na bacin rai Allah ta'ala ya ke cewa ; (kuma rayuwar duniya ba wani abu ba ne face jin dadi na rudi) , ya kai mutun ka yi kwadayi zuwa ga UbangijinKa ka dawwama bisa ga addu'a da rokon Allah Madaukakin sarki dukkan alheri da kuma neman tsarin shi daga dukkan sharri, Ubangijin mu Mai rahama ne Mai jinkai ya na so a roke shi abubuwa mafi daukaka Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisul kudusi (Ya ku bayi Na, da na farkonku da na karshenku da mutanenku da aljanunku za su hadu su hallara a kan kasa guda suka roke ni sa'an nan na basu na bawa ko wanne bukatarsa to ba abin da zai rage na daga abin da ke gare Ni face kamar abin da zai rage ne idan aka sa allura aka kamfata daga cikin kogi) Muslim ne ya rawaito daga Abu Zarri.
Na daga cikin adu'o'i mai amfani na kiyaye addini da kuma lafiyan jiki da kiyaye maslahohin duniya da kuma lahira  rokon Allah Madaukakin sarki waraka musamman a irin wadan nan musibu da su ke sauka na gamagari da 'irin bala'u masu girma, An karbo daga Abbas dan Abdulmuddalib Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : na ce ya Manzon Allah ka sanar da ni adu'an da zan roki Allah da shi , sai ya ce : (ka roki Ubangijinka lafiya sai na zauna  wasu ranaku sannan  na zo mishi , sai na ce ya Manzon Allah ka sanar da ni wani abu da zan roki Allah da shi sai ya ce ya Abbas ya baffan Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ka roki Allah waraka a duniya da lahira) Tirmizi ne ya rawaito ya ce wan nan hadisi ne sahihi.
(Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana girmama Abbas kuma ya na son shi kuma ya na bashi matsayi matsayin mahaifi ya kasance yana cewa ya baffa ka yawaita adu'a na neman waraka). Dabarani ne ya rawaito , sahabbai sun kasance su na girmama Abbas sayyidina Umar da sayyidina Usman Allah ya kara yarda a gare su idan su ka zo wucewa wurin Abbas sai su sauka daga kan abin  hawan su domin girmama shi, Imamul kurra'a da muhaddisai na zamanin shi Muhammad dan Aljazari Allah ya mar rahama ya ke cewa mai hankali ya yi dubi ga mikidarin wan nan kalma wanda Manzon Allah ya zabe ta  ga baffan shi domin duk mutumin da aka ba shi waraka to ya rabauta da abin da ya ke fata kuma da abin da ya ke so ciki da waje duniya da addini kuma za a kare shi daga abin da ya ke tsoro a duniya da lahira.
Ilimi na yakini hakika ya zo ta hanya mutawatiri daga gare shi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi adu'arSa ta neman waraka ko lafiya ya zo daga gare shi lafazin da ma'anan duka ta fiskoki da za su kai kaman hanyoyi hamsin, wannan hakika shi da an gafarta mishi abin da ya gabata na daga zunuban shi da abin da ya jinkirta kuma yana katangagge hakikatan to ta yaya kuma mu wadanda mu a ko yaushe mu na kai kan mu ga kifiyoyi na kaddara ma'ana zunubai da kuma abubuwa da su ke na tsakanin rayi da kuma shaidan da son rai ) maganan shi ya kare.
An karbo daga Abubakar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ku nemi Allah waraka ta lafiya lallai wani ba a ba shi wani abu ba bayan yakini da ya fi alheri akan waraka) Tirmizi ne ya rawaito da Ibnu Hibban da Hakim kuma ya ce isnadin shi ingantacce ne.
Yakini shi ne imani da Allah da mala'ikunSa da littatafanSa da ManzanninSa da lahi da ranar lahira da imani da kaddara na alheri da na sharri, da gaskatawa gaskatawa na yanke da abin da Annabi ya zo da shi na Alkur'ani da sunna wanda ba wani abu da zai cakudu da shi na shakku a cikin haka da kuma karkata zuwa ga Allah a dukkan komai da maida al'amari gaba daya zuwa gare shi, An karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi cewa wani mutumi ya zo wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ya Manzon Allah wani adu'a ne ya fi? sai ya ce (ka roki Ubangijinka lafiya da waraka a duniya da lahira)
san nan ya zo mishi a rana ta biyu, sai ya ce : ya Manzon Allah wani adu'a ne ya fi? , sai fada mishi kwatankwacin haka , sannan ya zo shi a rana ta uku , sai ya ce da shi kwatankwacin wancan ya ce: ( Idan an baka waraka na  duniya to an baka ita a lahira hakika ka rabauta )Tirmizi ne ya rawaito.  
An karbo daga Ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bai kasance ya kan bar wadan nan adu'o'in ba a lokacin da ya ke yammaci haka nan lokacin da ya ke wayan gari: ya Allah ina rokoKa lafiya a duniya da lahira ya Allah ina rokonka afuwa da kuma waraka a addini na da duniya ta da iyalaina da dukiya ta, ya Allah ka suturce al'aura ta ka amintar da tsoro na, ya Allah ka kiyaye ni ta daga gaba gareni haka nan daga bayana haka nan daga dama ta haka nan daga haguna haka nan daga sama ta kuma ina neman tsarinKa da kasaitanKa da a min  kisan gilla ta kasa ta ) Hadisi ne ingantacce Abu Dauda ya rawaito shi da Ibnu Majah da Hakim da Ibnu Hibban, Da adu'a Allah yake tunkude wan nan annoba da waninsa, An karbo daga Salman Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Ba abin da ya ke maida kaddara sai adu'a, ba abin da ke kara tsawon rai sai biyayya) Tirmizi ne ya rawaito da Hakin da Ibnu Hibban.
 Ambaton Allah da nau'ukansa duk gaba daya addu'a ne na ibada, Allah na tunkude bala'i da shi, ka yi lura da fadin Annabi tsira amincin Allah su tabbata a gare shi ga Abu Musa Al'ash'ari , ya ce ka ce: (Ba dabara ko karfi sai ga Allah , domin ita taska ce daga cikin taskokin aljanna) Buhari da Muslim ne suka rawaito,  da hadisin Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (La haula wa la kuwwata illa billahi waraka ce daga casa'in da tara na daga cututtuka, mafi saukin shi shi ne damuwa) Dabarani ne ya rawaito a cikin littafinsa Al'ausat haka nan Hakim ma a cikin littafin sa Almustadrak kuma ya ce sahihin isnadi ne, cikan amfani a zikiri akwai bukatan halarto da zuciya da kuma yakini wato sakankancewa, Hakika Allah Ta'ala ya umarci musulmai da adu'a da neman alheri da tunkude dukkan wani abu ya yi umarni da dogaro bisa ga Allah Madaukaki da kuma gaskiyar  komawa zuwa gare shi da dogaro na zuciya a gare shi , sai ya ke cewa:( ka dogara ga rayin da ba ya mutuwa) Allah ya ce (ka bauta mishi ka dogara a gare shi) Allah kuma ya lamuncewa duk mutumin da ya dogara a gare shi dogaro na gaskiya ya nemi mafaka zuwa gare shi da gaskiya Allah ya lamunce mishi isarwa , sai Allah subhanahu wa ta'ala ya ke cewa (Dukkan wanda ya dogara ga Allah to shi ne zai isam masa) kuma shari'a ta yi umarni da rungumar abubuwa na sababi tare da dogaro ga Mahaliccinta.
 An karbo daga Usama dan Sharik ya ce : Na kasance a wurin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sai larabawan kauye suka zo suka ce : ya Manzon Allah shin muna yin magani ? sai ya ce ( ya ku bayin Allah ku yi magani lallai Allah Mabuwayi bai saukar da wata cuta ba face ya sanya mata waraka banda cuta guda daya , sai suka ce menene ita ? sai ya ce tsufa) Ahmad ne ya rawaito da Tirmizi ya ce wan nan hadisi ne ingantacce.
Addu'a da neman tsarin Allah daga sharrace - sharrace dukkaninta na gaba daya da kuma na kebe na daga cikin sabuba wanda su ke abin da ya ke mukaddari wanda Ubangijinmu ya umarce mu da  mu yi aiki da su tare da magunguna, An karbo daga Abdullahi dan khubaib Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (kul a'uzai biyu ka fade su yayin da ka yi yammaci haka nan yayin da ka wayi gari ka karanta su sau uku za su isam maka daga dukkan komai) Abu Dauda  ya rawaito shi da Tirmizi .
Ka karanta kul huwallahu Ahad  ka yi tawassuli da sunayen shi Madaukaki da kuma muawwizai guda biyu; Neman tsarin Allah ne daga sharrace - sharrace na gaba daya da kuma na kebe na daga cikin sabuba na sharri dukkanin su da kuma dukkan wasu sabuba na sharri dukkaninsu , ya zo a hadisi ba wanda zai roki Allah da kwatankwacin su.
Na daga cikin abin da ya dace maimaita tunatar da shi, shi ne; taimakekeniya bisa ga daukan mataki na kariya ta hanyan bin nusarwan bangaren lafiya domin a samu daga kowa da kowa a tsallake wan nan musiba mai tsanani da kuma wannan tsanani wanda ke mai ban wahala, Allah ya  saka da alheri ga jagorori shuwagabanni - Allah ya kiyaye su - bisa ga kokarin da su ke yi na a yaba wurin fiskantar wannan annoba mai dauke jama'a da kuma kwadayin su mai tsanani wurin ingancin samun lafiyan 'yan kasa da kuma mazauna to lallai kiyaye koyarwansu da ka'idodin su zai karanta daga wan nan cutan na wan nan fairos din kuma Allah zai daga wan nan bala'i da izinin Shi, to rahamar Allah tana da yalwa kuma farin ciki na kusa Allah Madaukakin sarki yace : (Allah Ubangijinku ya ce ku roke Ni zan amsa muku lallai wadanda su ke girman kai bisa ga roko na za su shiga jahannama suna masu kaskanci) Allah ya sa mana albarka bisa alkur'ani mai girma .
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya halicci dukkan komai ya kaddara shi kaddarawa, kuma ya yalwaci dukkan komai a ilimi ya iyakance dukkan komai a adadi , Allah ya kasance Mai ji kuma Mai gani ina kyautata yabo ga Ubangijina kuma ina gode masa bisa ga ni'imomi da ba mai iyakance su sai shi, da abin da muka sani cikinsu da wanda ba mu sani ba, na shaida ba bu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya ba abin da zai gagare shi a kasa ne ko a sama na daga bada agaji da shi kuma duk wanda ya nemi agaji na gaggawa a wurin Allah to Allah zai tsirar da shi wanda kuma ya roki Allah kariyarSa to Allah zai kare shi wanda ya nemi taimakon Allah to Allah zai shiryar da shi ya bashi mafaka, haka nan kuma UbangijinKa ya isa mai shiryarwa kuma mai taimako na shaida Annabinmu kuma shugaban mu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, Allah ya turo shi da albishir kuma da gargadi, ya Allah ka yi dadin tsira da albarka ga bawanKa kuma ManzonKa Muhammad da iyalanSa da sahabbanSa dadin tsira da aminci mai yawa bayan haka ; ku ji tsoron Allah Mabuwayi da daukaka domin da tsoron Allah ne Allah ya ke bada kyautan lada kuma ya tsiratar daga azaba.
Ya ku mutane lallai ku kuna ji kuma kuna gani abin da ya faru a doron kasa na daga bakin ciki mai tsanani lallai annoba bala'i  na gamagari ba mai dauke shi sai Ubangijin talikai , na daga cikin sabuba na dauke shi shi ne taimakekeniya wurin daukan sabuba na shari'a da kuma na ilimin  rayuwa da su ke na halal mafi girman sabuban da su ke sa a dauke shi shi ne tuba na gaba daya daga  al'umma dukkansu, Allah Mabuwayi da daukaka ya na tausayawa ta hanyar  tuba da adu'a, abin da bayin shi ba za su iya dauke shi ba Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Halal a bayyane ya ke kuma haram a bayyane ya ke) Allah ya bamu kissa na dauke azaba daga mutanen Yunus ta hanyan tuba sai Allah ya ke cewa : (Ba don wata alkarya ta kasance imaninta ya mata amfani ba face mutanen Annabi Yunusa yayin da su ka yi imani mu ka yaye musu azaban walakanci a rayuwan duniya mu ka jiyar  da su dadi zuwa wani lokaci) .
Ibnu kasir Allah ya mishi rahama ya ke cewa: yayin da su ka rasa Annabinsu suka zaci cewa lallai azaba fa ya kusa zuwa gare su sai Allah ya jefa a cikin zukatansu tuba suka sanya rigar masu ibada Su ka rarraba tsakanin dukkan dabbobi da 'ya'yayensu san nan su ka yi ta ambaton Allah suna komawa zuwa gare shi har dare arba'in, yayin da Allah ya ga haka daga gare su da gaskiyan zukatan su da tubansu da nadama bisa ga abin da ya shude sai Allah ya yaye musu wannan azaba bayan an zuro azaban kusa gare su.
Ya ku bayin Allah lallai Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce.            

ALBISHIRINKU DA RAMADANA




 
الوصف: cbc250ed-6a0e-4037-8d54-a9eb3d0a0577المترجم : أمين سعد عبد الله

التاريخ :1/9/1441هـ
اللغة : الهوسا
Hudubar Masallacin Annabi 1/9/1441AH 24/4/2020 AD shaikh Salah Bin Muhammad Al budair
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah,bisa ga riskan watan ramadan, godiyan da zata cika ni'imarSa da kyautarSa, ina gode masa bisa abin da ya kwararo ya yalwata na alheri, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke, ba shi da abokin tarayya, ba wani abin bauta bisa cancanci koma bayanSa, kuma na shaida Annabinmu kuma shugabanmu  Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne. Kuma AnnabinSa  kuma zababbe ne, abokin ganawarsa masoyinSa kuma yardajjenSa, kuma zababbenSa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa, har abada muddin safiya na bayyana haske na fitowa.
Bayan haka
Ya ku masu azumi!
Ku ji tsoron Allah ta hanyar yin aiki zuwa ga neman yardarSa, da nesatan saba masa, (Ya ku wadanda suka bada gaskiya an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka gabace ku ko zaku samu takawa).
Wannan watan ramadana ne ga ta ta kunno, wata ne na busowan alheri ga ta ta bullo,  ga haske mai ban kaye ya sauka, ga shaidan abin jefewa ya kaskanta, An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Idan ramadan ya shigo sai a bude kofofin Aljanna, a rufe kofofin jahannama a kuma daure shaidanu) Buhari da muslim ne suka rawaito. A riwayar Muslim (a bude kofofin rahama) a riwayar Tirmizi ( sai a rufe kofofin wuta ba za a bude ko kofa guda ba, a kuma bude kofofin aljanna ba zaa rufe ko da kofa guda ba daga cikin su).
  Allah Mai girma wani irin abin farinciki ne wannan ! wani irin abun kaye ne wannan! Wani irin kyauta ce wannan! Wani irin kawa ne wannan! Wani irin daukaka ce wannan!
Ya ku musulmai !
Barkan ku da watan ramadana da  ke cike da kamshi, mai kore gurbacewa, dukufaffen annoba ko dare mai saibi ba zai iya gurbata hasken shi da kayen shi da daukakan shi ba, kada ku ji a ranku kamar wasu 'yan fursina da ke kulle cikin bakinciki wadanda suka hadu da jarabawa, to alfijir zai bayyana ka zama kana da aminta, domin kyakkyawan fata na ga wanda ke da aminta, fatan ka na alheri na bakin ka, yin sika da Allah ya isanmaka,
Zamu rayu cikin yanayi mai dadi tamkar kaka bayan bakinciki *
Kai ka ce bamu dandani daci a jiya ba.
Ku yi fatan alheri  duk da samuwar annoba da firgicinta, to zaa kashe wutanta da giragizai,
 Ku yi fatan alheri da sannu zaa yaye mana bakinciki, jamaa da ke shaukin masallaci su dawo,
Ku yi fatan alheri Allah zai hada mu mu ji dadi da abokai da sa'anni.
Bushara zata zo sai mu samu sa'ada da aminci yayin safiya mai fara'a da iska mai dadi.
Ku taho zuwa ga kofofinku an bude su, duk matafiyi mai yawo garuruwa ya fire zuwa inda ya ke so.
Ku kankan da kai,Allah shine Mafi karamcin wanda aka roka, yana warkar da musibu duka da falalarSa. 
     Ku kankan da kai da adu'a don ba mai daukewa ko tunkudewa ko gusarwa,  kuma ba mai yaye wannan annoba sai Allah  wanda ke  mallakar cutarwa da amfanarwa,  wanda ke tasarrufi a cikin halittun sa da abin da ya so  wanda halittu suka  rusunawa kasaitarSa  da daukakarSa , kuma    dukkan halittu  suka zama ba komai ba a gaba gare shi  , suka  tsananta roko suna maimaitawa ya  Ubangijinmu ya Ubangijinmu,  Hasanul Basari yake cewa a fadin sa :-(Sai Ubangijinsu ya  amsa musu) ,  ba su gushe ba suna cewa ya Ubabngijin mu ya Ubangijin mu har aka amsa musu .
Ya mai yaye damuwa da bakin ciki £ Gare ka muke guduwa  don neman mafaka

To ya  Ubangijin mu wannan annoban ya illan ta kuma ya boye wasu abokai  ya Allah ka janye shi  kar ka tsawaita wani tsanani akan mu a hannun ka ne yayewa ya ke, ya Allah  kar ka nuna mana  cikin wanda muke kauna sai abin da muke so , ya wanda  muke so ya  mafi rahamar  ma su rahama.
 YA KU MUSULMAI:
Ku sanya Alkur'ani a gidajen ku kamar kukan zuma  ku sanya ambaton Allah a watan ku abin maimaitawa , ku yi mudarasan  Alkur'ani   tare da iyalanku  da 'ya'yan ku tun daga farkon sa zuwa karshensa  ku kamsasa lebban ku da shi, ku turara bakunan ku da alkur'ani , ku raya mazaunin  ku  , da  unguwannin ku   da  gidajen ku da tilawa da  tarawihi  da  kunuti.
Ku yi sallan tarawihi a gidajen ku a  daidaiku ko a jam'i ko da ya ke   haduwan ya fi  sa nashadi  ga  iyalai kuma ya fi kwadaitarwa, kuma ya fi zamewa abin koyi  idan har mutum bai da karfin yin ta sai ta hanyar koyin din kuma ya ji tsoron barin ta in har a shi kadai zai yi  to a sallace  ta jam'i din shi ya fi dacewa  kuma shi  ya fi falala wurin ribatan dararraki masu daukaka,  idan kuma mutum yana da karfin himma  na yi shi kadai kuma ya himmatu da haka , ya kwadaitu da  ya sallace  ta shi kadai don neman kushu'i ko tsawaita karatu da ruku'u da sujjada , to zai iya yin hakan , al'amarin a cikin shi akwai yalwa .
Baya inganta mace ta limanci maza ko da a tarawihi ne ko ga dangin ta a cikin zance  mafi inganci ,  amma za ta iya limantan mata a gidan ta .

YA KU MUSULMAI:
Idan larura ta saka killacewa mataki ne na kariya  da ya hana ku yawo da shawagi , da kaura daga nan zuwa can to, lallai kuna da  wani fage na rahama a watan azumi da ba  haramtattu ba  da kuma wasu alheri dake busowa wanda ba a iya killace su , kada ku kasance  cikin wadan da za su shagalta da abubuwa masu shagaltarwa, suka gafala daga watan  alheri da rahama , wayoyi na   cikin abubuwan da aka kirkira aka sana'anta wanda abubuwan ban mamaki   a cikin su  na da yawa ababen nema a cikin su sun yawaita , faratunan su sun ta'allaka da mu,  abubuwan da ake shiga a cikin su sun sha bamban to ku kiyaye kar ku bar waya ya cinye mu ku lokutan wata mai albarka , wanda ba da jimawa ba zai zo ya wuce .
Ya kai wanda ke jin radadi da bakin ciki bisa rufe masallatayya ya rasa haduwa da gamayya a sahu, da haduwa a juma'a da jam'i da tarawihi, kar ku yawaita abubuwan na makoki kamar wake, kada kuma  kururuwa  ta musiba ta dauke ku domin haka bai da wanin amafani,  ku yawaita ambaton Allah  da tasbihi a gare shi da girmama shi da tunani cikin ayoyinSa da daukan izna ku yawaita nuna bukatuwar ku zuwa ga Allah da istigfari  , da bada hanzari da lura da wa'azantuwa .
Duk wanda bai ba da hanzari ba a yau to yaushe ne zai bada hanzari
Abin da Ubangiji na ya so ya kasance sai ya kasance * mutum ya kan kai kan shi ga halaka wasu lokuta
Rana ba ta bullowa ko ta bace  fa ce da umarnin  wanda sha'anin sa abin mamaki
Muna da sarki mai kyautatawa a gare mu * mu su wane ne in ba falalar sa a gare mu ba , tsarki ya tabbata a gare ka ya Allah
Ka yi aminci ka yi aminci  ka cika ni'imomi a gare mu kuma  ka cika
Allah ne Ubangiji na kuma  shi ne mai mulki  ba yi da abokin tarayya cikin mulkin sa        

   YA KU MUSULMAI:
Mai yawan dauwama da dogewa akan da'a  wanda ba ta gushe ba tana cikin dabi'arsa da halin sa , bai datse ba daga gare su sannan wannan annoba ya yi shamaki ya killace tsakanin shi da su  tare da son sa na yanke zuwa aikata su , da an kadarta a gare shi ,  to ana sa ran Allah zai rubuta mishi ladan shi cikakke , to, ana muku albishir ya ku wadan da kuka kasance kuna raya masallatayya da salla  da tsayuwa da tarawihi da karatun alkur'ani   albishirin ku ya ku wadan da kuka kasance  kuna shimfida sufura  don shayar da masu azumi Ubangijin ku Ma'abocin da'a ne da tausayi da karamci.
An karbo daga Jabir Allah kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Lallai a cikin madina akwai wasu mutane, ba wata tafiya da za ku yi  ko ku keta wani kori  face sun kasance tare da ku, '' rashin lafiya  ne ya tsare  su'') a wata riwaya face sun yi tarayya  da ku a lada,) Muslim ne ya rawaito. A  BUHARI kuma a  riwayar Anas. Allah kara yarda a gare shi (uzuri ne ya kange su).  
 Ibnul Munzir Allah ya masa rahama yace : (wanda bai samu zuwa ba sabo da uzuri to yana daidai da wanda ya je)
Muna kwadaitar da masu kyautatawa, masu abin hanu, da su yi tarayya a wannan hobbasa na aikin gidauniyar  ramadan na madina  wanda ke nufin ciyar da talakawa da miskinai  wadanda dalilin hana fita ya musu illa da  tsayawar ayyuka ,  mafi alherin sadaka shi ne sadakan cikin watan ramadana , (Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya kasance mafi kyautan mutane  kuma kyautan sa ya fi yin sa cikin azumi)
   Wanda ya shayar da mai azumi yana da kwatankwacin ladan shi ba tare da an tawaye  wani abu ba na daga ladan mai azumin ba, . shekul islam Ibn Taimiya Allah ya mishi rahama yana cewa  :- (''Abun da ake nufi da shayar da shi ; shi ne kosar da shi ''
An karbo daga salt Dan Basdam ya ce:- ''Hammad Dan Abi Sulaiman yana shayar da mai azumi hamsin  a ko wani rana a ramadan  , to idan kuma daren salla ya zo sai ya tufatar da ko wannen su tufafi –tufafi''.
Ku tausayawa  masu rauni da talakawa da gajiyayyu, to duk wanda baya tausayawa ba za a tausaya mi shi ba , ku sada zumunci da sadakoki .
Ba wata dukiya da  za ta saraya  idan ta haifar da godiya ga ma'abotan ta * sa dai dukiyan marowaci  ita take saraya ,  ina fadin abin da kuke ji kuma ina neman gafaran Allah  to ku nemi gafarar sa domin lallai shi ya kasance mai yawan gafara ne ga ma su komawa gare shi .




HUDUBA TA BIYU
Ya kai dan uwa na dan uwa na wanda aka shafe shi da wannan bala'i, aka  hada shi da wannan annoba aka killace shi aka yi nesa da shi  aka killace shi daga mutane  kada  ka kuntata abu mai fadi mai yalwa.
Duniya bata yi kunci ba gare ka da fadinta*
                                           Ba a rufe ma kofar yafiyar Allah ba


Ku yi bushara da waraka da lafiya, ku bazama zuwa ga sallah, ku kyautata zato ga Allah, ku debe kewa da ambaton Allah, da karatun Alkur'ani, kada ka yanke tsammani kada ka yanke kauna daga rahamar Allah, ku dogara ga rayayye wanda bai mutuwa.
Kada ka kashe kan ka da damuwa da bakinciki, domin damuwa ne dafi mafi hadari, ka nemi tsarin Allah daga damuwa da bakinciki, ba wani abu ba ne face wata musiba da ta sauka  kuma za ta gushe, kuma abin da iska ya dauko   sannan kuma zai bace  yarda da kaddara  kamar wata ganima ce na yammaci  kuma babbar itaciya ce ga maras lafiya ,  wannan firgici na tsorata  mara fasalin bayi da wani fa'ida  kuma ba a bada lada ga wannan cutan , lallai mafi girman sakayya  na ga mafi girman bala'i kuma idan Allah ya so mutane sai ya jarrabe su , duk wanda ya yarda to yana da yarda, duk wanda ya yi fushi  to, yana da fushi .
Muna mika jajen mu ga duk wani wanda ya rasa dansa da kuma   wacce ta rasa dan ta ,  abun kaunarsu  mai kima , muna  fatan shahada ga wanda ya mutu cikin  musulmai a dalilin  wannan annoba.
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah  su tabbata a gare shi ya ce:- (Shaihidai guda biyar ne ; wanda annoba ta kashe shi, da wanda ya mutu ta sababin ciwon ciki  da kuma  wanda ya mutu a ruwa  da kuma wanda gini ya fadi a kansa , da kuma wanda ya mutu a tafarkin Allah ) Buhari da Muslim ne suka rawaito
An karbo daga Rashid Dan Hubaish  Allah ya kara yarda a gare shi ,cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya shiga ga Ubadatu Dan Samid yana ziyartan shi a rashin lafiyan sa , sai  Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-ko kun san shahidi a cikin al'uma ta? sai Ubadata dan samid ya ce ya Manzon Allah :- shi ne mahakurci mai neman lada a wurin Allah , sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- ''  lallai shahidai a cikin al'umata in dai haka ne to, dan kadan ne  wanda aka kashe su a tafarkin Allah sun yi shahada , da wanda ya yi mutuwar annoba shi ma ya yi shahada, da kuma  mutuwa a ruwa shi ma shahada ne da mutuwa dalilin ciwon ciki shi ma shahada ne , da  mutuwa ta dalilin haihuwa dan na ta zai ja ta da cibiyar sa zuwa Aljanna
Abul Auwam ya kara da cewa '' da gobara da kuma ambaliya '' Ahmad ne ya fitar da shi
 YA KU MUSULMAI :-
 Ku lazimci matakan kariya da  nusarwa  da fiskantarwa , wanda ke hana yaduwan korona  ku kiyaye taruwa a wurin buda baki da sahur a cikin ramadana .
 Da kukan mutuwa gara killacewa a gida ,  ku yi salati da aminci bisa ga Ahmadu mai shiryarwa mai ceton bayi gaba daya
Duk wanda ya yi mar salati guda to Allah zai mar salati guda  goma.