الأحد، 22 مارس 2020

HAKURI BISA BALA'I


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Abdullahi Bin Abdurrahman Albuaijan  18-7-1441AH /12-3-2020AC
Hudubar Farko:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Mai amsa adu'a Mai yaye bakin ciki da bala'i ina gode mishi bisa ni'imomi daban daban, muna neman tsarin Allah daga sharrin abin da ya halitta na daga  bala'i da annoba yana sanya shi ga wanda ya so kuma ya tunkude shi daga wanda ya so.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bai da abokin tarayya, kasaita da yabo nashi ne da buwaya da girmame girmame da dawwama da wanzuwa duka nashi ne,  na shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne cikamakin Annabawa ma'abocin isra'i da mi'iraji da tabki da kuma lema, tsira da amincin Allah su tabbata a gare Shi da iyalansa da sahabbansa da wanda ya bisu da kyautatawa a halin sauki da kuma halin cuta.
 Bayan haka:
lallai mafi  kyan  zance shi ne littafin Allah mafi  alherin shiriya  shi ne  shiriyan  Manzon  Allah tsira da amincin Allah su tabbatauma a gare shi mafi sharrin al'amura sune fararrunta, dukkan bidi'a bata ce kuma dukkan bata na wuta.
ya ku bayin Allah : ina muku wasiyya da ni kaina da tsoron Allah, domin ita ce  mafaka, kuma  da bin sunnar  Annabi ne  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ake samun kubuta (Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah rai ya dubi abin da ya kaddamar sabo da gobe, ku ji tsoron Allah, lallai Allah Masani ne ga abin da ku ke aikatawa).

Ya tawagar musulmai
Duniya gida ce ta musibu da kuma bala'u da kuma jarabawowi da kuma fitintinu  gida ce ta jin zafi da kuma haduwa da ba- zata, gida ce ta radadi da kuma azaba da kuma lafiya da kuma cuta da rashin lafiya da kuma waraka da sauki da kuma bala'i gida ce ta farin ciki da bakin ciki, gida ce ta jin rashin dadi da kuma bacin rai da tsanani da wahalar duniya, kurkuku ce ga mumini kuma aljanna ce ga kafiri, akwai yawan musibu da kuma jarabawowi wanda  Allah ke jarraba mai da'a da fajiri da su, na mumini da kafiri, ba a jira bayan lafiya sai rashin lafiya bayan samarta sai tsufa, bayan wadatuwa sai talauci da rashi, hanyan rayuwa da ba ta canjawa kuma bata sauyawa daga su ne a duk yanda ilimi ya ci gaba aka samu habaka a'aha ko da dan adam ya kaura ne zuwa sarari na sama da kuma wata ko da ya kutsa cikin nitson karkashin kasa da koguna ya zauna a can dole ne zai hadu da tawaya da kuma gazawa kuma ilimi da hankali yana i'itirafi da gazawa irin na duniya.
(ya ku jama'r  aljanu da mutane in kuka samu damar ku fita daga sassan  sammai da kassai to ku fita, baza  ku fita ba sai da karfi ).
Lallai ita ce kudura  ta Allah wacce take tana da girma mashi'arSa da iradarSa  al'marinSa da hikimarSa dukkan wani abu a hanunsa ya ke al'mari nashi ne kafin da bayan, abin da ya so ya ke kasancewa, abin da bai so ba bai kasancewa, ba wani abu da ku ke so face abin da Allah ya so ba'a tambayan shi game da abin da ya ke aikatawa, sai dai al'marin shi idan ya so wani abu zai ce da shi ne kasance sai ya kasance tsarki ya tabbata ga Allah wanda mulkin komai ke hanun shi kuma zuwa gare shi za ku koma .

Ya ku bayin Allah :
Ya dace ga mumini a lokacin tsanani da yalwa da kunci da yalwa da wadata ya tuba zuwa ga Allah ya fawwala al'amarinshi zuwa gare shi ya nemi mafaka a wurin Allah  ya dogara gare shi duk wanda ya dogara ga Allah to Allah ya isam mashi kuma ya sani cewa duk wani abu da ya same shi bai kasance da ya kuskure shi ba duk kuma abin da ya kuskure shi bai kasance da ya sameshi ba abin mamaki da al'amarin mumini dukkan al'amuransa alheri ne a gare shi idan abu mai dadi ya same shi sai ya gode sai ya kasance alheri a gare shi idan kuma cuta ko wani abu mara kyau ya same shi sai ya yi hakuri hakan sai ya zama alheri gare shi (Ba wani abu da zai samu na musiba a doron kasa ko kuma a kan kawunan ku face yana rubuce a littafi kafun a halicce ta lallai hakan  ya ke gudana a wurin Allah, domin kada ku yi bakin ciki bisa ga abin da ya tsere muku ko kuma ku yi farin ciki bisa ga abin da ya zo muku Allah ba ya son mai takama mai  alfahari )
 To ya wajaba a gareku ku yarda ku nemi lada a wurin Allah ku nemi lada daga wurin Allah da sakayya ku mika wuya ga abin da Allah ya kaddarta ya hukunta ku sakankance ladan Allah bisa ga musiba da kuma cuta. Allah ya ce (ka yi albishir ga masu hakuri wadanda idan musiba ta same su sai su ce daga Allah muke kuma gare shi za mu koma wadan nan suna da kyakkyawan yabo daga wurin Ubangijinsu da kuma rahama wadannan su ne shiryayyu).

Huduba ta biyu

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya shar'anta halal da haram, Mahaliccin rayuka da jikkuna ya tunkude musibu da kuma rashin lafiya Mai yin ni'ma ga bayinSa da lafiya daga abubuwa masu bijirowa na dare da wuni daga  cikin bala'i ya sanya mishi rahama da daukaka da  kankaran zunubai daga cikin cuta ya sanya lada da kuma  adana da tsarkaka bisa ga lafiya da waraka ku kasance masu godiya bisa ga bala'i da azaba ku kasance masu hakuri, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinmu Muhammad amintacce da kuma bisa alayensa da sahabbansa da tabi'ai.

 
Ya ku bayin Allah :

Lallai annoba shi ne abin taimako  ga bakin ciki da kuma tashin hankali sa'an nan da ci baya da kuma tashin tasina gashi ya rikita sashi da yawa na duniya a cikin yan tsirarun kwanaki to ku yi kokari wurin tumbuke shi da kuma iyakance shi, An karbo daga Sa'd dan abi wakkas cewa ya tambayi  Usama dan zaid ya ce menene ka ji daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa game da annoba, Usama sai ya ce na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa (Annoba wata tsoratarwa ce ko kuma azaba ce da Allah ke turo ta ga banu isra'ila ko kuma ga wadanda suke kafin ku, to idan kun ji wani abu makamancinta a kasa to kada ku je kasan idan kuma ta faru a wata kasa kuna cikinta to kada ku fita domin guje mata) Muslim ne ya rawaito

Ya tawagan musulmai
Ku ji tsoron yada jita- jita, kage da kuma kambama abu da kuma tsoratarwa da isgilanci ku gode wa Allah bisa ga lafiya kada ku kai kanku ga bala'i ku ji tsoron sabuban yaduwar cuta da kuma wuraren annoba ku roki Allah lafiya da waraka da sauki  ku katangu da zikirori da adu'oyi duk wanda ya yi fata a wurin Allah ba zai yi hasara ba, ku gujewa kaddaran Allah zuwa wata kadarar Allah ku kankan da kai zuwa ga Allah kada kuma ku yanke tsammani daga rahamar Allah.

** ya ma'boci bakin  ciki lallai  bakin ciki yana  yayewa ****
** albishirinka  da  alheri domin mai yaye bakin ciki shi ne Allah ****
**shi yanke tsammani wani sa'i ya kan katse ga ma'bocin shi****
**kar ka yanke tsammani domin Allah shi ne mai isarwa ****

** Allah yana kawo sauki bayan bakin ciki****
**kar ka gaza ka gajiya lallai mai yayewa shi ne Allah****

**idan an jarrabeka to ka zama kana da aminci da Allah ka yarda  da shi****
**lallai wanda ya ke yaye bala'i shi ne Allah****

**idan Allah ya hukunta kawai ka mika wuya bisa ga kudurarSa ****

**mutum baida wani hila ko dabara cikin abin da Allah ya hukunta ****

**na rantse da Allah ba ka da wani koma bayan Allah ****

**Allah ya isan maka a ko wani abu kana da Allah ****

** ya ma'aboci bakin ciki lallai bakin ciki abin yayewa ne ****

** albishirinka da alheri lallai mai yaye bakin ciki shi ne Allah ****

Ya Allah Mai yaye bakin ciki ya mai amsa adu'a ka yaye mana bala'i ka dauke mana cuta ka gaggauto mana da waraka ka hore mana magani ba abin bautawa da gaskiya sai kai, tsarki ya tabbata a gare ka, mu mun kasance cikin wanda suka yi zalunci
Ya Allah ka tunkude mana tsada da annoba da riba da zina da girgizan kasa da bala'u da mummunan fitina abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya boyu daga gare mu musamman haka ma da sauran garuruwan musulmai baki daya.
Ya Allah ya Mai bada mulki makwarkwadan mu na hanunka hukuncin mu a hanunka ya ke abin da ka hukunta game da mu shi ne a'dalci muna neman tsari gareka daga mummunan kaddara da kuma fadawa kololuwa na tsiya da dariya na makiya da kuma saukan bala'i da yaduwar annoba , ya Allah ma'aboci  kasaita da girmame girmame ya Mai saukar da kyauta kai ne ka isar mana madalla kuma da abin dogaro ka gyara mana sha'ninmu gaba daya kar ka kyale mu zuwa ga kawunan mu ko da kebtawan ido ne muna rokonka amincin da bayansa babu jirkita  , da yarda wanda bayansa ba fushi da kuma yaye bakin ciki wanda bayansa ba bakin ciki , ya Alla gareka muka dogara kuma zuwa gareka muka mika wuya kuma zuwa gareka ne za mu koma muna neman tsarinka daga sharrace- sharracen kawunanmu da kuma sharrin ko wace dabba da kai ke rike da makwarkwadanta .                  
  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق