الأحد، 22 مارس 2020

ALLAH MAI TAUSAYI NE GA BAYINSA


Hudubar Masallacin Annabi Na shaikh Ahmad Dalib 25/7/1441AH/ 20/3/2020AC
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne.tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da aminci tabbatacce.
(Ya ku wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face kuna musulmai)
(ya ku mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji tsoron Allah da ku ke roko da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance mai tsaro ne a kan ku.)
(ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta mai girma.)

Lalle zance mafi gaskiya shine littafin Allah,  kuma  mafi kyaun shiryarwa  shi ne shiryarwan Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, mafi sharrin al'amura shi ne  fararrun su , kuma dukkan fararrun abubuwa bidi'a  ne  , kuma dukkan bidi'a bata ce  , kuma dukkan bata na wuta 
Bayan haka:
Ya ku mutane
Ku sani lalle Ubangijinku Allah ne wanda ba abin bautawa da gaskiya sai shi,ya yalwaci dukkan komai a rahama da ilimi, ya halicci dukkan komai ya kaddara shi kaddarawa, ya iyakance dukkan komai a adadi, ya gudanar da shi gudanarwa,
Ya yi ludufi da abin da ya so cikin abin da ya ke so zuwa ga wanda ya so. Ya kasance da boyayyiyar kaddararSa da iliminSa mai zurfi goni ne Mai tausayi  ga abin da ya boyu na daga halittunSa , da kuma zartarwa ga hukuncin sa .
 Ya yi ludufi da basirarSa bisa ga abin da ya ke na gani na hakika sai ya riske shi, yayi ludufi   da jinSa ga boyeyyen sautuka  sai ya tantance su , ya yi ludufi da ilimin sa   ga abubuwan da suke kananu  masu halartowa a zuciya  sai ya  banbance su ,
    (Wanda ya fari halittan sammai da kasa,  ta yaya zai kasance yana da Da a halin  bai da mata , kuma  ya halicci  dukkan komai  a hali kuwa shi masani ne ga dukkan komai. Wancanninku shi ne Ubangijin ku ba abin bautawa da gaskiya sai shi  mahaliccin dukkan komai , to ku bauta mishi lallai shi  wakili ne ga dukkan komai,  gani ba ya riskan shi  a hali  kuwa shi  mai tausayi ne goni ).

(Kuma ku boye fadin ku ko ku bayyana shi , lalle shi masani ne  ga abin da ke cikin kiraza . Ku saurara ashe , bai sani ba ; wanda ya yi halitta alhali kuwa shi Mai tausayi ne  goni).
Ya yi ludufi ga abubuwan da suka boyu na wahayin sa  tun daga mulakutin sammai da ayoyinSa da ake karantawa wanda aka sauke su a rarrabe ga matayen Annabi ma'abota dakuna tun daga Baitul Izza har zuwa gidan Annabtaka
(Ku tuna abin da ake karantawa a gidajenku na daga ayoyin Allah da hikima kuma lalle Allah Mai ludufi ne mai bada labari).
Ya zartar da ludufin al'amarin shi, ruwa daga sararin sama zuwa doron kasa inda ba tsirrai ko shuka, ya shayar   da shi zuwa ga tsirrai   da jijiyoyin itace masu koshi da ruwa ya isar da ruwa mai dadin sha ga lambuna.

(Ashe ba ka ga Allah ya saukar da ruwa daga sama  sai kasa  ta zama koriya  lallai Allah mai ludufi ne kuma goni).
Ya zartar da ludufin shi cikin halittun shi  da irin ludufi na halittan sa  zuwa ga  mai raya bitane ya fitar da su, da tsanani irin na jiki  sai ya halaka ta,  da kuma  gungu mai yawa sai ya rarraba su, kuma da dunbin  dukiyaya halaka ya wargaza shi,  Ya yi shawagi  ga wuyan jabberawa  sai ya kaskantar da su,  da lafiya na yanayin su sai ya illantar da ita, da tabbatattun kafafuwan su sai ya zamar da su, ya daga benaye abin daukakawa sun  tsawaita da runduna  abin karfafawa, da masu yawan ibada da masu bauta  da masu keta iyaka da masharrata.
Ya haura zuwa ga  biranen rayuka masu cunkoso da jikuna da suke hade babu sauti na motsin kafa ko  shafa, kamar ba a rayu ba a jiya.
Ya yi gaba da masoya ya muamalance su da halin  makiya, sai suka zama sun yanke masa zumunci sun yi nesa da shi, sai shamaki ya katange tsakanin masoya juna.suna yiwa rogo kallon kitse tamkar yadda mai jin kishi ya ke kallon kawalwainiya.
Ba don komai ba sai don wani abu da ya faru daga gare mu, da wani abu da ya dauke daga gare mu, kada ku zaci cewa makiyi ya yi galaba ne, sai dai Mai kiyayewan ne (Allah) ya juya baya. Ko zasu kankan da kai, ko zasu komo, ko zasu wa'azantu.
Tsatsan zukata ta yawaita, to sai Masanin gaibi  ya tausasa, duk abin da ya yi tsauri zai yi rauni, kuma duk abin da ya yi taushi zai yi tsauri, domin Allah ya dauraye wadanda suka yi imani ya koke kafirai. Kuma ya san wadanda suka yi nifaka.kuma ya dauki fansa daga wadanda suka yi laifi ya warkar da zukatar muminai,kuma ya riki masu shahada a cikin su, lalle Ubangiji na Mai ludufi ne ga wanda ya so. lalle shi Masani ne Mai hikima.    

Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya isa, tsira da aminci ga AnnabinSa zababbe, da iyalansa da sahabbai ma'abota biyayya da wafa'i, da wanda ya bi da kyautatawa ya bi sawunsu.
Bayan haka ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa, duk wanda ya ji tsoron Allah zai sanya masa mafita kuma ya azurta shi ta inda bai zata ba. (Duk wanda ya dogara ga Allah to shi ya isan masa, Lalle Allah Mai iyar da umarninSa ne,) Lalle Allah ya sanya ma'auni ga dukkan komai.(Wanda ya ji tsoron Allah zai sanya masa sauki cikin al'amarinsa) (Wanda ya ji tsoron Allah zai kankare masa laifukansa kuma ya girmama ladansa.)
     Ya ku musulmai!
Allah Mai tausayi ne ga bayinSa yana tausaya wa mai karamin karfi dalilin mai rauni cikin halittu, ko da masu karfi sun ki, yana zartar da ludufinSa mai zurfi ga kaskantacce a cikin bayinSa ko da masu izza sun ki, yana azurta wanda ya so Shi Mai karfi ne Mabuwayi tsarki ya tabbata a gare shi,.. yana karanta ni'imomi masu yawa ga bayinSa kuma ya habaka kadan na daga da'a ga bawanSa,
Iya gwargwadon zurfin ludufi iya gwargwadon riskarsa, shine wanda in ka kira shi zai amsa ma, in ka nufe shi zai baka mafaka, kuma in ka kaunace shi zai kusanto ka, kuma idan ka masa da'a sai ya saka maka, idan ka saba masa sai yana iya baka waraka , idan ka juya masa baya sai ya kira ka, idan ka kusanto shi sai ya shirye ka.
Yana sakanya a gare ka in ka kyautata yana yafiya a gare ka in ka gajarta duk wanda ya rusuna a gare shi zai daukaka shi wanda ya nuna bukatuwa zuwa gare shi zai wadata shi ba ya bukata daga masoya wasu hanyoyi ko kuma sabuba umarninSa kusantarwa ne haninSa kuma ladabtarwa ne kyautanSa zabi ne haninSa adana ne matattaran ludufanSa tausasawa ne da kusantarwa shi makusanci ne mai amsawa duk wanda ya shaida Allah  ga  zuciyansa to zai dauke masa duk wasu abubuwa masu yawa mafi ludufi da kuma mafi girman shi mafi darajan shi da daukakan shi shi ne ya yi  ludufi cikin bayinSa ta hanyan taimakawa a cikin kaddara kuma da yarda da kuma tawali'u da  tuba da kankan da kai da komawa da rusunawa da imani.
Bayan  haka ya ku bayin Allah
Ku sanya gidajenku alkibila ku tsaida sallah ku yi da'a  ga wanda Allah ya jagorantar da al'amuranku a gare su cikin da'a wa Allah ku yi sallah ku yi salati da aminci bisa ga alkibila mafi tsarki da kuma mashaya na farin ciki da kuma  Annabi mafi daukaka da kuma waliyyi mafi kusa shugabanmu Muhammadu Annabi Ummiyi hakika Allah ya zabe shi, lallai Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi .


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق