Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah, muna gode maSa kuma muna neman taimakonSa
Muna neman tsarin Allah daga
sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu,
duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai
shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke
ba shi da abokin tarayya,kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma
ManzonSa. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da
sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.
Bayan haka, ku ji tsoron Allah
-ya ku bayin Allah- cancancin tsoronSa, duk wanda ya ji tsoron Ubangijinsa zai
tsira wanda ya bijire daga ambatonSa zai fadi.
Ya ku musulmai :
Ni'imomin Allah ga bayi basu kididdiguwa, (kuma duk wani abu da ke gare ku na ni'ima to daga Allah ne).
Harshe na daga cikin ni'imomi masu girma da
wasu ludufa na daga aikin Allah masu ban mamaki, Allah ya baiwa da shi ne ga
bayinSa sai yace :(Ase bamu sanya idanuwa biyu gare
shi ba da harshe da lebba biyu)?
da shi ne ilimi da bayani da karrama Dan-Adam
ke samuwa Allah Madaukakin sarki ya ce :(Mai-rahama,
ya koyar da Alkur'ani, ya halicci mutum, ya sanar da shi bayani.)
Duk abin da ya ke fada ana kiyaye shi a
sahifarsa wacce da ita zai hadu da Ubangijin Shi ranar Alkiyama, Allah
Madaukakin Sarki ya ce :(Ba ya furuci da wata magana
face like da shi akwai mai tsaro halartacce) sabo da haka ne Allah
ya umarci bayinSa da su fadi magana madaidaiciya, sai yace : (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi
magana madaidaiciya) kamar kuma yadda ya umarce su da fadi magana
mafi dadi mafi kyau, (kuma ka ce wa bayiNa su fadi kalma wacce take mafi kyau)
Na daga cikin wajibabbun imani kiyaye harshe
face daga alheri, Manzon Allah tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi ya
ce : (Duk wanda ya kasance yana imani da Allah da ranar lahira to ya fadi alheri ko
ya yi shuru.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Allah ya yabi bayinSa muminai da suke bijirewa wasa na fadi ko aiki sai
yace : (Da wadanda suke juya baya ga lagawu(wasa).
Musulmi shine wanda ya kiyaye harshensa, Manzon
Allah tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Musulmi shine wanda musulmai suka kubuta daga sharrin
harshensa da hannunsa). Buhari
da Muslim ne suka rawaito.
Ta hanyar kiyaye shi ne ake samun fifikon
matsayi tsakanin bayi, an tambayi Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi wa ya fi alheri cikin musulmai sai yace shine wanda musulmai suka aminta daga harshensa da
hannunsa).Muslim ne ya rawaito.
Kuma Aljanna sakayya ne ga wanda ya kiyaye
harshensa. Manzon Allah tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Wa zai kiyaye min bakinsa da farjinsa na lamunce mishi aljanna). Buhari
ne ya rawaito.
Harshe karamin abu ne amma yana da amfani mai
yawa.kuma ya kan iya kasancewa mai tsananin cutarwa sabo da haka Annabi ya nemi
tsari daga sharrinsa sai yace : , (Ya Allah ina neman tsarinka daga sharrin harshe na) Abu
Dauda ne ya rawaito.
Kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya tsoracewa sahabbansa da al'umarsa shi, Sufyan
dan Abdullahi Assakafi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Nace ya Manzon
Allah me ka fi tsorace min? sai ya rike harshensa ya ce :wannan).Tirmizi
ne ya rawaito.
Bisa tsoronsa ne sahabbai suka tafi, Abubakar Allah ya kara
yarda a gare shi ya fitar da harshensa sai ya ce :
(wannan shi ya kai ni ya baro ni).
Ibnu Abbas ya kasance yana rike harshensa sai
ya ce :(kaitonka ka fadi alheri za ka rabauta ko
ka yi shuru daga mummuna zaka kubuta, in ba haka ba to ka sani zaka yi nadama).
Harshe hadarinsa na da girma a duniya da lahira,
sau da yawa kalma guda kan bata rayuwar mutane, Ibnu Mas'ud Allah ya kara yarda
a gare shi yace : (Ba wani abu da ya fi bukatar
kulle shi a kurkuku na tsawon lokaci kamar harshe na).
Magana kan halaka ma'abocinsa har ya hadu da
Allah yana Muflisi Manzon Allah tsira da aminci Allah su tabbata a gare
shi ya ce : (ko kun sansa muflis sai suka ce
Muflis shine wanda bai da dirhami ko wani abu na kayan jin dadi, manzon Allah
yace : Lalle muflis a cikin al'uma ta shine wanda zai zo da sallah da azumi da
zakka, ya zo a halin ya zagi wannan yayi kazafi ga wannan, ya ci dukiyar wannan
ya zubar da jinin wannan ya daki wannan, sai a bawa wannan daga kyawawansa,
wancan ma a bashi daga kyawawansa, idan kyawawansa sun kare kafin a kare biyan
bashin da ke kansasai a dauko daga laifukansu a dora kansa sannan a jefa shi
wuta.) Muslim ne ya rawaito.
An tambayi Annabi game
da abin da ya fi shigar da mutane wuta sai yace baki da farji) Tirmizi
ne ya rawaito.
Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi yace :(lallai bawa
zai yi magana da kalma ba zai bayyana mishi (hadarinta) ba, zai zame cikin wuta
a dalilinta fiye da nisan mahudan rana da mafadanta) Buhari da Muslim ne suka
rawaito.
Mafi girman laifi na harshe
shine kiran wanin Allah da sanya mishi kishiya Allah Madaukakin Sarki ya ce :(wa nene ya fi bata sama da wanda ya ke kiran wani komabayan
Allah wanda ba zai amsa mishi ba har zuwa eanar alkiyama a halin su sun gafala
daga adu'arsu)
(Duk wanda ya mutu a halin yana kiran wanin Allah to zai
shiga wuta.) Buhari
ne ya rawaito.
Na daga cikin rokon
wanin Allah akwai neman ruwan sama ta hanyar amfani da taurari, Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace
: Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisul kudsi ( An wayi gari cikin bayi na akwai mai imani da ni da kuma
mai kafurci, to duk wanda yace : Mun samu ruwa ne da falalanAllah da rahamarSa
to wannan shine wanda ya yi imani da ni kuma ya kafurcewa taurari) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Neman tsari daga wanin Allah ba abin da ya ke
karawa mai yinsa sai tsoro da rauni, Allah
Madaukakin Sarki ya ce : (Kuma lalle ne shi, wasu
maza daga cikin mutane sun kasance suna neman tsari da wasu maza daga cikin
aljanu, saboda haka suka kara musu girman kai).
Na daga cikin shirka da
Allah a magana akwai rantsuwa da wanin Allah, Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi yace :( wanda ya rantse da
wanin Allah to hakika ya kafirta ko kuma
ya yi shirka).Muslim ne ya rawaito
(wanda ya rantse da wani addini ba musulunci ba bisa
karya da gangan to shi ya zama kamar yadda ya ce ) bukari ne ya
rawaito
(wanda ya rantse da amana to baya tre da mu) abu dauda
ne ya rawaito
Allah tsarki ya tabbata
a gare Shi ya na da cikakken kamala na mulki na saki waiwai wanda ya sa suna
irin wanda Allah ya kebanta da shi to
Allah zai kaskantar da shi manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare Shi ya ce : (mafi kaskancin suna a wurin
Allah shi ne mutumin da zai sa suna sarkin sarakuna ba wani mai mulki sa Allah)
bukari da muslim ne suka rawaito al'mari na Allah ne shi shi kadan shi ba a'
hada shi da wani a mashi'arSa tsarki ya tabbata a gare Shi a ta bangaren
daidaitawa a lafazi ne ko a ma'na Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare Shi ya ke cewa (kada ku ce Allah
ya so wane ma ya so sai dai ku ce Allah ya so sa'an nan wane ma ya so)
Abu Dauda ne ya rawaito.
Kaddara kudura ce daga
gurin Allah da imani da shi kuma rukuni ne cikin rukunan imani, baa cewa ina ma
da na aikata kaza da kaza zai faru da kaza," ba don ba" na bude aikin
shaidan.
Fushi bisa abin da
Allah ya kaddara na daga magana na cikin al'amarin jahiliyya.
(mai kukar mutuwa in bata tuba ba daga aikinta zata tashi
a ranar alkiyama tana tare da rigar karfe na harshen wuta). Muslim
ne ya rawaito.
Allah ke tafiyar da dare da wuni, kuma zagin
zamani na warware imani ko kuma yana raunana shi,
Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare Shi ya ke cewa (kada ku zagi zamani domin Allah shine zamani).
Muslim ne ya rawaito.
Wanda ya munana zato ga
Allah ya kuma yankewa halittun Allah tsammani daga rahamarSa, to hakika ya kai
kansa ga ukuba ta Allah, wani mai ibada a cikin banu isra'ila yace da wani mai
sabo a cikinsu : (wallahi Allah ba zai gafarta
wa wane ba, sai Allah yace da shi wane ne ya ke min shishigi da rantsuwar bazan
yafewa wane ba, to lalle hakika na gafarta masa kai kuma na rusa aikinka)
Muslim ne ya rawaito.
Abu Huraira –Allah ya kara yarda a gare shi yace : "Na
rantse da wanda rai na ke hanunSa ya fadi kalmar da ta halaka masa duniyarsa da
lahirarsa"
(Wanda yace mutane sun
halaka to shine mafi halakarsu)
Sanin ilimin gaibi ya
kebanta ne ga Allah subhanahu wa taala, Allah
Madaukakin Sarki ya ce : (Kace babu wanda ya san
abin da ya faku a cikin sammai da kasa face Allah),
(wanda ya je gun mai duba ya tambaye shi daga wani
abu to ba zaa karba mishi wata sallah
har dare arba'in). Muslim ne ya rawaito.
(wanda ya je gun boka ko mai duba kuma ya gaskata shi
cikin abin da ya ke fadi, to hakika ya kafirta da abin da aka saukarwa Muhammad
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi)Ahmad ne ya rawaito.
Na daga cikin mafi
girman muharamai fadin magana game da Allah ba tare da ilimi ba,
Allah Madaukakin Sarki
ya ce : (Kace abin sani Ubangiji na ya haramta
alfahasha abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya boyu da zunubi da
rarraba jama'a ba , da wani hakki ba kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da
bai saukar da wani dalili ba gare shi , kuma da ku fadi abin da ba ku sani ba ,
ga Allah ) izgianci da addini ya na
fitar da ma'bocin shi daga cikin addinin Allah madaukakin sarki ya ce :
(Ka ce shin da Allah da kuma a'yoyinSa da ManzonSa
kuka kasance kuna izgilanci ?) (kada ku
kawo wani uzuri hakika kun kafirta a bayan imanin ku)
Kuma karya na daga
cikin munanan zunubbai da alfasha masu aibi kuma shi ne asalin dukkan sharri
shi ne kuma ya ke cikin alamomi na munafunci yana shiryarwa zuwa ga fajirci ,
lallai fajirci yana shiryarwa zuwa ga wuta mutum ba zai gushe ba ya na kirdadan
karya har a rubuta shi a wurin Allah makaryaci .
Mafi munin karya shi ne
wanda ya kasance a kan Allah da Manzon Sa Allah subhanahu wa ta'ala yana cewa (kuma a Ranar Kiyama kana ganin wadanda su ka yi karya ga
Allah fuskokinsu suna masu yin baki . Ashe, babu mazauni a cikin jahannama ga masu girman kai ) Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce : ( duk wanda ya min
karya da gangan to ya shirya makomansa a cikin wuta) Muslim ne ya
rawaito ,( duk wanda yarantse bisa karya yan mai
tune ga al'marin da ya shudai to rantsuwanSa rantsuwa ce ta gamus
(nitsatstsiyan rantsauwa cikin zunubai )
(duk wanda ya rantse bisa ga
dukiyan mutum musulmi ba tare da hakki ba zai hadu da Allah ahalin Allah ya na
fushi da shi ) Bukari
da Muslim ne suka rawaito , na daga cikin karya shi ne iddia'a'I wurin
dangantaka Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(ba wani mutumin da
zai jingina kanshi ga wani mahaifinshi a halin yana sane face ya kafurta ,ko ya
yi da'wan wani dangin da ba nashi ba to ya shirya makomansa a wuta )
Bukari da Muslim ne suka rawaito .
Na daga cikin manyan zunubbai shaidan zur
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ashe ba zan baku lbarin mafi girman zunubbai ba? sau uku
sai suka ce iye ya Manzon allah sai ya ce : hada Allah da wani da kuma cin
zarafin iyaye sai ya zauna da yana kishingide ne sai ya ce ku saurara da fadin
zur bai gushe ba yana ta maimaitata har muka ce ina ma da ya yi shuru ,)
Bukari da Muslim ne suka rawaito . dukkan
musulmi a kan musulmi haramun ne jininSa sa dukiyanSa da mutuncinSa , na
daga cikin manyan zunubbai mutun ya zagi iyayensa suka ce : ya Manzon Allah
yaya mutun zai zagi iyayenSa ?( sai ya ce iye ,
(ya zagi baban wani wanin kuma ya zagi babanshi ya zagi uwar wani wanin kuma ya
zagi mamanshi ) Bukari da muslim ne suka rawaito .
Na daga cikin abubuwa masu halakarwa akwai
kazafin mata katangaggu gafalallu mumunai Allah madaukakin sarki ya ce (lallai ne wadanda suke jifar mata masu kamun kai gafilai, muminai
an la'ne su a cikin duniya da lahira kuma suna da azaba mai girma)
kage jifan wanda ya barranta ne daga abinda bai tare da shi Allah madaukakin
sarki ya ce (kuma wanda ya yi tsiwir-wirin kuskure ko kuwa zunubi sa/annan kuma ya jefi
wani barrantacce da shi to lalle ne ya tattali kirkiran karya da zunubi
bayyananne)
Cin
naman wani shine ambaton dan'uwanka da abin da bai so, kuma yana cikin manyan
zunubai Allah madaukakin sarki ya ce (kada sashenku
su yi giban sashe) Ibnu Abbas Allah ya kara yarda a gare shi shi da
mahaifin shi- yace : (Allah ya haramta giba
kamar yadda ya haramta mushe)
Na daga cikin laifuka na harshe kai komo da annamimanci tsakanin halittu
Allah Subhanahu yake cewa : (kada ka bi dukkan mai
yawan rantsuwa, walakantacce. Mai zunde mai yawo da gulma mai hana alheri mai
zalunci mai zunubi).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : (Mai annamimanci ba zai shiga
a ljanna ba) Bukari da Muslim ne suka rawaito.
Yahya bin kasir Allah ya mishi rahama yace :(Mai annamimanci kan bata cikin saa guda abin da mai
sihiri ke batawa a shekara guda.)
Zagin Musulmi fasikanci ne (ba wani da zai jefi wani da fasikanci ko ya jefeshi da
kafurci face ta dawo zuwa gre shi muddin bai kasance wan nan ma'bocin shin
hakan ya ke ba) Bkari ne ya rawaito tsine wa mumini kaman kashe shi
ne duk wanda ya tsine wa wani wanda ba ahlinta ba to tsinuwan za ta dawo kanshi
mumini bai kasance mai yawan suka ba ko yawan tsinuwa ba Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (lallai
masu yawan tsinuwa basa kasancewa masu ceto kuma basa zama masu shaida a ranar
alkiyama ) Muslim ne ya rawaito .
Izgilanci ga halittu yana cikin nau'in girman
kai ya isa sharri mutum ya rena dan uwanshi musulmi Allah madaukaki ya ce (ya ku wadanda suka yi imani kada wadansu mutane su yi izgili
game da wadansu mutane mai yiwuwa ne (abin yi wa izgilin) su kasance mafifita
daga gare su (masu izgilin), kuma wadansu mata kada su yi izgili game da
wadansu mata mai yiwuwa ne su kasance mafifita daga gare su , kuma kada ku
aibanta kanku , kuma kada ku jefi juna da miyagun sunaye na lakabobi tir da
suna na fasicci a bayan imani kuma wanda bai tuba ba to wadannan su ne
azzalumai) abubuwa guda hudu ya cikin abubuwan jahiliyya alfahari da
dangi da suka da nasaba da kuma neman saukan ruwa ta hanyan amfani da taurari
da kuma kukan mutuwa .
Kamar yadda musulunci ya harrama zagin rayayyu
haka ma kuma ya harrama zagin matattu Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce (kada ku zagi matattu,
domin sun riga sun shude zuwa ga abinda suka kaddamar) Bukari ne ya
rawaito . kai musulunci ya hana zagin iska ma da ma zazzabi da kuma dabbobi da
ma wasun hakan duk wanda ya bayyana mummuna to hakika ya kai kanshi ga tonon
silili daga wurin Allah Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce (dukkan aiumma na suna samun waraka
amma banda masu bayyana sabo) Bukari da muslim ne suka rawaito .