الجمعة، 24 يناير 2020

SAKAMAKO MAI DACEWA


Hudubar Masllacin Annabi na SheikhAbdulmuhsin Bin Muhammad Alkasim  15-5-1441AH 10-1-2020 A
Hudubar farko
Sakamako mai dacewa
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa kuma muna neman taimakonsa
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu  da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya,kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.

Bayan haka, ku ji tsoron Allah -ya ku bayin Allah- cancancin tsoronSa, ku yi murakabarSa a halin sirri da ganawa,
Ya ku musulmai!
Allah ya kagi halittar halitu sai ya kyautata abin da ya sana'anta, tsarki ya tabbata a gare shi ya kuma kyautata addininSa da abin da ya shar'anta, Mai hikima ne kuma Masani, Adili ne Mai jinkai, cikin halittarsa da umarninSa akwai sunnoni da basu sabawa ko sauyawa game da halittunSa, daga ciki akwai sakawa bayi  daidai da ayyukan da suka yi, in na alheri to da alheri in na sharri to da sharri, (Sakamako mai dacewa) da kaddara da sharia duk sun yi taron dangi bisa hakan, Allah Madaukakin sarki yace : (To wanda ya aikata wani aiki  gwargwado nauyin zarra na alheri to zai gan shi. To wanda ya aikata  wani aiki  gwargwado nauyin zarra na sharri to zai gan shi).
Allah ya gandaya ladaddaki masu yawa ga ayyukan alheri wanda yake irin su kuma daidai da su, sakayyar kan kasance daga jinsin da'ar , shehun musulunci Ibnu Taimiyya  Allah ya masa rahama ya ce: (sakayya a ko yaushe daga na kasancewa daga jinsin aikin da  mutum ya yi ne).kuma babu wata sakayya ga wanda ya kyautata sai kyautatawa Allah Madaukakin sarki yace : (shin kyautatawa na da wani sakamako face kyautatawa).
Wanda ya kiyaye dokokin Allah da hakkokinSa to Allah ma zai kiyaye shi a duniya da lahira, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: (ka kiyaye Allah sai Allah ya kiyaye ka) Tirmizi ne ya rawaito
Idan bawa ya nemi shiriya da gaskiya sai Allah ya shiryar da shi Allah Madaukakin sarki yace : (Wadanda suka bi shiriya sai Allah ya kara musu shiriya).
Cika alkawarin Allah na daga cikin imani da shi da kuma da abin da ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya zo da shi, sakayyarsa shine Allah na saka wa ma'abocinsa da aljanna. Allah Madaukakin sarki yace : (kuma ku cika alkawari na zan cika muku naku alkawarin)
Wanda ya gaskata Allah sai Allah ya karrama shi da abin da ya ke so da kuma kari Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: (muddin ka yi wa Allah gaskiya to zai gaskata ka.) Nasa'i ne ya rawaito. Ibnu kayyim  Allah ya masa rahama ya ce: (Bawa bai da wani abu da ya fi amfani kamar gaskiyarsa ga Ubangijinsa, duk wanda ya mu'amalanci Allah da gaskiya cikin dukkan al'amuransa sai Allah ya mishi abin da ya fi abin da ya ke yi wa waninsa na kyautatawa).
Iya gwargwadon kusantar bawa ga Ubangijinsa ta hanyar da'a da ibada iya kusancin Allah gare shi, Allah Madaukakin sarki ya ce a  hadisul kudusi : : (muddin bawa na ya kusance ni da taki to zan kusance shi da zira'i, idan ya kusance ni da zira'i zan kusance shi da ba'i) Buhari ne ya rawaito.
Bawa na da abinda ya zata daga ubangijin sa in alkairi ne to zai samu alheri in kuma ya munana zato to zai samu kwatankwacin haka manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ina inda bawa na ya zace ni) bukari ne ya rawaito
Kuma tauhidi shi ne tushen alheri da sa'ada duk wanda ya hadu da Allah da shi to zai rabauta da aljanna Aa farkon lamari ko karshen sa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Allah madaukakiun sarki ya ce (ya dan adam da za ka zo mini da cikin kasa na kusakwarai sannan ka hadu da ni ba ka hadani da wani to da zan zo maka da cikin kasa na gafara  )tirmizi ne ya rawaito
Duk wanda ya kyautata a wan nan duniya da imani da tauhidi to a lahira yana da aljanna da ganin ubangiji mai daukaka Allah Madaukakin sarki ya ce : (ga wadanda  su ka kyautata suna da kyakkyawa da klari ) sallah na da kofa a cikin aljanna da za a rika kiran masu yinta daga gare shi saboda sheki na gabban alwala  da tsarki za a gane wannan alumma ranar alkiyama da shi Mnzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce(lallai aluamma ta za a kira su ranar alkiyama suna masu hasken goshi da kafafuwa sakamakon gurbin alola ) bukari da muslim ne suka rawaito
(kayan ado da bawa  ya ke sawa yana isa ga mumini har inda alolan sa ya isa ) muslim ne ya rawaito
Mai kiran sallah ya na daga muryanshi da shelantawa na sallah sai sakayyarsa  ya zama daga jinsin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (mai kiran sallan shi ne mafi tsawon wuya a mutane ranar alkiyama )  muslim ne ya rawaito (ba wanda zai ji iya sautin mai kiran sallah aljani ne ko mutun  ko itaciya ko dutse face ya yi mishi  shaida ranar alkiyama  ) bukari ne ya rawaito Allah ya yi izini a daukaka masallatayya a ambaci ku sunan shi a cikin su  duk wanda ya gina wa Allah masallaci alhlin yana nemar  yardan Allah to Allah zai gina mishi kwatan kwacin shi  a alja) bukari da muslim na su ka rawaito
Kuma sadaka dalili ne na imani kuma rance ne abin ribanyawa a wurin Allah  duk wanda ya ciyar da wani abu to Allah zai maye  mishi  da abinda ya fii shi na alheri
Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Allah madakakin sarki ya ce : ya kai dan adam ka ciyar zan ciyar da kai ) bukari da muslim ne suka rawaito
(ba wata rana da bayi za su wayi gari a cikin shi face malayiku biyu sun sauka dayansu sai ya ce ya allah duk mai ciyarwa ka maye mishi daya kuma ya ce : ya allah duk mutumin da ke kame hanu to ka bashi lalatacce  ) Bukari da muslim ne su ka rawaito
  (ku ci ku sha ababan farin ciki sakamakon abin da ku ka gabatar a ranakun da su ka shude )
Mujahid Allah ya mishi rahama yace : (Ta sauka ne akan masu azumi). Za a kirayesu ne ta kofan rayyan kuma warin baskin mai azumi ya fi kamshin turaren almiski a wurin Allah
 Duk wanda ya mutu yana halin ihrami to za a tashi yana mai talbiya,
Ambaton Allah na raya zukata kuma yana sa karfin jiki, ma'abotansa basu da sakayya da ya fi Allah ya ambace su, Allah Madaukakin sarki ya ce : (ku ambace ni zan ambace ku)    Duk wanda ya ambaci Allah a wani hali to Allah zai ambace shi a hali mafi kyau Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin kudsi (Ni ina tare da shi idan ya ambace ni, idan ya ambace ni a zuciyarsa sai na ambace shi a zuciya ta, idan kuma ya ambace ni cikin jama'a ne to sai na ambace shi a jama'ar da suka fi alheri a kan su.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Majalisai na zikiri dausayi ne na aljanna, bawa na da abin da ya ke so a cikinta gun Ubangijinsa, wasu mutane uku suka fiskanto Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, dayansu sai ya ga wani wuri a majlisin sai ya zauna a wurin amma dayan sai ya zauna a bayansu, amma na ukun sai ya juya baya ya tafi sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :Ase ba zan baku labari game da mutanen nan uku ba? Shi na farkon su ya nemi mafaka a gurin Allah sai Allah ya ba shi, shi dayan kuma sai ya ya ji kunya sai Allah ma ya ji kunyarsa, amma dayan sai ya juya baya sai Allah ma ya juya masa baya. Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Addini daukaka ne ga ma'abotansa, to duk wanda ya taimaki addinin Allah to shi wanda zaa taimaka wa ne  Allah Madaukakin sarki ya ce :(Lalle Allah zai taimakawa wanda ya taimaki addininSa)
Wanda ya nusar ga alheri to yana da lada kwatankwacin ladan wanda ya yi aikin, kuma wanda ya sunnanta wata sunna kyakkyawa to yana da ladanta da ladan wanda ya yi aiki da ita har zuwa ranar alkiyama.
Kuma jarabawa sunnar Allah ce a halittunSa, kuma girma sakayya na ga girman jarabawar, duk wanda ya rungumi kaddara ya yarda to yana da yardar Allah, wanda ya yi fushi kuma zai hadu da fushin Allah.
Hakuri wajibi ne a umarni da hani da kuanyar shiga Aljannama kaddara, duk wanda ya jure ya yi hakuri to Allah zai bashi juriya da hakuri, duk wanda ya nemi sanin Allah a halin sauki to  Allah zai kawo mishi dauki yayin tsanani.
Gyaruwan al'uma na ga ilimi, :(wanda ya bi wata hanya yana mai neman ilimi to Allah zi saukake mishi da shi hanyar zuwa aljanna.)Muslim ne ya rawaito shi.
Dukkan dan Adam mai kuskure ne kuma mafi alherin masu kuskure sune masu tuba).

   
Wanda Allah ya datar da shi zuwa ga tuba sai ya fiskanci Allah yana mai tuba to Allah zai karbi tubansa kuma ya bashi lada  Allah Madaukakin sarki ya ce : (wanda ya tuba bayan zalunci da ya yi ya kuma gyara to Allah zai karbi tubarsa.
 Mumini idan mutuwa ta zo mishi sai a mishi albishir da yardar Allah da karamarSa, to sai ya zama ba wani abu da ya fi soyuwa a gare shi sama da abin da ke gaba gare shi sai ya kaunaci gamuwa da Allah sai Allah ma ya so haduwa da shi,  duk wanda ya muamalanci halittu da alheri sai Allah ya muamalance shi da kwatankwacinsa a duniya da lahira. Kuma mafi karamcin halittu shine Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, duk wanda ya mishi salati guda to Allah zai mishi guda goma, Ansarawa (sahaban Annabi na madina) ba mai son su sai mumuni, wanda ya so su Allah zai so shi.
Kuma Allah na tausayawa masu tausayi ne cikin bayinSa, duk wanda ba ya tausayawa mutane to Allah ma ba zai tausaya mishi ba, Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (wanda bai tausayi to ba zaa tausaya mishi ba) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Wata mace mazinaciya ta tausaya wa kare sai Allah ya mata rahama ya gafarta mata.
Wadanda suka fi dacewa da kyautatawa sune 'yan uwa makusanta, wanda ya sada zumuncinsa sai Allah ma ya sada masa.
Akwai aminci cikin sallama wa mutane, Manzo Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ku yada sallama za ku samu aminci) Ibnu Hibban ne ya rawaito.
Wadanda ya kankan da kai sabo da Allah to zai daukaka shi, Allah bai karawa bawa wani abu sabo da yafiya face buwaya, Allah Madaukakin sarki ya ce : (su yi rangwami su yi afuwa shin ba ku son Allah ya muku gafara ne).

Ibnu kasir Allah ya mishi rahama yace : (To lalle sakayya na daga jinsin irin wannan aiki to kamar yadda zaka yafe wa wanda ya ma laifi kai ma za a yafe maka haka nan kamar yadda ka yi rangwami kai ma za a ma rangwami ).
Duk wanda ya kaunaci wani bawa don Allah to Allah zai kaunace shi, haka duk wanda ya yi wa dan'uwansa adu'a a bayan idonsa to sai mala'ikan da aka wakilta da shi ya ce :amin kai ma Allah ya baka kwatankwacinsa.
Kuma buda wa wani a majlisai  sakayyarsa na daga jinsinsa,     Allah Madaukakin sarki ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani da Allah idan an ce da ku ku buda a majlisai to ku buda Allah zai buda muku).
Duk wanda ya yafe wa musulmi to Allah ma zai yafe masa kurakuransa ranar alkiyama.
Allah na kasance wa tare da mutum kamar yadda mutum ke tsayawa dan'uwansa musulmi,
Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya tsaya wurin biya wa dan uwansa bukata to Allah ma zai kasance cikin biya masa bukata, duk wanda ya yaye wa musulmi wani bakinciki to Allah ma zai yaye masa bakinciki daga bakincikin ranar alkiyama, duk wanda ya rufa asirin wani musulmi to Allah ma zai rufa asirinsa ranar alkiyama)Buhari da muslim ne suka rawaito.
(duk wanda ya yassara wa mara galihu to shi ma Allah zai yassara mishi duniya da lahira. Allah na taimakon bawa muddin bawa na taimakon dan'uwansa) Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya yafe wa halittu  shi ma Allah zai yafe masa, duk wanda ya 'yanta bawa, Allah zai 'yanta shi daga wuta gaba a madadin gaba. Duk wanda ya ci bashin dukiyar mutane yana nufin ya biya to Allah zai biya mishi, duk wanda ya wadatu da Allah da kuma abin da ya bashi to, to Allah zai wadata shi kuma ya isan mishi, Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya nemi wadatar Allah to Allah zai wadata shi) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Idan mutum ya kame kai daga haram da rokon mutane to Allah zai sanya shi ya zama mai kame wa, Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Lalle ne duk wanda ya nemi ya zama mai kamun kai to Allah zai maida shi mai kamewa.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Ba wani bawa da zai tausayawa wani bawa face shi ma Allah ya tausaya masa, Manzon Allah tsira da amincin Allaah su tabbata a gare shi ya ce :(Ya Allah duk wanda ya jibinci wani abu na jagoranci a cikin al'umata ya kuma tausaya musu to ya Allah ka tausaya masa.) Muslim ne ya rawaito.
 Alheri na zuwa da alheri ne, ta daya hanun kuma shi ma sharri na zuwa da sharri ne, to sakayyar mummuna ita ce mummuna kwatankwaciyarta. (Kuma ba a saka muku face da abin da ku ka kasance kuna aikatawa.)
Wanda zuciyarsa ta makance daga ganin gaskiya sai Allah ya makantar da ganinsa a Matattara, (Kuma wanda ya kasance a nan makaho to a lahira yana makaho kuma mafi bace wa bisa tafarki).
Duk wanda ya kaucewa gaskiya bayan ya santa to Allah zai karkatar da zuciyarsa daga shiriya ya jefa mishi shakku da tabewa.  (Kuma a yayin da suka karkace sai Allah ya karkatar da zukatansu).
Bijirewa alheri da addini karshensa tube rigar imani ne,  
Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma hakika idan aka saukar da wata sura sai sashinsu ya yi dubi zuwa ga sashi(su ce), shin wani mutum yana ganinku? Sa'anan kuma sai su juya. Allah ya juyar da zukatansu, domin hakika su mutane ne da ba su fahimta.)
Duk wanda ya bar da'a  ya shakala yinta da gangan to Allah zai tabar da shi ya mantar da shi kansa ya bar shi cikin azaba, Allah Madaukakin sarki ya ce : (sun mance  Allah sai ya manta da su)
Lalacewar badini akibar ta kara lalacewar, Allah Madaukakin sarki ya ce : (A cikin zukatansu akwai wata cuta sai Allah ya kara musu wata cuta.)
Duk wanda ya yi shamaki wa basirarsa daga addini to Allah zai masa shamaki daga ganinsa ranar sakayya, Allah Madaukakin sarki ya ce : (A a ha lalle ne su a wannan ranar abin shamakacewa ne daga Ubangijinsu).
Shirka shine mafi girman zunubi  to duk wanda ya ta'allaka zuciyarsa da wani abu ba Allah ba sai a kyale shi da shi, duk wanda ya nufi riya ko sum'a  neman a ji da aikinsa  sai a saka mishi da irin aikin shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce : (Duk wanda ya yi sum'a(neman aji) to sai Allah ya sa a ji shi wanda ya  yi riya sai Allah ya mai da shi mai riya) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Mai bauta wa wanin Allah tababbe ne a duniya da lahira,
 Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma suka riki gumaka baicin Allah domin su kasance mataimaka a gare su. A aha za su kafirta da ibadar su kuma su kasance makiyansu.)
Wanda ya yi wani aiki ya hada Allah da wani a cikinsa sai Allah ya bar shi da shirkansa, wanda ya kasance yana bautawa wani abu baicin Allah to zai bi shi cikin wutar jahannama, duk wanda ya rantse da wani addini bisa karya koma bayan musulunci to ya koma kamar yadda ya ambata, duk wanda ya suranta sura zaa azabtar da shi da ita ranar alkiyama, kuma a kallafa masa da ya busa masa rai, kuma ba zai iya busawa ba, duk wanda ya nemi yardan mutane wajen fusata Allah, to Allah zai yi fushi da shi kuma ya sanya mutane ma su yi fushi da shi, duk wanda ya tsani haduwa da Allah da Allah to Allah ma ya tsani haduwa da shi, duk wanda ya nufi ya yi kaidi da yaudara da makirci da hila ga addini to Allah zai mishi daurin talala kuma in ya tashi ya mishi kamun ba zata, Allah Madaukakin sarki ya ce : (su ka yi makirci kuma Allah ya shirya musu sakamakon makircinsu Allah shi ne ya fi makirai sakamakon makirci ) kuma ya ce : (suna  yaudaran Allah shi kuma ya na maida musu   yaudaran su )
Wanda ya jinkirta salla Allah zai jinkirta shi  Manzon Allsah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (wasu mutane ba za su gushe ba suna yin jinkiri har sai Allah ya jinkirta su ) muslim ne ya rawaito  duk wanda ya ki yin sujjada a duniya sai a hana shi yinta ranar alkiyama  Allah Madaukakin sarki ya ce (ranar da ake  yayewa ga makengema kuma a kira su zuwa ga sujjada ba za su samu daama ba )(gannansu ta na wulakance saboda wulakanci tana lullube su ana kiransu a duniya zuwa sujjada alhalin sauna masu lafiya ) girman kai shi ne dagun kai a kan gaskiya ga halittu sai a tada ma'botan shi kamar kwayan zarra mutane na taka su duk wanda ya yi karya guda daya da ta yadu to lallai Allah ranar alkiyama zai juya muka mukinsa zuwa keyasa mazinata wani harshen wuta zai rika zuwa musu tun diga kasansu Allah ya na debe albarkan riba  maciyinshi kuma za a rika wurwurishi da duwatsu a cikin bakin shi  ranar alkiyama duk wanda ya boye ilimi Allah zai sanya mishi linzami irin linzami na wuta ranar alkiyama duk wanda ya ci gululi zai zo da abinda ya ci na gululi ranar alkiyama duk wanda ya hana saurar ruwa Allah zai ce da shi ranar alkiyama a yau zan hana ka falalata kamar yanda ka hana abinda ba hanunka ne ya aikatashi ba duk wanda ya sha giya a duniya san nan bai tuba ba to an haramta mishi ita ranar alkiyama wanda ya sanya alhariri daga cikin maza a duniya to ba zai sanya ta ba a lahira wanda kuma ya yi da'awa irin da'wa na karya domin ya kara dukiya ba abinda zai kara mishi a wurin Allah sai talauci butulcewa ni'ma yana shelanta gushewanta Allah ba ya canja wani abu na ni'ma tare da mutane da jin dadi na rayuwa har sai sun canja daga kawunan su da zalunci da sabo izgilanci da addini da ma'botan addini sakayyansa na daga jinsinsa wanda ya yi izgilanci ga bayin Allah Allah ma zai mar izgili alaman munafiki shi ne kin mutanen madina na daga nasarawa wanda kuma ya ki su Allah zai ki shi duk wanda ya kashe rayi tare da wani abu to za a rika azabtar da shi da wannan abun har ranar alkiyama , mai sata na miji ya shinpida hanunshi ne akan barna saboda haka ta cancanci a yanketa ,duk wanda ya yi kazafi wa kuyangansa ko kuma bawansa alhali kuma shi ya barranta daga wannan to za amishi bulala ranar alkiyama za a kafawa   mahayinci tuta wanda za a sanshi da shi a ranar alkiyama duk wanda ya la'anci wani abu wanda wannan abun bai cancanci hakan ba to la'nan zata dawo kanshi Allah ya tsine wa wanda ya tsine wa iyayenshi zalunci duhhai ne ranar alkiyama duk wanda ya yi zalunci gorgodon kaidi na taki Allah zai nadeshi daga kassai guda bakwai
Yanke zumunci na makusanta yafi muni akan waninsa Allah yana cewa ga mahaifa (ba ki yarda na sadar da wanda ya sadaki ba na yanke wanda ya yankeki ba ) bukari da muslim ne suka rawaito Allah ya yi alkawarin narkon azaba ga wadanda suke azabtar da mutane ba tare da hakki ba Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (lallai Allah yana azabtar da wadanda suke azabtar da mutane a duniya ) muslim ne ya rawaito riskar da cutarwa da wahalarwa ga halittu karshensa baya haifar da da mai ido Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (duk wanda ya cutar to Allah ma ya cutar da shi duk wanda ya wahalar to shi ma Allah ya wahalar da shi) tirmizi ne ya rawaito , duk wanda aka bawa wani abu na jagoranci na musulmai sai ya kuntata musu ko kuma ya shamaki tsakaninshi da su gameda bukatunsu to Allah ma sai ya yi shamaki tsakaninshi da shi duk wanda ya bibiyi al'auran mutane to Allah ma zai bibiyi al'aurarsa har sai ya kunyatashi a gidansa mai cin nama yana kekketa mutuncin mutane da harshensa zai zo ranar alkiyama yanada farata daga karafunan nuhas bagwanja yana pippige fiskansa da su wanda ya ji zancen wasu mutane wanda suke suna kin hakan za a kwararamishi a kunnenshi harsashi na narkakken dalma ranar alkiyama garin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi amintacce ne duk wanda ya bada tsoro ga mutanenta Allah ma zai tsorata shi wanda ya kasance yanada mata biyu ya karkata zuwa ga dayansu zai zo ranar alkiyama tsaginshi a karkace idan bawa ya bude kofan roko to Allah zai bude mishi kofan talauci rowa da kamkame hanu yana goge albarka kuma yana wajabta tsananin hisabi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (kada ka kididdige Allah ma sai ya kididdige maka) bukari da muslim ne suka rawaito
Bayan haka ya ku musulmai :
Allah mai dubi ne ga bayinsa kuma yana dakonsu a madakata kuma zai sakanya wa kowa abunda ya aikata sakayya na daga jinsin aikin wanda ya yi daidai da shi a alheri ne ko na sharri kamar yanda ka ke hisabi kaima za amaka hisabi duk wanda ya nufi ya san makomansa a wurin Ubangijinsa to ya duba abinda ya ke da shi a wurin Allah domin Allah yana saukar da bawa ne inda bawa ya saukar da kansa
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jifa
Duk wanda ya yi aiki na kwarai to don kansa wanda kuma ya munana to don kansa Ubangijinka bai zama mai zalunci ba ga bayi Allah sa mini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma

                     Huduba ta biyu
dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawansa dukkan godiya bisa ga datarwansa da kuma baiwansa , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya ina mai girmama sha'ninsa na shaida cewa annabin mu Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalanshi da aminci tabbatacce mai kari

ya ku musulmai
duniya gida ne na aiki lahira kuma gida ne na sakayya Allah ya kan gaggauto wa bawansa da wani sakayya a nan duniya shi ni'man da ke hade da godiya ga ma'bota da'a albishir ne  , su kuma musibu tare da hakuri daukaka ne ko kankaran zunubai , amma mai sabo wanda ya juya baya to idan an jarrabeshi to wannan ukuba ce da gaggawa abinda ya ke gurin Allah shi ya fi tsanani idan kuma an jinkirta ukubarsa to jinkirin da Allah ya misahi kamar  daurin talala ne
sannan ku sani Allah yana umurtan ku da salati da aminci ga annabin sa.              

LOKACIN HUNTURU GA MUSULMI


Hudubar Masllacin Annabi na Sheikh Salah Bin Muhammad Albudair  22-5-1441AH 17-1-2020 AC
Hudubar farko
Ya ku musulmai
Hunturu ya sauka gare ku bayan shudewar bazara mai tururi, busa irin na jaura ya kada muku bayan hurawan garji, tsananin sanyi ya zo muku bayan gushewar yanayin zafi.
(Allah yana juyar da dare da yini, lalle ne a cikin wannan akwai abin lura ga masu basira.)
To ku yi lura da ido na basira cikin shanin girman Allah da ikonSa da halittarSa, ku yi tunani game da hunturu da gajimare da ruwan sama, ku yi lura ga yayyafi da mamakon ruwa, ku dubi yadda yankin  gajimare ke saukowa ga girgije mai girma, ku yi dubi zuwa ga duwatsu masu sanyi da garuruwa masu kankara, da birane da sanyi ya mamaye su da fari fari, ku yi tasbihi ga Allah Mahalicci Masani Mai girma,Wanda ya kirkiri duniya ya samar da ita, kuma ku ba komi ba ne face wani yanki dan kadan daga halittanSa na ban mamaki mai ban tsoro, to ku girmama Allah cancancin girmamawanSa ku ji tsoron tsananinSa da azabanSa ku kame daga saba masa da rena shanin hakkinSa .
Ya ku musulmai
Hakika hunturu ya zo da karfinsa da tsananinsa da kuma tsaurinsa, to ku kiyaye daga sanyi domin yana kankarar da gine-gine kuma yana rusa jiki yana tsofatar da tsoffi , Rabi'u Bin Dabi'u ya ce : (Idan hunturu ya zo to ku dundumani domin tsoho hunturu na lalata sha'nin sa)
 wani kuma ya ce : (Hunturu ya zo ga shi ba ni da rigan sanyi, *** tsananin  sanyi kuma abokin jayayya ne  ba a maida shi  sai dai ana mishi garkuwa).
An rawaito cewa Umar Allah ya kara mishi yarda ya ce : (lallai hunturu ya zo kuma shi makiyi ne to ku kimtsa masa kimtsawa na daga fata da huffofi da safanni, ku riki fatu ya zama rigan waje da 'yar ciki, domin lallai sanyi makiyi ne mai saurin shiga jiki mai wuyan fita).
Ya ku iyaye da kuma majibinta al'amura  : ku tausaya wa 'yan yaran ku da jariranku  ku tufatar da su ku musu rahama, to ita rahama ba a a cire ta  sai daga zuciyan shakiyyi, kuma sau dayawa akan samu baba da ya kaurace wa 'yayansa ya daina ciyar da su, sabo da sabaninsa da matarsa ko wacce ya sake ta, baya tufatar da su alokacin bazara ko hunturu ko idi baya basu ciyarwa ko ya kyautata musu sai wasu bare sun musu sadaka da makusanta, to wani irin kekashewar zuciya ce wannan wani irin tsauri ne wannan wani irin hankali ne wannan wani irin tunani ne  ya sa wannan baba azzalumi ja'iri ne wanda ya wofantar da yaransa ya kyale su ya yada su ya barsu su ka daidaice!?  wani maula ( Bawa) ya ce ga Abdullahi dan Amr Allah ya kara yarda a gare shi : (lallai ni ina so na zauna wata guda a wannan gari na baitul-makdis sai ya ce da shi : shin ka barwa iyalanka abin da zai ciyar da su na wannan wata ?  sai ya ce: a'a , sai ya ce : to koma zuwa ga iyalanka ka bar musu abincin su,Lallai ni na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa : (ya isa laifi ga mutun ya wofantar da wanda ya ke ciyarwa ) Ahmad ne ya rawaito da Abu Dauda , a wurin muslim kuma : (ya isa laifi ga mutun da ya buya daga wanda ya ke mallakan ciyarwansa)
Ya ku musulmai !
Ba abin da ya fi tsanani kamar gagaran daukan nauyin hunturu da kuma ta'azzara a gare ka na tufatarwa a halin kuma kana da laruran haka kana bukatan shi, mutun nawa ne cikin talakawa suka gagara rigan sanyi da za su sa ko mayafi ko abun lullubuwa ko kuma abun karyawa ko kuma magani ya gagare su ko na yaransu ba za su iya samun kudinsa ba, an ce da wasu mai ka tanadar wa sanyi sai ya ce : (tsawon karkarwa da kadawan jiki da kekasawa).
 To ku tuna masu rauni da talakawa da miskinai da wadanda mazajensu suka rasu suka barsu na daga mata da marayu da kuma mabukata, ku tuna 'yan gudun hijira da wadanda suke yasassu da kuma wadanda aka kora daga garuruwansu wanda sanyin hunturu ya bugesu kankara ya lullubesu, iska mai tsanani ya kakkashe su, talaka yana kuka mai rauni yana neman taimako wanda yake halin kaka ni kayi yana ta kururuwa hanunsa ya kuntata (baida abinda zai ci) kokawansa ya yi girma tsananin sanyi na hunturu ya sauka gidan sa dattijo ya kwana yana sandare, Mumunai su ne makukusantan mutane da rahama da shafaka da tausayawa da kyautatawa su suka fi tausayawa ga talakawa kuma da yatimai da miskinai su suka fi bada kulawa ga wadanda mazajensu suka mutu suka barsu da ku wadanda aka sake su da kuma masu rauni sune suka fi tausayawa wadanda suke masu tsananin bukata kuma suka fi amfanar da wadanda suke cikin kunci da bakin ciki ba wani abu da suke da shi da zai ishe su ba mafaka da za su fake to ku bibiyesu ku bincikesu ku taimaka musu ku lullubesu da mayafai da fatu ku agaza musu da hanyoyi na jin dumi .
Tausayawa da kyautatawa daga musulmi ga dan uwan shi musulmi shi ne abu mafi girma na dumamawa ga wanda ba yi da abin dumi .
An karbo daga Abu sa'id Alkudri Allah ya kara yarda a gare shi ya ce yayin da muna cikin halin yanayi na tafiya tare da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi sai wani mutumi ya zo akan abar hawansa sai ya rinka juya ganinsa yana kallo dama da hagu sai Manzon  Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa: (To duk wanda ya kasance yana da wani sauran abin hawa to ya taimaka da shi ga wanda bai da abin hawa, wanda ya ke da wani saura na  guzuri to ya taimaka ga wanda bai da guzuri) sai ya ambata nau'uka daban daban na dukiya abin da ya  ambata har muka ga cewa wani bai da wani hakki a cikinmu akan wani abin da ya karu kan bukatu a dukiyansa, muslim ne ya rawaitoshi
Ya ku musulmai !
Karamci a lokacin hunturu da tsanani da ciyarwa da kyautatawa idan har an samu karanci na guzuri da abinci da yawan fari abu ne mai daraja kuma  abun girmamawa ba masu siffantuwa da shi sai mutane masu yawan kyauta da tausayawa Allah Mabuwayi ya ce  :(ko  kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abucin yunwa, ga maraya ma'abucin zumunta, ko kuwa wani matalauci ma'abucin turbaya).
      Ibrahim Annakha'i yake cewa : a irin ranakun da abinci yana da wahala a wannan ranan .
Muhammad dan Abdus bamalike ya yi sadaka a wani daren hunturu da kiman amfanin gonansa gaba daya alhali kuma kimansu ya kai dinari dari na zinari ya ce ban yi bacci ba a daren saboda bakinciki game da talakawan al'umman Muhammad,
 Darfat binul Abd yake cewa : mu a lokacin hunturu muna kira ne ( kowa da kowa) tawaga tawaga *** ba a gani mai gayyatan abinci  a cikinmu yana kiran daidaiku  .
Kansa' ta ce Allah ya kara yarda a gare ta a lokacin da take wakan juyayi ga dan uwanta sakhr : lallai sakhr din nan shi ne mai kula da mu kuma shi ne shugaban mu lallai sakra din nan a lokacin da aka yi hunturu mai yawan soke dabba ne.
Aus binu hajar yake cewa : masu suka ne a wurin yaki sa'annan kuma masu ciyarwa ne ga baki*** idan sararin samaniya ya yi fatsi fatsi saboda tsananin sanyi
Shi kuma kars : shi ne tsananin sanyi mai ratsa jiki
Wani yake cewa : dan uwan hunturu bakonsa ya san cewa abin da ke tukunyarsa  *** zai yawaita kuma zai yi dadi
Wani kuma yake cewa : dan uwan hunturu tukunyansa ba ya gushewa  *** yana zuba a cikinsa sannan kuma yana fita.
Ku yi kyauta, ku yi sadaka, ku ciyar da mayunwaci da wanda ke cikin talauci  mayunwaci, ku shayar da wanda ya fada cikin tsananin kishi da mai jin kishi kuma ku tufata da mukamukinsa ke karkadawa jijiyoyin wuyansa ke girgizuwa saboda tsanani sanyi ku bibiyi makobtanku da  wanda suke muku hidima da ma'aikata da makusanta da talakawa da masu rauni da masu kiwo a sahara ba mumini ba ne mutuminda zai koshi makobcinsa na cikin yunwa ku toshe yunwan miskini da bukatansa da talaucinsa  , an karbo daga a'yisha Allah ya kara yarda a gare ta ta ce  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (lallai Allah yana renon dabinon dayanku da lomansa kamar yanda dayanku yake rainon irinsa har ya zame kaman dutsen uhudu) Ahmad ne ya rawaito
Ina fadin abinda kuke ji ina neman gafaran Allah kuma ku nemi gafaranshi domin shi lallai mai yawan  karban tuba ne kuma mai gafara .
Huduba ta biyu
Ya ku musulmai
A lokacin hunturu ne mutane ke neman jin dumi daga sanyi da wuta suna jin dadin shi kuma suna kewaye shi kuma su kunnashi a gidajensu da gonakinsu da kuma shemominsu kamar shi ne iyayan itacensu , abincinsu kuma abinda ke hadasu
Wuta ita ce 'ya'yan itace da ake ki lokacin hunturu duk wanda ya ke son cin 'ya'yan itace na hunturu to ya ji dumi Allah mabuwayi da daukaka yake cewa (wannan wuta din mun sanyata a matsayin tunatarwa ne da kuma jin dadi ga mutane da suke matafiya) duk wanda ya ruruta wutansa ya kunnata ya yi dafu da ita ya dafa masa ya ji dumi ya rike shi kaman abin hira ya amfana da ita to kar ya bar gaushi  ko wuta a makamashin ko abin sanya gaushin face ya kashe ta a dare ne ko wuni tsoron gobara ko shakewa (da hayakinta) domin wuta fa makiyi ne da ba a sa mar linzami tartsatsinsa kan fire baa kuma amintuwa da harshensa,
  
Daga ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare su daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce : kar ku bar wuta a gidajenku yayin barci) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Daga Abu Musa Al'Ash'ari Allah ya kara yarda a gare shi  yace an yi gobara a wani gida ya kone da mutanen gidan a garin Madina cikin dare a yayin da a ka labartawa Manzon Allah tsira da amincin Allah su game da shaninsu sai yace : ( Lalle ita wuta makiyiya ce a gare kum to idan kun zo barci to ku kashe ta ) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Haka ma na'urorin jin dumi na wutan lantarki  in an tsoraci zafin wutan nata ko tururin nata to an shar'anta da a kashe ta bayan kammala bukata da ita, a yi nesa da wayoyinta  daga shinfidi da tufafi da fefofi da yara don gujewa hatsura da aukuwan mummunar abin da ba a zata ba.
Ku yi salati da aminci ga Ahmad mai shiryarwa mai ceton bayi kaffataninsu.


FALALAN GARIN MADINA


Hudubar Masllacin Annabi na SheikhAbdullah Bin Abdurrahman Abuaijan   29-5-1441AH 24-1-2020 A
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa kuma muna neman taimakonsa muna neman gafararsa
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu  da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, yana halitta abin da ya so kuma ya zabi abin da ya so, wanda ya kagi sammai da kasa, komai a kaddare ya ke a gare shi, na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne amintacce, cikamakin Annabawa da manzanni, ya isar da sako, ya sauke amana  ya kuma yi nasiha ga al'uma, ya yi jahadi don Allah cancancin jahadi har mutuwa ta zo mishi, Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa baki daya.
Bayan haka,
Mafi alherin zance shine maganar Allah, mafi alherin shiriya shi ne koyarwar Annabi Muhammad, mafi sharrin al'amura shine fararrunsu, kuma dukkan bid'ah bata ce, kuma dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah ku ji tsoron Allah cikin umarninsa ku hanu daga abin da ya yi hani a kai ya kuma tsawatar. Ku sani duk wani babba da karami abu ne rubutacce a littafi  (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah kuma rayi ya yi dubi ga abin da ya gabatar don gobe, ku ji tsoron Allah lalle Allah Masani ne ga abin da ku ke aikatawa)
Ya ku jama'ar musulmai!
Allah kan zabawa fifiko mahalli da wuri kamar yadda ya ke zaba mishi lokaci da zamani, da ahali, da mataimaka, hakika Allah ya fifita awasu sassa a doron kasa sai suka zama sune mafi daukakan garuruwa kamar yadda ya sanya makka masaukar wahayi, kuma alkibla ga musulmai, kuma ya sanya ta uwar alkaryu kuma gari mai aminci da masallaci mai alfarma, gurin da zukatan mumunai ke karkata zuwa gare shi.
Garin Madina ya samu daukaka ne sabo da hijiran Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a nan ne musulunci ya yadu, ana ce da shi Daiba
Zama ya yi dadi a cikinshi tsakanin duwatsun shi biyu harami ne kuma shi ne masulala na I'mani da mafakarsa da masaukinsa kuma da makoncinsa da mabinnansa
Ya ku bayin Allah :
Hakika Allah ya daukaka garin madina ya fifitashi kuma ya umarci annabinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da ya yi hijira zuwa gare shi ya haramta abinda ke tsakanin duwatsun shi biyu ya tsine wa duk wanda ya yi barna a cikin shi kuma kokuma  ya bada mafaka ga mabarnaci a cikin shi to ku bawa garin hakkin shi kuma ku ji alhurman da ya ke tattare da shi  an karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Madina  harami ne daga kaza zuwa kaza ba a'a yanke itaciyansa ba a'a farsar da barna a cikinsa to duk wanda ya farar da barna a cikinsa to tsinuwan Allah ta tabbata a gare shi da mala'iku da mutane baki daya) Buhari ne ya rawaito
An karbo daga A'mir dan Sa'ad daga baban shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (lallai ni na haramta tsakanin duwatsun garin madina guda biyu da atsinke kayansa ko a kashe abin farautansa ) Muslim ne ya rawaito
Kuma an karbo daga Aliyu Allah ya kara yarda a gare shi lallai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (garin Madina haram ne daga  A'ir zuwa kaza duk wanda ya farar da barna a cikinsa to tsinuwan Allah ta tabbata a gare shi da Mala'iku da mutane baki daya ba za a karba mishi nafila ko farilla ba ) Buhari ne ya rawaito
Ya jama'ar musulmai
Madina masulala ne na i'mani Allah ya ambace shi da gida da kuma i'mani, a cikinsa ne alkura'ani ya yi ta sauka mai dumbin yawa, a ciki ne aka shar'anta hukunce hukunce, rukunnai suka kafu, zaman lafiya ta tabbatu,   
   Daga nan ne tutocin musulunci suka taso a ka bude garuruwa, Allah ya daukaka addininSa ya taimaki bawanSa ya rusa makiyanSa,
Daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lalle imani na sulalewa zuwa Madina kamar yadda maciji ke sulalewa zuwa raminsa.) Muslim ne ya rawaito.
Madina sulke ne mai bada kariya, kuma garkuwa ne mai tsawo, ya kore kazantarsa yana tsarkake mai dadinsa, mala'iku na tsaronsa daga kofofinsa, firgicin Masih-Addujjal ba zai shige shi ba, ko annoba, daga Anas dan Malik, Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ba wani gari face dujjal zai taka shi face Makkah da Madina, ba wani kofa daga cikin kofofinta face Mala'iku na jere cikin sahu suna kare su, sannan Madina zai kada da mutanen cikinsa girgizawa uku, sai Allah ya fitar da duk wani kafiri da munafuki,) Buhari ne ya rawaito.
Daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (A kofofin Madina akwai Mala'iku annoba ko dujjal ba zai shiga garin ba) Muslim ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah ! ma'abocin Kazanta ko kaidi bai da mazauni a garin Madina, amincin Allah ya tabbata a gare shi,
Daga Aisha diyar Sa'ad ta ce na ji Sa'ad Allah kara yarda a gare shi ya na cewa, na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya na cewa :Ba wanda zai yi wa mutanen madina kaidi face ya narke kamar yadda gishiri ke narkewa a ruwa,) Buhari ne ya rawaito.
An karbo daga Jabir Allah kara yarda a gare su ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : Madina tamkar zuga zugi ne ya kore kazantarsa ya tace mai tsarkinsa.) Muslim ne ya rawaito.  
Lalle Ibarahim ya haramta Makkah ya mar adu'a da albarka, kuma lalle Annabi ya haramta Madina ya yi mar adu'a da ribin abin da Annabi Ibrahim ya roka wa mutanen  Makka An karbo daga Abdullahi bin zaid Bin Asim cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( Lalle Ibrahim ya sanya alfarma ga Makka ya yi adu'a ga mutanenta, lalle ni kuma na sanya alfarma ga Madina kamar yadda Ibrahim ya sanya wa Makka, ni kuma na roki Allah game da sa'in madina da mudunsa da ribin abin da Ibrahim ya roka wa mutanen makka) Muslim ne ya rawaito.  
   Daga Anas -Allah ya kara yarda a gare shi- daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ya Allah ka sanya albarka ga Madina ribin abin da ka sanya a makka).  Buhari ne ya rawaito.

Ya ku bayin Allah!
Lallai Madina ya kasance mafi soyuwan gari ga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana nuna masa kauna da wafa'i kuma yana bayyana hakan karara An karbo daga A'isha Allah ya kara yarda a gare ta tace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (ya Allah ka sanya mana kaunar Madina kamar yadda ka sa mana kaunar Makka ko ma sama da haka. Ya Allah ka sa albarka ga sa'inmu da mudunmu ka inganta mana shi, ka kaurar da Annoban zazzabinsa zuwa juhfa)  Buhari ne ya rawaito.
   Daga Anas -Allah ya kara yarda a gare shi- idan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya dawo daga tafiya ya hangi gine –ginen Madina sai ya saki dabbarsa in yana kan dabbarsa ne sai ya kada ta sabo da kaunar Madina.) . Buhari ne ya rawaito.
Ya kasance idan ya fiskanto Madina sai ya kara sauri idan dutsen Uhud ya bayyana gare shi sai yace : wannan dutse ne da ya ke sonmu mu ma muna son shi,
An karbo daga Abu Humaid yace mun fita tare da Manzon Allah a yakin tabuka ya koro hadisin sannan ya ce : sai muka fiskanto har muka zo wadil kura sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :( Lalle ni zan kara sauri wanda ya ke so cikin ku to ya yi sauri tare da ni wanda ya so kuma ya zauna, sai muka fita har muka kusanto Madina sai yace : Wannan Daba ne wannan dutsen Uhudu ne shi dutse ne da yana son mu muna son shi). Muslim ne ya rawaito.
Hakika zukatan masu ziyara ta ta'allaku da Madina kuma ya bar wasu abubuwa na tarihi a zukatansu na  tsananin kauna sai zukatansu ta tausasa zuwa ga garin suna masu tsanani shauki , ya Allah ka sanya mu daga cikin masu son sa (garin ke nan)
Ya jama'ar musulmai :
Madina shi ya fi muku alheri kar ku ki shi   Allah ya zabe shi ga Annabin ku to ku zabi abinda ya zaba ku ladabtu da kusanci ku san hakkin makobci an karbo daga abi  Zuhair Allah ya kara yarda da a gare shi ya ce  na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa (za a bude garin yaman wasu mutane za su zo suna kora dabbobinsu suna daukan iyalansu da ma wadanda suka biye musu, Madina yafi alheri agare su da sun sani za abude Sham sai wasu mutane su zo suna kora dabbobinsu sai su dibi iyalansu da ma wadanda suka musu da'a alhali Madina yafi alheri a gare su da sun kasance suna sani kuma za a bude  garin Iraki sai wasu mutane su zo suna kora dabbobinsu sai su dibi iyalansu da ma wadanda suka musu da'a alhali Madina yafi alheri a gare su da sun kasance suna sani) Bukari ne ya rawaito
An karbo daga ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Duk wanda zai mutu a Madina to ya mutu a cikinsa lallai ni  zan yi  ceto ga wanda ya mutu a cikin shi ) Tirmizi ne ya rawaitoshi kuma ya inganta shi
An karbo daga A'mir dan Sa'd daga babansa Allah ya kara yarda a gare su ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Madina ya fi alheri a gare su da sun kasance suna sani duk wanda ya bar garin halin ya tsani garin to Allah zai sanja shi da wani wanda ya fi alheri ba wani da zai tabbata a ciki ya yi hakuri da  wahala da tsanani irin nashi face na kasance mai ceto a gare shi ko mai shaida a gare shi ranar alkiyama) Muslim ne ya rawaito ,Allah ya samini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma

Huduba ta biyu  
Ya ku bayin Allah
  lallai Madina na da daukaka da falala to ku nemeshi da alhurma da kima da wasu laduba da ya ya wajaba a yi ladabi a iyakoki na harami dama masallacin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi haka nan kuma da wurinda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke lallai adabi tare da shi yana raye kamar yimishi ladabi ne a bayan ya rasu hakika Allah ya umarci a yi ladabi gaba gare shi a kuma yi kasa da murya , Allah madaukakin sarki ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani kada ku sha gaban Allah da Manzonsa ku ji tsoron Allah lallai Allah mai ji ne  masani )(ya ku wadanda su ka yi I'mani kar ku daga sautukanku sama da sautin Annabi kada kuma ku bayyana zance a gare shi kamar yanda sashinku ke daga murya ga sashi don kada ayyukanku su rushe a halin baku sani ba)( lallai wadanda su ke kankan da sauti gaba daManzon Allah wadan nan su ne wadanda Allah ya jarabi zukatansu da takawa suna da wata gafara da lada mai girma )(lallai wadanda su ke kiranka a bayan dakuna mafiya yawansu basu da hankali ) (da a ce sun yi hakuri har ka fito zuwa gare su da ya kasance mafi alheri a gare su Allah mai gafara ne mai jin kai )
ku ladabtu ya ku bayin Allah a gaba gare shi da kyakyawan laduba an karbo daga Sa'ib da yazid ya ce : na kasance ina tsaye a masallaci sai wani ya jefeni da tsakuwa sai na duba sai naga Umar dan kaddabi ne sai ya ce je ka taho  min da wadancan mutane guda biyu sai na taho mishi da shi sai ya ce : ku waye ? ko kuma daga ina ku ke sai suka ce : daga garin Dayif sai ya ce : da kun kasance mutanen garin Madina ne da na jiyar da ku a jikinku (da na azabtar da ku) kuna daga muryan ku a masallacin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ? ) Buhari ne ya rawaito .
Allah ka daukaka musulunci da musulmai .      

الأحد، 5 يناير 2020

BARNA A KASA DA BAWA DUKIYA KARIYA A MUSULUNCI


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Husain bin Abdul'aziz Al- Ashaikh 8-5-1441Ah /3-1-2020Ac

Na daga cikin ginshiki na yanke a wannan addini namu akwai haramcin cin kazantacciyar dukiya, na daga cikin mafi munin dukiya na haram ribatar da wasu ke yi a ma'aikata ko watanta na yin awun gaba da dukiyar al'uma (sata) ko yi ma dukiyar ta'annuti, ta kowace fiska a ka yi ta ko ta wace hanya aka bijiro da ita. Allah Madaukakin sarki ya ce (ya ku wadanda suka yi imani kada ku ci dukiyarku  a tsakanin ku bisa bata sai dai ta hanyar kasuwanci bisa yarjejeniya daga gare ku.)  
To dukiyar kasa asalinta tana da alhurma sabo da mallakan al'uma ne baki daya, ana sarrafa ta ne wajen amfanin kowa da kowa, da maslahohin da ake tarayya a kanta.
To duk wanda ya riki wani aiki, kowani irin aiki ne to shi abin tambaya ne gaba ga Allah na dukkan nauyin da aka dora masa, to ba ya halatta ya yi gaban kansa a ciki face abin da ya zo daidai da koyarwar shariar Allah a kankanin abu ne ko babba, sawa'un cikin abu mai kima ne ko mara kima, da kuma abin da tsari ya shirya don cinma maslahohi na gabadaya da amfani iri iri na kowa da kowa.
Lalle sakaci cikin shanin kowane dukiya yana komawa ne ga bangaren wanda ya yi sakacin ko da wani ma'aikaci ne kuwa wannan laifi ne a mahanga na sharia tsarkakakkiya, haka ma yin rufa-rufa ga wani sabo da dangantaka ko abokantaka ko don neman wani anfanin kai, to duka sun shigo cikin satan dukiyar al'uma, kuma yana cikin barna a doron kasa da ha'intar shugaban kasa jagoran musulmai da kuma ha'intar al'uma, sakamakon abin da wannan ha'inci ya kumsa na hadura da ke barazana ga zaman lafiyar al'uma da tattalin arzikinta da habakanta da ci gabanta da yalwanta. Allah Madaukakin sarki ya ce (Duk wanda ya ci gululi zai zo da abin da ya ci na gululi  ranar alkiyama sa'annan a cika wa kowane rai  sakamakon abin da ya aikata kuma ba za a zalunce su ba).
Ana cewa  gallar rajulu fa huwa  yagullu wato mutum ya yi gululi idan ya yi ha'inci, Al'aghlal : shine cin amanar wani nauyi da aka dorawa mutum wanda ya hada dukkan nau'ukanta, kuma ana fassara ta da satan dukiyar al'uma ta dukkan fiskokin sata, sabo da haka ne a ke cewa ga mahauci ya yi gululi idan ya saci wani abu na nama bayan ya dauki fata.
   
   Allah Madaukakin sarki ya ce (kada ku yi barna a ban kasa bayan an gyara ta.)
Al'uma ba zata ta ba gyaruwa ta yi kyau ba sai kowa ya tashi da nauyin da ke kan shi na amana bisa yanayi mafi kyau, a yi taimakekeniya gurin kiyaye dukiyar al'uma, ta kowace hanya da ta sawwaka, Allah Madaukakin sarki ya ce game da AnnabinSa yusuf   (ka sanya ni a kan taskokin kasa, lalle ne ni, mai tsarewa ne, kuma masani.)
 Haka kuma a kissar musa game da yaran mata biyu na shuaibu ( ya Baba ka bashi aikin kodago, lalle ne mafi alherin wanda ka bawa aikin kodago shi ne mai karfi amintacce.)
  Lalle ribatar dama na aiki ko waninsa don a yi awun gaba da dukiyar al'uma ba bisa halacci ba na daga cikin manyan laifuka na zunubai da kuma munanan al'amura, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle wasu mutane na kutsawa cikin dukiyar Allah ba tare da hakki ba,to wuta ta tabbata a gare su ranar alkiyama) Buhari ne ya rawaito.
Ibnu Hajar Allah ya masa rahama yace : ( wato suna barna a dukiyar musulmai).
Lalle kalmar malaman fikihun musulunci ta nassatan cewa dukiyar al'uma kamar dukiyar maraya ne wurin wajabcin kiyaye ta, da haramcin dauka daga gare ta, da matsanancin kwadayin tafiyar da ita a gurarenta da suka dace ba tare da yin sakaci ba ko tawace fiska.
Ya 'Yan uwa a Musulunci
Na daga cikin abubuwa na bayyane da ke faruwa daga wasu ma'aikata na gabatar da wasu a matsayi da fifita su a kan wasu ba tare da cancanci ba, tare da fakewa da wata doka da ta fito daga shugaban kasa, don tabbatar da maslahar kowa da kowa na daga 'yan kasa, sai wannan ma'aikacin ya riki wannan kamar wata garabasa yana zaton tamkar dukiyarsa ne na aljihunsa, sai ya gabatar da wanda bai cancanta ba bisa wanda ya cancanta. Na daga cikin irin wannan akwai sakaci da wasu ke yi wajen bada kwangila ba bisa ka'ida ba, ko don maslahar kai, da wuce gona da iri wajen sanya farashin aikin, wanda in da na kan shi ne bai zai yarda da haka ba. Yana daga cikin sakaci na rashin kulawa  da dukiyar al'uma kamar lambuna da asibitoci da wuraren shakatawa  da hanyoyi da makamantarsu.
Yana daga ciki amfani da abin da yake mallakar hukuma ne wurin bukatun kai ba tare da izini da ke bisa tsari ba daga shugaban kasa.
Na daga cikin sakaci da wasu ke yi akwai tafiyar da magani  na kasa da makamantarsa da raba shi ba ga bigerin shi da ya dace ba,na daga ciki akwai kasuwantar da daukan aiki da cin riba a cikinsa, ko srayar da lokacin aiki ko jinkirta abin da aka dorawa mutum na aiki ta fiskar da ba haka ya dace ba, wadannan da makamantarsu na cikin nau'uka na barna, kuma ha'intar jagoran al'umar musulmi ne da ita kanta al'umar sabo da abin da ke ciki na barna  mai girma da sharri mai fadi wanda zai haifar da cutarwarsa mai tsanani, kuma zai kawo cikas ga ci gaban kasa da habakarta da ma mutanenta    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle sau da yawa wani na kutsawa cikin dukiyar Allah da manzonSa cikin abin da ransa ya so ranar alkiyama bai da wani abu sai wuta.) Tirmizi ne ya rawaito kuma yace Hadisi ne Hasan sahih, kuma Ibnu Hibban ma ya rawaito shi a littafinsa Sahih da sanadi ingantacce.

Ya ku bayin Allah
Lalle abin da yak e wajibi ga duk wanda ya biye wa ransa abin da ya raya masa har ya yi gaba da fadi da dukiyar al'uma ta ko wace irin hanya ce daga cikin hanyoyi da ya koma ga Ubangijinsa ya tuba ga Mahaliccinsa ya rabu da wannan kudin haramun ta hanyar maida shi ga taskar kasa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : : (Yana kan mutuum abin da ya sata har sai ya mayar da shi).Ahmad da Abu Dauda da Tirmizi ne suka rawaito kuma Tirmizi ya ce Hadisi ne ingantacce.

Malaman fikihu sun yi tarayya kan cewa duk wanda ya lalata wani abu na dukiyar al'uma to dole ne ya biya haka kuma in ya dauki wani abu daga ciki ba tare da hakki ba to ya dawo da shi ga taskar kasa wato Baitul mali na musulmai.
Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kafa mana wata ka'ida  ga duk wanda ya rike wata amana na musulmai da kada ya ribaci wani abu na aikin hukuma da makamancinsa ya yi amfani da shi cikin maslahar kansa, wannan shi ake cewa ilimin tsarin gudanarwa  Tushe da bada kariya ga dukiyar al'uma, sai yace ga wanda ya je tattaro dukiyar zakka bayan yace wannan naku ne wannan kuma an bani kyauta ne :   (To me ya sa dayanku ba zai zauna a gidan iyayensa ba ya ga ko za a kawo masa kyauta ko aa, na rantse da wanda rai na ke hanunSa dayanku ba zai dauki wani abu ba face ya zo da shi ranar alkiyama yana dauke da shi a wuyarsa.) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Ku ji tsoron Allah yak u bayin Allah ku yi taimakekeniya dukkanku wurin kiyaye dukiyar al'uma ta dukkan hanyoyi da za ku iya yin hakan ku kiyaye kada ku yi sakaci da hakan Allah Madaukakin sarki yace : (ku yi taimakon juna bias da'a da takawa kada ku yi taimakekeniya a kan laifi da gaba)
Duk wanda ya biye wa ransa wurin sabo ko wani irin sabo ne da ya sani in ya faku daga idon mutane to fa  Allah na tsinkayar sirrinsa da bayyanensa ku tuna fadin Allah Madaukakin sarki : (ku sani lalle Allah yana sanin abin da ke cikin zukatanku to lalle ku kiyaye shi) da fadinSa  : (ya san maha'intar idanuwa da abin da zukata ke boyewa.)
Na daga cikin nusarwar Manzon Allah : (Duk namar da ta tsiro daga haram to wuta ce ta fi dace wa da ita). Kada ka gabatar da duniya mai karewa a kan lahira mai wanzuwa, kada ka shigar da wani abu ga kanka da iyalanka sai halal mai tsarki da dukiya tsarkakakkiya.
Ya zo cikin kissar yaron da mashi da ba a san daga ina ba ya kashe shi a yakin khaibar mutane na cewa barkan shi da samun Aljanna sai  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (A'a  ahir, na rantse da wanda rai na ke hanunSa lalle bargon da ya dauka a ranan khaibar kafin a raba ganima na babbaka da wuta a kan shi). Buhari da Muslim ne suka rawaito.
An rawaito daga Abubakar :"Duk wanda ya nemi arziki ta hanyar haram to zai rasa albarkan, ba za ka ga wani gurbi na kwarai ba a dukiyarsa idan ya ciyar da dukiyarsa gurin abincinsa to zai hadu da ukubarsa  a lahira, idan ya ciyar da iyalansa da shi to hakika  ya ha'ince su bai kyauta musu  ba, kuma ba abin mamaki ba ne in dansa ya zama mara biyayya a gare shi. Halayen wadanda yake daukan nauyi ya lalace, suka zama kwatankwacinsa kuma ya hadu da alhakin abin da ya aikata a rayuwarsa ta duniya kuma azabar lahira ta fi tsanani."

Huduba ta biyu
Ya tabbata daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : (Kafafuwan bawa ba za su gusa ba a ranar alkiyama har sai an tambaye shi game da rayuwarsa yadda ya tafiyar daita, da iliminsa cikin abin da ya tafiyar da shi da dukiyarsa ta wacce hanya ya same ta kuma ta yaya ya kasha ta, da jikinsa ta yaya ya tsofatar da shi).
Ku tsarkakar da hanyar ku ta neman abinci ku nesanci kazantattun hanyoyi za ku tsarkaka ku rabauta, za ku yi nasara kuma ku ji dadi.
Ibnu Taimiyya Allah ya masa rahama yace: "Abinci na hadewa ne ya cakudu da jiki  ya tsiro da shi sai ya zama kamar sinadari ne nasa, idan abincin ya zaman a kazanta ne sai jikin ma ya kazance sai wuta ta wajaba a gare shi, sabo da haka ne Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi y ace : (Duk namar da ta tsiro daga haram to wuta ce ta fi dace wa da ita). Aljanna tsarkakakkiya ce bam ai shiganta sai mai tsarki."
Abin da ake nufi da ci ya kunshi da wani abu da ya ke amfana da shi a kan saya a ji dadi a wannan rayuwa.