HUDUBAR MASALLACIN
ANNABI NA SHAIKH ABDULMUHSIN ALKASIM 24 -2-1440AH
HUDUBAR FARKO :
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin
sarki muna gode mishi kuma muna neman
taimakonsa , muna neman gafarar sa ,
kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu ,
duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar
kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu
bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da
iyalansa da sahabbansa da aminci
tabbatacce mai yawa .
Bayan haka:
Ku ji tsoron Allah - ya ku bayin Allah – cancancin tsoronSa da shi ne
ake neman ni'imomi kuma ake tunkude azaba.
Ya ku musulmai!
Duniya gidan jarrabawa ne da gwaji, an dabi'antar da ita bisa gurbata da
da kuma wahala,mutum zai yi kokari a cikinta tare da wahala Allah Madaukakin
sarki ya ce : ( Hakika mun haliccin mutum cikin wahala)
Rayuwar mutum a duniya kadan ne, bai da wani abu a rayuwarsa sai abin da
ya tsarkaka,
Kuma hutu da gushewar bakin ciki da bacin rai abin nema ne ga kowani dan
–adam, da haka ne zaa samu daddadan rayuwa, da morewa na jin dadi.
Dukkan halittu na cigiyar walwala da jin dadin rayuwa kuma suna nemanta,
Asalin sa'ida shi ne yelwatar zuciya, da samun kwanciyar hankali, idan Allah ya
nufi bawa da alheri zai fadada kirjinsa babu wata ni'ima mafi daukaka da ta kai ta, ita ce
sababi mafi girma na shiriya da ni'ima
mafi daukaka, Ibnul Kayyim Allah ya mishi rahama ya ce : (kamar yadda yalwar zuciya take sababi na shiriya to kuwa
asali ne na dukkan ni'ima da Alheri)
Sabo da girman wannan ni'imar ne Annabi Musa ya roki UbangijinSa Allah ya mishi baiwar wannan a farko lokacin
da ya tura shi zuwa ga Fir'auna sai ya ce : (Ya
Ubangiji na ka bude Min kirji na)
Allah ya fara kirgo ni'imarsa da shi ga Annabi sai ya ce : ( shin bamu bude kirjinka ba ne).
Allah ya sanya shi sababi na dukkan komi a duk lokacin da abu ya yi
girma to sabuban shi sai su yawaita,samun
shi ya saukaka,mafi cikan sabuba da kamalarta shi ne wanda sharia ta yi nuni
gare ta ta shiryar, Babu
abin da ya fi buda kirji kamar sanin Allah da sunayenSa da sifofinSa da kadaita
shi da bauta,-tsarki ya tabbata a gare shi, gwargwadon haka da karfinSa gwargwadon
budewar zuciyarsa da samun sawabarsa, Ibnu Hazmi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce " Na
yi tunani game da ayyukan bayi sai naga duka suna neman abu guda ne,ko da kuwa hanyoyinsu ya sha
banban gurin samun shi amma gaba daya na ga suna yi ne don tunkude bakinciki da
bacin rai daga kawunansu,ban ga hanya ba cikin hanyoyi da zai kai gare shi,-
watakila wasun su ma suna kai wa ga akasin haka ne –sai da fiskantar Allah shi
kadai da fifita neman yardarsa akan duk wani abu da ke kishiyantarsa, bawa bai
da abin da ya fi wannan hanya kuma yafi sadarwa zuwa ga walwala da jin dadi
kamarsa".
Mafi kamalan halittu a dukkan wata sifa da ke sanya walwala da jin
dadi shi ne Annabin mu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,
kuma mafi koyi da shi cikin mutane shi ya fi samun cikakken natsuwa da budewan
kirji da jin dadi da samun ni'ima.
Mafi girman abin da ake samun walwala da jin dadi shi ne imani da aiki
na kwarai, da su ne zuciya da gabbai ke gyaruwa, da daidaituwar ciki da waje,da
shi ne ake samun daddadan rayuwa da walwala na har abada, Allah Madaukakin
sarki ya ce : (wanda ya yi aiki na gari na miji ko mace alhali yana mumini lalle zamu
raya shi rayuwa daddada ) AL Nahl :97
Ba abin da ya fi sa walwala da jin dadi da kwanciyar hankali kamar
kaunar Allah da komawa gare shi da jin dadin bauta masa, Shaikhul Islam Allah
kara ya rahamce shi ya ce : (Idan baka jin dadin
aiki a cikin zuciyarka ba da kwanciyar hankali to ka tuhumi zuciyarka don kuwa
lalle Allah Mai girma Mai yawan godiya
ne )
Zabin Allah ga mutum ya fi zabinsa ga kansa, Allah shi ya fi tausayawa
bayi akan kansu, wanda yayi imani da kaddara na alherin sa da sharrinsa zai samu kwanciyar
hankali da budewar kirji,Allah Madaukakin sarki ya
ce : ( Wanda ya yi imani da Allah zai shiryar da zuciyarsa) Alkama Allah ya mishi rahama ya ce :(shi ne
muminin da musiba zata same shi sai ya san daga Allah ne sai ya yarda ya mika
wuya)
Bayi suna kai komo ne a rayuwarsu
a tsakanin sauki da tsanani ba wanda ya
isa ya fita daga dayan biyun ko ta kaka, samun walwala cikin hukuncin Allah da
godiya a halin yalwa da hakuri a halin kunci ko cuta Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce : Mamaki da al'amarin
mumini, lalle al'amarinsa duka alheri ne a gare shi, ba wanda ke da haka sai
mumini, in yalwa ko sauki ya same shi
sai ya yi godiya, sai ya kasance alheri a gare shi, idan tsanani ya same shi
sai yayi hakuri sai ya zama alheri gare shi.) Muslim ne ya rawaito.
Abin da Allah ya hukunta wa bawansa shi ya fi alheri gare shi, ya yin da
Allah ya jarrabi Maryam da haihuwar yaro ba tare da Uba ba sai ya ce da ita : (To ki ci ki sha ki sanyaya idanuwanki)
Wanda yayi imani da gamuwa da Allah da ladarSa sai ransa ya ta' allaka
da Maifalala akan abin da bai kai shi falala ba,sai abin da aka alkawarta masa
ya rarrashe shi daga abin da aka rasa shi, da
wannan ne duniyarsa da lahirarsa zasu gyaru,
Kyautata zato ga Allah na cikin ibadoji da ke haifar da aminci da
walwala ma'abocinta, baw na da abin da ya zata game da Ubangijinsa in alheri ya
samu alheri in kuma sharri ya samu
sharri, Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin Alkudsi : (Ni ina gun da bawa na ya zace ni) Bukhari da Muslim suka
rawaito.
Fatan nagari na kawo budewar kirji da kwanciyar hankali,kuma yana daga
cikin kyautata zato ga Allah Madaukaki.
Mabudan al'amura da ragamarsu na hanun Allah ne shi kadan shi, yana juya
zukata yadda ya so wurin baci ko gyaruwa ko kunci ko kwanciyar hankali da
walwala, da jin dadi ko tashin hankali, to dogaro ga wanda hakan ke hanunshi da
maida al'amari zuwa gare shi da aminta da shi wajibi ne a sharia, kuma garkuwa
ce ga ma'abotanta, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Duk
wanda ya dogara ga Allah to Allah ne ma'ishinsa)
To arzikin bayi a hanun Allah ya ke ba wani rayi da zai mutu sai ya kammala cinye arzikinsa to ka yarda ka gamsu ka ji dadi da abin da Allah ya baka
na kasonka,
Duk wanda ya koma zuwa ga Allah to Allah zai taimake shi ya shige mishi
gaba ya isan mishi,Allah Madaukakin sarki ya ce: ( Wadan
da mutane suka ce da su Lalle mutanen sun muku gangami ku tsorace su, sai hakan ya kara musu imani kuma suka ce ;Allah
ne Ma'ishinmu kuma madallah da abin dogaro. Sai suka juya da ni'ima daga Allah da falala, ba mummunar abu da
ya shafe su kuma suka bi yardar Allah Allah ma'aboci falala ne mai girma ).
Duk wanda ya yi kwadayin samun
sa'ida da walwala da kwanciyar hankali to ya kwankwasa kofar Mai karamci
to lalle Allah na kusa da wanda ya roke shi, kuma bai tabar da wanda ya yi fata
daga gare shi, da adua ne al'amuran duniya da lahira ke gyaruwa, na daga cikin
adu'o'in Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Ya Allah ka gyara min addini na wanda shi ne kariya ga
al'amari na, ka gyara min duniya ta wacce cikinta rayuwa ta take, ka gyara min lahira ta wacce gare ta zan
koma ka sanya rayuwa gare ni kari ne ga dukkan alheri , ka sanya mutuwa ta zama
hutu gare ni daga dukkan sharri)Muslim ne ya rawaito.
Ambaton Allah na da tasiri na ban al'ajabi wurin samar da kwanciyar
hankali walwala da natsuwar zuciya da gusar da bakin ciki da bacin rai Allah ya
ce : (wadanda suka bada gaskiya zuciyarsu take
natsuwa da ambaton Allah, to da ambaton Allah zukata ke natsuwa,)
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana cewa yayin bakin ciki : ( "La
ilaha illallahul-Azimul-Halim. La ilaha illallahu Rabbul-'Arshil-'Azim. La
ilaha illallahu Rabbus-samawati, wa Rabbul-ardi, wa Rabbul-'Arshil- Karim.) Babu abin bautawa da
gaskiya sai Allah Maigirma mai hakuri .ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
ubangijin Al'arshi mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah ubangijin
sammai kuma Ubangijin kasa kuma Ubangijin Al'arshi mai girma) Bukhari ne ya rawaito
Bukhari ne ya rawaito
Mafi falalan zikiri shine
Alkur'ani mai girma shi ne maganar Allah akwai shiriya tattare da shi da waraka, Allah
Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku mutane hakika
gargadi ya zo muku daga Ubangijinku da waraka
ga abin da ke cikin kiraza da shiriya
da jinkai ga muminai )
Mafi cancantan wadanda zasu
samu walwalar zuciya da kwanciyar
hankali a halittu sune mahaddatan Alkur'ani, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Taha. Bamu saukar da Alkur'ani gare ka don ka wahala ba
)
A Tasbihi da Tahmidi da yawan
sujada da dimantan biyayya akwai samun annashwa da kwanciyar hankali, da
tafiyar da bakinciki da kunci, Allah
Madaukakin sarki ya ce : (Hakika mun san lalle
kirjinka na kuntata sabo da abin da suke
fada. To sai ka yi tasbihi da godiyar Ubangijinka kasance cikin masu sujada . ka
bautawa Ubangijinka har mutuwa ta zo ma.)
Da lazimtar tsoron Allah akan samu yayewan bakin ciki da tafiyar da bacin rai, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Duk wanda ya ji tsoron Allah zai sanya mishi mafita ) kuma
da ita ne akan samu saukin abubuwa Allah Madaukakin sarki ya ce : (Duk wanda ya ji tsoron Allah zai sanya mishi sauki cikin
lamuransa)
Sallah haske ne ga ma'abocinta
kuma tana taimakawa wurin samar
da kwanciyar hankali da natsuwa da tafiyar da bakin ciki Allah Madaukakin sarki
ya ce : (ku nemi taimako da hakuri sallah)
Na daga cikin koyarwan shi Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
idan wani abu matsananci ya dame shi
sai ya bazama zuwa ga sallah.) Abu Dauda
ne ya rawaito.
Idan bawa ya bude wuninsa da sallah sai sauran wunin nasa ya yi kyau, to
duk wanda ya yi sallar asuba yana cikin kariyar Allah, wanda ya yi ta tare da
nafilarta Allah zai isan masa karshen wuninsa, Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Allah
yana cewa ya Dan-Adam : kar ka gaza yin raka'a hudu a farkon wuni to zan kare
ka karshensa)Ahmad ne ya rawaito.
Ilimin da aka gado daga Allah da manzonsa tsira da amincin Allah ya
tabbata a gare shi idan ya hadu da aiki
yana sanya kwanciyar hankali da walwala har zuciyar ta fadada ta fi duniya
fadi, ma'abota ilimin kuma zasu fi kowa kwanciyar hankali cikin mutane da
walwala da fadin kirji da jin dadin rayuwa, kuma mafi kyan mutane dabi'u.
A duk lokacin da ilimin bawa ya karu to zai dada samun kwanciyan hankali
da walwala a zuciyarsa , Allah Madaukakin sarki ya ce : (Shin kuma wanda ya kasance matacce sa'annan muka rayar da shi kuma muka sanya
wani haske dominsa, yana tafiya da shi yana zama kamar wanda misalinsa yana
cikin duffai, shi kuma ba mai fita ba daga gare su?)
Ibnul kayyim ya ce game da shaikhul Islam : "Ban
ga wanda ya fi shi jin dadin rayuwa ba duk da matsatsi da yake ciki da rashin
wadata na abin duniya,sai dai ma kishiyan hakan, tare da daure shi da ake yi da
tsoratarwa da tursasawa, amma duk da haka yana cikin wanda ya fi mutane jin
dadin rayuwa ya fi su fadin kirji da
kwanciyar hankali, da karfin hali da dadin rai ga fiskarsa cike da fara'a da
walwala ta ni'ima."
Kyautatawa mutane alheri ne bai kawo wani abu sai alheri, ba za ka taba
ganin mutum mai karamci mai kyautata wa mutane ba face shine mafi kwanciyar
hankali cikin mutane, kuma mafi zama cikin dadin rai a mutane kuma mafi ni'imar zuciyarsa a cikinsu, Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce : (Misali marowaci da
mai sadaka, kamar mutane biyu ne ke sanye da sulken yaki ya takure hannayensu
zuwa nononsu da hakarkarinsu a duk
lokacin da mai sadaka ya yi sadaka sai silken ya dada fadada har ya suturce shi zuwa yatsun shi yana share gurbin sa, amma
shi munafuki a duk lokacin da ya nufi sadaka sai sulken ya kuntata ko wani da'ira na sarkan ya manne a gurbin shi.) Muslim ne ya rawaito.
Wanda ya muamalanci
mutane don Allah ya huta domin ba zai
nemi tsinkayan yabo ko kuma
nadaman suka ba halin shi tamkar
misalin fadin Allah ne . ( Tamkar fadin
Allah madaukakin sarki ne :- Lallai mu muna ciyar da ku ne , don
neman yardan Allah ba ma bukatan sakayya
ko godiya daga gare ku ).
Hakan na dada karfafa a
wurin mu'amala da makusanta da
kuma wanda ke da karfin alaka da su .
Hakika za ka ga abin da ba ka so daga wasu
mutane , to, mai hankali bazai tawaye kyautatawan su ba sabo da
tawaya da ya fito daga gare su ko ka yanke musu zumunci sabo da
gajartawa da haka ne mutum zai rayu cikin tsanakin shi da kwanciyan hankali a ko wani hali , Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : - (Kar mumini
ya tsani mumina –wato: kar ya ki ta – idan ya tsani wani hali daga gareta to
zai yarda da wani halin) Muslim ne ya rawaito
A cikin zama da salihai
da ma'abota ilimi da addini akwai wani
abu na debe kewa da samun walwala kuma a
nan ne mutum ke samun ilimi da hikima
zuciyar sa ta tsarkaka ya zama
mai kyau a cikin abokan sa wanda ya koma
zuwa ga ma'abota shawara da hankali
cikin al'amuran sa zai samu
kwanciyar hankali da waraka na zuciya
abinda ya rikice mishi zai gushe
Allah madaukakin sarki ya ce :-(Idan
wani al'amari ya zo musu na aminci ko
tsoro sai su yada shi , dama sun maida shi
zuwa ga Manzon Allah da jagororin
su ma'abota ra'ayi a cikin su da wadan da suke tsinkayo fahimta ko hukunci da sun san shi daga cikin su ).
Kiyayyan shaidan da dan
adam baya yankewa cikin yin neman tsari
daga shaidan akwai koran wasuwasin na shi dake jirkita
kwanciyar hankalin dewa daga cikin mutane , musulunci
na kwakwari don samar da sabuban
da za su kwantar da hankali su haifar da walwala ga musulmi tun lokacin
da ya tashi daga baci shaidan na aiki don akasin haka Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : (Lallai shaidan yana kulli uku a
karshen kayin dayan ku idan ya yi barci yana buga ko wani daya daga cikin kullin kana da
dare mai tsawo , ka kwanta to
idanya tashi ya ambaci Allah sai kulli guda ya warware in ya yi alwala sai
kulli guda ya warware idan ya yi salla sai kulli guda ya warware sai ya wayi gari mai kuzari cikin tsarkakakken rayi idan baiyi haka ba sai ya wayi gari yana da
kazantaccen rayi mai kasala ) Buhari
da muslim ne suka rawaito
Kuma karfin mumini tushe
ne mai girma na samun warakan zuciya da walwala
ba zai biyewa abubuwa na wahami ba zai kuma saki jiki don bakin ciki ba ko ya samu rauni a gaban abubuwa na ki sai dai ma zuciyan shi na kafe yana kuma
tare da yakini da sakankancewa
cewa lallai tare da wahala akwai sauki idan bawa ya halarto da falalar Allah da ni'imar sa a gare shi hakan sai ya haifar
masa da
sabon godiya da zai kwantar
mishi da hankali kuma
ya sanya mishi walwala .
Kuma wadatar zuci tushe
ne na arziki, kuma yana daga cikin mafi amfanin abin da ake
yin magani da shi na zukata , abinda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya nusar zuwa gare shi a fadin sa (ku yi dubi zuwa ga wanda ke kasa da ku kar ku yi dubi
zuwa ga wanda ke sama da ku don hakan
shi ya fi dacewa da kar ku raina ni'imar
Allah a gare ku)Buhari da muslim ne suka
rawaito shi
Wanda ya tattara zuciyar
sa a bisa wunin sa da lokacin sa zuciyan shi za ta natsu ba zai yi bakin ciki
ba cikin abin da ya shude ba zai bata
rai ba cikin abin da yake fiskantowa to
abinda ya shude ba zai dawo ba . Abu mai
fiskantowa kuma gaibi ne rubutacce na daga cikin adu'o'in shi Manzon Allaha
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
akwai ;;;( Ya Allah ina neman tsarin ka daga sharrin bakin ciki da bacin rai) . Buhari ne ya rawaito
Rashin amfana da lokaci
tushe ne na bakin ciki da bacin rai
, wanda ya raya lokacin shi da
aiki na kwarai ko ilimi mai amfani
wannan duka zai tafi daga gare shi, abunda ya tattaro walwala da sa'ada
na cikin neman taimakon Allah bisa ga
abin da zai amfanar da yin nesa da abin
da zai sanya rauni ga bawa ko ya raunana
zuciyar sa da
karfin sa Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-(
Ka yi kwadayi bisa ga abin da zai amfane ka
ka nemi taimakon Allah , idan wani abu ya same ka kar ka ce ba don na yi kaza-da kaza ba da kaza zai
kasance domin lau tana bude aikin shaidan )Muslim ne ya rawaito .
Zunubai kofa ce da musibu ke zuwa ta gunta
ga bayi , da abin da ake sakawa
mai laifi da ita na daga bakin ciki da bacin rai da
kunci na zuci da kekasan zuciya
don ya zama ukuba na duniya kafin
na lahira mafita daga haka shi ne yin
nesa daga sabo da tuba zuwa ga Allah don ya warware wurin kuncin
da fadaduwan zuciya haka nan kuma a wurin kadaici ya sanya debe
kewa .
Tsarkake zuciya daga cututtukan sa yana
kawo yayewan zuciya ta samu walwala yana kuma fadada shi yana daga cikin adu'ar mumini (Kada ka
sanya kulli a cikin zukatan mu game da wadan da suka yi imani ya Uabangijin mu lallai kai mai tausayi ne
mai jin kai) bisa ga
wannan sifa 'yan aljanna suke kasancewa Allah madaukakin sarki ya ce:- (Muka ci re daga cikin kirajen su na kulli
kwaramai yana gudana a karkashin su kuma suka ce dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah wanda ya shiryar
da mu zuwa ga wannan ba mu kasance da mu shiryu ba ba don Allah ya shiryar da mu
ba )
BAYAN
HAKA:
YA KU MUSULMAI:-
To shi musulunci tushe ne na dukkan alheri kuma
masdari ne na dukkan samun sa
'ida da walwala ma'abotan shi suna
cikin aljanna na gaggawa da ni'ima da
baya yankewa Allah madaukakin sarki ya
ce :-(Wanda suyka kyautata a nan duniya da
kyakkyawa suna da kyakkyawa kuma gidan lahira ya fi alheri madalla da gidan masu tsoron Allah )
Duk wanda ya san shakawa irin na jahiliyya da ma'abotan shi zai san falala na ni'imar musulunci da ma'abotan sa ba abin da zai isar mishi sai godewa Allah bisa ga hakan ,
da kuma riko da addinin sa da alfahari da shi da tabbatuwa a kan shi da kiran halittu zuwa
gare shi.
Ina neman
tsarin Allah daga shaidan abin jefewa
Duk wanda Allah ya nufi
ya shirye shi zai fadada zuciyar shi don musulunci, wanda kuma ya nufi ya batar da shi zai sanya
kirjin sa a kuntace cikin kunci kai ka
ce yana haurawa ne cikin sama
haka ne Allah yake sanya kazanta ga wadan da ba sa imani ya Allah ka sanya albarka gare ni da ku a
alkur'ani mai girma .
HUDUBA NA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah bisa kyutatawan
sa da godiya a gare shi bisa datarwarsa da baiwar sa
na shaida ba abin bautawa da
gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya ina mai girmama sha'anin sa kuma na shaida
Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban
shi da amincin tabbatacce mai yawa da aminci mai kari .
YA KU MUSULMAI:-
Allah ya yalwata kasar
saudiya da ni'imomi masu yawa wanda ya fi ko wanne a cikin su shi ne ni'imar
musulunci da yaduwar shi da kuma raya masallatai biyu masu alfarma da
musu hidima da girmama wanda suka fiskanto su da bugawa da yada alkur'ani mai
girma a cikin sararin duniya da bawa musulmai kulawa da musu hidima a
al'amuran su da yin hukunci da shari'ar Allah a kasar sa kuma
ya sanya ta alkibla na musulmai , kuma zuciyar duniyar musulunci tare da
abin da ya ni'imta a gare su na daga aminci da zaman lafiya da yalwa na rayu da
jin dadin shi da kuma hadin kan jama'anta
da dunkulewan su dukkan hakan da
wanin sa a falalan Allah ne shi kadan shi
da kuma datarwa da Allah ya yiwa jagororin ta
suka sanya abu na farko mafi muhimmanci
tun daga kafa wannan daula na musulunci tabbatar da kadaita Allah da bin
Annabin sa tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi da hidima wa musulmai
da yada ilimi na shari'a wanda aka ciro
shi daga
littafi da sunna da kuma bin
sawun magabata na wannan al'uma kuma duk
yanda abu ya caccanza da sautukan wadan da suka saba mana ba abinda zai karawa wannan kasa face riko da musulunci da haduwa a kan kalma tsakanin mabiya da jagororin su.
Ya wajaba ga musulmai su kau da kai daga wasu jefe –jefe da jita-jitan masu tada zaune tsaye da rashin sauraro zuwa gare su da shagaltuwa da abin da zai amfanar .
Sannan ku sani lallai Allah na umartan ku da salati
da aminci ga Annabin shi sai ya ce a
cikin littafin shi mafi hikima da saukar
:- (Lallai Allah da mala'iku suna salati ga
Annabi ya ku wadan da suka yi imani ku
yi salati a gare shi da aminci
tabbatacce )
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق