السبت، 3 نوفمبر 2018

KWANCIYAR HANKALI A MUSULUNCI


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH ABDULMUHSIN ALKASIM 24 -2-1440AH
HUDUBAR FARKO :
  Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin sarki  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa , muna neman gafarar sa  , kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa  da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa .
Bayan haka:
Ku ji tsoron Allah - ya ku bayin Allah – cancancin tsoronSa da shi ne ake neman ni'imomi  kuma ake tunkude azaba.
Ya ku musulmai!
Duniya gidan jarrabawa ne da gwaji, an dabi'antar da ita bisa gurbata da da kuma wahala,mutum zai yi kokari a cikinta tare da wahala Allah Madaukakin sarki ya ce : ( Hakika mun haliccin mutum cikin wahala)
Rayuwar mutum a duniya kadan ne, bai da wani abu a rayuwarsa sai abin da ya tsarkaka,
Kuma hutu da gushewar bakin ciki da bacin rai abin nema ne ga kowani dan –adam, da haka ne zaa samu daddadan rayuwa, da morewa na jin dadi.
Dukkan halittu na cigiyar walwala da jin dadin rayuwa kuma suna nemanta, Asalin sa'ida shi ne yelwatar zuciya, da samun kwanciyar hankali, idan Allah ya nufi bawa da alheri zai fadada kirjinsa babu wata  ni'ima mafi daukaka da ta kai ta, ita ce sababi  mafi girma na shiriya da ni'ima mafi daukaka, Ibnul Kayyim Allah ya mishi rahama ya ce : (kamar yadda yalwar zuciya take sababi na shiriya to kuwa asali ne na dukkan ni'ima da Alheri)
Sabo da girman wannan ni'imar ne Annabi Musa ya roki UbangijinSa  Allah ya mishi baiwar wannan a farko lokacin da ya tura shi zuwa ga Fir'auna sai ya ce : (Ya Ubangiji na ka bude Min kirji na)
Allah ya fara kirgo ni'imarsa da shi ga Annabi sai ya ce : (  shin bamu bude kirjinka ba ne).
Allah ya sanya shi sababi na dukkan komi a duk lokacin da abu ya yi girma to sabuban shi sai su  yawaita,samun shi ya saukaka,mafi cikan sabuba da kamalarta shi ne wanda sharia ta yi nuni gare ta ta  shiryar,   Babu abin da ya fi buda kirji kamar sanin Allah da sunayenSa da sifofinSa da kadaita shi da bauta,-tsarki ya tabbata a gare shi, gwargwadon haka da karfinSa gwargwadon  budewar zuciyarsa da samun sawabarsa, Ibnu Hazmi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce " Na yi tunani game da ayyukan bayi sai naga duka suna neman  abu guda ne,ko da kuwa hanyoyinsu ya sha banban gurin samun shi amma gaba daya na ga suna yi ne don tunkude bakinciki da bacin rai daga kawunansu,ban ga hanya ba cikin hanyoyi da zai kai gare shi,- watakila wasun su ma suna kai wa ga akasin haka ne –sai da fiskantar Allah shi kadai da fifita neman yardarsa akan duk wani abu da ke kishiyantarsa, bawa bai da abin da ya fi wannan hanya kuma yafi sadarwa zuwa ga walwala da jin dadi kamarsa".
Mafi kamalan  halittu  a dukkan wata sifa da ke sanya walwala da jin dadi shi ne Annabin mu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma mafi koyi da shi cikin mutane shi ya fi samun cikakken natsuwa da budewan kirji da jin dadi da samun ni'ima.
Mafi girman abin da ake samun walwala da jin dadi shi ne imani da aiki na kwarai, da su ne zuciya da gabbai ke gyaruwa, da daidaituwar ciki da waje,da shi ne ake samun daddadan rayuwa da walwala na har abada, Allah Madaukakin sarki ya ce  : (wanda ya yi aiki na gari na miji ko mace alhali yana mumini lalle zamu raya shi rayuwa daddada ) AL Nahl :97
Ba abin da ya fi sa walwala da jin dadi da kwanciyar hankali kamar kaunar Allah da komawa gare shi da jin dadin bauta masa, Shaikhul Islam Allah kara ya rahamce shi ya ce : (Idan baka jin dadin aiki a cikin zuciyarka ba da kwanciyar hankali to ka tuhumi zuciyarka don kuwa lalle Allah Mai girma  Mai yawan godiya ne )  
Zabin Allah ga mutum ya fi zabinsa ga kansa, Allah shi ya fi tausayawa bayi akan kansu, wanda yayi imani da kaddara  na alherin sa da sharrinsa zai samu kwanciyar hankali da budewar kirji,Allah Madaukakin sarki ya ce : ( Wanda ya yi imani da Allah zai shiryar da zuciyarsa)  Alkama Allah ya mishi rahama  ya ce :(shi ne muminin da musiba zata same shi sai ya san daga Allah ne sai ya yarda ya mika wuya)
Bayi suna kai komo  ne a rayuwarsu a tsakanin sauki da tsanani  ba wanda ya isa ya fita daga dayan biyun ko ta kaka, samun walwala cikin hukuncin Allah da godiya a halin yalwa da hakuri a halin kunci  ko cuta Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Mamaki da al'amarin mumini, lalle al'amarinsa duka alheri ne a gare shi, ba wanda ke da haka sai mumini, in yalwa ko  sauki ya same shi sai ya yi godiya, sai ya kasance alheri a gare shi, idan tsanani ya same shi sai yayi hakuri sai ya zama alheri gare shi.) Muslim ne ya rawaito.
Abin da Allah ya hukunta wa bawansa shi ya fi alheri gare shi, ya yin da Allah ya jarrabi Maryam da haihuwar yaro ba tare da Uba ba sai ya ce da ita : (To ki ci ki sha ki sanyaya idanuwanki)
Wanda yayi imani da gamuwa da Allah da ladarSa sai ransa ya ta' allaka da Maifalala akan abin da bai kai shi falala ba,sai abin da aka alkawarta masa ya rarrashe shi daga abin da aka rasa  shi,  da wannan ne duniyarsa  da lahirarsa zasu  gyaru,
Kyautata zato ga Allah na cikin ibadoji da ke haifar da aminci da walwala ma'abocinta, baw na da abin da ya zata game da Ubangijinsa in alheri ya samu alheri in kuma  sharri ya samu sharri, Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin Alkudsi : (Ni ina gun da bawa na ya zace ni) Bukhari da Muslim suka rawaito.
Fatan nagari na kawo budewar kirji da kwanciyar hankali,kuma yana daga cikin  kyautata zato ga Allah Madaukaki.
Mabudan al'amura da ragamarsu na hanun Allah ne shi kadan shi, yana juya zukata yadda ya so wurin baci ko gyaruwa ko kunci ko kwanciyar hankali da walwala, da jin dadi ko tashin hankali, to dogaro ga wanda hakan ke hanunshi da maida al'amari zuwa gare shi da aminta da shi wajibi ne a sharia, kuma garkuwa ce ga ma'abotanta, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Duk wanda ya dogara ga Allah to Allah ne ma'ishinsa)
To arzikin bayi a hanun Allah ya ke ba wani rayi  da zai mutu sai ya kammala  cinye  arzikinsa to ka yarda  ka gamsu ka ji dadi da abin da Allah ya baka na kasonka,
Duk wanda ya koma zuwa ga Allah to Allah zai taimake shi ya shige mishi gaba ya isan mishi,Allah Madaukakin sarki ya ce: ( Wadan da mutane suka ce da su Lalle mutanen sun muku gangami ku tsorace su, sai  hakan ya kara musu imani kuma suka ce ;Allah ne Ma'ishinmu kuma madallah da abin dogaro. Sai suka juya da ni'ima daga  Allah da falala, ba mummunar  abu  da ya shafe su kuma suka bi yardar Allah Allah ma'aboci falala ne mai girma ).
Duk wanda ya yi kwadayin samun  sa'ida da walwala da kwanciyar hankali to ya kwankwasa kofar Mai karamci to lalle Allah na kusa da wanda ya roke shi, kuma bai tabar da wanda ya yi fata daga gare shi, da adua ne al'amuran duniya da lahira ke gyaruwa, na daga cikin adu'o'in Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Ya Allah ka gyara min addini na wanda shi ne kariya ga al'amari na, ka gyara min duniya ta wacce cikinta rayuwa ta  take, ka gyara min lahira ta wacce gare ta zan koma ka sanya rayuwa gare ni kari ne ga dukkan alheri , ka sanya mutuwa ta zama hutu gare ni daga dukkan sharri)Muslim ne ya rawaito.
Ambaton Allah na da tasiri na ban al'ajabi wurin samar da kwanciyar hankali walwala da natsuwar zuciya da gusar da bakin ciki da bacin rai Allah ya ce : (wadanda suka bada gaskiya zuciyarsu take natsuwa da ambaton Allah, to da ambaton Allah zukata ke natsuwa,)
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance  yana cewa yayin bakin ciki : (   "La ilaha illallahul-Azimul-Halim. La ilaha illallahu Rabbul-'Arshil-'Azim. La ilaha illallahu Rabbus-samawati, wa Rabbul-ardi, wa Rabbul-'Arshil- Karim.) Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Maigirma mai hakuri .ba abin bautawa da gaskiya sai Allah ubangijin Al'arshi mai girma, Ba abin bautawa da gaskiya sai Allah ubangijin sammai kuma Ubangijin  kasa  kuma Ubangijin Al'arshi mai girma)  Bukhari ne ya rawaito
Bukhari ne ya rawaito
Mafi  falalan zikiri shine Alkur'ani mai girma shi ne maganar Allah  akwai shiriya tattare da shi da waraka, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku mutane hakika gargadi ya zo muku daga Ubangijinku da waraka  ga abin da ke cikin kiraza da shiriya  da jinkai ga muminai )
Mafi cancantan  wadanda zasu samu  walwalar zuciya da kwanciyar hankali a halittu sune mahaddatan Alkur'ani, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Taha. Bamu saukar da Alkur'ani gare ka don ka wahala ba )   
A Tasbihi da Tahmidi  da yawan sujada  da dimantan biyayya  akwai samun annashwa da kwanciyar hankali, da tafiyar da bakinciki da kunci,  Allah Madaukakin sarki ya ce : (Hakika mun san lalle kirjinka na kuntata  sabo da abin da suke fada. To sai ka yi tasbihi da godiyar Ubangijinka kasance cikin masu sujada . ka bautawa Ubangijinka har mutuwa  ta zo ma.)
Da lazimtar tsoron Allah akan samu yayewan bakin ciki da tafiyar  da bacin rai, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Duk wanda ya ji tsoron Allah zai sanya mishi mafita ) kuma da ita ne akan samu saukin abubuwa Allah Madaukakin sarki ya ce : (Duk wanda ya ji tsoron Allah zai sanya mishi sauki cikin lamuransa)  
Sallah haske ne ga ma'abocinta  kuma tana taimakawa  wurin samar da kwanciyar hankali da natsuwa da tafiyar da bakin ciki Allah Madaukakin sarki ya ce : (ku nemi taimako da hakuri  sallah)
Na daga cikin koyarwan shi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi idan wani abu matsananci ya  dame shi sai ya  bazama zuwa ga sallah.) Abu Dauda ne ya rawaito.
Idan bawa ya bude wuninsa da sallah sai sauran wunin nasa ya yi kyau, to duk wanda ya yi sallar asuba yana cikin kariyar Allah, wanda ya yi ta tare da nafilarta Allah zai isan masa karshen wuninsa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Allah yana cewa ya Dan-Adam : kar ka gaza yin raka'a hudu a farkon wuni to zan kare ka karshensa)Ahmad ne ya rawaito.
Ilimin da aka gado daga Allah da manzonsa tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi  idan ya hadu da aiki yana sanya kwanciyar hankali da walwala har zuciyar ta fadada ta fi duniya fadi, ma'abota ilimin kuma zasu fi kowa kwanciyar hankali cikin mutane da walwala da fadin kirji da jin dadin rayuwa, kuma mafi kyan mutane dabi'u.
A duk lokacin da ilimin bawa ya karu to zai dada samun kwanciyan hankali da walwala a zuciyarsa , Allah Madaukakin sarki ya ce : (Shin kuma wanda ya kasance matacce  sa'annan muka rayar da shi kuma muka sanya wani haske dominsa, yana tafiya da shi yana zama kamar wanda misalinsa yana cikin duffai, shi kuma ba mai fita ba daga gare su?)
Ibnul kayyim ya ce game da shaikhul Islam : "Ban ga wanda ya fi shi jin dadin rayuwa ba duk da matsatsi da yake ciki da rashin wadata na abin duniya,sai dai ma kishiyan hakan, tare da daure shi da ake yi da tsoratarwa da tursasawa, amma duk da haka yana cikin wanda ya fi mutane jin dadin rayuwa  ya fi su fadin kirji da kwanciyar hankali, da karfin hali da dadin rai ga fiskarsa cike da fara'a da walwala ta ni'ima."
Kyautatawa mutane alheri ne bai kawo wani abu sai alheri, ba za ka taba ganin mutum mai karamci mai kyautata wa mutane ba face shine mafi kwanciyar hankali cikin mutane, kuma mafi zama cikin dadin rai a mutane  kuma mafi ni'imar zuciyarsa  a cikinsu, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Misali marowaci da mai sadaka, kamar mutane biyu ne ke sanye da sulken yaki ya takure hannayensu zuwa nononsu da hakarkarinsu  a duk lokacin da mai sadaka ya yi  sadaka sai  silken ya dada fadada  har ya suturce shi  zuwa yatsun shi yana share gurbin sa, amma shi munafuki a duk lokacin da ya nufi sadaka sai sulken ya kuntata  ko wani da'ira na sarkan  ya manne a gurbin shi.) Muslim ne ya rawaito.
Wanda ya muamalanci mutane don Allah ya huta  domin ba zai nemi tsinkayan  yabo  ko kuma  nadaman suka ba  halin shi tamkar misalin fadin Allah ne . ( Tamkar fadin Allah  madaukakin sarki ne :-   Lallai mu muna ciyar da ku ne  ,  don neman yardan Allah  ba ma bukatan sakayya ko godiya daga gare ku  ).
Hakan na dada karfafa a wurin mu'amala da  makusanta  da  kuma wanda ke da karfin alaka da su .
 Hakika za ka ga abin da ba ka so daga wasu mutane ,  to, mai hankali  bazai tawaye kyautatawan su ba sabo da tawaya  da ya fito daga gare su  ko ka yanke musu zumunci sabo da gajartawa  da haka ne mutum zai rayu  cikin tsanakin shi  da kwanciyan hankali  a ko wani hali  , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : - (Kar mumini ya tsani mumina –wato: kar ya ki ta – idan ya tsani wani hali daga gareta to zai yarda da wani halin) Muslim ne ya rawaito
A cikin zama da salihai da ma'abota ilimi da addini  akwai wani abu na debe kewa da samun walwala  kuma a nan ne mutum ke samun ilimi da hikima  zuciyar sa ta tsarkaka  ya zama mai kyau a cikin abokan sa  wanda ya koma zuwa ga ma'abota shawara da hankali  cikin al'amuran sa  zai samu kwanciyar hankali da waraka na zuciya  abinda ya rikice mishi zai gushe  Allah madaukakin sarki ya ce :-(Idan wani al'amari ya zo musu  na aminci ko tsoro sai su yada shi , dama sun maida shi  zuwa ga Manzon Allah  da jagororin su  ma'abota ra'ayi a cikin su  da wadan da suke tsinkayo fahimta ko hukunci  da sun san shi daga cikin su ).
Kiyayyan shaidan da dan adam baya yankewa   cikin yin neman tsari daga shaidan akwai koran wasuwasin na shi  dake jirkita   kwanciyar hankalin dewa daga cikin mutane ,  musulunci  na kwakwari don samar da sabuban   da za su kwantar da hankali su haifar da walwala ga musulmi tun lokacin da ya tashi daga baci shaidan na aiki don akasin haka  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lallai shaidan yana   kulli  uku  a karshen kayin dayan ku  idan ya yi barci  yana buga ko wani daya daga cikin kullin  kana da  dare mai tsawo , ka kwanta   to idanya tashi ya ambaci Allah sai kulli guda ya warware in ya yi alwala sai kulli guda ya warware idan ya yi salla sai kulli guda ya warware  sai ya wayi gari mai kuzari  cikin tsarkakakken rayi   idan baiyi haka ba sai ya wayi gari yana da kazantaccen rayi mai kasala    ) Buhari da muslim ne suka rawaito
Kuma karfin mumini tushe ne mai girma   na samun  warakan zuciya  da walwala  ba zai biyewa abubuwa na wahami ba  zai kuma saki jiki don bakin ciki ba ko ya samu rauni  a gaban abubuwa na ki  sai dai ma zuciyan shi na kafe  yana kuma  tare da yakini da sakankancewa   cewa   lallai tare da  wahala akwai sauki   idan bawa ya halarto da falalar Allah  da ni'imar sa a gare shi hakan sai ya haifar masa  da  sabon godiya  da zai kwantar mishi  da hankali   kuma   ya sanya mishi walwala  .
Kuma wadatar zuci tushe ne na arziki,    kuma yana daga cikin mafi amfanin abin da ake yin magani da shi na zukata , abinda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya nusar zuwa gare  shi a fadin sa (ku yi dubi zuwa ga wanda ke kasa da ku kar ku yi dubi zuwa ga wanda ke sama da ku  don hakan shi ya fi dacewa  da kar ku raina ni'imar Allah  a gare ku)Buhari da muslim ne suka rawaito shi
Wanda ya tattara zuciyar sa  a bisa wunin sa da lokacin sa  zuciyan shi za ta natsu ba zai yi bakin ciki ba cikin abin da ya shude  ba zai bata rai ba cikin abin da yake fiskantowa   to abinda ya shude ba zai dawo ba  . Abu mai fiskantowa kuma gaibi ne rubutacce na daga cikin adu'o'in shi Manzon Allaha tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi   akwai ;;;( Ya Allah ina neman  tsarin ka daga  sharrin bakin ciki da bacin rai)  . Buhari ne ya rawaito
           Rashin amfana da  lokaci  tushe ne na bakin ciki da bacin rai  ,    wanda ya raya lokacin shi da aiki na kwarai ko ilimi mai amfani  wannan duka zai tafi daga gare shi, abunda ya tattaro walwala da sa'ada na cikin   neman taimakon Allah bisa ga abin da zai amfanar  da yin nesa da abin da zai sanya rauni ga bawa  ko ya raunana  zuciyar sa    da  karfin sa  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Ka yi kwadayi bisa ga abin da zai amfane ka  ka nemi taimakon Allah , idan wani abu ya same ka kar ka  ce ba don na yi kaza-da kaza ba da kaza zai kasance domin lau tana bude aikin  shaidan )Muslim ne ya rawaito .
      Zunubai kofa ce  da musibu ke zuwa  ta gunta  ga bayi ,  da abin da ake sakawa mai laifi   da ita na daga bakin ciki da bacin rai da kunci    na zuci da kekasan zuciya  don ya zama ukuba na duniya  kafin na lahira  mafita daga haka shi ne yin nesa  daga sabo  da tuba zuwa ga Allah don ya warware  wurin kuncin  da  fadaduwan zuciya  haka nan kuma a wurin kadaici ya sanya debe kewa  .
     Tsarkake zuciya daga cututtukan sa yana kawo yayewan zuciya  ta samu walwala  yana kuma fadada shi  yana daga cikin adu'ar mumini  (Kada ka sanya kulli a cikin zukatan mu game da wadan da suka yi imani  ya Uabangijin mu lallai kai mai tausayi ne mai jin kai) bisa ga wannan sifa 'yan aljanna suke kasancewa Allah madaukakin sarki ya ce:-   (Muka  ci re daga cikin kirajen su  na kulli  kwaramai yana gudana a karkashin su kuma suka ce dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah   wanda ya shiryar da mu  zuwa ga wannan  ba mu kasance da  mu shiryu ba ba don Allah ya shiryar da mu ba  )
                BAYAN HAKA:
YA KU MUSULMAI:-
  To shi musulunci tushe ne na dukkan alheri   kuma  masdari ne na  dukkan samun sa 'ida da walwala   ma'abotan shi suna cikin aljanna  na gaggawa da ni'ima da baya yankewa  Allah madaukakin sarki ya ce :-(Wanda suyka kyautata a nan duniya da kyakkyawa suna  da kyakkyawa kuma  gidan lahira ya fi alheri  madalla da gidan masu tsoron Allah )
  Duk wanda ya san  shakawa irin na  jahiliyya da ma'abotan shi  zai san falala na ni'imar musulunci  da ma'abotan sa ba abin da zai  isar mishi sai godewa Allah bisa ga  hakan ,  da kuma riko da addinin sa da alfahari da shi  da tabbatuwa a kan shi da kiran halittu zuwa gare shi.
 Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa 
Duk wanda Allah ya nufi ya shirye shi zai fadada zuciyar shi don musulunci,  wanda kuma ya nufi ya batar da shi zai sanya kirjin sa a kuntace cikin kunci  kai ka ce  yana haurawa ne  cikin sama  haka ne Allah yake sanya kazanta ga wadan da ba sa imani  ya Allah ka sanya albarka gare ni da ku a alkur'ani mai girma .
 HUDUBA NA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah    bisa kyutatawan sa   da godiya a  gare shi bisa datarwarsa  da baiwar sa  na shaida  ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya  ina mai girmama sha'anin sa kuma na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne   tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi da amincin tabbatacce mai yawa da aminci mai kari .

YA KU  MUSULMAI:-
Allah ya yalwata kasar saudiya da ni'imomi masu yawa wanda ya fi ko wanne a cikin su shi ne ni'imar musulunci  da yaduwar shi  da kuma raya masallatai biyu masu alfarma da musu hidima da girmama wanda suka fiskanto su da bugawa da yada alkur'ani mai girma  a cikin sararin duniya  da bawa musulmai kulawa da musu hidima   a al'amuran su da yin hukunci da shari'ar Allah a kasar sa  kuma  ya sanya ta alkibla na musulmai , kuma zuciyar duniyar musulunci tare da abin da ya ni'imta a gare su na daga aminci da zaman lafiya da yalwa na rayu da jin dadin shi da kuma hadin kan jama'anta   da dunkulewan su  dukkan hakan da wanin sa  a falalan Allah ne  shi kadan shi  da kuma datarwa da Allah ya yiwa jagororin  ta   suka sanya abu na farko mafi muhimmanci  tun daga kafa wannan daula na musulunci tabbatar da kadaita Allah da bin Annabin sa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da hidima wa musulmai da yada ilimi na shari'a   wanda aka ciro shi  daga  littafi da sunna  da kuma bin sawun magabata na wannan al'uma  kuma duk yanda abu ya caccanza  da sautukan  wadan da suka saba mana  ba abinda zai karawa wannan kasa face  riko da musulunci da haduwa a kan kalma  tsakanin mabiya da jagororin su.
 Ya wajaba ga musulmai su kau da kai daga  wasu   jefe –jefe   da   jita-jitan masu  tada zaune tsaye  da rashin sauraro zuwa gare su   da shagaltuwa da abin da zai amfanar  . 
 Sannan ku sani lallai Allah na umartan ku da salati da aminci ga Annabin shi sai ya ce  a cikin littafin shi mafi hikima da  saukar :- (Lallai Allah da mala'iku suna salati ga Annabi  ya ku wadan da suka yi imani ku yi salati a gare shi  da aminci tabbatacce )
       



ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق