السبت، 17 نوفمبر 2018

HARSHE DA ILLOLIN SHI


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA  A GARE SHI 8-3-1440 NA SHAIK ABDALLAH BIN ABDURRAHMAN ALBU'AIJAN
HUDUBAR FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya halicci mutum  ya fifita shi, ya bashi hankali ,  wanda da shi ne ake gane abu  sannan kuma shari'a take hawa kan mutum,  ya horar da shi kuma ya bashi kyautan harshe wanda da shi ne ake iya magana   da bayani  ya kuma sanar da shi  ,  tsarki ya tabbata  ga wanda   ya yi shi kuma ya daidai ta shi      kuma albarkar Allah ta bayyana,Mafi kyawun masu halittawa .
   Na  shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya   , kuma na shaida  Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne    kuma ya turo shi da shiriya da addini na gaskiya  yana mai shaida kuma da albishir da gargadi   sai ya zo da gaskiya  ya kuma yi gaskiya tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ,  da iyalan sa da sahabban sa da aminci tabbatacce mai yawa  
BAYAN HAKA:
      To  lallai  mafi alherin zance shi ne maganan Allah   mafi alherin shiriya  kuma  shi ne shiryarwar Muhammadu dan Abdullahi  ,  kuma dukkan bidi'a bata ne kuma dukkan bata yana wuta .
      YA KU BAYIN ALLAH !
  Ina muku wasiyya da ni kai na da jin tsoron Allah ,  shi ne wasiyyar Allah ga mutanen farko da na karshe   (Hakika mun yi wasiyya ga wadan da aka bawa littafi gabannin ku da ku kan ku da ku ji tsoron Allah )
   YA JAMA'AR MUSULMI:
          Suka irin na harshe  yana shiga da zurfi  kuma yana da tasiri matsananci  da ke tsayawa a zuciya .   
Suka irin na mashi yana iya warkewa  *** Amma suka irin na  harshe bai warkewa
    Harshe   na'ura ne na bayyana magana da fasaha kuma   shi  ke  fassara  abin da ke zuciya  sifan shi dan karami ne amma  sukan shi na da girma  biyayya gare shi  abu ne mai girma  da laifin shi abu ne mai girma da shi ne kafurci ke bayyana  ko imani  wanda kuma su dinnan su ne makura na da'a da sabo ,  yana da fage mai fadi a alheri , kamar yanda  yake da    da makamancin shi wurin girma na sharri,  da shi ne  ake yada tuhume-tuhume    ake kuma kazafi  ga mata katangaggu gafalallu muminai , da shi ne kuma fitintinu da rikece-rikece ke aukuwa  kuma da shi ne boyayyun abubuwa ke bayyana  , kuma  da shi ne ake halatta abubuwa dake masu alfarma ,  kuma ake shuka fitintinu da gaba da bakin ciki da hasara cikin zukata  , da shi ne kuma ake zagi kuma ake yaface  ake annamimanci kuma da zunde, da yada jita-jita  kuma da tsinuwa da cin nama da  kazafi da alfasha da kuma maganar banza, da batsa da suka , bai gajiya da motsi , kuma bai raguwa sabo da magana, amma kuma dukkan haka abu ne kiyayye , adananne, kuma zaa yi wa mutum hisabi game da su ranan da zaa yi narkon azaba. (Baya lafazi da wata magana face a  like da shi akwai mai tsaro halartacce )  (Wata rana Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya rike harshen sa sai ya ce :- ya Mu'az ka kiyayi wannan!  sai Mu'az ya ce : wai shin ana kama mu da abin da muke furtawa?  sai Annabi ya ce : Mahaifiyar ka ta yi wabin ka   ya kai Mu'az  shin akwai abin da yake kifar da mutane cikin wuta a bisa fuskokin su  ko hancin su  face abin da harsunan su ke girbe musu .
   (An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi  kan cewa  ya ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa :- '' Lallai bawa yana fadin magana ta kalma  da zata shigar da shi cikin wuta  ta kai shi nesa da ya fi nisan tsakanin  gabaci da yammaci)
         
(An karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- wani yaro ya yi shahada a cikin mu ranar Uhud sai a ka samu  wani dutse a daure a cikin shi sabo da  yunwa  sai mahaifiyarsa ta share masa turbaya a fiskan shi ta kuma ce: ''  Ina maka murna ya dana da Aljanna  sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce wa ya sanar da ke  watakila ko yana yin zance cikin abin da bai shafe shi ba '')     
 Wata rana Ibnu Mas'ud ya hau kan dutsen safa sai ya rike harshensa sai  yace : (ya harshe ka fadi alheri za ka samu riba, ka kame daga fadan sharri zaka kubuta,tun kafin ka yi nadama.sannan sai ya ce : (na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa : Mafi yawan kusakuran dan'adam  na samuwa ne daga harshensa).
Ya ku bayin Allah!
Ya ishi mutum laifi ya rena dan'uwansa musulmi, dukkan musulmi haramun ne jininsa da dukiyansa da mutuncinsa gurin  musulmi ,
Lallai   ambaton musulmi ga dan uwan shi da wani abu da baya so,  a yana halarce   zagi ne da suka  a baya nan kuma  in ya yi sukan a jikinsa ne ko addininsa  ko duniyarsa  ko cikin halittan sa ko dabi'un sa ko  dukiyarsa ko dansa  ko matarsa  ko tufafinsa  ko harkarsa  duka daya ne sawa'un da lafazi ya yi ko nuni  ko da wata alama ko da rubutu  ko hikaya,   to duka wannan in har yana tattare da shi giba  ne,  idan kuma babu tare da shi giba ne da zalunci da karya da kage .
  YA KU BAYIN ALLAH:
Cin kudin ruwa (RIBA) yana da kofofi saba'in da   biyu mafi karancin sa shi ne   mutum ya yi zina da mahaifiyar sa  dirhami  na riba  ya fi zina sau talatin da shida  lallai  kuma riban da ya fi ko wanne     lallai  kuma riban da ya fi ko wanne shi ne ka  kutsa cikin cin mutuncin dan uwanka musulmi ba tare da hakki  ba  .
     YA KU JAMA'AR MUSULMAI:
Lallai mafi girman laifuka na harshe da musibarsa  da ragar sa  da tarkon sa ;  shi ne yada jita-jita wanda  suke na karya    da  tsegumi  dabab-daban,   da saka karerayi na banza  da cire yarda tsakanin musulmai har a samu mummunan zato tsakanin su, da rashin jituwa  zai bata 'yan uwantaka dake tsakanin su  sai su rarrabu,  hadin kansu ya wargaje su rasa aminci .
 Sau nawa ne jita-jita   take fadawa akan wadan da suka barranta ta sa su cikin  damuwa  sau da yawa tana rusa manya   sau da yawa kuma tana katse  zumunci ,  sau dayawa tana haifar da manyan laifuka   , sau dayawa  takan rabe alaka da abokantaka  kuma sau da yawa tana rusa  al'uma    sau da yawa ta rusa iyalai ta raba tsakanin masoya  sau da yawa ta sa hasaran dukiya  kuma ta sarayar da  lokaci ,  kuma sau dayawa ta bakanta zukata   sau dayawa ta bakanta zuciya kuma ta kuntata  rayi  ta  haifar da hasara,  sau da yawa  jita-jita  ta wargaza tafiyar  wasu mutane.
     Hakika Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Ya ku wadan da suka yi imani   ku  nisanci mafiya yawan  zato   lallai sashin zato laifi ne )
(Ya ku wadan da suka yi imani idan fasiki ya zo muku da wani babban labari  to ku nemi bayani domin kada ku cuci wadansu mutane a cikin jahilci,  sabo da haka  ku wayi gari akan abin da kuka aikata kuna masu nadama )    
An karbo daga Abdullahi dan Umar ya ce na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gage shi  yana cewa  (Duk mutumin da ya ambaci wani mumini da abin da babu shi tare  da  shi  , Allah zai bashi masauki na  RIDGATUL KHABAL  shi ne wuri mai matsanancin  tabo da diwa na  'yan wuta )
(An karbo daga sahal  dan Mu'az daga mahaifin shi  Allah ya kara yarda a gare su  ya ce:  Daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce duk mutumin da ya jefi wani musulmi  da wani abu don ya bata shi   Allah zai tsare shi akan gadan jahannama ` har sai ya fita daga abin da ya ambata ).
     YA KU JAMA'AR MUSULMAI:
Lallai Allah ya haramta taba mutuncin Musulmai kamar yadda ya haramta  jininsu da dukiyoyinsu  sai dai ma ya shar'anta bada kariya  ga mutuncin su  ta hanyar amfani   da rai  da dukiya  lallai   taba mutuncin musulmi  ta hanyar  jita –jita  da yada   ta a sarari  da kuma  da tallata ta  ta hanyar amfani  da jefa  shakku da  zato  da kirkira   da karya da kage da   fadin zur da  da izgilanci  da yada guba da fitintinu  ta hanyoyin sadarwa  da kuma kafafen  sadarwa   dukkan hakan na daga cikin cin mutunci wadda aka hana   kuma yana cikin manyan laifuka masu halakarwa  da fitintinu masu batarwa  ya wajaba ga ko wani musulmi ya kiyayi irin wadan nan.
 An karbo daga Abu Darda Allah ya kara yarda a gare shi ya jingina shi zuwa ga manzon Allah ya ce :- (Duk wanda ya yada wata kalma mara kyau game da musulmi  don ya bata shi da ita a duniya  to ya zama hakki  a kan Allah da ya narkar da shi  a wuta har sai ya kawo  abunda ke zartar da ita ).
Ku saurara; duk wanda ya yada alfasha  kamar wanda ya fare ta ne kuma yana da alhakinta da alhakin wanda ya nakalto  ta daga gare shi har  zuwa karshenta.
  (An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare  shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:  ya ishi mutum  karya  da ya bada  labarin duk abin da ya ji  muslim ne ya  rawaito.
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan abin jefewa
(A lokacin  da kuke marabarsa  da harsunan ku  kuma kuna cewa  da bakunan ku  abin da ba ku da wani ilimi game da shi ,  kuma kuna zaton sa mai sauki ,  alhali kuwa,  shi a wurin Allah  , babba ne )

HUDUBA TA BIYU
Dukkan  yabo  da godiya sun tabbata ga ga Allah  wanda  ya  kare jini da mutunci da dukiya   ta hanyar addininsa  kuma ya yi alkawarin narkon azaba ga  wanda ya  ketare iyaka akan su   da ayyuka ne ko da fadi,  ya sanya muminai  'yan uwan juna ya shuka soyayya da kauna a tsakanin su  .
  YA JAMA'AR MUSULMAI :
 Lallai keta alfarma da kuma bibiyan  al'aura yana daga cikin manyan  musibu da kuma jarabawa  da kuma matsanancin fitintinu  da mafi girman abin ki  daga cikin abin da yake haifar da shi  shi ne raunin imani a zukuta.
  An karbo daga Abi Barza Al-aslami   Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-  ( Ya tawagar wadan da suka yi imani da harshe alhali imanin bai shiga cikin zuciyarsu ba!   kada ku ci naman musulmai , kada ku bibiyi al'auransu   ,  domin duk wanda ke bibiyan al'auran su Allah ma zai bibiyi al'auransa  , wanda Allah ya bibiyi  al'auransa to zai kunyata shi har a cikin gidansa ) Ahmad ne ya rawaito.
          To ku kare mutuncinku ku kiyaye harsunanku.
Ya ku bayin Allah!
Lalle musulmi na da alfarma mai girma wacce shari'a ta bata kariya kuma ta kiyaye ta,   kuma ya yi narkon azaba ga wanda ya mata ta'addanci, baya dacewa ga musulmi da ya ci zarafin ta  ko kuma ya yi kokari wurin   keta alfarmarta .
  Abdullahi dan Umar ya dubi kaba wata ran sai ya ce :- '' Abun mamaki da irin girman ki abin mamaki da irin girman  alhurmar ki amma kuma mumini  alfarmar shi ya fi girma a wurin Allah  akan ki   ''
 An karbo daga abi bakarata Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya  yi mana khuduba ranar   sallan laiha sai ya ce :  ko kun san wani yini ne yau? sai muka ce Allah da Manzon sa ne suka  fi sani. sai ya yi shuru , har muka zaci cewa zai sanja mishi suna ne.  sai ya ce a she wannan ba ranar babban salla ba ne ? sai muka ce ,  e, haka ne , sai ya ce wani wata ne wannan?, sai muka ce Allah da Manzonsa ne suka fi sani  , sai ya yi shuru har muka zaci zai sanja mishi suna ne sai ya ce: -  ashe ba zulhijja ba ne ? ,  sai muka ce: e, haka ne,  sai ya ce wani gari ne wannan? Sai muka ce: Allah da  Manzon sa ne suka fi sani.  sai ya yi shuru har muka zaci zai sanja mishi suna ne sai ya ce: ase ba gari mai alfarma ba ne?,  sai muka ce e, haka ne.    sai ya ce lallai jinannakin ku da dukiyoyin ku da mutuncin ku  haramun ne a gare ku kamar alfarmar wannan wunin na ku  a  cikin wannan wata na ku a wannan garin  na ku har zuwa ranar da  za ku hadu da Ubangijin ku , ku saurara shin na isar da sako?  sai suka ce e, sai ya ce: ya Allah ka shaida  . To wanda yake halarce ya isar ga wanda baya nan  sau da yawa wanda ake isarwa  sai ya fi kiyayewa akan wanda  ya ji.  kar ku koma kafurai a bayana   sashin ku na dukan wuyan sashi ) Buhari ne ya rawaito

BAYIN ALLAH :
Lallai nisantar abubuwan da aka haramta kuma aka yi hani a kai ana fifita shi da ayyukan da'a na kwarai da kyawawa da ayyuka na gari , lallai wanda aka yiwa wasoso shi ne wanda zai yi kokari yayi aiki kuma ya tattara   sai dai shi din nan wawa ne, yana almubazzarantar da abin da ya tattaro.
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi  ya ce: Manzon Allah tsira da  amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : -ko kun san wane ne muflis  sai suka ce  '' Muflis a cikin mu shi ne wanda ba yi da dirhami ko  kuma wani abu na jin dadi  sai ya ce : - (; Lallai muflis  a cikin al'uma ta shi ne  wanda zai zo  ranar alkiyama da salla da azumi da zakka  zai zo ya zagi wancan , ya yi kazafi ga wancan   ya ci dukiyan wancan , ya zubar da jinin wancan  ya duki wancan  , sai a bawa wannan daga kyawawansa shi ma wancan a bashi daga kyawawan sa  to idan kyawawan sa sun kare  kafin a kare hukuncin abin da ke kanshi  nasu,  sai a dauko daga kusakuran su  a  dora mishi sannan sai a jefa shi a wuta )    
 YA KU JAMA'AR MUSULMAI :
Lallai Gamammiyar daular larabawa ta kasar saudiya  gari mai masallatai biyu masu alfarma kuma masaukar wahayi , kuma alkiblar musulmai ,  kuma abin son zukatan su  Allah ya zabe ta   don ta zama wurin da addinin shi zai taso   kuma mimbarin  da'awa zuwa gare shi  ,  kuma makoma ne na masu kadaita Allah , hasken musulunci  ya  yadu daga nan ginshiki na  adalci ya kafu  da aminci da ilimi da imani  ta rungumi  duk  wanda ya zo gare ta cikin musulmai  irin rungumar da uwa take yiwa dan ta tare da tausayi  to Allah ya sakawa jagororin ta da sakayya mafi alheri .
 Ku saurara lallai  tsegumi  da yada  jita-jita da abubuwan takaici, wanda mahassada ke rurawa, masu kulli a zuci game da wannan kasa  mai albarka su yayata shi,lalle ba wani abu ba ne sai fitintinu da matsanancin yaki da makiya addininnmu suke kunnawa, masu dakon wani mummunan abu ya faru ga al'umarmu, to muna kankan da kai zuwa ga Allah muke neman tunkude sharrinsu da shi ka mana maganinsu,
Ya Allah ka kiyaye mana wannan gari da kiyayewanka, ka bata kulawa da kulawarka,
Ya Allah ka sanya ta cikin aminci da natsuwa, da sauran garuruwan musulmai, ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai.   

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق