HUDUBAR MASALLACIN
ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA
A GARE SHI 8-3-1440 NA SHAIK ABDALLAH BIN ABDURRAHMAN ALBU'AIJAN
HUDUBAR FARKO
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah wanda ya halicci mutum
ya fifita shi, ya bashi hankali ,
wanda da shi ne ake gane abu
sannan kuma shari'a take hawa kan mutum,
ya horar da shi kuma ya bashi kyautan harshe wanda da shi ne ake iya
magana da bayani ya kuma sanar da shi ,
tsarki ya tabbata ga wanda ya yi shi kuma ya daidai ta shi kuma
albarkar Allah ta bayyana,Mafi kyawun masu halittawa .
Na
shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da
abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa
ne kuma ya turo shi da shiriya da
addini na gaskiya yana mai shaida kuma
da albishir da gargadi sai ya zo da
gaskiya ya kuma yi gaskiya tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi
, da iyalan sa da sahabban sa da
aminci tabbatacce mai yawa
BAYAN HAKA:
To lallai mafi alherin zance shi ne maganan Allah mafi alherin shiriya kuma
shi ne shiryarwar Muhammadu dan Abdullahi , kuma
dukkan bidi'a bata ne kuma dukkan bata yana wuta .
YA KU BAYIN ALLAH !
Ina muku wasiyya da ni kai na da jin tsoron
Allah , shi ne wasiyyar Allah ga mutanen
farko da na karshe (Hakika mun yi
wasiyya ga wadan da aka bawa littafi gabannin ku da ku kan ku da ku ji tsoron
Allah )
YA JAMA'AR MUSULMI:
Suka irin na harshe yana shiga da zurfi kuma yana da tasiri matsananci da ke tsayawa a zuciya .
Suka
irin na mashi yana iya warkewa *** Amma
suka irin na harshe bai warkewa
Harshe
na'ura ne na bayyana magana da
fasaha kuma shi ke
fassara abin da ke zuciya sifan shi dan karami ne amma sukan shi na da girma biyayya gare shi abu ne mai girma da laifin shi abu ne mai girma da shi ne
kafurci ke bayyana ko imani wanda kuma su dinnan su ne makura na da'a da
sabo , yana da fage mai fadi a alheri ,
kamar yanda yake da da makamancin shi wurin girma na sharri, da shi ne
ake yada tuhume-tuhume ake kuma
kazafi ga mata katangaggu gafalallu
muminai , da shi ne kuma fitintinu da rikece-rikece ke aukuwa kuma da shi ne boyayyun abubuwa ke
bayyana , kuma da shi ne ake halatta abubuwa dake masu
alfarma , kuma ake shuka fitintinu da
gaba da bakin ciki da hasara cikin zukata
, da shi ne kuma ake zagi kuma ake yaface ake annamimanci kuma da zunde, da yada
jita-jita kuma da tsinuwa da cin nama
da kazafi da alfasha da kuma maganar
banza, da batsa da suka , bai gajiya da motsi , kuma bai raguwa sabo da magana,
amma kuma dukkan haka abu ne kiyayye , adananne, kuma zaa yi wa mutum hisabi
game da su ranan da zaa yi narkon azaba. (Baya lafazi da wata magana face
a like da shi akwai mai tsaro halartacce
) (Wata rana Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya rike harshen sa sai ya ce :- ya Mu'az ka
kiyayi wannan! sai Mu'az ya ce : wai shin
ana kama mu da abin da muke furtawa? sai
Annabi ya ce : Mahaifiyar ka ta yi wabin ka
ya kai Mu'az shin akwai abin da
yake kifar da mutane cikin wuta a bisa fuskokin su ko hancin su
face abin da harsunan su ke girbe musu .
(An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara
yarda a gare shi kan cewa ya ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi yana cewa :- '' Lallai bawa yana fadin magana ta kalma da zata shigar da shi cikin wuta ta kai shi nesa da ya fi nisan tsakanin gabaci da yammaci)
(An
karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- wani yaro ya yi shahada
a cikin mu ranar Uhud sai a ka samu wani
dutse a daure a cikin shi sabo da
yunwa sai mahaifiyarsa ta share
masa turbaya a fiskan shi ta kuma ce: ''
Ina maka murna ya dana da Aljanna
sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce wa
ya sanar da ke watakila ko yana yin
zance cikin abin da bai shafe shi ba '')
Wata rana Ibnu Mas'ud ya hau kan dutsen safa
sai ya rike harshensa sai yace : (ya
harshe ka fadi alheri za ka samu riba, ka kame daga fadan sharri zaka kubuta,tun
kafin ka yi nadama.sannan sai ya ce : (na ji Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa : Mafi yawan kusakuran dan'adam na samuwa ne daga harshensa).
Ya ku bayin Allah!
Ya ishi
mutum laifi ya rena dan'uwansa musulmi, dukkan musulmi haramun ne jininsa da
dukiyansa da mutuncinsa gurin musulmi ,
Lallai ambaton musulmi ga dan uwan shi da wani abu
da baya so, a yana halarce zagi ne da suka a baya nan kuma in ya yi sukan a jikinsa ne ko addininsa ko duniyarsa
ko cikin halittan sa ko dabi'un sa ko
dukiyarsa ko dansa ko matarsa ko tufafinsa
ko harkarsa duka daya ne sawa'un
da lafazi ya yi ko nuni ko da wata alama
ko da rubutu ko hikaya, to duka wannan in har yana tattare da shi
giba ne,
idan kuma babu tare da shi giba ne da zalunci da karya da kage .
YA
KU BAYIN ALLAH:
Cin kudin ruwa (RIBA)
yana da kofofi saba'in da biyu mafi karancin sa shi ne mutum ya yi zina da mahaifiyar sa dirhami
na riba ya fi zina sau talatin da
shida lallai kuma riban da ya fi ko wanne lallai kuma riban da ya fi ko wanne shi ne ka kutsa cikin cin mutuncin dan uwanka musulmi
ba tare da hakki ba .
YA KU JAMA'AR MUSULMAI:
Lallai mafi girman
laifuka na harshe da musibarsa da ragar
sa da tarkon sa ; shi ne yada jita-jita wanda suke na karya da
tsegumi dabab-daban, da saka karerayi na banza da cire yarda tsakanin musulmai har a samu
mummunan zato tsakanin su, da rashin jituwa
zai bata 'yan uwantaka dake tsakanin su
sai su rarrabu, hadin kansu ya
wargaje su rasa aminci .
Sau nawa ne jita-jita take fadawa akan wadan da suka barranta ta
sa su cikin damuwa sau da yawa tana rusa manya sau da yawa kuma tana katse zumunci ,
sau dayawa tana haifar da manyan laifuka , sau dayawa
takan rabe alaka da abokantaka
kuma sau da yawa tana rusa al'uma
sau da yawa ta rusa iyalai ta raba
tsakanin masoya sau da yawa ta sa
hasaran dukiya kuma ta sarayar da lokaci ,
kuma sau dayawa ta bakanta zukata
sau dayawa ta bakanta zuciya kuma ta kuntata rayi
ta haifar da hasara, sau da yawa
jita-jita ta wargaza tafiyar wasu mutane.
Hakika Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Ya ku wadan da suka yi imani ku
nisanci mafiya yawan zato lallai sashin zato laifi ne )
(Ya ku
wadan da suka yi imani idan fasiki ya zo muku da wani babban labari to ku nemi bayani domin kada ku cuci wadansu
mutane a cikin jahilci, sabo da
haka ku wayi gari akan abin da kuka
aikata kuna masu nadama )
An karbo
daga Abdullahi dan Umar ya ce na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gage shi yana cewa (Duk mutumin da ya ambaci wani mumini da abin da babu
shi tare da shi ,
Allah zai bashi masauki na RIDGATUL KHABAL shi ne wuri mai matsanancin tabo da diwa na 'yan wuta )
(An
karbo daga sahal dan Mu'az daga mahaifin
shi Allah ya kara yarda a gare su ya ce:
Daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce duk
mutumin da ya jefi wani musulmi da wani
abu don ya bata shi Allah zai tsare shi
akan gadan jahannama ` har sai ya fita daga abin da ya ambata ).
YA KU JAMA'AR MUSULMAI:
Lallai
Allah ya haramta taba mutuncin Musulmai kamar yadda ya haramta jininsu da dukiyoyinsu sai dai ma ya shar'anta bada kariya ga mutuncin su ta hanyar amfani da rai
da dukiya lallai taba mutuncin
musulmi ta hanyar jita –jita da yada ta a sarari
da kuma da tallata ta ta hanyar amfani da jefa
shakku da zato da kirkira
da karya da kage da fadin zur da da izgilanci
da yada guba da fitintinu ta
hanyoyin sadarwa da kuma kafafen sadarwa
dukkan hakan na daga cikin cin mutunci wadda aka hana kuma yana cikin manyan laifuka masu
halakarwa da fitintinu masu batarwa ya wajaba ga ko wani musulmi ya kiyayi irin
wadan nan.
An karbo daga Abu Darda Allah ya kara yarda a
gare shi ya jingina shi zuwa ga manzon Allah ya ce :- (Duk wanda ya yada
wata kalma mara kyau game da musulmi don
ya bata shi da ita a duniya to ya zama
hakki a kan Allah da ya narkar da
shi a wuta har sai ya kawo abunda ke zartar da ita ).
Ku saurara;
duk wanda ya yada alfasha kamar wanda ya
fare ta ne kuma yana da alhakinta da alhakin wanda ya nakalto ta daga gare shi har zuwa karshenta.
(An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara
yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ya ishi mutum
karya da ya bada labarin duk abin da ya ji muslim ne ya
rawaito.
Ina
neman tsarin Allah daga sharrin shaidan abin jefewa
(A
lokacin da kuke marabarsa da harsunan ku kuma kuna cewa da bakunan ku
abin da ba ku da wani ilimi game da shi , kuma kuna zaton sa mai sauki , alhali kuwa,
shi a wurin Allah , babba ne )
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da
godiya sun tabbata ga ga Allah
wanda ya kare jini da mutunci da dukiya ta hanyar addininsa kuma ya yi alkawarin narkon azaba ga wanda ya
ketare iyaka akan su da ayyuka
ne ko da fadi, ya sanya muminai 'yan uwan juna ya shuka soyayya da kauna a
tsakanin su .
YA
JAMA'AR MUSULMAI :
Lallai keta alfarma da kuma bibiyan al'aura yana daga cikin manyan musibu da kuma jarabawa da kuma matsanancin fitintinu da mafi girman abin ki daga cikin abin da yake haifar da shi shi ne raunin imani a zukuta.
An karbo daga Abi Barza Al-aslami Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- ( Ya tawagar wadan da suka yi imani da harshe
alhali imanin bai shiga cikin zuciyarsu ba!
kada ku ci naman musulmai , kada ku bibiyi al'auransu ,
domin duk wanda ke bibiyan al'auran su Allah ma zai bibiyi al'auransa , wanda Allah ya bibiyi al'auransa to zai kunyata shi har a cikin
gidansa ) Ahmad ne ya rawaito.
To ku kare mutuncinku ku kiyaye harsunanku.
Ya ku bayin Allah!
Lalle musulmi na da
alfarma mai girma wacce shari'a ta bata kariya kuma ta kiyaye ta, kuma ya
yi narkon azaba ga wanda ya mata ta'addanci, baya dacewa ga musulmi da ya ci
zarafin ta ko kuma ya yi kokari
wurin keta alfarmarta .
Abdullahi dan
Umar ya dubi kaba wata ran sai ya ce :- '' Abun mamaki da irin girman ki abin
mamaki da irin girman alhurmar ki amma
kuma mumini alfarmar shi ya fi girma a
wurin Allah akan ki ''
An karbo daga abi bakarata Allah ya kara
yarda a gare shi ya ce :- Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya yi mana khuduba ranar sallan
laiha sai ya ce : ko kun san wani yini
ne yau? sai muka ce Allah da Manzon sa ne suka fi sani. sai ya yi shuru , har muka zaci cewa
zai sanja mishi suna ne. sai ya ce a she
wannan ba ranar babban salla ba ne ? sai muka ce , e, haka ne , sai ya ce wani wata ne wannan?,
sai muka ce Allah da Manzonsa ne suka fi sani
, sai ya yi shuru har muka zaci zai sanja mishi suna ne sai ya ce:
- ashe ba zulhijja ba ne ? , sai muka ce: e, haka ne, sai ya ce wani gari ne wannan? Sai muka ce:
Allah da Manzon sa ne suka fi sani. sai ya yi shuru har muka zaci zai sanja mishi
suna ne sai ya ce: ase ba gari mai alfarma ba ne?, sai muka ce e, haka ne. sai ya ce lallai jinannakin ku da dukiyoyin ku
da mutuncin ku haramun ne a gare ku
kamar alfarmar wannan wunin na ku a cikin wannan wata na ku a wannan garin na ku har zuwa ranar da za ku hadu da Ubangijin ku , ku saurara shin
na isar da sako? sai suka ce e, sai ya
ce: ya Allah ka shaida . To wanda yake
halarce ya isar ga wanda baya nan sau da
yawa wanda ake isarwa sai ya fi kiyayewa
akan wanda ya ji. kar ku koma kafurai a bayana sashin ku na dukan wuyan sashi ) Buhari ne
ya rawaito
BAYIN
ALLAH :
Lallai
nisantar abubuwan da aka haramta kuma aka yi hani a kai ana fifita shi da ayyukan
da'a na kwarai da kyawawa da ayyuka na gari , lallai wanda aka yiwa wasoso shi
ne wanda zai yi kokari yayi aiki kuma ya tattara sai dai shi din nan wawa ne, yana almubazzarantar
da abin da ya tattaro.
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara
yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce : -ko kun san wane ne muflis
sai suka ce '' Muflis a cikin mu
shi ne wanda ba yi da dirhami ko kuma
wani abu na jin dadi sai ya ce : - (;
Lallai muflis a cikin al'uma ta shi
ne wanda zai zo ranar alkiyama da salla da azumi da
zakka zai zo ya zagi wancan , ya yi
kazafi ga wancan ya ci dukiyan wancan , ya zubar da jinin
wancan ya duki wancan , sai a bawa wannan daga kyawawansa shi ma
wancan a bashi daga kyawawan sa to idan
kyawawan sa sun kare kafin a kare
hukuncin abin da ke kanshi nasu, sai a dauko daga kusakuran su a dora
mishi sannan sai a jefa shi a wuta )
YA KU JAMA'AR MUSULMAI :
Lallai Gamammiyar
daular larabawa ta kasar saudiya gari
mai masallatai biyu masu alfarma kuma masaukar wahayi , kuma alkiblar musulmai
, kuma abin son zukatan su Allah ya zabe ta don ta zama wurin da addinin shi zai
taso kuma mimbarin da'awa zuwa gare shi , kuma
makoma ne na masu kadaita Allah , hasken musulunci ya yadu
daga nan ginshiki na adalci ya kafu da aminci da ilimi da imani ta rungumi duk wanda ya zo gare ta cikin musulmai irin rungumar da uwa take yiwa dan ta tare da
tausayi to Allah ya sakawa jagororin ta
da sakayya mafi alheri .
Ku saurara lallai tsegumi
da yada jita-jita da abubuwan
takaici, wanda mahassada ke rurawa, masu kulli a zuci game da wannan kasa mai albarka su yayata shi,lalle ba wani abu ba
ne sai fitintinu da matsanancin yaki da makiya addininnmu suke kunnawa, masu
dakon wani mummunan abu ya faru ga al'umarmu, to muna kankan da kai zuwa ga
Allah muke neman tunkude sharrinsu da shi ka mana maganinsu,
Ya Allah ka
kiyaye mana wannan gari da kiyayewanka, ka bata kulawa da kulawarka,
Ya Allah ka
sanya ta cikin aminci da natsuwa, da sauran garuruwan musulmai, ya Ubangijin
talikai.
Ya Allah ka
daukaka musulunci da musulmai.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق