الجمعة، 19 أكتوبر 2018

FALALAR AYATUL KURSI


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH ABDUL BARI ASSUBAITI 10-2-1440AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah,tsayayye Rayayye, ina gode mishi tsarki ya tabbata a gare shi,bacci ba ya daukan shi ko gyangyadi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya,Madaukaki Mai girma, na shaida Annabinmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne,ya nusar da mu zuwa ga tafarkin Allah mikakke, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da iyalan shi,da sahabbansa masu tafiya akan tafarki mikakke, bayan haka,
Ina muku wasiya da ni kai na da ku ji tsoron Allah ,Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku wadan da ku ka yi imani ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa, kar ku mutu face kuna musulmai)
(Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ya Abul Munzir ! ko kasan wace aya ce mafi girma ka ke da ita a cikin littafin Allah? Yace sai na ce :Allah da Manzonsa ne suka fi sani, sai yace: ya Abul Munzir ! ko kasan wace aya ce mafi girma ka ke da ita a cikin littafin Allah? Yace sai na ce : (Allahu La'ilaha illa huwal Hayyul Kayyum) sai ya buga kirji na yace " Madalla da ilimi irin naka ya Abul Munzir",   
Ayatul kursi ta zama aya mafi girma ne sabo da ta tattaro tushen sunayen Allah da sifofinsa, ta bayyana kudura na Allah Mai girma.
 (ALLAHU LA'ILAHA ILLAHUWA) :- Allah ba abin bautawa da gaskiya sai shi ) ,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Imani  kashi saba'in da dori ne ko sittin da dori  mafi girmanta shi ne fadin LA'ILAHA'ILLALLAH ;  )    shi ne mai gaskiya tsarki ya tabbata a gare shi , fadin sa kuma shi ne gaskiya alkawarin shi ma gaskiya ne  addinin shi ma  shi ne na gaskiya , kuma littafin shi ma gaskiya  kuma duk abin da ya bada labari gaskiya , kuma duk abin da ya yi umarni da shi gaskiya ne  a zatin sa da sifofinsa  mai cikakken sifofi , shi ne wanda bai gushe ba kuma ba zai gushe ba ya siffantu  da daukaka da kyau da kamala   haka nan kuma  bai gushe ba kuma ba zai gushe ba  wanda aka san shi da ihsani .
        ( ALHAYYUL –KAYYUM) :-Rayayye tsayayye  shi dinnan shi ne rayayye wanda baya mutuwa ko ya halaka ; yana da rayuwa na dindindin da wanzuwa  wanda  bayi da farko ko karshe   da za a iya iyakance shi  kuma (ALKAYYAUM)   ya kunshi  kamalar wadatuwar sa da kamalar kudurar sa  domin shi tsayyayye ne a kan kansa  sannan kuma  yake  dawainiya da wasu  ,  wanin sa ba zai iya tsayuwa ba sai da tsayuwar sa  wadan nan sunayen biyu sai suka kintsu  wajen tabbatar da kamalar sa  to, sai ya kasance shi ne abin neman agaji  da wadannan sunaye biyun  kuma ana neman agaji da dukkan suna daga cikin sunayen Ubangiji  madaukaki da kuma dukkan siffa daga cikin siffofin shi  , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance maiyana yawan adu'a da wadannan sunaye biyun ,   idan wani abin bakin ciki ya same shi sai ya ce :-  (YA HAYYU-YA KAYYUM  BI RAHMATIKA ASTAGIS)   Rayayye tsayayye  da rahamarka nake neman agaji . Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce  duk wanda ya ce Astagfirulllahal lazi la'ilaha illahuwal  hayyul kayyum wa atubu ilaik)    ina neman gafaran Allah wanda ba abin bautawa da  gaskiya sai shi rayyayye tsayayye  kuma ina tuba zuwa gare shi ,  to,   za a gafarta mi shi zunuban shi ko da ya gudu daga fagen yaki ne .
    Idan Musulmi ya lura  ya san cewa Ubangijin shi dinnan rayayye ne tsayayye  ( sai  zuciyan shi ya samu natsuwa  da kwanciyan hankali  ;    hakika an  isar mishi  daga bakin cikin duk wani shiri , kuma an bashi kariya daga dukkan wasu sharrace-sharrace da laifuka .
  ( LATA'AKUZUHU –SINATUN WALA NAUM)    Gyangyadi ko bacci bai daukan shi  to shi mabuwayi mai daukaka ya tsarkaka daga dukkan wata nakasa  ko gajiyawa ko aibi  irin wanda ke tattare ga bayin sa : -  Yanda duniya  ke gudana cikin tsari  shaida ne akan haka ,  haka nan yanda rayuwa  ke tafiya , da kuma yanda halittu ke rayuwa   ( LATA'AKUZUHU –SINATUN WALA NAUM) Gyangyadi ko bacci bai daukan shi, in ba don haka ba kuwa da wannan duniyan ta rikirkice ,  tafiyar sa ya baci ,   tsarin sa  ya rikirkice ,,(Bai dace ga rana ba ta riski wata  ko kuma dare ya sha gaban yini ) da  kuma ruwan koguna sun rinka ambaliya  da koramai .
      A lokacin da  idanuwa suka yi bacci   taurari     suka bayyana to lallai wasu mutane cikin muminai hakarkarin  su na yin nesa daga makwanci :-  suna ganawa da wanda gyangyadi ko bacci bai kama shi ,  sai ya amsa musu  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce :- (Ubangiji mu  mabuwayi da daukaka na sauka  a dukkan dare  zuwa ga saman duniya  daidai sulusin karshe na dare  sai ya ce :- wa zai roke ni na amsa mishi  kuma wa zai tambaye ni na bashi kuma wa zai nemi gafara ta na gafarta mishi).
      Abin da ke cikin sammai da kassai duka na shi ne  dukkan komai da ke cikin su  yana karkashin mulkin sa ne da kudurar sa  da kuma kaddarawan sa da  falalan sa   da fifikon sa da hukuncin sa  da hikimar sa   falakoki da duniyoyi masu girma : shi ne mahaliccin su,Mai mallakansu abin bautansu,ba abin bauta da gaskiya koma bayanSa  basu da wani Ubangiji koma bayanSa,                     
(wanene zai yi ceto gaba gare shi in ba da izininSa ba)? Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Wanda ya fi samun ceto na ranar Alkiyama shi ne wanda ya ce La'ilaha illallah yana mai ikhlasi daga zuciyarsa).
(yasan abin da ke gaban su da abin da ke bayansu, ba su iyakance wani abu na iliminsa sai abin da ya so) Shi ne wanda tsarki ya tabbata a gare shi Mai ji Mai gani Masani kuma Gwani,   yana ganin  tafiyan bakar tururuwa  akan sandararren dutse  a cikin dare mai duhu  yana ganin abin da ke damfare da jijiyoyin ta da gudun abinci a cikin  gabbanta  .
  ( Yana da mabudan gaibi ba wanda ya san su sai shi   kuma ya san abin da ke tudu da kogi , ba wani abu da ke faduwa na ganyen itaciya face ya sani ko kwaya a cikin duhun kasa  , ko danyen abu ko busasshe face yana  rubuce a littafi bayyananne )  ba abin da ya kewaye ilimin sa Mala'ika ne na kusa  ko wani Annabi manzo , to, ta yaya  masu duba da bokaye da 'yan tsubbu  za su iyakance ilimin shi ,  wadanda  suke da'awan sanin abin da zai faru nan gaba  Allah madaukakin sarki ya ce :-  (Ba wanda ya san gaibi cikin wanda suke sammai da kasa   face Allah ) .
     (wasi'a kursiyyuhussamawati wal ardi )  kujerarSa ta fi fadin sammai da kasa   abin mamaki da girman Allah  abin bauta maigirma madaukaki  kudurarSa ta bayyana tsarki ya tabbata a gare shi  , idan wannan shi ne girman kujerarSa  na cewa ya fi fadin sammai da kasa  duk da girman sunnan  da girman wanda ke cikin su  to ina ga girman mahaliccin su   da kuma wanda ya kirkire su   , to shi ne;   tsarki ya tabbata a gare shi mai yalwa a iliminSa , kuma mai yalwa a wadatarSa  kuma mai yalwa a falalar sa  da ni'imtarwanSa  da kyautarSa  shi ne kuma mai yalwa a karfinSa da kasaitarSa   kuma shi ne mai yalwa a  ikon sa,   kuma mai yalwa a hikimarSa kuma mai yalwa a gafararSa da rahamarSa .
  To Musulmi  yana bautawa Ubangiji wanda kyautarSa na da yalwa a dukkan komai  ,  falalarSa kuma ta ketare dukkan abin da ake fata  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi umarni   game da rokon mai adu'a ga UbangijinSa   ba tare da ya ga  cewa ya yawaita mishi ba sai ya ce , (idan  dayan ku ya zo roko to ya yawaita domin Ubangijinsa fa ya ke roko).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Idan za ku roki Allah to ku roke shi Aljannar firdausi don ita ce tsaka –tsakin Aljanna kuma mafi daukakanta, kuma samanta Al'arshin Mai rahama yake daga nan ne koramun Aljanna ke bubbugowa).
(Kiyaye su ba zai nauyayi Allah ba) Dukkan wani abu da ke duniya na cikin kiyayewa na Allah ne, shine Alhaafiz kuma Alhafeez) shi ne mai kiyaye ayyukan Mukallafi, kuma shi ne mai kiyaye sharri da cuta da bala'i ga wanda ya so.
Na daga ciki aduar da Annabi ya koyar da mu ita (Ya Allah ka kiyaye ni ta gaba na da ta baya na da ta dama na da ta hagu na, kuma da ta sama na, ina neman tsarinka da kasaitarka da a mini kisan gilla ta kasa ta.)
Allah- Mai tsarki -shi kadan shi ne mai kiyaye mutum in ya kiyaye dokokin Allah ya nesaci abin da ya haramta.
Allah Madaukakin sarki ya ce :(To managartan mata masu bi ne  ga mazajensu masu kiyayewa ne a fakuwa, sabo da Allah ya kiyaye su da yiwa maza wasiyya dasu )
Ayatul kursi : ganima ce ga musulmai kuma ni'ima ce daga cikin  ni'imomin Allah  mafi girma, tana daga cikin zikiri mafi karfi na safiya da maraice , wanda da ita ake samun kiyayewa mai karfi na Allah, game da ita ne manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Duk wanda ya karanta ayatul kursi karshen kowace  sallah ba abin da zai hana shi shiga Aljanna sai mutuwa) kuma idan ka karanta yayin da ka zo barci (Bai zai gushe ba kana samun kariyan Allah kuma  ba wani shaidan da zai kusance ka har ka wayi gari)
HUDUBA TA BIYU
Alokacin da magana ta yawaita kuma tashoshin watsa labarai suka cika da naji ance(kila da kala) to wajibi a kan musulmi shi ne ya auna abin da yake gani da abin da ya ke ji da abin da yake fada bisa mizani na sharia da hankali,idan ka samu kalma da zata kashe fitina ta sanya fata na gari ta kawo zaman lafiya ta karfafi kwanciyan hankali, ta kuma binne balbali ta rufe kofar fitina kuma ta rinjayar da maslahar kasa kuma zata taimaka guri dunkulewar Al'uma ta kuma kiyaye wa jagororin Addini hakkokinsu, to wannan ita ce kalma mai kyau.
To idan kalma na kara wutan fitina ne, ta na gusar da zaman lafiya kuma tana tada balbalin bala'i  tana girgiza aminta da jagororin Addini, tana taba mutuncin malamai tana kawo rarrabuwar al'uma kuma tana cin karo da maslahar kasa, to wannan ita ce kazantacciyar kalma, to binne ta tun tana karama ya fi dacewa, kuma kaurace mata shine tafarki mafi daukaka.
Kasar saudiya tana da gini mai karfi wanda ta kafu a zuciya, taba darajarta kaskanci ne, duk wanda ya yi gaba da ita zai fadi ya kaskanta, yin kokarin kawo mata zaman lafiya da amincin masallatayya biyu masu alfarma,kuma tare Masun da aka nufe ta da su, da karfafa dunkulewarta abu ne na wajibi a sharia, kuma abu ne da ya dace duk wani maihankali ya nema, (To su bautawa Ubangijin wannan daki. Wanda ya ciyar da su daga yunwa, ya amintar da su daga tsoro.)  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق