الاثنين، 15 أكتوبر 2018

Tsarkake Rai


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI  25-1-1440 NA SHAIKH  ABDULLAHI BIN ABDURRAHMAN AL-BUAIJAN
HUDUBAR  FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga wanda ya halicci zukata ya daidaita su, ya  kimsa fajircewarsu da takawar su, kuma ya wajabta  rabauta ga tsarkake ta, hasara ta tabbata ga wanda ya  biye wa son ransa.
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunan mu da munanan ayyukanmu, wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, wanda ya batar da shi ba bu mai shiryar da shi,
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, dahir kuma tabbas, kuma na shaida cewa Annabi Muhammad bawan sa ne kuma Manzonsa ne,tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, aminci tabbatacce mai yawa,
Bayan haka, mafi alherin zance shi ne maganar Allah,kuma mafi kyan shiryarwa shi ne koyarwar Annabi Muhammad, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, mafi sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan fararrun abubuwa bidi'a ne, kuma dukkan bidi'a bata ce.
Ya ku bayin Allah !
 ina muku wasiyya da ku ji tsoron Allah, da ku yi wa kan ku hisabi, ( ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah kuma rai ya yi dubi ga abin da ya kaddamar don gobe, ku ji tsoron Allah. Lalle Allah masani ne ga  abin da ku ke aikatawa ,)   ALHASHR 18
Ya taron musulmi !
Lalle Allah ya hallici mutum ya sanar da shi fasaha, ya bashi kyautan hankali da harshe, ya nusar da shi hanyoyi  biyu, ya bayyana mishi hanya ko ya gode ko ya butulce.
Ya jarraba shi da kiyayyar rayi da shaidan ya rubuta masa dace  ko tabewa, ya sanya makomansa wuta ko aljanna.
Ya shar'anta  sharia sabo da shi, ya saukar da littatafai ya turo manzanni  suna masu albishir masu gargadi, cikin mutane akwai wanda ya amsa kira ya tsarkaku, duk wanda ya tsarkaka to don kansa, daga cikin su akwai wanda ya juya baya ya ki ya warware, wanda ya warware to don kansa.
Ya jama'ar musulmi!
 Ku sani rai abokin gaba ne kuma mai umarni da mummuna ne,mai yanke tsakani zukata da Ubangiji  masanin gaibi.
Rai a dabi'arsa mai kwadayi ne ga abin  sha'awe sha'awe  da son jin dadi, mai nawa ne gurin da'a  da ayyukan alheri, rai abin hawan shaidan, ne motarsa ne, kuma wasilarsa ne , kuma kayan alatonsa ne, ta hanyarsu ne ake masa biyayya, kuma hujjarsa ne kuma katangarsa ne. (sai iblis ya fada yayin da aka hukunta Al'amari Lalle Allah ya muku alkawari alkawarin  gaskiya ni kuma na yi muku alkawari na karya na saba muku, kuma ba ni da wani karfi  akan ku, sai dai na kira ku ne ku ka amsa min, kada ku zarge ni ku zargi kawunanku) Ibrahim 22
Rai na yawan umarni da mummuna, mai yawan karkata ga son rai  (Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa gaban UbangijinSa ya hana kansa ga barin   soye-soyen rai , to, lallai aljanna ita ce makoma)  kuma ya ce :-(Ase baka ga wanda ya riki abin bautar sa son ransa ba kuma Allah ya batar da shi bisa ilimi ya toshe jinsa da zuciyan sa  ya sanya rufi a ganin sa  to wa zai shiryar da shi bayan Allah ).
    Rai  matattara ce ta alheri da sharri  Allah madaukakin sarki ya ce :-(  Wanda a ka kiyashe shi kwadayin kan sa wadancannin ka su ne hakikanin marabauta)  al hashir aya 8 ,  kuma ya ce:- ( Lallai rayi  mai yawan umarni ne da mummuna ) .
 Ya ku bayin Allah ;
 Lallai Allah yana yiwa zuciya ilhami na alheri da na sharri , kamar yanda Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Da rayukan dan adam da wanda ya daidaita su . kuma ya kimtsa mata fajircin ta da tsoron Allah ) surah asshams aya 7-8 .
 Kamar yanda Allah ya bawa mutum kyautan ji na zahiri , to, haka kuma ya bashi kyautar rayi  wanda ita ce ta tattari basira na ciki  Allah madaukakin sarki ya ce :-(  Bari !  shi mutum malami ne a bisa kansa  ko da zai zo da hanzare-hanzaren sa )
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni zuwa ga haka  sai ya ce:- (Shi laifi shi ne abin da ya sosa a zuciyan ka ka sani mutane su gane shi )
YA KU BAYIN ALLAH:
Lallai rayi na da bukatan kulawa  da sa ido  da tarbiyantarwa  da kuma tsarkakewa da bibiya    sabo da haka ne annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da husaini dan munzir : - (Ka ce ya  Allah ka  kimtsa mini shiriya ta  ka kare ni daga sharrin rayi na )  ya zo a cikin khudubatul haja (  Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunan mu ).
YA JAMA'AR MUSULMI:
Lallai hanyar kubuta daga sharrin rayi shi ne a tsarkake ta  a bata kulawa  a kuma bibkiye ta ,  kuma hakika Allah ya yi rantsuwa a cikin littafin shi a wurare goma sha daya a jere  bisa ga rabautan  wanda  ya tsarkake  ta  , kuma da hasaran wanda ya turbude ta  sai  ya ce :- (Allah ya yi rantsuwa da rana da hasken walahan ta .    Da wata  idan ya bi ta .     Da wuni idan ya bayyana rana   .     Da dare idan ya lullube ta.    Da sama da  wanda ya gina ta.    da kasa da wanda ya shimfida ta .  Da rayukan dan adam da wanda ya daifdaita ta  kuma ya kintsa mata fajircinta da tsoron Allah.   Hakika wanda ya tsarkake ta ya rabauta.   Hakika wanda ya turbude ta ya tabe.
      Allah ya yiwa muminai baiwa da ni'ima mafi girma sai ya ce : -( Hakika Allah ya yi baiwa  bisa muminai  da ya aiko Manzo a cikin su daga kawunan su  yana karanta ayoyin sa a gare su  yana tsarkake su yana sanar da su alkur'ani da hikima , hakika  su sun kasance gabanin aiko shi  lallai suna cikin bata mabayyani ).
          Allah   ya bada labari kan cewa tsarkake rayi wasila ce  na samun babban rabo da rabauta da aljanna  sai ya ce  : -( Hakika  wanda ya tsarkaka ya rabauta , ya ambaci Ubangijin sa  ya yi  salla ).
      Kuma ya ce :- (Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa gaban UbangijinSa ya hana kansa ga barin   soye-soyen rai , to, lallai aljanna ita ce makoma)  
YA KU BAYIN ALLAH :
 Lallai tsarkake rayuka  bai samuwa  sai da matsayi na  ihsani :-  Kan ka bautawa  Allah kamar kana ganin shi , in kai baka ganin shi to shi yana ganin ka .
 Baya samuwa sai da sabawa son rai  da lazimtar tsoron Allah  kuma bai samuwa sai da sabawa rayi mai umarni da  mummuna , da kyale abubuwa na jin dadin rai da sha'awe-sha'awenta.
To duk mai ciyar da rayi abin da take sha'awa
Tamkar mai ciyar da wuta ne busasshen kirare

To duk wanda  aka datar ya fi karfin zuciyar shi to ya cinma manufa kuma ya habaka rayin sa.    Wanda ya sake mata linzami  sai ta wurga shi  cikin hanyoyi na  halaka.
Duk  wanda ya kauracewa jin dadi zai cinma manufa
Wanda ya dukufa akan ababan jin dadi zai yi nadama
Daukakan rai na cikin tunkude sha'awarta
Cikin  samun abin da yake sha'awa   akwai kaskanci na har abada
Kar ka shagalta sai da abin da zai kawo ma daukaka
Kar ka yarda da halaka ga rai mai tsada
                                                                                                                                                                                                                               
YA KU JAMA'AR MUSULMAI :
Jihadi shi ne kololuwan tozo na musulunci  farilla ne   mafi  girma daga cikin farillai  mafi girman jihadi shi ne jihadin rai  , ku sa mata linzami game da abubuwan jin dadin ta , ku yaye ta daga sha'awe-sha'awen ta , daukakan ta na daga cikin fin karfinta game da sha'awe-sha'awen ta,  kaskancinta da walakantar ta na cikin bata dama game da sha'awanta
 Rayi kamar jariri yake wurin shan nono  in an kyale shi sai ya girma
a kan haka  in an yaye shi sai ya yayu
Ka yaki ranka da shaidan ka saba musu
Idan sun maka  nasiha to ka tuhume su
 Kar ka yi biyayya gare su  suna abokan jayayya ko hukunci
Domin kai dinnan kasan kaidi irin na abokin jayayya  da kuma mai hukunci

Gaba irin na rayi kwatankwacin gaba irin na shaidan ne  kuma hakika Allah ya gargade mu game da musu da'a a cikin alkur'ani ((Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa gaban UbangijinSa ya hana kansa ga barin   soye-soyen rai , to, lallai aljanna ita ce makoma).
Allah ya sa muku albarka ni da ku  a cikin alkur'ani.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya halicci  mutum ya daidaita shi ya girmama shi ya fifita shi , ya kuma kalifantar da shi ya ba shi aminci ,  kuma ya ba shi kiwo  ya daga  darajar shi kuma ya azurta shi  kuma ya masa baiwa ya mar kyauta   .
Tsira da amincin Allah su tabbata ga wanda Allah ya zaba  Annabin mu Muhammad dan Abdullahi   da iyalan sa da sahabban sa da duk wanda ya bi tafarkin sa kuma ya bi shiriyar sa .
 YA JAMA'AR MUSULMI:
Rayi mai yawan umarni ne da mummuna   ita dinnan ta hada yawan zalunci da kuma yawan jahilci, tana yin jiji da kai da kuma nuna girman kai  da kuma hasada da riya   da fushi da kuma  kwadayi ,  da handama da babakere,  da rowa da  kankamo   da tsoron talauci da kuma   da sauran su na daga cututtuka.
    Tsarkake ta  shi ne  a cire mata wadan nan  sifofin  .
   Tsarkake rayi shi ne siffantuwa da kyawawan dabi'u  da kuma kyawawan halaye da laduba irin na shari'a   kamar  kauna  da ikhlasi da hakuri da gaskiya  da kuma kankan da kai  da tsoro da fata  da karamci da kyauta da tuba da istigfari ,  da kuma tuna mutuwa da karewa  da juya baya ga duniya  da fiskantar Allah madaukaki.
  Tsarkake rayi  yana tabbatuwa ta hanyar sabawa son arai da rashin amsa bukatun ta , da kuma yaye ta daga sha'awe-sha'awen ta   da jin dadin ta  da kuma yi mata inkari  da zarginta  Allah madaukakin sarki ya ce: - (Duk wanda  ya tsarkaka ya rabauta  . Ya kuma ambaci sunan Ubangijin shi.  Ya tsarkake  sunan Ubangijin shi mafi daukaka  )
  YA KU BAYIN ALLAH :
Ku yi kokari wurin tsarkake rayuka   kafin mutuwar gaggawa ta zo mu ku  da kuma yin da na sani ,(Ranar da ko wace rai take samun abin da ta aikata  na alheri  abin halartarwa da abin da ta aikata mummuna   tana burin da hakika akwai fage mai nisa ).
     Ku yi kokari wurin tsarkake rayuka  kafin  rayi ya zo ya ce ya hasara na bisa ga sakaci da na yi a sha'anin Allah  ko da kuwa na kasance cikin masu yin isgilanci  ko kuma ta ce  ina  ma da Allah ya shiryar da ni  da na kasance cikin masu tsoron Allah  , ko kuma ta ce ya yin da ta ga azaba  ina ma da  ina da kome sai in kasance cikin masu kyautatawa.
  Ku yi kokari  wurin tsarkake rayuka  kafin a toshe baki ba zai iya yin furuci ba , shaidu za su tsaya abokan jayayya  sune gabbai  kamar yanda Allah ya ce :- ( A yau ne muke yumkewa  bakunan su , hannayen su za su yi mana zance , kafafuwan su za su yi mana magana   za su shaida  bisa ga abin da suka kasance suna aikatawa)
(Ranar da muke tara makiya Allah to su ana kora su  (zuwa wuta). Har yayin da suka zo mana  sai kunnuwan su da idanuwan su da fatun su suka shaida a gare su da abin da suka kasance suna aikatawa ,  za su fada ga fatun su don me kuka yi shaida a kanmu , sai suka ce Allah ne ya furtar da mu  wanda ya furtar da ko wani abu  shi ne ya halicce ku  marrar farko izuwa gare shi ake komawa da ku.   Ba ku kasance kuna buya ga miyagun al'amura  don kunnuwan ku da idanuwan ku   da fatun ku su yi muku mummunar shaida ba, kai dai kun yi zato ne ya yin buyan ku cewa  hakika Allah bai san yawanci daga abin da kuke aikatawa ba , abin da kuke boyewa ba  .  Wancannin ku zaton ku wanda kuka zata ga Ubangijin ku shi ne ya halakar da ku  ku ka zamanto daga cikin tababbu .
   In sun  yi hakuri  to wuta ne makomar su , in suka nemi a yarda da su to su basa daga cikin ababen yarda . )
         Ku yi kokari wajen tsarkake  rayi  kafun  ranan da zai zame a cikin shi ( Ranar da mutum zai gujewa dan uwan shi.    Da uwar sa da Uban sa .   Da matar sa da diyar sa . Ko wani mutum a cikin  su a wannan ranar yana da sha'ani da zai shagalar da shi .
  YA KU BAYIN ALLAH:
Mai wayo shi ne wanda  ya yiwa kan sa hisabi ya yi aiki domin abin da zai zo bayan mutuwa , shi kuma gajiyayye shi ne wanda ranshi ya bi abin da yake so , ya yi ta gurace-gurace a wurin Allah  .
   Ku yiwa kan ku hisabi kafin a yi muku hisabi  ku auna kafin a auna ku  , lallai hakan ya fi saukin hisabi a gobe   idan kuka yiwa kan ku hisabi a yau   kuka yi ado  domin halartowa a wuri mafi girma , a wannan ranar ne za a kawo ku  babu wani mai tsoro a cikin ku .
  Wata rana Umar dan khaddab Allah  ya yarda da shi ya  shiga wani kango sai ya kebanta da ranshi yana mata hisabi  Anas dan Malik Allah ya yarda da shi yana sa mishi ido daga nesa ta inda  baya ganin shi  , sai ya ji umar shugaban muminai  yana cewa  sannu, sannu  na rantse  da Allah ya kai dan Khaddab  ko dai ka ji tsoron Allah ko Allah ya azabtar da kai .
  Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah , ku sani fa zaku hadu da shi
Ya Allah zukatan mu ka bata tsoron Allah
Ya Allah ka daukaka musulunci ga musulmai .      

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق