HUDUBAR JUMA'A NA MASALLACIN
ANNABI NA SHAIK ALIYU AL-HUZAIFI 14\11\1439
HUDUBAR FARKO
Da sunan Allah Mai rahama Mai jin kai
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Mabuwayi mai hikima , mai
rahama mai jin kai ina kyautata yabo ga
Ubangijina ina kuma gode masa
bisa ni'imomin sa wadanda muka sani da
wadan da ba mu sani ba to shi din nan
ahli ne na a ambace shi ba za a manta
shi ba a kuma gode mishi ba za a saba mishi ba , shi ne mawadaci mai karamci , na shaida ba
abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaadai yake bashi da abokin tarayya ,
madaukaki mai girma na shaida Annabin mu
kuma shugaban mu Muhammad bawan sa ne
kuma Manzon sa ne wanda Allah ya fifita
shi akan bayin sa ga dukkan dabi'u na karamci , ya Allah ka yi dadin tsira
da aminci bisa ga bawan ka kuma
Manzonka Muhammad da iyalan sa da
sahabban sa masu shiryarwa zuwa ga
tafarki mikakke bayan haka ku ji tsoron
Allah ta hanyar neman kusanci zuwa gare
shi da neman yardan shi da barin abubuwan da ya haramta su ba masu rabauta sai masu tsoron Allah ba masu hasara sai masu sabon Allah mabarnata .
Ya ku musulmai :
Mumini shi mai karfi ne da imanin sa sa'annan kuma mai karfi ne da 'yan uwan
sa, Mumini yana karkata ne zuwa ga
imanin sa da Ubangijin sa a lokacin tsanani da bakin ciki
kuma yana riko da imanin sa da Ubangijin sa a lokacin da wasu shubuhohi
suka bulla da kuma sha'awe –sha'awe
kuma yana ganin haske ne da imanin sa a
lokacin duhun fitintinu da musibu Allah sai ya kare shi da imanin sa lokacin sauki
da lafiya da faraga domin kar ya fada ya
halaka cikin jin dadin abubuwan da aka
haramta .
Allah yakan raya shi da
imanin sa a duniya irin rayuwa mai albarka mai walwala
abin yarda mai amfani kyakkyawa mai kyakkyawan karshe da imanin sa da Ubangijin sa ne zai riski
daraja madaukakiya bayan mutuwa Allah madaukakin sarki yake cewa: ( lallai wadan da suka yi imani suka yi aiki na
kwarai Ubangijin su zai shirye su
dalilin imanin su kwaraimai na
gudana a karkashin su a cikin lambuna
masu ni'ima adu'a an su a cikinta shi
ne tsarki ya tabbata a gare ka ya
Allah gaisuwan su kuma a cikinta
aminci , karshen da'awar su shi ne
dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai , ).
An
karbo daga salman Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : (Abin mamaki da al'amarin mumini lallai dukkan al'amarin
sa alheri ne ba wanda yake da wannan
face mumini idan abin jin dadi ya same
shi sai ya gode to sai hakan ya zama alheri a gare shi idan kuma cuta ya same
shi sai ya yi hakuri sai hakan ya zama alheri a gare shi ) Muslim ne ya rawaito
To shi mumini madaukaki ne
mai walwala ne kuma wanda ya yi dace ne da imanin sa kamar yanda mumini yana da karfi ta hanyar 'yan uwan sa domin 'yan uwantaka na musulunci ya fi karfi
akan 'yan uwantaka na jini sabo da haka ne ma
gado ke datsewa tsakanin musulmi da kafiri, Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Musulmi baya gadan kafiri haka
kafiri baya gadan musulmi) Buhari da Muslim ne suka rawaito daga
hadisin Usama dan Zaid Allah ya kara yarda a gare su , to, 'yan uwantaka na
Musulunci ya fi girma akan alaka da zumunci
da dunkulewa Allah madaukakin
sarki ya ce : ( muminai maza da muminai mata sashin su waliyyai ne ga sashi suna
umarni da kyakkyawa kuma suna hani ga
mummuna suna kuma tsaida sallah suna
kuma bada zakka kuma suna yiwa Allah da'a da Manzon sa wadan nan Allah zai
jikan su , lallai Allah mabuwayi ne mai hikima) . Allah madaukakin
sarki ya ce : ( Lallai muminai 'yan uwan juna ne) Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : ( Musulmi dan uwan musulmi ne ba zai zalunce shi
ba ba zai tabar da shi ba) . muslim ne
ya rawaito shi
To 'yan
uwantaka na musulunci yana kasancewa ta hanyar taimakekeniya a addini da karfin hadin kai Allah madaukakin sarki ya ce ga Annabin shi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi : ( Shi ne wanda
ya karfafe ka da taimakon shi da kuma
muminai ya kuma hada zukatan su da ka
ciyar da duk abin da ke doron kasa gaba daya da ba ka iya hada zukatan su ba
sai dai Allah shi ya hada zukatan su, lallai shi din nan mabuwayi ne mai hikima ) kuma Allah madaukakin sarki
ya ce : ( Ya ku wadanda kuka yi imani
ku ji tsoron Allah cancancin tsoron shi
kada ku mutu face kuna musulmai , ku yi riko da igiyan Allah baki daya
kar ku rarraba ku ambaci ni'imar
Ubangiji a gare ku zamanin da kuka kasance makiya juna sai kuka zama 'yan uwa sabo da ni'imar
Allah ,
a da kun kasance a gabar rami na
wuta ya tsamo ku daga gare ta )
'Yan uwantakan
addini yana kasancewa ne ta hanyar
taimakekeniya wurin tabbatar da
maslahohi da tunkude barna da bada kariya ga al'umma
daga masu ketare iyaka Allah
madaukaakin sarki ya ce: ( ku yi taimakekeniya akan da'a da kuma tsoron
Allah , kada ku yi taimakekeniya akan laifi da kiyayya ) Allah madaukakin
sarki ya ce : ( Ya kasance a cikin ku akwai wata al'uma da tana kira
zuwa ga alheri, kuma suna umarni da kyakkyawa , kuma
suna hani da mummuna wadannan sune masu rabauta ).
'Yan uwantaka na
musulunci yana kasancewa ta hanyar jin
kai da tausayawa juna da kuma taimakekeniya , da kuma
hadin guiwa wurin samar da abin
da al'uma ke bukata da kyakkyawan tsarin
rayuwa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce : ( Misalin muminai cikin
kaunar su da son junan su da tausayawa junan su kamar gangan jiki ne guda idan
wani gaba ya tabu da rashin lafiya sai
sauran jikin ya amsa da zugi da rashin
bacci ) Buhari ne ya rawaito da muslim daga Hadisin Abu Musa Al-ash'ari
Na daga cikin abin da ke kawo dadin rayuwa
akwai wanzuwar kauna a tsakanin
musulmai Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Na rantse da wanda raina yake hanun shi ba za ku taba shiga aljanna ba har sai kun yi
imani , ba za ku yi imani ba kuma har
sai kun so junan ku , ase ba zan nusar
da ku bisa ga aabin da idan kun aikata
shi za ku kaunaci junan ku ba to ku
yada sallama a tsakanin ku .,
YA JAMA'AR MUSULMI:
Rayuwa fa ba za ta daidaita ba har sai kun
tashi da hakkoki na 'yan uwantaka na musulunci
, to abubuwan da suke na wajibi
akwai wanda suke na Ubangiji madaukakin
sarki , wannan shi ne wajibi mafi girma
da kadaita Allah da bauta mishi ,
daga ciki kuma akwai abin da yake hakki ne na halittu
, kuma hakkokin musulmai iri uku
ne :-
Mafi girman su shi ne fifita wani akan kai (isar)
wato gabatar da bukatar musulmi da hakkin shi akan hakkin kai wannan ita ce daraja da muhajirun suka
rabauta da ita da kuma ansar Allah ya kara yarda a gare su Allah madaukakin sarki ya ce: (Wadanda
suke zaune a madina suka kudure imani tun gabanin su suna son wanda yayi hijira gare su ya yi
kaura basa hasada da abinda ya basu suna fifitawa 'yan uwan su a kan kansu koda akwai wani bukata a gare su izuwa abinda suka fifita wani da shi , wanda aka kiyashe shi kwadayin
kansa wadancannin ka su ne
hakikanin marabauta ).
Wannan na maimaituwa a ko wani zamani da ko wani wuri idan imani ya cika tarihi ya kiyaye mana wasu sifofi na fifita wani akan kai masu
yawa a lokuta daban-daban
Daraja na tsakatsakiya kuma daga cikin darajoji na
'yan uwantaka shi ne mutum musulmi ya so wa dan uwansa abin da ya so wa kan sa an
karbo daga Anas Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (
Imanin dayan ku ba zai cika ba har sai ya so wa dan uwan shi abin da yake
so wa kanshi) Buhari da Muslim ne suka rawaito
Mafi daraja na
kasa kuma wanda musulmi zai tashi da shi
game da hakkin dan uwan shi musulmi shi ne ka kame sharrin ka daga gare shi , ba za ka zalunce shi ba a jini ne ko dukiya
ko mutunci , ba za ka zare harshen ka ba
akan shi ko hanun ka ko kuma ka tawaye mishi wani hakkin da yake na shi ne , ko
ka hana shi hakkin sa tare da yin kokari
yin abin da Allah zai datar da kai zuwa
gare shi na alheri, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya ce da Abu zarri (kuma ka kame sharrinka daga mutane, domin hakan sadaka
ne gare ka a kan ka,)
Ya ku musulmai!
Lallai abin da ya fi cutar da 'yan uwantaka na musulunci shine bidi'a
mai batarwa, don dan bidi'a yana kiyayya ga duk wanda bai aminta da bidi'arsa, ba abin da zai hada
zukatar musulmai sai akidar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi, da sahabbansa da wadanda suka bi su da kyautatawa , su ne masu son
juna don Allah, na karshen su na son na farkonsu, Allah Madaukakin sarki ya ce:
( Wadan da suka zo bayansu suna cewa :Ya
Ubangijinmu ka gafarta mana da 'yan uwan
mu da suka gabace mu da imani kar ka sanya kulli cikin zuciyarmu game da wadan
da suka yi imani ya Ubangijinmu kai mai tausayi ne mai jinkai)
Na daga cikin abin da ke cutar da 'yan uwantaka ta musulunci akwai
fifita duniya akan lahira, da mutuwa don ita. Har ya zama mafi yawan mutane kan haka suke 'yan
uwantakarsu, da gina kiyayya kan kawar duniya da jin dadinta.
Na daga cikin abin da ke cutar da 'yan uwantaka zalunci da yaduwar wannan zalunci ta hanyar
hana mutane hakkokinsu, ko kwace hakki, don rayin dan adam na tsanan duk wanda
ya zalunce ta, kuma tana neman daukar fansa, daga gare shi,
Na daga cikin abin da ke cutar da 'yan uwantaka na musulunci akwai hasada, domin yana janyo
gaba da kiyayya.
Na daga cikin abin da ke haifar da illa ga 'yan uwantaka na musulunci
mutum ya rika ganin kansa a matsayin
kamili ya ke ganin waninsa
da reni da tawaya. To ga ku jama'ar musulmi jikunanku sun hadu a
farillu na musulunci, a hajji da juma'a
da sallar jam'i da sallolin idi, to ku
hada zukatanku a kan akidar magabata na kwarai, da kur'ani da sunna , ku tuna
cew za ku koma ga Allah Madaukaki, ku bar duk wani abu da ke kange ku daga
gaskiya, ku tsaya gaba ga Ubangijinku huntaye tsirara, ba kaciya, ba wani abu
tare da ku sai kyawawan ayyukanku da munana, to ku zo wa kyawawan ayyuka ku
kiyayi munanan ayyuka,Allah Madaukakin sarki ya ce : (ku yi gaggawa zuwa ga
gafara daga Ubangijinku da Aljanna
fadinta ya kai sammai da kasa an tanade ta don masu tsoron Allah. Wadan da suke
ciyarwa a lokacin sauki da tsanani, da masu hadiye fushi da masu yafiya ga
mutane, Allah na son masu kyautatawa,)
Allah sanya mini albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma,
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah a kowane hali, muna neman
tsarin shi daga hali irin na 'yan wuta, wadan da ayyukansu ya jefa su cikin
wulakanci da azaba, ina gode wa Ubangiji na bisa ga kyauta mai girma,Na shaida
ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya
Mai girma Maabocin daukaka, Na shaida Annabin mu kuma shugabanmu Muhammad
bawansa ne kuma Manzonsa ne.
Allah ka yi dadin tsira a gare shi da sahabbansa da iyalai, bayan haka
ku ji tsoron Allah ku mishi biyayya, ku kiyayi fushinsa da bushewar ido cikin saba masa, ya ku bayin
Allah hakika hujja fa ta tsayu a kanku, hanya ta bayyana a gare ku, kuma duk
wasu uzurori sun yanke, to ku fiskanci aiki kada buri ya rude ku, Allah
Madaukakin sarki na cewa : (Ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijin ku ku kiyayi
wata rana da Mahaifi ba zai fanshi dansa ba ko shi da ya fanshi mahaifinsa da wani abu ba, Alkawarin Allah gaskiya ne
kada rayuwar duniya ta rude ku, kada kuma wani abin rudi ya rude ku daga Allah)
To ku tuna mutuwa da abin da ke bi mata na daga azaba da ba mai kubutar da mutum daga shi sai
ayyuka na kwarai, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya ce ku yawaita ambato mai datse jin dadi, wato mutuwa ,
Ya ku bayin Allah lale Allah da Mala'ikunsa su na salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani
ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce,
Har karshen Adua.