ترجمة الخطبة
اسم
المترجم :أمين سعد عبد الله
اللغة : الهوسا
التاريخ : 6-10-1441هـ
Hudubar Juma'a a Masallacin Annabi Na
shaikh Ahmad Dalib 6/10/1441AH/29/5/ 2020AC
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa,
muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda
Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai
shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake
ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma
manzonSa ne. tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da aminci
tabbatacce.
(Ya ku
wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu
face kuna musulmai)
(ya ku
mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta
matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji
tsoron Allah da ku ke roko da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance
mai tsaro ne a kan ku.)
(ya ku
wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara
muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah
biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta mai girma.)
Bayan haka,
lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce
shiriyar Annabinmu Muhammad, kuma sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan
bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta.
Lalle ni ina
muku godiya ga Allah Ubangijin talikai. Mai rahama Mai jinkai.Mai mulki ranar
sakayya.
(Dukkan
yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya halicci sammai da kasa, kuma ya
sanya duhu da haske, sannan wadanda suka kafirta suna karkacewa Ubangijinsu).
(Wanda
ya saukar da littafi ga bawanSa bai sanya karkata ba gare shi.madaidaici domin
ya yi gargadi da azaba mai tsanani daga gare shi. Kuma ya yi albishir ga
muminai wadanda suke aikata ayyuka na kwarai da (cewa) suna da wata lada mai
kyau. Suna masu dawwama a cikinta har abada).
(Wanda
bai riki da ba. Kuma bai da abokin tarayya, kuma bai da wani majibinci da zai
taimake shi daga walakanci).
(wanda yake abin da ya ke cikin sammai da kasa
nasa ne.godiya tasa ce a lahira, kuma shi Mai hikima ne Mai labartawa. Ya san
abin da yake shiga cikin kasa da abin da ya ke fitowa daga gare ta, Shine Mai
rahama Mai gafara).
(Wanda
ya fari halittan sammai da kasa,Mai sanya mala'iku manzanni masu fukafukai
bibbiyu da uku-uku da hurhudu, yana kara abin da yaso cikin halittar, lalle
Allah Mai iko ne ga dukkan komai).
(Wanda
ya sanya muku kasa tabbatacciya, da sama ginanniya kuma ya suranta ku, sa'annan
ya kyautata surorinku, kuma ya azurta ku daga abubuwa masu dadi. Wancan shine Allah
Ubangijinku, albarkar Allah Ubangijin talikai ta bayyana.(Shine rayayye ba abin
bautawa face shi, ku kira shi kuna masu tsarkake addini a gare shi, Godiya ta
tabbata ga Allah Ubangijin halittu).
To yabo da
godiya sun tabbata ga Allah,wanda ya ke ciyarwa ba a ciyar da shi, ya mana
baiwa sai ya ciyar da mu ya shayar da mu, dukkan wani abu mai kyau na jarabawa
Allah ya mana.
Godiya ga Allah ba irin na mai bankwana, ko wanda ake sakawa
ba ko mai butulcewa ba ko kuma wanda ya wadatu daga gare shi ba Ubangijinmu.
Godiya tasa ce bisa halittanmu da azurta mu da shiryar da mu
da yayi, godiya gare shi bisa ilmantar da mu da ya yi, ya kuma tseratar da mu
ya yaye mana bakinciki, ya bamu mafaka, godiya gare shi bisa imani, godiya gare
shi bisa musulunci, godiya gare shi bisa Alkur'ani. godiya gare shi bisa iyalai
da dukiya da waraka, ya wulakanta makiyinmu ya yalwata mana arziki ya bayyana
amincinmu ya hada rarrabarmu,ya kyautata samun lafiyarmu, kuma ya bamu dukkan
abin da muka roke shi to dukkan yabo da godiya na shi ne mai yawa mai tsarki
mai albarka a cikinsa kamar yadda Ubangijinmu ya ke so kuma ya yarda.
(Sabo
da haka godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin sammai kuma Ubangijin kasa,
Ubangijin halittu. Kuma gare shi ne girma ya ke a cikin sammai da kasa, kuma Shi
ne Mabuwayi Mai hikima). Dukkan yabo da godiya ta sa ce kamar yadda muke fadi, dukkan
yabo da godiya ta sa ce sama da yadda muke fadi, dukkan yabo da godiya ta sa ce
har sai ya yarda, dukkan yabo da godiya
ta sa ce har bayan yarda, kuma godiya
tasa ce a farko kuma godiya tasa ce a karshe, kuma godiya tasa ce a bayyane
kuma godiya tasa ce a boye, kuma dukkan godiya tasa ce a kowane hali, Mai girma
Madaukaki.
Ya samar da mu kuma ya tattale mu ya taimake mu,to godiya
tasa ce, ya datar da mu ya fahimtar da mu ya mana ilhama, to godiya ta tabbata
a gare shi,ya shaidar da mu kuma ya shiryar da mu ya sanya mana walwala, to
godiya ta tabbata a gare shi.
Ya tsaida mai shaidar rahama cikinmu sai ya kubutar da mai
lafiya ya warkar da mara lafiya, ya zabi wanda ya kai ga ajalinsa cikinmu zuwa
kusancinSa. Ya katange zukata daga firgici da gazawa da kwadayi.
ya bibiye mu da yalwan falalolinSa, bai muamalance mu da
tsagoron adalcinsa ba, ya isar da mu zuwa watan ramadan ya jiyar da mu
alkur'ani daga kwarin daki mai alfarma da kusa da raudan abin girmamawa.ya
tsaida wanda ya so a cikin su daga bayinSa a matsaya na salihai masu azumi da
tsayuwa da tilawa da ambato da tadabburi da tafakkuri da tuntuntuni da godiya,
kebantar da su ya tabbata fatan ka sa su cikin kebabbunka.
Allah ya yawaita mana juma'o'i a cikinsa ya bibiyar da
alherori a cikinsa ya kwarara mana albarkokin sama, sannan Allah ya cika mana
da kammaluwan ranakunsa da dararakinsa, da halartan girmama Ubangijinmu. Da
daukaka daren ja'izozi da wayan garinsa da taimakonsa ga shan ruwa da da buda
baki da cin abinci, to godiya ta tabbata a gare shi.
Godiya ta tabbata a ga
Allah da ya nunawa musulmai alheri mai yawa a kansu sau da yawa aka kammala
karatun Alkur'ani a gidaje, raka'o'i da dama an sallata a dakuna, littafi mai
amfani nawa aka karanta,darusa nawa aka yada su kuma suka amfanar kuma
wa'azuzzuka nawa ne aka yada su ta gidajen radiyo suka fadakar.
Godiya ta tabbata ga Allah da ya bayyana boyayyen imani daga
gurin da aka manta shi, kur'anai da dama an kaurace musu sai gasu an fito da
suka ga haske,zukata nawa ne suka kakashe sai ga su sun lausasa, idanuwa nawa
ne da suka bushe sai gasu suna zubar da hawaye, rayuka nawa ne suka saba sai
gasu sun hada kai, mutum nawa ne suka juya wa juna baya sai gasu sun fiskanto
juna, ruhi nawa ne suka yanke zumunci sai gasu sun sadar,
Godiya ta tabbata ga
Allah da ya sanya musulmai a cikin miskinai kamar Ansar a cikin Muhajirun,
wadanda suka bayar da masauki suka yi taimako, suka karfafe su suka karbe su
kuma suka yi shafa'a suka bada shafa'a. suka tattaro suka rarraba, suka ciyar
suka fifita, arziki nawa suka raba,da basuka da aka biya, mata nawa ne da suka
rasa mazajensu suka rufa musu asiri,
marayu nawa aka dau nauyi, bukatu nawa aka biya, kwanukan abinci nawa aka
shimfida, tafuka nawa aka hana roko, gidaje nawa ne aka cika su da alheri,basu
kasance da su kauracewa sunnonin Manzon Allah ba ko su bar koyarwarsa ba, gari mai kyau tsirransa na fita da izinin
Ubangijinsa.
Godiya ta tabbata ga Allah da ya nuna mana tausayi irin na
jagora da nasiha irin na mataimaki, da shiryarwa irin na alami,da agazawa na
likita,da kulawa irin na mai tsaro, da tausayi irin mai nasiha, da daukaka
kiran sallah, da walakantuwa irin na fajirci da fasikanci da sabo.
Godiya ta tabbata ga Allah da ya shafe mu da rinjaye irin
nasa.sabo da horarwa, ya zartar da ludufi na kudurarSa a cikinmu domin
ladabtarwa, da ya so da ya kama mu da fushinSa ya azabtar da mu azabtarwa. (kuma da Allah yana kama mutane saboda abin da suka aikata,
da bai bar wata dabba ba a kanta(kasa) amma yana jinkirta musu zuwa ga ajalin
da aka ambata, sa'anan idan ajalin su ya zo to lalle Allah ya kasance Mai gani
ga bayinSa).
(To shin kuna fatan idan kun juya (daga umarnin) za ku yi barna a cikin kasa kuma ku yanke zumuntan
ku )
Shin ya wuci idan kun samu dama da ku yi barna a bayan kasa , ku watsar da littafin Ubangijin ku a bayan bayan ku ! shin kuna fatan idan kun
samu aminci da ku yi barna a doron kasa kuma ku aminta da makirci na Ubangijin
ku shin kuna fatan idan kun bayyana da
ku yi barna a doron kasa kuma ku bi
soye-soyen rayukan ku, shin kuna fatan
idan kun sauka kasuwannin ku da kuma makwancinku, da ku bayyana abin da aka ki ku bi
sha'awe-sha'wen ku! Shin kuna fatan idan
mai kiran sallan ku idan ya kira salla da ku yi barna a doron kasa! Ba
za ku amsa zuwa ga abinda zai rayar da ku ba .
YA KU BAYIN ALLAH :
Idan kun tsoraci talauci to ku nemi wadata cikin talakawan
ku, idan kun tsoraci galaba to, ku nemi taimako cikin masu raunin ku , domin da su ne ake azurta ku
kuma ake baku nasara , da zaluntan su kuma da fin karfin su da'ira take juyawa
akan ku sa'annan ayi galaba akan ku a
rinjaye ku .
Zaku sulale daga shari'a ne a sadade idan musiba ta sauka sai ku ce daga ina ne wannan! (Ka ce shi daga wurin kawunan ku ya ke lalle Allah mai iko ne ga dukkan komai )
Ku sani lallai izza na cikin da'a , kaskanci kuma na cikin
sabo
(Wanda ya kasance yana
son daukaka to daukaka a wurin Allah ne yake
gaba daya zuwa gare shi magana mai dadi ke hawa , kuma aiki na kwarai yana dauka ta , kuma wadan da ke yin makircin munanan
ayuka suna da wata azaba mai
tsanani kuma makircin wadannan yana yin
tasgaro ).
(Izza na Allah ne da
Manzon shi da muminai sai dai munafukai ba su sani ba )
Ba makawa a samu mai
shaida a halittu bisa kalmar gaskiya ,
cikin ma'abota rarrabuwa da
,munafunci , sai su ambaci irin jinsin fadin masoyan su na daga kafurai da
mushirikai , (Hakika cututtuka da sauki sun shafi iyayen mu) har su yardar
da rayukan su shakiyyai kame da ayukan
su masu halakarwa , sai wasu mutane su riske su -muna neman tsarin Allah daga
halin su sun yi alkawari da Allah a
lokacin cuta to idan ya yaye azaba sai su saba alkawarin , (Sai ya biyar
mu su da munafunci a cikin zukatan su
har zuwa ga ranar da su ke haduwa da shi
sabo da sabawa Allah ga abin da suka yi masa alkawari, kuma sabo da abin
da suka kasance suna yi na karya shin ba
su sani ba cewa lalle ne Allah yana sanin asirin su da ganawan su Kuma lalle
Allah ne Masanin abubuwan fake? ) (Ka da ranka ta tafi zuwa gare su kana mai
hasara ) ( Kada ka yi bakin ciki a gare su kuma
kar ka kasance cikin kunci bisa abin da suke yi na makirci , lalle
Allah yana tare da wadan da suka yi takawa , kuma yana tare da masu kyautatawa).
Amma ma'abota imani
sun gaskata abin da suka
alkawartawa Allah a gare shi a cikin su akwai wanda ya biya bukatan
sa akwai kuma wanda ya ke jira basu
sanja ba .(Kuma da wadan su, sunyi furuci da laifin su sun hada aiki na kwarai da wani
mummuna, akwai tsammanin Allah ya karbi tubansu, lalle Allah Mai gafara ne Mai
jinkai ).
Suna cewa:-
(Ya Ubangijinmu mun zalunci kawunanmu to
muddin ba ka gafarta mana ba ka jikanmu ba zamu kasance cikin hasararru)
Suna cewa
:-(Ya Ubangijinmu ka gafarta mana zunubanmu da barnanmu a cikin al'amarinmu, kuma
ka tabbatar da digadigan mu , kuma ka taimake mu akan mutanennan kafurai).
Suna cewa:- (Ya Ubangijinmu kar ka rike mu idan mun yi mantuwa ko
kuskure, Ya Ubangijin mu kuma kada ka aza nauyi a kan mu kamar yanda ka aza
nauyi akan wadanda suka gabace mu . Ya Ubangijin mu kada ka sanya mu daukan abin
da babu iko gare mu da shi, kuma ka yafe
mana , kuma ka gafarta mana kuma ka yi
jinkai a gare mu kai ne Majibincinmu sabo da haka ka taimake mu
akan mutanennan kafurai).
Misalin tawaga biyu kamar
makaho da kurma da mai gani da mai ji
shin za su yi daidai ase ba za ku wa'azantu
ba (Godiya ta tabbata ga Allah sai dai mafiya yawan su ba su sani ba ..
HUDUBA TA
BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah kamar yanda ya
dace da girman fuskanSa da kasaitan ikon sa kuma
godiya na sa ne kamar yanda ya dace
da yalwan afuwar sa da kayun kayutatawanSa kuma kyakkyawan yabo
na shi ne kamar yanda ya dace da girman rahamar sa da yalwan gafararSa.
Yana da godiya na har abada , godiyan da adadi bai iyakance shi , kuma har abda ba zai katse shi ba , kamar
yanda ya dace da a gode mi shi.
Dukkan godiya na shi
ne bisa ga ni'imomi wanda ba sa
kidanyuwa da da falalolin da ba sa
iyakantuwa , da kuma hukuncin da ba a maidawa , godiya na shi ne bisa ga rahamarsa wacce ta yalwaci dukkan komai na
shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah majibincin salihai, na shaida kuma
shugabanmu Muhammadu bawan sa ne kumsa Manzon sa ne shugaban masu takawa
(Ya ku wadanda suka yi
imani ku ji tsoron Allah ku kasance tare da masu gaskiya ) ku tuna ni'imomin Allah
kuma ku tuna ranakun Allah ku
kiyaye ni'imomin ; ta hanyan da'a wa
Allah , kuma ku nemi karin su ta hanyan godewa Allah , ku dauki izina a cikin
halittun Allah da kuma abin da aka nuna muku na daga ayoyin Allah , ba abin da
ya fi zama wa'azi a gare ku kamar maganan Allah .
Allah yana cewa:- Ka ce: « Godiya ta tabbata ga A1lah, kuma aminci
ya tabbata bisa ga bãyinSa, waɗanda Ya zãɓa. » Shin Allah ne Mafi alhẽri
koabin da suke yin shirki da Shi?
60. Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma
Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu
sha'awa, ba ya kasancẽwa gare ku, ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin
bautãwa tãre da Allah? Ã'a, sũ mutãne ne suna daidaitãwa ( Allah da
wani ) .
61. Kõ kuwa wãne ne Ya sanya ƙasa
tabbatacciya, kuma Ya sanya kõguna a tsakãninta kuma Ya sanya mata manyan
duwãtsu tabatattu, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãnin tẽkuna biyu? Shin
akwai wani abin bautãwa tãre da Allah. Ã'a, mafi yawansu ba su sanĩ ba.
62. Kõ wãne ne yake karɓã , kuma ya sanya ku
mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin
tunãni.
63. Kõ wãne ne yake shiryarwa a cikin duffan
ƙasa da tẽku,kuma wãne ne Yake aikõwar iskõki dõmin bãyar da bushãra a gaba ga
rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? tsarki yã tabbata ga
Allah daga barin abin da suke shirki da Shi.
64. Kõ
wãne ne yake fã ra halitta sa'an nan kuma ya mayar da ita,kuma Wãne ne Ya
azurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? Ka
ce: « Ku kãwo dalĩlinku idan kun kasance mãsu gaskiya. »
65. Ka ce: « Bãbu wanda ya san gaibi a
cikin sammai da ƙasa fãce Allah. Kuma bã su sansancẽwar a yaushe ne zã a tãyar
da su. »
66. Ã'a, saninsu ya kai a cikin Lãhira Ã'a,
sunã cikin shakka daga gare ta. Ã'a, sũ da gare ta makãfin zũci ne.
67. Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: «
Shin idan mun kasance turɓaya, mu da ubanninmu, shin, haƙĩƙa, waɗanda ake
fitarwa ne? »
68. « Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana wa'adi
ga wannan, mũ da ubanninmu, daga gabãnin haka. Wannan bã kõme ba ne fãce
tãtsũniyõyin farko. »
69. Ka ce: « Ku yi tafiya a cikin ƙasa,
sa'an nan ku dũba, yãya ãƙibar mãsu laifi take? »
70. Kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma
kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke ƙullãwa na mãkirci.
71. Kuma sunã cẽwa, « A yaushe wannan
wa'adi ( zai auku ) , idan kun kasance mãsu gaskiya? »
72. Ka ce: « Akwai fatan sãshen abin da
kuke, nẽman gaggãwarsa, ya kasance yã kuturta ( 1 ) a gare ku. »
73. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa Mai
falala ne a kan mutãne kuma amma mafi yawansu, bã su gõdẽwa.
74. Kuma lalle Ubangijinka, haƙĩƙa Yanã sanin
abin da ƙirãzansu suke, ɓõyẽwa, da abin da suke hayyanãwa.
75. Kuma bãbu wata ( mas'ala ) mai
bõyuwa, a cikin sama da ƙasa fãce tanã a cikin littafi bayyananne.
76. Lalle ne wannan Alƙur'ãni ( 2 )
yanã gaya wa Banĩ Isrãĩla mafi yawan abin da sũ suke sãɓa wa jũnansu a ciki.
77. Kuma
lalle shi haƙĩƙa shiriya ce da rahama ga mũminai.
78. « Lalle Ubangijinka Yanã yin hukunci
a tsakãninsu da hukuncinsa, kuma Shi ne Mabuwãyi, Masani. »
79. Sabõda haka, ka dõgara ga Allah, lalle ne,
kai ne a kan gaskiya bayyananniya.
80. Lalle ne kai, bã ka jiyar da matattu, kuma
bã ka sa kurãme su ji kiranka, idan sun jũya sunã mãsu bãyar da bãya.
81. Kuma kai ba ka zama mai shiryar da ɗimammu
daga ɓata ba. Bã ka jiyarwa fãce wanda yake yin ĩmãni da ãyõyinMu. To, sũ ne
mãsu sallamãwa ( al'amari zuwa ga Allah ) .
82. Kuma idan magana ta auku a kansu, Munã
fitar musu da wata dabba ( 1 ) daga ƙasa, tanã yi musu magana,
cẽwa « Lalle mutãne sun kasance game da ayoyinMu, ba su yin ĩmãnin yaƙĩni.
»
83. Kuma a rãnar da Muke tãrãwa daga kõwace
al'umma, wata ƙungiya daga waɗanda suke ƙaryata ãyõyinMu, sai ga su anã
kangesu. ( ga kõra )
84. Har idan sun zo, ( Allah ) zai
ce, « Ashe kun ƙaryata ãyõyinNa, kuma ba ku kẽwaye su da sani ba? To, mẽne
ne kuka kasance kunã aikatãwa? »
85. Kuma magana ta auku a kansu, sabõda
zãluncin da suka yi. To, sũ bã su da ta cẽwa.
86. Shin, ba su gani ba, cẽwa, lalle Mũ, Mun
sanya dare dõmin su natsu a cikinsa, kuma da yini mai sanya gani? Lalle a cikin
wancan akwai ãyõyi! Dõmin mutãne waɗanda suka yi ĩmãni.
87. Kuma da rãnar ( 2 ) da ake hũsa
a cikin ƙaho, sai wandayake a cikin sammai da waɗanda suke a cikin ƙasa su
firgita, fãce wanda Allah Ya so, kuma dukansu, su je Masa sunã ƙasƙantattu.
88. Kuma kanã ganin duwãtsu, kanã zaton su
sandararru, alhãli kuwa sũ sunã shũɗẽwa shũɗewar girgije, bisa sanã'ar Allah
wanda Ya kyautata kõwane abu. Lalle Shi, Mai lãbartãwa ne game da abin da kuke
aikatãwa.
89. Wanda
ya zo da kyakkyawan aiki guda, to, yanã da mafi alhẽri daga gare shi. Kuma sũ
daga wata firgita, ( 1 ) a yinin nan, amintattu ne.
90. Kuma wanda ya zo da mugun aiki, to, an
kife fuskõkinsu a cikin wuta. Ko zã a sãka muku fãce da abin da kuka kasance
kũnã aikatãwa?
91. ( Ka ce ) : « An umurce ni,
in bauta wa Ubangijin wannan Gari, ( 2 ) Wanda Ya mayar da shi
Hurumi, kuma Yanã da dukan kõme. Kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu
sallamãwa. »
92. « Kuma inã karanta Alƙur'ãni.
» To, wanda ya shiryu, yã shiryu ne dõmin kansa kawai. Kuma wanda ya ɓãce,
to, ka ce: « Ni daga mãsu gargaɗi kawai nake. »
93. Kuma ka ce: « Gõdiya ta tabbata ga
Allah. Zai nũna muku ãyõyinSa, har ku sansu. » Kuma Ubangijinka bai zama
Mai shagala daga barin abin da kuke aikatãwa ba.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق