السبت، 13 يونيو 2020

BUKATUWARMU GA FADAKA

اسم المترجم : أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاؤيخ : 20-10-1441هـ                                                                                                                            

 

Hudubar farko

Ya ku musulmi!

 Fadaka na daya daga cikin manyan abubuwa masu kima, da kuma abu mafi tsarki da ya dace a dasa shi , ba aminci sai da shi  babu zaman lafiya kuma sai da kulawa da shi   da bin shi ; fadaka; shi ne kiyayewa  daga duk wani abubuwa kanana da fahimta mai zurfi    an karbo daga Aisha Allah ya kara yarda a gare ta ta ce :- Manzon Allah tsira  da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce gamae da saukar wahayi :- (Sai ya tafiyar da ni da hankali na  a halin na kiyaye abin da ya fada ). A wani lafazi (sai na kiyaye abin da ya ke fadi ) Buhari ne fito da shi

Katada Allah ya mi shi rahama ya ce :- (Kunnuwa na ba za su ji wani abu ba face zuciya na ta kiyaye shi )  fadakakkiya ita ce wacce  ta hankalci abin da yake daga  Allah madaukaki da kuma amfana da abin da ta ji  na daga littafin Allah da sunnar Manzon sa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce :-(Kunnuwa masu fadakuwa) ya kawo shi bisa ga tankiri  bai kawo shi a sigar jam'i  ba  sabo da karancin masu kiyayewan da fadakuwa.

An karbo daga Zaid dan sabid Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- na ji Manzon Allah tsira  da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa:- (Allah ya haskaka fiskan duk mutumin da ya ji magana ta sai ya kiyaye ta  ya fadaku da ita  sannan ya sadar da ita zuwa ga wanda bai ji ta ba ,  sau da yawa  wanda ke dauke da  fakihu  alhali shi ba fakihi ba , sau da yawa  kuma wani kan dauki  fikihu zuwa ga wanda  ya fi shi fahimta ) Tirmizi ne ya rawaito).

Ramah Ramazi  Allah ya mi shi rahama ya ce :- ( Sai Annabi ya bambance tsakanin mai nakalto sunna da mai fadakuwa da ita ya  yi nuni zuwa  ga falalan mai fadakuwa a fadin  shi , sau da yawa wani kan dauki fikihu amma shi ba fakihi ba sau da yawa kuma wani  kan dauki fikihu zuwa ga wanda ya fi shi fikihu ).

 Ya ku musulmi:

Jakar mutum ita  ce :- zuciyarsa da  hankalinsa  da suke tattaro iliminsa da kudurinsa da kimarsa  da tunaninsa  da jinsa (na jiki), kar ka sanya a jakar ka sai abin da ya dace da  addininka  da hankalinka da dabi'unka .

Alheri wanzuwa yake ko da zamani ya yi nisa sharri kuma shi ne kazanta mafi muni da ka kiyaye na guzuri .

Ubangijin mu ya ce:-  game da  kafiraia masu girman kai   (Kuma Allah shi ne mafi sanin abin da suke tarawa ) wato  ya san  abin da suke tattarowa su boye a cikin zukatan su  na kiyayya ga Manzon Allah da muminai .

Abdullahi Dan Mas'ud Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- (Lallai wadannan zukata jaka ce, to, ku shagaltar da ita da  Alkur'ani, kar ku shagaltar da ita da wanin sa   ko wani abu  wajen shi na buso da abin da ke cikin  shi  ne,  harshen sa kuma na furta abin da ke zuciyar shi )

Abin da ke  zuciya ya ki sai ya bayyana *** Kuma dukkan kwano   yana nason abin da ke cikin shi ne

 Wanda asalin shi bai kasance tsarkakke ba *** To ba zai fitar da abu mai tsarki ba daga bakin shi.

Dukkan mutum aikin shi na kama da shi *** kofi na kamshin abin da ke cikinsa ne.

 

                           Ya ku musulmi:

Ana samun fadaka ne ta hanyar ilimi da natsuwa da fahimta   da bincike  tana karfafuwa kuma ta hanyar abota da masu yalwan hankali wanda  ya goge a harkar yau da kullum ya san jiya da yau.

 Hakika ance abin da ya rage  ya isa mai bada labari game da abin da  ya wuce, abin da suka jarraba  ya isa abin lura ga masu hankula, fadakuwa   na karuwa ne ta hanyar tambayan ma'abota ilimi  da gogewa a rayuwa  da basira a al'amura  da shekaru  da kuma sani. 

An tambayi Dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su ya ce:- (D a harshe mai yawan tambaya da zuciya mai yawan hankalta  da rayi wanda  bai gajiya).

Fadakuwa  na habaka  ne ta hanyar shawara da ma'abota hankula da basira  da kuma tattaunawa da masu hikima  da ma'abota hankula .

Mai hankali idan al'amura suka rikice mi shi *** Sai ya hade al'amuran  ta hanyar tattaunawa da kuma neman shawara

Amma ma'abota jahilci yana fandarewa da ra'ayin shi*** Sai ka ganshi yana taran  aradu da ka    

  Abin sani fadakuwa na iya karuwa kuma yana iya raguwa , hakika ance musharaka cikin al'amura yana bawa mutum  goge , atisayi kuma yana daga ma'abocin shi  zuwa ga  darajoji na kamala

 

 Mai hankali fadakakke  yana gane  nauyin da ke wuyansa, kuma  yana dubi zuwa ga karshen al'amura kafin su bayyana  ya kiyasta wani abu da makamancin shi  kuma ya dauki izina daga wanin sa  ya kiyaye daga sharri kafin ya same shi .

Mai basira ne da karshen al'amura  kai ka ce **** yana dubi ne  da ra'ayin sa na dai-dai zuwa ga abin da ya ke aukuwa

Huzaifa Dan Yamani Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :- (Mutane sun kasance suna tambayan Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  akan alheri , ni kuma na kasance ina tambayan shi game da sharri, tsoron

Mai hankali fadakakke  yana kiyayewa daga  abin da akwai kaskanci  ko tawaya  kuma yana taka tsantsan cikin abin da akwai aibi  akan shi , ko kuma akwai cutarwa ga wanin shi, kuma yana tsarkaka daga abin da yake akwai kazanta , ya kuma kauce daga abin  kyama ya kuma kare kan shi daga abin da bai dace ba,  kyau da kawa  daga  gare  shi ya ke fitowa,  alheri kuma daga gare shi ya ke gangarowa.

 Ya ku musulmi:

Karancin fadakuwa  musiba ce  da ta tsaya akan kwabri na jahilci,  da kuma  raunin hankali da wauta  da karancin gogewa,  kuma yin ko inkula  na daga cikin  bala'in da ya ke kasancewa ra'ayi , ga wanda yake da iko ba ga wanda ya ke kallo ba, ta yaya mutum zai musanta abinda ya ke hakika ne  ya kuma gaskata abinda ya ke na bata ne ko karairayi , ya maida abubuwan da  suke ana ji  ana gani   ya rasa rarrabewa  , zane da layi suka rikirkice mi shi  ya kasa rarrabe tsakanin zare da abawa   da kuma tsakanin gaskiya da wasa   da kuma abu mai kyau da mara kyau  bai yi dubi ba zuwa ga karshen ala'amura  ,  bai gano girman hadarin ba  kuma bai yi riko da azama ba , bai dauki mataki na kariya da iyakancewa ba  da farkawa  ba , ya bi son rai  ya kosar da zuciyan sa sha'awe-sha'awen sa  ba tare da yayi dubi zuwa ga makomar al'amura ba, to ta yaya zai zamana ya amsa kiran mai nasiha ko ya damu da  abin da   yake cewa.

Na daga cikin musiba zargin wanda  ba zai gargadu ba*** dabga zaluncin shi  da kuma magana da wanda bai fahimta

Ba wani abu ba ne cuta  sai dai ka ilmantar da wanda yake jahili *** Shi kuma yana zato cikin jahilcin shi  cewa ya fi ka sani

Ya ku musulmi:

Ku gyaru da ilimi , ku amsa kira da fahimta ku ja damara da basira, ku sa rigar kariya  da fadaka.

Fadakuwa abu ne   na dole *** ba mai rabauta sai mai yi da gaske

Tir da wanda ya san abu na gaske kuma  ya ki ya ki ya tafi akai , muna jin  radadi a yayin da muka ga wanda ya ke jin koyarwa na kariya  da kuma abubuwa da aka yadawa na fadakarwa da dalilai na shiryarwa  da kuma tsari na kare kai da ke fitowa daga  bangaren jami'an tsaro da jami'an lafiya musamman daga abin da ya shafi korona  sai ya yi kunnen uwar shegu , kamar bai ji ba  ya rinka fiskantar su da izgilanci  da ko inkula  ya doge yana mai sabawa  da musu  ya haifarwa kansa da iyayensa da 'ya'yansa da iyalansa  ya jawo bala'i da cuta ya raba musu a tsakiyar gidansu ya bude mu su kofofinta ya dauke musu shamakinta , ya rinka kuma kashewa mutane gwuiwa daga  bin matakan kariya , ya kuma yada tsakanin mutane cewa korona karya ne  da yaudara, ya makance daga dubannin matattu da wadan da suka kamu, wadan da suka dandani daci da tsananin cutan .

 

Yana tinkaran dukkan kokari da kasashe ke yi na iyakan cewa da yin galaba da yaduwan shi , to ku kiyaye daga raunin hankali  da raunin alkalami  da magana  ku sake bitan hankula ku yi lura cikin tunanin da kuke yadawa da lafuzan da kuke saka  da abubuwa da kukle yadawa , ku ji tsoron Allah cikin abin da kuke fadi , ku bar abin da ba ku  iya  kyautata  kada ku kusa cikin abin da ba ku sani ba , kar ku yi amfani da jahilci wurin yakar ilimi da zato wurin yakini ,  da abin da yake na shirme  da karairayi wanda ba su da  makama ,   ku kyautata  al'amarin ku , ku shiga taitayin ku, hakika ance   .

Ra'ayi mai gudana da idanuwan mutane  na bacci***Ra'ayin da ya kaddamar da takatsatsan  baya jinkirta azama. Ina fadan abin da kuke ji kuma ina neman gafaran Allah kuma kuma ku nemi gafarar shi lallai shi ya kasance ga masu  yawan komawa gare  shi mai yawan gafara ne .

 

Huduba na biyu

Ya ku jama'ar musulmi :

Hakika  abubuwan da suka faru na wannan yanayi da ake ciki na korona   da abubuwan da suka auku ya bayyana  bukatuwanmu zuwa ga sake gina fadakarwa , ga 'ya'ya da kuma al'uma da mata da maza ,  da yawa mun gani na daga dajjalanci  da karairayi  wanda suke amfani da wannan annoban  wurin cimma  kazantattun manufofin su  da neman abin duniya walakantacce , wofantacce mai da'awan karyan da bayi da ilimin likitanci  ko kuma ba yi da wani  abu da zai taimaka mishi wajen tabbatar da binciken ilimi mai zurfi , ba kuma na'ura  da zai yi amfani da shi wurin gano maganin korona , amma zai yi da'awan ya gano maganin cutar korona , mutumin da yake likitanci na karya  da yaranta da yaudara zai bada magani na kwayar cuta da ta gagari center ta bincike na duniya. Shi mai kwadayin abin duniya mai son handama, maras dabi'u masu kyau zai boye kayaki da sumbattoci   da kuma ababan tsabtace wuri da magungunan kashe koyoyin cuta , domin ya rinka wasa da farashin su ,    da kuma ,mai yin algus da dabaru yana mai sana'anta magunguna na karya da  da abubuwan kashe koyoyin cuta na boge wacce ke iya yin illa wa lafiya  kuma yakan taba lafiyan jiki  da mai karyan ilimi rudadde , wanda yake  bushewan ido da bada fatawa  da yin ijtihadi a cikin abubuwa da suke sabbi, da matsaloli da suke da alaka da korona  , yana mai fiskantar da mutane ta yanda za su yi salla su tsarkaka su yi ibada alhali kuwa bai mallaki cancanci na ijtihadi ba ko fatawa .

 Za ka ga wawa yana kaucewa duk wani abu na mutunci*** yana sauraron duk wani abu na wauta.

Ba mai aminta da masu wadannan da'awar sai mara fadaka da ganewa da lafiyayyen hankali.

Ku ji tsoron Allah ya ku musulmi  ku hanu ku kame kai daga abubuwan aibi da laifi da abin kunya, ga Al-kur'ani da suna gaba gare ku, suna cike da hikima da hukunce – hukunce da ka'idoji da wa'azuzzuka, da laduba da wadanda su ne shugabannin ilmuka kuma mabubbuga ne na fahimta kuma hanya ce ta samun daukaka da ake nema, to ku kiyaye su,ku yada su, da wahayi ne da fadaka hankula ke cika, shakku da wahami ke gushewa.duhu ke yayewa,

Ku   farkar da zukata  daga gafala ku tuba daga zunubai da kusakurai, bala'i bai sauka sai da zunubi, ba a daukewa sai da tuba, ku nemi saukar rahama da adu'a, duk wanda ya nuna talaucin shi zuwa ga Allah  to Allah ya wadata shi, duk wanda ya nemi mafaka a wurin shi Allah sai ya daukaka shi duk wanda ya nemi kariya daga gun shi sai Allah ya kare shi idan har bayan jirkicewa ne to sai Allah ya bashi kwanciyar hankali idan bayan ruwan sama ne kuma sai ta yi fayau, rana tana buya kuma tana hudowa , fure kan yankwane sannan kuma ya yi 'yaya , dukkan wani tsanani to zuwa ga sauki ,dukkan kuma wani wahala to zuwa ga yayewa, ku yawaita kankan da kai da adu'a da fatan alheri.

Waka :

***duk wanda ya ke neman mafaka kuma yana fata ***

 annoba ya bayyana sai gashi matambayi ya zo zuwa gare ka***

*** idan ka bada taimako to dukkan bala'ai zai yaye ***

Idan ka kwarara to dukkan alheri zai sauka ***

***idan ka yi rahama to dukkan cuta zai katse ***

Idan ka warkar to dukkan cuta zai sushe ***

*** kasa idan ta yi fari a shekara to zai tafe ***

To wanene mai karanci a gare mu mai yawan yawan kyauta mai yawn zubar da ruwan sama ***

*** idan annoba ya taho a kan guiwansa a kwangwan nin mu ***

To wanene mai jin kai a gare mu ko a'agajin gaggawa ***

*** idan ya yafe to Shi Mai karamci Mai yalwa ***

Idan Ya yi hukunci to Shi ne mai hukunci na a'adalci

Ku yi salati da  sallama ga  Ahmad  mai shiriya mai ceto ga halittu.          

  

 

 

  

 

 

 

 

 

 

 

 

 

  

  

 

 

Allah Abin godiya

                                                                                                     

ترجمة الخطبة

اسم المترجم :أمين سعد عبد الله

اللغة : الهوسا

التاريخ : 6-10-1441هـ

 

Hudubar Juma'a a Masallacin Annabi Na shaikh Ahmad Dalib 6/10/1441AH/29/5/ 2020AC

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzonSa ne. tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da aminci tabbatacce.

(Ya ku wadanda suka bada gaskiya ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa kada ku mutu face kuna musulmai)

(ya ku mutane ku ji tsoron Allah wanda ya halitta ku daga rai guda kuma ya halitta matarsa daga gare shi ya yada daga gare su mazaje masu yawa da mata, ku ji tsoron Allah da ku ke roko da (sunan) shi. Da zumunci, lalle Allah ya kasance mai tsaro ne a kan ku.)

(ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi zance na daidai. zai gyara muku ayyukan ku kuma ya gafarta muku zunubanku, duk wanda ya ke yi wa Allah biyayya da ManzonSa to ya rabauta rabauta mai girma.)

 

Bayan haka, lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiriya ita ce shiriyar Annabinmu Muhammad, kuma sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan bidi'a bata ce, kuma dukkan bata na wuta.

Lalle ni ina muku godiya ga Allah Ubangijin talikai. Mai rahama Mai jinkai.Mai mulki ranar sakayya.

(Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya halicci sammai da kasa, kuma ya sanya duhu da haske, sannan wadanda suka kafirta suna karkacewa Ubangijinsu).

(Wanda ya saukar da littafi ga bawanSa bai sanya karkata ba gare shi.madaidaici domin ya yi gargadi da azaba mai tsanani daga gare shi. Kuma ya yi albishir ga muminai wadanda suke aikata ayyuka na kwarai da (cewa) suna da wata lada mai kyau. Suna masu dawwama a cikinta har abada).

(Wanda bai riki da ba. Kuma bai da abokin tarayya, kuma bai da wani majibinci da zai taimake shi daga walakanci).

 (wanda yake abin da ya ke cikin sammai da kasa nasa ne.godiya tasa ce a lahira, kuma shi Mai hikima ne Mai labartawa. Ya san abin da yake shiga cikin kasa da abin da ya ke fitowa daga gare ta, Shine Mai rahama Mai gafara).

(Wanda ya fari halittan sammai da kasa,Mai sanya mala'iku manzanni masu fukafukai bibbiyu da uku-uku da hurhudu, yana kara abin da yaso cikin halittar, lalle Allah Mai iko ne ga dukkan komai).

(Wanda ya sanya muku kasa tabbatacciya, da sama ginanniya kuma ya suranta ku, sa'annan ya kyautata surorinku, kuma ya azurta ku daga abubuwa masu dadi. Wancan shine Allah Ubangijinku, albarkar Allah Ubangijin talikai ta bayyana.(Shine rayayye ba abin bautawa face shi, ku kira shi kuna masu tsarkake addini a gare shi, Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu).

   To yabo da godiya sun tabbata ga Allah,wanda ya ke ciyarwa ba a ciyar da shi, ya mana baiwa sai ya ciyar da mu ya shayar da mu, dukkan wani abu mai kyau na jarabawa Allah ya mana.

Godiya ga Allah ba irin na mai bankwana, ko wanda ake sakawa ba ko mai butulcewa ba ko kuma wanda ya wadatu daga gare shi ba Ubangijinmu.

Godiya tasa ce bisa halittanmu da azurta mu da shiryar da mu da yayi, godiya gare shi bisa ilmantar da mu da ya yi, ya kuma tseratar da mu ya yaye mana bakinciki, ya bamu mafaka, godiya gare shi bisa imani, godiya gare shi bisa musulunci, godiya gare shi bisa Alkur'ani. godiya gare shi bisa iyalai da dukiya da waraka, ya wulakanta makiyinmu ya yalwata mana arziki ya bayyana amincinmu ya hada rarrabarmu,ya kyautata samun lafiyarmu, kuma ya bamu dukkan abin da muka roke shi to dukkan yabo da godiya na shi ne mai yawa mai tsarki mai albarka a cikinsa kamar yadda Ubangijinmu ya ke so kuma ya yarda.

(Sabo da haka godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin sammai kuma Ubangijin kasa, Ubangijin halittu. Kuma gare shi ne girma ya ke a cikin sammai da kasa, kuma Shi ne Mabuwayi Mai hikima). Dukkan yabo da godiya ta sa ce kamar yadda muke fadi, dukkan yabo da godiya ta sa ce sama da yadda muke fadi, dukkan yabo da godiya ta sa ce har sai ya  yarda, dukkan yabo da godiya ta sa ce har bayan  yarda, kuma godiya tasa ce a farko kuma godiya tasa ce a karshe, kuma godiya tasa ce a bayyane kuma godiya tasa ce a boye, kuma dukkan godiya tasa ce a kowane hali, Mai girma Madaukaki.

Ya samar da mu kuma ya tattale mu ya taimake mu,to godiya tasa ce, ya datar da mu ya fahimtar da mu ya mana ilhama, to godiya ta tabbata a gare shi,ya shaidar da mu kuma ya shiryar da mu ya sanya mana walwala, to godiya ta tabbata a gare shi.

Ya tsaida mai shaidar rahama cikinmu sai ya kubutar da mai lafiya ya warkar da mara lafiya, ya zabi wanda ya kai ga ajalinsa cikinmu zuwa kusancinSa. Ya katange zukata daga firgici da gazawa da kwadayi.

ya bibiye mu da yalwan falalolinSa, bai muamalance mu da tsagoron adalcinsa ba, ya isar da mu zuwa watan ramadan ya jiyar da mu alkur'ani daga kwarin daki mai alfarma da kusa da raudan abin girmamawa.ya tsaida wanda ya so a cikin su daga bayinSa a matsaya na salihai masu azumi da tsayuwa da tilawa da ambato da tadabburi da tafakkuri da tuntuntuni da godiya, kebantar da su ya tabbata fatan ka sa su cikin kebabbunka.

Allah ya yawaita mana juma'o'i a cikinsa ya bibiyar da alherori a cikinsa ya kwarara mana albarkokin sama, sannan Allah ya cika mana da kammaluwan ranakunsa da dararakinsa, da halartan girmama Ubangijinmu. Da daukaka daren ja'izozi da wayan garinsa da taimakonsa ga shan ruwa da da buda baki da cin abinci, to godiya ta tabbata a gare shi.

 Godiya ta tabbata a ga Allah da ya nunawa musulmai alheri mai yawa a kansu sau da yawa aka kammala karatun Alkur'ani a gidaje, raka'o'i da dama an sallata a dakuna, littafi mai amfani nawa aka karanta,darusa nawa aka yada su kuma suka amfanar kuma wa'azuzzuka nawa ne aka yada su ta gidajen radiyo suka fadakar.

Godiya ta tabbata ga Allah da ya bayyana boyayyen imani daga gurin da aka manta shi, kur'anai da dama an kaurace musu sai gasu an fito da suka ga haske,zukata nawa ne suka kakashe sai ga su sun lausasa, idanuwa nawa ne da suka bushe sai gasu suna zubar da hawaye, rayuka nawa ne suka saba sai gasu sun hada kai, mutum nawa ne suka juya wa juna baya sai gasu sun fiskanto juna, ruhi nawa ne suka yanke zumunci sai gasu sun sadar,

Godiya ta tabbata  ga Allah da ya sanya musulmai a cikin miskinai kamar Ansar a cikin Muhajirun, wadanda suka bayar da masauki suka yi taimako, suka karfafe su suka karbe su kuma suka yi shafa'a suka bada shafa'a. suka tattaro suka rarraba, suka ciyar suka fifita, arziki nawa suka raba,da basuka da aka biya, mata nawa ne da suka rasa  mazajensu suka rufa musu asiri, marayu nawa aka dau nauyi, bukatu nawa aka biya, kwanukan abinci nawa aka shimfida, tafuka nawa aka hana roko, gidaje nawa ne aka cika su da alheri,basu kasance da su kauracewa sunnonin Manzon Allah ba ko su bar koyarwarsa  ba, gari mai kyau tsirransa na fita da izinin Ubangijinsa.

Godiya ta tabbata ga Allah da ya nuna mana tausayi irin na jagora da nasiha irin na mataimaki, da shiryarwa irin na alami,da agazawa na likita,da kulawa irin na mai tsaro, da tausayi irin mai nasiha, da daukaka kiran sallah, da walakantuwa irin na fajirci da fasikanci da sabo.

Godiya ta tabbata ga Allah da ya shafe mu da rinjaye irin nasa.sabo da horarwa, ya zartar da ludufi na kudurarSa a cikinmu domin ladabtarwa, da ya so da ya kama mu da fushinSa ya azabtar da mu azabtarwa. (kuma da Allah yana kama mutane saboda abin da suka aikata, da bai bar wata dabba ba a kanta(kasa) amma yana jinkirta musu zuwa ga ajalin da aka ambata, sa'anan idan ajalin su ya zo to lalle Allah ya kasance Mai gani ga bayinSa).

             (To shin  kuna fatan idan kun juya (daga umarnin)  za ku yi barna a cikin kasa kuma ku yanke zumuntan ku )

Shin ya wuci idan kun samu dama da ku yi barna a  bayan kasa ,   ku watsar da littafin Ubangijin ku  a bayan bayan ku ! shin kuna fatan idan kun samu aminci da ku yi barna a doron kasa kuma ku aminta da makirci na Ubangijin ku  shin kuna fatan idan kun bayyana da ku yi barna a doron kasa  kuma ku bi soye-soyen rayukan ku, shin kuna fatan  idan kun sauka kasuwannin ku da kuma makwancinku,  da ku bayyana abin da aka ki ku bi sha'awe-sha'wen ku! Shin kuna fatan idan  mai kiran sallan ku idan ya kira salla da ku yi barna a doron kasa! Ba za ku amsa zuwa ga abinda zai rayar da ku ba .

YA KU BAYIN ALLAH :

Idan kun tsoraci talauci to ku nemi wadata cikin talakawan ku, idan kun tsoraci galaba to, ku nemi taimako cikin  masu raunin ku , domin da su ne ake azurta ku kuma ake baku nasara , da zaluntan su kuma da fin karfin su da'ira take juyawa akan ku  sa'annan ayi galaba akan ku   a rinjaye ku .

Zaku sulale daga shari'a ne a sadade  idan musiba ta sauka sai  ku ce daga ina ne wannan! (Ka ce shi daga wurin kawunan ku ya  ke lalle Allah mai iko ne ga dukkan komai )

Ku sani lallai izza na cikin da'a , kaskanci kuma na cikin sabo

(Wanda ya kasance yana son daukaka to daukaka a wurin Allah ne yake  gaba daya zuwa gare shi magana mai dadi ke hawa , kuma aiki na  kwarai yana dauka ta ,  kuma wadan da ke yin makircin munanan ayuka  suna da wata azaba mai tsanani  kuma makircin wadannan yana yin tasgaro ).

(Izza na Allah ne da Manzon shi da muminai sai dai munafukai ba su sani ba )  

Ba makawa  a samu mai shaida a halittu bisa kalmar gaskiya ,  cikin  ma'abota rarrabuwa da ,munafunci , sai su ambaci irin jinsin fadin masoyan su na daga kafurai da mushirikai , (Hakika cututtuka da sauki  sun shafi iyayen mu) har su yardar da rayukan su shakiyyai  kame da ayukan su masu halakarwa , sai wasu mutane su riske su -muna neman tsarin Allah daga halin su  sun yi alkawari da Allah a lokacin cuta to idan ya yaye azaba sai su saba alkawarin ,  (Sai ya biyar mu su da munafunci a cikin zukatan su  har zuwa ga ranar da su ke haduwa da shi  sabo da sabawa Allah ga abin da suka yi masa alkawari, kuma sabo da abin da suka kasance suna yi na karya shin  ba su sani ba cewa lalle ne Allah yana sanin asirin su da ganawan su Kuma lalle Allah ne  Masanin abubuwan fake?  ) (Ka da ranka ta tafi zuwa gare su kana mai hasara ) ( Kada ka yi bakin ciki a gare su kuma  kar ka kasance cikin kunci bisa abin da suke yi na makirci , lalle Allah  yana tare da wadan da suka yi takawa  , kuma yana tare da masu kyautatawa).

Amma ma'abota imani  sun gaskata  abin da suka alkawartawa  Allah a gare shi  a cikin su akwai wanda ya biya bukatan sa  akwai kuma wanda ya ke jira basu sanja ba .(Kuma da  wadan su, sunyi furuci  da laifin su sun hada aiki na kwarai da wani mummuna, akwai tsammanin Allah ya karbi tubansu, lalle Allah Mai gafara ne Mai jinkai ).

Suna cewa:-  (Ya Ubangijinmu mun zalunci kawunanmu to muddin ba ka gafarta mana ba ka jikanmu ba zamu kasance cikin hasararru)

Suna cewa :-(Ya Ubangijinmu ka gafarta mana zunubanmu da barnanmu a cikin al'amarinmu, kuma ka tabbatar da digadigan mu , kuma ka taimake mu akan mutanennan kafurai).

Suna cewa:- (Ya Ubangijinmu kar ka rike mu idan mun yi mantuwa ko kuskure, Ya Ubangijin mu  kuma kada  ka aza nauyi a kan mu kamar yanda ka aza nauyi akan wadanda suka gabace  mu .  Ya Ubangijin mu kada ka sanya mu daukan abin da babu iko gare mu  da shi, kuma ka yafe mana , kuma ka gafarta mana  kuma ka yi jinkai  a gare mu kai  ne Majibincinmu sabo da haka ka taimake mu akan mutanennan kafurai).

Misalin tawaga biyu kamar makaho da kurma   da mai gani da mai ji shin za su yi daidai ase ba za ku wa'azantu  ba (Godiya ta tabbata ga Allah sai dai mafiya yawan su ba su sani ba ..

 

 

   HUDUBA TA BIYU

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah kamar yanda ya dace da girman  fuskanSa  da kasaitan ikon sa  kuma  godiya na sa ne kamar yanda ya dace  da  yalwan afuwar sa  da kayun kayutatawanSa kuma kyakkyawan yabo na shi ne kamar yanda ya dace da girman rahamar sa da yalwan gafararSa.

Yana da godiya na har abada , godiyan da  adadi bai iyakance shi ,  kuma har abda ba zai katse shi ba , kamar yanda ya dace da a gode mi shi.

 Dukkan godiya na shi ne bisa ga ni'imomi  wanda ba sa kidanyuwa da da falalolin da  ba sa iyakantuwa , da kuma hukuncin da ba a maidawa , godiya na  shi ne bisa ga  rahamarsa wacce ta yalwaci dukkan komai na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah majibincin salihai, na shaida kuma shugabanmu Muhammadu bawan sa ne kumsa Manzon sa ne  shugaban masu takawa

(Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku kasance tare da masu gaskiya ) ku tuna ni'imomin Allah  kuma ku tuna ranakun Allah  ku kiyaye ni'imomin ; ta hanyan da'a  wa Allah , kuma ku nemi karin su ta hanyan godewa Allah , ku dauki izina a cikin halittun Allah da kuma abin da aka nuna muku na daga ayoyin Allah , ba abin da ya fi zama wa'azi a gare ku kamar maganan Allah .

Allah yana cewa:- Ka ce: « Godiya ta tabbata ga A1lah, kuma aminci ya tabbata bisa ga bãyinSa, waɗanda Ya zãɓa. » Shin Allah ne Mafi alhẽri koabin da suke yin shirki da Shi?
60. Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu sha'awa, ba ya kasancẽwa gare ku, ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin bautãwa tãre da Allah? Ã'a, sũ mutãne ne suna daidaitãwa ( Allah da wani ) .
61. Kõ kuwa wãne ne Ya sanya ƙasa tabbatacciya, kuma Ya sanya kõguna a tsakãninta kuma Ya sanya mata manyan duwãtsu tabatattu, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãnin tẽkuna biyu? Shin akwai wani abin bautãwa tãre da Allah. Ã'a, mafi yawansu ba su sanĩ ba.
62. Kõ wãne ne yake karɓã , kuma ya sanya ku mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni.
63. Kõ wãne ne yake shiryarwa a cikin duffan ƙasa da tẽku,kuma wãne ne Yake aikõwar iskõki dõmin bãyar da bushãra a gaba ga rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? tsarki yã tabbata ga Allah daga barin abin da suke shirki da Shi.

64. Kõ wãne ne yake fã ra halitta sa'an nan kuma ya mayar da ita,kuma Wãne ne Ya azurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? Ka ce: « Ku kãwo dalĩlinku idan kun kasance mãsu gaskiya. »
65. Ka ce: « Bãbu wanda ya san gaibi a cikin sammai da ƙasa fãce Allah. Kuma bã su sansancẽwar a yaushe ne zã a tãyar da su. »
66. Ã'a, saninsu ya kai a cikin Lãhira Ã'a, sunã cikin shakka daga gare ta. Ã'a, sũ da gare ta makãfin zũci ne.
67. Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: « Shin idan mun kasance turɓaya, mu da ubanninmu, shin, haƙĩƙa, waɗanda ake fitarwa ne? »
68. « Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana wa'adi ga wannan, mũ da ubanninmu, daga gabãnin haka. Wannan bã kõme ba ne fãce tãtsũniyõyin farko. »
69. Ka ce: « Ku yi tafiya a cikin ƙasa, sa'an nan ku dũba, yãya ãƙibar mãsu laifi take? »
70. Kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma kada ka kasance a cikin ƙuncin rai daga abin da suke ƙullãwa na mãkirci.
71. Kuma sunã cẽwa, « A yaushe wannan wa'adi ( zai auku ) , idan kun kasance mãsu gaskiya? »
72. Ka ce: « Akwai fatan sãshen abin da kuke, nẽman gaggãwarsa, ya kasance yã kuturta ( 1 ) a gare ku. »
73. Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa Mai falala ne a kan mutãne kuma amma mafi yawansu, bã su gõdẽwa.
74. Kuma lalle Ubangijinka, haƙĩƙa Yanã sanin abin da ƙirãzansu suke, ɓõyẽwa, da abin da suke hayyanãwa.
75. Kuma bãbu wata ( mas'ala ) mai bõyuwa, a cikin sama da ƙasa fãce tanã a cikin littafi bayyananne.
76. Lalle ne wannan Alƙur'ãni ( 2 ) yanã gaya wa Banĩ Isrãĩla mafi yawan abin da sũ suke sãɓa wa jũnansu a ciki.

77. Kuma lalle shi haƙĩƙa shiriya ce da rahama ga mũminai.
78. « Lalle Ubangijinka Yanã yin hukunci a tsakãninsu da hukuncinsa, kuma Shi ne Mabuwãyi, Masani. »
79. Sabõda haka, ka dõgara ga Allah, lalle ne, kai ne a kan gaskiya bayyananniya.
80. Lalle ne kai, bã ka jiyar da matattu, kuma bã ka sa kurãme su ji kiranka, idan sun jũya sunã mãsu bãyar da bãya.
81. Kuma kai ba ka zama mai shiryar da ɗimammu daga ɓata ba. Bã ka jiyarwa fãce wanda yake yin ĩmãni da ãyõyinMu. To, sũ ne mãsu sallamãwa ( al'amari zuwa ga Allah ) .
82. Kuma idan magana ta auku a kansu, Munã fitar musu da wata dabba ( 1 ) daga ƙasa, tanã yi musu magana, cẽwa « Lalle mutãne sun kasance game da ayoyinMu, ba su yin ĩmãnin yaƙĩni. »
83. Kuma a rãnar da Muke tãrãwa daga kõwace al'umma, wata ƙungiya daga waɗanda suke ƙaryata ãyõyinMu, sai ga su anã kangesu. ( ga kõra )
84. Har idan sun zo, ( Allah ) zai ce, « Ashe kun ƙaryata ãyõyinNa, kuma ba ku kẽwaye su da sani ba? To, mẽne ne kuka kasance kunã aikatãwa? »
85. Kuma magana ta auku a kansu, sabõda zãluncin da suka yi. To, sũ bã su da ta cẽwa.
86. Shin, ba su gani ba, cẽwa, lalle Mũ, Mun sanya dare dõmin su natsu a cikinsa, kuma da yini mai sanya gani? Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi! Dõmin mutãne waɗanda suka yi ĩmãni.
87. Kuma da rãnar ( 2 ) da ake hũsa a cikin ƙaho, sai wandayake a cikin sammai da waɗanda suke a cikin ƙasa su firgita, fãce wanda Allah Ya so, kuma dukansu, su je Masa sunã ƙasƙantattu.
88. Kuma kanã ganin duwãtsu, kanã zaton su sandararru, alhãli kuwa sũ sunã shũɗẽwa shũɗewar girgije, bisa sanã'ar Allah wanda Ya kyautata kõwane abu. Lalle Shi, Mai lãbartãwa ne game da abin da kuke aikatãwa.

89. Wanda ya zo da kyakkyawan aiki guda, to, yanã da mafi alhẽri daga gare shi. Kuma sũ daga wata firgita, ( 1 ) a yinin nan, amintattu ne.
90. Kuma wanda ya zo da mugun aiki, to, an kife fuskõkinsu a cikin wuta. Ko zã a sãka muku fãce da abin da kuka kasance kũnã aikatãwa?
91. ( Ka ce ) : « An umurce ni, in bauta wa Ubangijin wannan Gari, ( 2 ) Wanda Ya mayar da shi Hurumi, kuma Yanã da dukan kõme. Kuma an umurce ni da in kasance daga mãsu sallamãwa. »
92. « Kuma inã karanta Alƙur'ãni. » To, wanda ya shiryu, yã shiryu ne dõmin kansa kawai. Kuma wanda ya ɓãce, to, ka ce: « Ni daga mãsu gargaɗi kawai nake. »
93. Kuma ka ce: « Gõdiya ta tabbata ga Allah. Zai nũna muku ãyõyinSa, har ku sansu. » Kuma Ubangijinka bai zama Mai shagala daga barin abin da kuke aikatãwa ba.


Sunan Allah "Al-Hakim" Mai Hikima

اسم المترجم : أمين سعد عبد الله

اللغة  : الهوسا

التاريخ : 13/10/1441هـ

 

 

Hudubar Masllacin Annabi na SheikhAbdulmuhsin Bin Muhammad Alkasim 13-10-1441AH / 5-6-2020 AH

Hudubar farko

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode maSa kuma muna neman taimakonSa

Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu  da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya,kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.

Bayan haka, ku ji tsoron Allah -ya ku bayin Allah-cancancin tsoronSa ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci

Ya ku musulmai

Fidira ta shaida duniya na da Ubangiji Mai kamala a zatinSa da sifofinSa, yana siffantuwa da dukkan sifa ta kamala mafi kamalarta da mafi girmanta da gayarta, dukkan yabo da godiya da kyautata ambato na shi ne, na daga cikin girmama Allah tabbatar masa da siffofinSa ta kamala da daukaka.

Sunan Allah "Al-Hakim" yazo cikin littafin Allah sama da gurare casa'in (90).

Allah Mai hikima ne yana sanya abubuwa bigirin su yana saukar da su a wurarensu da ya dace da su a cikin halitta da umarninSa yana da cikakken hikima wacce ke hade da daukaka Mabuwaya da ilimi da gwanancewa da kuma yalwa da kuma tuba da godiya, hikimarSa ta kai kololuwa da ta gagari hankula iyakancewa a hakikaninta harsuna sun kasa furta hakikaninta bayani game da ita , da hikimarSa ne ( Abin da ke cikin sammai da kasa suka yi tasbihi zuwa ga Allah).

Tsarki ya tabbata a gare Shi Mai hikima ne abin bauta a sama da kasa (Lallai shi ne abin bautawa a sama kuma Shi ne abin bautawa a kasa yana da hikima kuma Masani ne) ya godewa kansa da kansa saboda shi Mai hikima ne (Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ke cikin sammai da abin da ke cikin kasa duka nashi ne kuma yana da yabo a lahira kuma Shi Mai hikima ne Gwani) Allah ya yabi kanshi tsarki ya tabbata gare Shi lallai cewa yana da girmame - girmame kuma ya cikamake ayar da cewa Shi Mai hikima ne  (Yana da girmame - girmame a cikin sammai da kasa kuma shi Mabuwayi ne Mai hikima) kuma yana da rundunoni a sama da kasa yana gudanar da su kaman yanda ya so shi Mai hikima (Allah na da rundunan sammai da kasa kuma Allah ya kasance Masani ne kuma Mai hikima) ya kirayi Musa Alaihissalam ya sanar da shi da zatinSa cewa shi Mai hikima ne  (Ya musa lalle ne Ni Mabuwayi ne kuma Mai hikima).

Ya kyautata yabo ga littafinSa cewa lallai ya zo ne daga wurinUbangiji Mai hikima yana sanya ko wani abu a bigiren Shi kuma ya saukar da shi a wurin shi matsayin shi sai ya kasance littafi ne gamamme da ya kunshi cikakkiyar hikima Allah subhanahu wa ta'ala ya ce :(Littafi ne da an kyautata ayoyinsa kuma aka yi bayanin shi daki daki daga wurin Mai hikima Mai labartawa) da hikimanSa subhanahu ya bude arziki ga mutane kuma ya ke rike ta (Ba wani abin da Allah ya ke budewa mutane na arziki na rahama ko kuma ya rike face da abin da Allah ke bude wa mutane na rahama ba mai rike haka nan kuma abin da ya ke rikewa ba mai turo ta bayan Shi  lallai Shi Mabuwayi ne mai hikima) , Mala'iku suna matsayi na yarda da gazawa da kuma kasawa a ilimi sun tabbatar da ilimin Allah suka mika wuya ga al'amarinSa (sai suka ce tsarki ya tabbata a gare Ka ba mu da ilimi sai abin da ka ilmantar da mu lallai kai din nan Masani ne kuma Mai hikima) masu daukan al'arshi da wanda ke kewayenta suna adu'a wa musulmai da gafara da shiga gidajen aljannah kuma da cikamake addu'ansu cewa lallai shi din nan da sunan shi  tsarkakakke kuma Mai hikima  (Ya Ubangijinmu ka shigar da su gidajen Aljanna na adn wanda ka yi alkawarin shi gare su kuma ka gyara daga cikin iyayen su da matayen su da kuma zuri'an su lallai kai din nan Mabuwayi ne Mai hikima) .

Allah ya ce ga dukkan Manzannai cewa wahayin da ya ke saukarwa daga gun Shi ne Mai hikima (Haka nan ne ya ke wahayi zuwa gareka da wadanda su ke kafun kai Allah Mabuwayi Mai hikima) Annabawa amincin Allah su tabbata a gare su sun kasance suna rokon Allah ne wurin tabbatar da fatan su da kuma burace - buracen su da sunan Shi tsarki ya tabbata a gare Shi Mai hikima , Ibrahim Alaihissalatu wassalam ya roki Ubangijinsa da sunan Shi Mai hikima da ya turo zuwa gare mu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Ya Ubangiji ka turo a cikinsu manzo wanda ya ke karanta a gare su ayoyinKa kuma yana sanar da su littafi kuma da hikima yana tsarkake su, lallai kai din nan Mabuwayi ne Mai hikima) Ibrahim amincin Allah su tabbata a gare shi ya zo garin shi ya yi hijira zuwa ga Allah sai ya ce lallai Allah Mai hikima ne (sai ya ce lallai ni zan kaura zuwa Ubangijina kuma lallai shi din nan shi ne Mabuwayi Mai hikima), zamani ya tsawaita ga Ibrahim amincin Allah su tabbata a gare shi bai haihu ba ba a haifa mishi ba, sai mala'iku suka yi wa matarsa  albishir da wani da wanda  a halin ita tana tsohuwa kuma bakarariya, sai ta yi mamakin haka sai mala'iku suka ce da ita lallai Allah Masani ne Mai hikima (sai suka ce haka nan ne Ubangijinki ya ce domin lalle Shi Mai hikima ne kuma Masani) Yakubu alaihissalatu wassalam tare da hakurin shi da sauraron yaye bakin ciki sakamakon rasa yusuf da ya yi da dan uwan shi ya tabbatar da ilimin Allah a cikin zaben zamani da ya dace saboda abin da ya ke fata a gare shi na yaye bakin ciki ya sakankance da hikimar Allah wurin shirya sabuba na yaye bakin ciki sai ya fiskanci Allah da sunan shi Mai hikima tare da fatan shi da addu'a (To hakuri  abu ne  mai kyau ya wuci Allah ya  kawo mini su gaba daya lallai  shi din nan Masani ne Mai hikima) bayan yayewan bakin ciki daga Yusuf alaihissalatu wassalam da tsawon musibu da wahalhalu wanda ya hadu da su ya tuna ni'imomin Allah da falalanSa sai ya tabbatar da su tare da tabbatar da ni'iman Allah a hakan sai ya ke cewa (Hakika ya kyautata mini tunda ya fitar da ni daga kurkuku ya zo mini da ku daga kauye bayan shaidan ya shiga tsakani na da 'yan uwana lallah Ubangijina Mai ludufi ne ga abin da ya so kuma lallai Shi Masani ne Mai hikima).

Kuma sunan Shi Subhanahu Mai hikima ya kumshi hikimomi a halittanSa da umarninSa wurin iradarSa ta adiini da kuma ta duniya , Ibnul kayyim Allah ya mishi rahama ya ke cewa tare da izza kamalar kudurarSa da hikima kuma kamalar iliminSa wadan nan siffofi biyu Allah kan hukunta abin da ya so  kuma ya umarnin abin da ya so ya yi hanin abin da ya so kuma ya kyautata yabo kuma ya bi kadu wadan nan siffofi ne da su ke masdarin su shi ne halitta da umarni.

Da hikimansa ne Allah subhanahu wa ta'ala ya halicci halittu gaba daya da tsari mafi kyau ya jera su mafi kamalan jerawa ya kyautata gudanar da su ya kyautata kaddara su ya bawa ko wani mahaluki halittarsa da ta dace da shi ta dace da shi (Ya bawa kowa halittar da ta dace da shi san nan ya shiryar) Allah ya kalubalanci halittu cewa su kawo ko da halitta daya ne wanda akwai tawaya cikin halittarSa, Allah ya kalubalanci da su samar da cikin halittanSa guda daya wanda akwai rashi daidaitu (ka sake dubawa da gani shin za ka ga akwai wani abu na tsagewa?) Da a ce hankulan halittu gaba daya za su hadu domin su bada shawara ga misalin halittan Mai rahama ko kuma abin da ke kusantan shi ko kuma abin da ke kusa da shi ko kuma abin da Allah ya sanya cikin halittan Sa abubuwa na rayayyu na daga kyau da kuma tsari da kyautatawa ba za su iya ba saboda haka Allah ya umarci halittu da su wadatu da ta'ammuli da lura cikin abin da Allah ya halitta Mai hikima cikin halittunSa tare da tsinkayan bisa wasu abin da ke ciki na daga kyau da kyautatawa (ka yi dubi me ke cikin sammai da kasa) da hikimarSa ne Subhanahu ya samar da bayinSa da zatinSa tsarkakakka da kuma mika wuya da umarninSa da haninSa, ya saukar da littafinSa kuma yana so da ya karbi tuban mu kuma ba gyaruwa game da al'amuran duniya sai da addini haka nan kuma wasu magabata suke cewa (Ba don a cikin umarninSa da shari'ansa ba sai wannan hikima mai girma wanda ita ce tushe na alheru da kuma kamalan zatinSa da hakan ya kasance abu ne cikakke kuma mai waraka).

Shi ne wanda tsarki ya tabbata a gare Shi Mai hikima cikin  umarninSa a cikin duniya  wanda ya ke jarabta bayinSa da shi domin ya gyara su  ya daga darajar su ba wani abu da bawa zai kasance yana da shi na zabi kaman nufin rashin lafiya da tawayan arziki kawai abin da zai yi to ya yi imani ne kuma ya yarda  kuma ya riki abubuwa na sababi wanda aka  shar'anta da kuma abubuwan da suke na halal sai ya tunkude kaddaran Allah da abin da ke gudana wa bawa ba tare da zabin shi ba wanda ba yi da karfi wurin tunkude shi sai ya yarda kuma ya mika wuya ya shaida izzan Allah ne a cikin hukuncinSa da kuma a'adalcinSa da kuma abin da ya hukunta.

HikimanSa na gudana a gare Shi kuma lallai duk abin da ya same shi bai kasance da ya kuskure shi ba abin da kuma ya kuskure shi bai kasance da ya same shi ba lallai hakan ke wajabta masa a'adalcin Allah da hikimanSa lallai Allah Mabuwayi hakika ya bayyana wasu hikimomi ga bayinSa sai ya bada labari cewa saukar da littafi da ya ke yi don tabbatar da mumunai ne ya shiryar da su kuma da yin albishir a gare su (ka ce ruhi mai tsarki ya sauka da shi daga Ubangijinka (Mala'ika Jibril) da gaskiya domin ya tabbatar da wadanda suka yi imani kuma da shiriya ne da albishir ga musulmai) ya tura manzanni domin kada wani ya zama yana da hujjar cewa shi ya jahilci addini (Manzanni ne masu albishir kuma da gargadi domin kada ya zamana mutane suna da hujja a kan Allah bayan zuwan manzanni ) Hakika kuma Allah ya jarabci mutane yana kuma yi musu ibtila'i kuma zai sake yi musu ibtila'i  domin ya duba ya ga gaskiyan ta'allukin su da Shi Allah(Wai mutane suna zaton za su ce sun yi imani ne a kyale su a halin kuma ba a'a jarraba su) Allah ya shamake ilimin gaibi ga bayinSa sai ya kebantar da shi ga kansa saboda hikima , (Masanin gaibi abin da ya faku da kuma shahada Shi Mai hikima ne kuma Gwani).

Bayan haka ya ku musulmai:

Lallai Allah Shi kadan shi halitta da umarni na Shi ne yana aikata abin da ya so a cikin duniyarSa, a cikin shari'arSa yana hukunta abin da ya ke so abin da ya nufa , ba a fiskantar da tambaya gare shi, ba a suka cikin hikimanSa da wata magana (Ba a'a tambaya don me ya ke aikatawa amma su (halittu) ana tambayan su )

Musulmi yana bautawa Allah ne da abin da sunan Alhakimu ya kumsa na ma'ana, idan bawa ya sakankance da hikimar Allah sai ya ji dadi da halittan Allah wanda ya ke Albadi'u da aikin Shi wanda akwai kyautatawa a ciki da kwarewa da kuma girmama shari'an Allah ya ji tsoron shi Allah Madaukaki, ya ji kunya daga  saba mishi ko ya ji kunya daga kurakuran shi, ya mika wuya ga umarnin shi da hanin shi ya tsananta farin ciki da cewa Allah ya shiryar da shi zuwa ga wannan addini saboda hikimanSa da ya nufa da ita game da shi kuma lallai shari'a daga mai hikima ne ta zo domin ya sanya dan adam cikin walwala ko da bala'i ya sauka a gare shi sai ya yarda da abin da Allah ya hukunta ya kaddara masa ya mika wsuya cewa hakan Allah ya hukunta a gare shi cikin gyara da kuma alheri (Ya wuci ku tsani wani abu kuma sai ya zamana alheri a gare ku) kuma ya sakankance cewa bayan hakan akwai hikima  da bai santa ba  kuma lallai yana  kai komo cikin ni'iman Allah ne a halin yalwa kuma da halin cuta , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ke cewa: (Mamaki da ala'amarin mumini, lallai dukkan ala'amarin shi alheri ne a gare shi hakan baya kasancewa ga wani sai ga mumini idan alheri ya same shi sai ya yi godiya sai hakan ya zama alheri a gare shi idan kuma cuta ta same shi sai ya yi hakuri hakan sai ya zama alheri a gare shi) Muslim ne ya rawaito.

Ina neman tsarin Allah diga sharrin shaidan abin jefewa.

(Yana gudanar da ala'amura ba wani mai ceto face bayan izinin Shi wancannin ku Shi ne Allah Ubangijin ku, ku bauta miShi, ba za ku yi tunani ba ?) Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin Alkur'ani mai girma.

 

Huduba ta biyu:

  Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawanSa, godiya a gare Shi bisa datarwanSa da kuma baiwanSa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya ina mai girmama sha'aninSa na shaida Annabin mu Muhammad bawanSa ne kuma Manzon Sa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacce mai kari.

Ya ku musulmai:

Allah ya gina al'amuran bayinSa da ya sanar da su wasu ma'anoni  na dalilin halittansu  da umarninSa ba tare da zurfafawa cikin su ba da kuma bayanin su daya bayan daya ba, wan nan abu ne da ke faruwa a cikin ala'amura a tushensu da kuma rassansu abin da ba ya boyuwa ga bayi wasu ma'nonin na hikimanSa cikin abin da ya kirkira haka nan kuma da umarninSa da shari'anSa da kuma abin da ke kasancewa a duniya na kaddara ya ishesu cikin saninSa ta fiska na gaba daya abin da ya kumsa na hikima  da ya kai kololuwa su fahimci hakikanin bayaninSa daki daki ba ko hikimansa daki daki ba daya bayan daya hakan kuma yana daga cikin ilimin gaibi ne wanda Allah ya barwa kanSa shi .

 sannan ku sani lallai Allah ya umarce ku da salati da aminci ga AnnabinSa sai ya ce: a cikin littafinSa mafi hikima da ya saukar (Ya ku wadanda suka yi imani lallai Allah da mala'ikunSa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce mai yawa).