الجمعة، 19 أبريل 2019

watan sha'aban shiri ne don ramadan


Tarjamar Hudubar Masllacin Annabi Na shaikh Abdullah bin Abdurrahman Albuaijan 14-8-1440AH/19/4/2019AD

Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya halicci sammai da kasa, ya sanya duhu da haske, mai sauya ranaku da watanni, mai karar da shekaru da zamuna.
Ina gode masa ga dukkan al'amura,muddin iskar gabas da ta yamma na kadawa.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, bisa gaskiya da yakini. Ina adana ta ga Allah  ranar da rai bai mallaki wani abu ba ga wani rai, kuma al'amari a wannan rana na Allah ne.
Kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne, ya isar da sako ya sauke.amana, ya yi jahadi a tafarkin Allah har yakini ya zo mishi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi baki daya.
Bayan haka !Lalle Alkur'ani shine zance da magana mafi kyau,Addini a gurin Allah shine musulunci,Mafi alherin shiriya shine koyarwar Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,(Ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijinku ku tsoraci wata rana da mahaifi ba zai fanshi danSa ba, ko shi da ya fanshi mahaifinSa da wani abu, lalle alkawarin Allah gaskiya ne kada rayuwar duniya ta rude ku, kada wani mai rudi game da Allah ya rude ku.)
     Ya Ku jama'ar musulmi!
Lalle Allah ya sanya lokuta tamkar wata ma'adana ce ga aiki, (To duk wanda ya yi wani aiki da ya kai kwayar zarra na alheri zai gan shi. To duk wanda ya yi wani aiki da ya kai kwayar zarra na sharri zai gan shi)
Wanda ya yi hasara shi ne wanda ya hasarar da lokuta mafi alheri, mahrumi shine wanda aka hana shi ribatar lokutan da'a, hakika Allah ya sanya zamani ya zama hanya ne ga muminai zuwa ga biyayya ga Ubangijinsu, hasara ce ga wasu mutane da zai zama gafala ne ga kawunan su, to ku raya kawunanku,ta hanyar yin biyayya ga Allah, domin zukata na rayuwa ne da ambaton Allah (Abin da ku ka gabatar na alheri don kawunanku zaku same shi a gurin Allah).
Ya ku bayin Allah!
Lalle zamani na da fifiko kan sashi bisa ranaku ko watanni ko sa'oi, mafi alherin abin da mutum zai raya shekarunsa da shi ya raya lokacinsa sune ayyuka masu falala da abin da zai kusanto da kai ga ubangiji, da aikata ayyukan alheri da da'a, Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma shine wanda ya sanya dare da yini akan mayewa ga wanda ya ke son ya yi tunani ko kuwa ya yi nufin ya gode,)
Ku saurara! Lalle kuna cikin wata mai girma wanda da yawa daga cikin mutane na gafala daga shi tir da gafala kason wadanda aka hana alheri,kayan hajan lalatatu,
Ku saurara! Lalle kuna cikin wata mai girma da ake daga ayyuka a cikinsa zuwa ga Ubangijin talikai, to ku cike karshensa da tuba, da ayyuka na kwarai,ko Allah zai bamu kyakkyawan karshe,
Ku saurara! Lalle kuna cikin wata mai girma da manzon Allah ke kokarin yin azumi a cikin shi.
An karbo daga Usama dan Zaid yace da Manzon Allah tsira amincin Allah su tabbata a gare shi, ban ga kana yawaita azumi a wani wata ba kamar yadda naga ka ke yawaita wa a wannan watan na sha'abana ba, sai yace :( Ai wannan wata ne da mutane ke gafala daga shi yana tsakanin rajab da ramadan kuma wata ne da ake daga ayyuka zuwa ga Ubangijin talikai to sai na so a daga ayyuka na ina mai azumi.
An karbo daga Aisha Allah kara yarda agare ta tace : Manzon Allah ya kasance yana azumi har muce ba zai sha ba, wani sa'i kuma yana sha har muce ba zai yi azumi ba,ban taba ganin manzon Allah ya cika wani wata  yana azumi ba sai ramadan ba watan da naga yana yawaita azumi acikin shi kamar  sha'aban,)Muslim ne ya rawaito
An karbo daga gare ta ta ce: ya kasance mafi soyuwan watanni a gurin manzon Allah da ya azumce shi shine sha'aban) Abu Dawuda ne ya rawaito shi a sunan nashi kuma Albani ya inganta shi.
Ya Ku jama'ar musulmi!
Lalle a daren  tsakiyan sha'aban Allah na da gafara da take game muminai amma ana haramtawa masu gaba da kiyayya da kullin juna da kafurai, An karbo daga Abu Musa Al'ash'ari Allah ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: (Lalle Allah na tsinkaya a tsakiyar daren sha'aban sai ya gafartawa dukkan halittun shi banda mushriki ko mai gaba da wani,)Ibnu Majah ne ya rawaito da waninsa,Ibnu Hibban da Albani sun inganta shi    
 Ku yafe ku yi rangwame  ku dauke kai ku tausayawa juna, ku yi afuwa, ku sada zumunci, kar ku yi hasada, kar ku yi munajasha, kar ku yi kiyayya kar ku juyawa juna baya, ku zama bayin Allah  'yan uwan juna.
 An karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: (Lalle ana bude kofofin Aljanna ranar litini da ranar Alhamis, sai a gafartawa dukkan bawan da bai hada Allah da wani face mutumin da akwai kiyayya da dan'uwan shi, sai ace : ku dakanci wadannan biyun har sai sun yi sulhu! ku dakanci wadannan biyun har sai sun yi sulhu! ku dakanci wadannan biyun har sai sun yi sulhu!) Muslim ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah!
Sha'aban sha gaban daya daga cikin rukunnen musulunci ne, shine Azumin watan ramadan da aka saukar da Alkur'ani a cikinsa.
To shi fage ne na sabo da koyo, da kimtsawa da shiryawa, da shigowan watan imani don fiskantar watan ramadan,
Sha'aban da ramadan kamar sunnoni ne na ratibi  ga sallolin farillah. Shi kamar wani gwaji ne don sabo da watan ramadan don rage wahalansa da nauyin sa da dandana zakin azumi da dadinsa sai mutum ya shiga azumin ramadana da kuzarinsa da karsashinsa.
 Ya Ku jama'ar musulmi!
Duk wanda akwai biyan azumin watan ramadana da ya gabata a kansa to ya gaggauta azumtarsa kafin shigowan watan ramadan, don jinkiri game da haka zai iya zama sababi daga cikin sabuba na sakaci,
An karbo daga Aisha Allah kara yarda a gare ta tace : Azumi na kasancewa a kai na ba na samun daman biyansa har sai sha'aban sabo da matsayin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,)
To ku gaggauta ayyukan alheri –Allah ya muku rahama- kafin ajali ya zo, (ku gaggauta  zuwa ga gafara daga Ubangijinku, da Aljanna wanda fadinta ya kai sammai da kasa an tanade shi ga masu takawa.)

 Huduba ta biyu.
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah bisa kyautatawarsa godiya ta tabbata a gare shi bisa datarwarsa  da baiwarsa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, ina mai girmama shaninsa,na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzon sa ne, mai kira zuwa ga neman yardarsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.
Ya ku musulmai!
Lalle Allah madaukakin sarki, ya farlanta azumin watan ramadan a wannan wata, wato ina nufin  sha'aban  a shekara ta uku bayan hijira: Manzon Allah ya yi azumi
Ramadan sau tara, sannan ya koma ga Ubangijinsa.
 Allah madaukakin sarki yace; (Ya ku wadanda suka yi imani An wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta shi ga wadanda suka gabace ku ko zaku ji tsoron Alla)
. Ranaku ne kididdigaggu to duk wanda ya ke maralafiya a cikinku ko yana matafiyi to gwargwadon abin da ya sha na daga kwanaki a wadansu kwanaki yana kansa. Fidiya yana kan wadanda ke da ikon yin azumi tare da wahala ita ce abincin miskinai, duk wanda ya yi tadauwa'i na alheri to ya fi alheri a gare shi, ku yi azumi shi ya fi amfani a gare ku, in kun kasance kun san hakan yafi ( watan ramadan shine wanda aka sauke Alkur'ani a cikinsa mai shiryar da mutane daga bata, ayoyi na shiriya mabayyana da rarrabewa tsakanin karya da gaskiya. Duka wanda ya ga wata daga cikin ku to ya azumce shi, wanda ya kasance mara lafiya ko a kan tafiya to gwargwadon abin da ya sha na kansa na wasu kwanaki, Allah na nufin sauki gare ku bai nufin tsanani gare ku, sabo da ku cika adadin kuma ku girmama Allah bisa shiryarwar da ya muku kuma don ku gode masa bisa wannan ni'ima,)
An karbo daga Abdullahi dan umar Allah ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: (Lalle An gina musulunci akan  abubuwa biyar :Bisa a bautawa Allah a kafurcewa waninsa, ya tsaida salla ya bada zakka da hajji dakin Allah da azumin ramadan )Muslim ne ya rawaito.
An karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: (wanda ya yi azumin ramadana yana mai imani da neman lada zaa gafarta masa abin da ya gabata na daga zunubansa kuma wanda ya yi tsayuwan dare na ramadan bisa imani da neman lada to zaa gafarta mishi dukkan abin da ya gabata na daga zunubansa) Bukhari ne ya rawaito
 Ya ku bayin Allah!
Ba abin da ya rage a wannan wata sai ranaku kididdigaggu, to ya dace ga musulmai da su shirya wa wannan wata,da su kimtsa masa, kuma su yi gaggawa  su yi tsere da rigegeniya bisa biyayya ga Allah . to sam barka ga wanda ya riski ramadan,barka da duk wanda aka datar da shi zuwa ga alheri da ayyukan kwarai, ya mai neman alheri ka fiskanto ya mai neman sharri ka gajarta,
To ku nuna wa Allah alheri daga kawunanku, don matsiyaci shine wanda aka haramta mishi biyayya  ga ubangijinsa, kuma lokutan alheri suka tsere mishi bai fadaku ba. Ya yiwa kansa barna har mutuwa ta shammace shi bai tuba daga zunubansa ba.  


   


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق