HUDUBAR FARKO :
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin
sarki, muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa , kuma
muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk
wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma
babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi
kadai yake bai da abokin tarayya,
Wanzuwa da kyakkyawan yabo nasa ne, Kaddartawa da hukuntawa na hanunsa,
shi ke gudanar da al'amura daga kasa zuwa sama, yana aikata abin da ya so, ba
za ku samu damar ku so abu ba sai idan Allah ya nufa.
kuma na shaida Annabi Muhammadu
bawanSa ne kuma ManzonSa ne, ya isar da sako ya bada amana, yayi nasiha ga
al'uma, ya yi jihadi a tafarkin Allah cancancin jihadi har yakini ya zo masa
(Mutuwa) tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da
sahabbansa baki daya.
Bayan haka :
Lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi alherin shiryarwa shine shiryarwar
Annabi Muhammad, kuma mafi sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan bidiah
bata ne kuma dukkan bata na wuta,
Ya ku bayin Allah ina muku wasiyya
da ni kai na da ku ji tsoron Allah, shine wasiyar Allah ga mutanen farko da na
karshe, Allah Madaukakin sarki ya ce :(, haƙĩƙa, Mun yi wasiyya ga waɗanda aka bai wa
Littãfi a gabãninku, da kũ, cewa ku bi Allah da taƙawa,)
Allah
Madaukakin sarki ya ce :
( Ya ku mutãne! Ku bi
Ubangijinku da taƙawa Wanda Ya halitta ku daga rai guda, kuma Ya halitta, daga
gare shi, matarsa, kuma Ya watsa daga gare su maza mãsu yawa da mãtã. Kuma ku
bi Allah da taƙawa Wanda kuke rõƙon jũna da (sũnan), shi, da kuma
zumunta . Lalle ne Allah Ya kasance, a kanku, Mai tsaro ne).
Ya ku jama'ar
musulmi!
Hakika Allah ya
yalwata mana ni'imomi da ba zasu kididdigu ba,kuma ya bude mana kofofin kyautarsa gare mu, kyautar da ba za ta kirgu
ba, ya girmama mu da aminci da yalwa,da kwanciyar hankali da wadata, ya yi nesa
da mu daga fitintinu da bala'i da musibu na tsautsayi da hasara, da falalar
Allah tare da rikon mu da akidarmu da kokarin jagororinmu da malamanmu, Allah
madaukakin sarki ya ce : ( Ku tuna a lõkacin da kuke kaɗan, waɗanda ake
raunanarwã a cikin ƙasa kunã tsõron mutãne su cafe ku, sai Ya tattara ku (a
wurin natsuwa, Maɗina), kuma Ya ƙarfafã ku da taimakonSa kuma Ya azurtã ku daga
abũbuwa mãsu dãɗi; Tsammãninku, kunã gõdewa).
Zaman
lafiya na daya daga cikin abubuwan da ke mikar da rayuwan mutum, da shi ake samun
kwanciyar hankali da natsuwa,
Zaman
lafiya na daga cikin hadafin da kowace al'uma ke nema.kuma ta yi amfani da duk
wata hanya ko karfi da take da sh,
Zaman
lafiya ni'ima ce da ba wanda ya san kimanta da girman muhimmancinta face wanda
ya konu da wutan rashinta,
Zaman lafiya ni'ima ce da rayuwa bai
dadi in babu ita,haka ba natsuwa da tabbatuwa guri guda in an rasa ta, Manzo Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya wayi gari cikin aminci
a gidansa da lafiya a jikinsa, yana da abincin wuninsa to tamkar an tattara
masa duniya ne)
Lalle
amincin rai da mutunci da dukiya na daga cikin mafi girman ni'imomi,duk dan adam na
bukatarsa, a dukkan zamani da wuri,don ya samu hutu da natsuwa,
Amma
idan wutan fitina ta kunnu al'amura suka rikirkice, ya tsoracewa rai da mutunci
da dukiya, kuma mutane suka farga daga tashin hankali na bala'i idanuwa suka
karkace, zukata suka isa makogoro sabo da tsoro to a nan ne mutum zai yi nadama
a lokacin da nadama ba zata yi amfani ba, sai ya yi da na sani game da sakaci
da yayi game da aminci da ni'imomi.
Ku
yi dubi da idanuwa ga wasu al'umu da
garuruwa, da sun kasance cikin alheri da nitsuwa, yayin da wutar fitina ta
kunnu a cikinsu kasa ta yi musu kunci yanayi ya sauya ba daya daga cikinsu da
ya samu kwanciyar hankali, to lalle cikin wannan akwai abin lura da waazi ga
duk wani wanda akwai kwayar zarra na imani a zuciyarsa.
Hakika
alkur'ani ya yi bayani daki daki kuma ya buga misalai mafi ban kaye:(kuma
Allah ya buga misalin wata alkarya ta kasance tana cikin aminci da natsuwa,
arzikinta na zuwa mata da yalwa daga ko ina sai ta butulcewa ni'imomin Allah
sai ya dandana musu azbar yunwa da tsoro sabo da abin da suka kasance suna
aikatawa)
Ku
dubi yanda Allah ya ni'imta wasu mutane ya kwarara musu ruwan ni'ima daga
taskarsa amma suka juya baya sai bala'i ya sauka a gare su
(Lalle hakika akwai aya ga Saba'awa a cikin mazauninsu: gonakin lambu
biyu, dama da hagu, "Ku ci daga arzikin Ubangijinku, kuma ku yi godiya
gare shi. Gari mai dadin zama, da Ubangiji Mai gafara" sai suka bijire,
sabo da haka muka saki malalin Arimi (Dam) a kan su, kuma muka musanya musu
gonakinsu biyu da wadansu gonaki biyu masu 'ya'yan ita ce kadan: talakiya da
goruba da wani abu na magarya kadan, wancan, da shi muka yi musu sakamako sabo
da kafurcinsu.kuma lallai ba mu yi wa kowa irin wannan sakamako face kafurai. . Kuma
Muka sanya, a tsakaninsu da tsakãnin garũruwan da Muka Sanya albarka a
cikinsu, waɗansu garũruwa mãsuganin jũna kuma Muka ƙaddara tafiya a cikinsu,
"Ku yi tafiya a cikinsu, darũruwa da rãnaiku, kunã amintattu." Sai suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka nĩsantar
da tsakãnin tafiyõyinmu," kuma suka zãlunci kansu, sabõda haka Muka sanya
su lãbãran hĩra kuma Muka kekkħce su kõwace, irin kekkħcewa. Lalle a cikin
wancan akwai ãyõyi ga dukan mai yawan haƙuri, mai yawan gõdiya).
. Ya Ku Jama'ar musulmai!
. Ya Ku Jama'ar musulmai!
Rudani
da hayaniya ba su sa a cinma manufa sai dai fitintinu da bala'i, ba abin da
zasu haifar face tashin- tashina da
rikici da hasara, mun gani kuru kuru abin da ya faru da wasu al'umu a da yawa
daga cikin wasu garuruwa a sakamakon hakan.rayuka da dama da basu ci ba basu
sha ba aka sarayar da su,!Dukiya adananna da yawa an lalata ta,aka keta
mutuncin masu mutunci,
jama'a da dama sun gudu, dangi da iyalai an tarwatsa su,wasu yara an maida su
marayu,an rusa gidaje.
Lalle tada fitina makauniyar kira ce da abokan gaba suka shirya
ta, wawaye da maha'inta kuma suke tallata ta, mashirmata kuma suke biye mata.
Abin da yake
wajibinmu shi ne mu yake ta, mu zama tsintsiya madaurinki daya a gaban duk
wanda ke son yayi batanci gare mu ko raba kanmu,ko ya ke barazana ga zaman
lafiyarmu,ko ya yi tawaye ga jagororinmu da shuwagabanninmu.
To ku yi riko da
addininku, ku dunkule ku hade don fiskantan abokan gabanku, ku tsayu a kan
tafarkinku.
Ku sani lalle Allah
ya wajabta muku biyayya ga jagororinku, Allah Madaukakin sarki yace : (ya ku wadanda suka
yi imani ku yi da'a ga Allah kuma ku yi da'a ga Manzon Allah, da ma'abota
jagoranci daga cikinku),
To biyayya ga
jagororinmu na daga cikin addininmu wanda shine kariya ga al'amarinmu, akwai
kuma gyara ga duniyarmu da muke rayuwa a cikinta.
An
karbo daga Irbad dan sariya Allah ya kara yarda a gare shi ya ce, Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya mana sallar asuba sai ya juyo
ya mana wani wazi mai ratsa jiki wanda zukata sun tsorata, idanuwa sun zubar da
hawaye, sai muka ce ya Manzon Allah tamkar wannan wazi ne na ban kwana, to a
mana wasiya, sai yace :(Ina muku wasiya da ku ji tsoron Allah ku ji ku bi ko da
kuwa an dora muku jagorancin bawa ne dan habasha,to duk wanda ya rayu cikinku
zai ga sabani mai yawa,to ku yi riko da sunna ta da sunnar kalifofi na shiryayyu
wadanda aka shiryar da su,ku riko ta da hakoran cin tuwonku,na hore ku da ku
nesaci fararrun abubuwa a addini don dukkan bidia bata ce)Hakim ne ya rawaito
shi a Mustadrak.
Ku roki Allah
tabbatuwa a kan addininku,ku kiyayi fitintinu, ku zama kuna tare da
jagororinku,kuna komawa zuwa ga malamanku, ku hada kai don fiskantar makiyanku
da duk wanda ke son ku samu matsala a zaman lafiyarku da hadin kanku,
Ina
neman tsarin Allah daga sharrin shaidan abin jefewa. (. Yã
kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ɗã'a ga Allah, kuma ku yi ɗã'a ga ManzonSa, da
ma'abũta al'amari daga cikinku.(3) Idan
kun yi jãyayya a cikin wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da ManzonSa
idan kun kasance kunã ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira. Wannan ne mafi alheri,
kuma mafi kyau ga fassara).
Allah sa mini
Albarka da ni da ku cikin Alkur'ani mai gairma, ya amfane ni da ku da abin da
ke ciki na ayoyi da ambato mai hikima,
Ina fadin abin da
kuke ji, ina neman gafarar Allah ni da ku da sauran musulmai daga dukkan
zunubai, to ku nemi gafararSa don shi mai gafara ne Mai jinkai.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da
godiya sun tabbata ga Allah da ya sako ni'imomi, ya tunkude azaba, ya sanya mu
al'uma mafi alheri, ya cusa imani a cikin zukatanmu, ya sanya aminci da zaman
lafiya a kasarmu, to godiya ta tabbata ga Allah a farko da karshe, hukunci
nashi ne kuma gare shi zaku koma.
Ya ku bayin Allah!
Allah ya halicci
mutane a mataki mataki, ya sanya fifiko a tsakaninsu cikin kudura da baiwa, ya
sanya malamai magada Annabawa, ya daga matsayin su da darajojin su, wannan
falala ne na Allah ya na bawa wanda ya so, ya shiryar da mutane ga komawa gare
su da koyi da su,To su ne masu rikon ilimi da bada kariya ga addini, da kiyaye mutunci, ya tabbata daga
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Adilai ne na kowane mamaya Zasu dauki wannanan ilimi, zasu kore
jirkitawan masu ketare iyaka, da cogen mabarnata, da tawilin jahilai) .
To idan fitina ta
taso, bidi'o'i suka cakuda da sunna, wawayen mutane suka tsoma baki cikin
al'amarin al'uma, gaskiya ta jirkita da bata, malami da jahili suka jirkice,
abubuwa suka rincabe,to ku riki akidarku da gaske, ku aminta da malamanku da
jagororinku, ku ji tsoron Allah akan kawunan ku da al'umarku, kar ku bi ko wani
mai ihu, ku banbance tsakanin jerin gwanon kalmomi na gaba da na baya.
(Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun haɗu da
wata ƙungiyar yãƙi, to, ku tabbata, kuma ku ambaci(2) Allah
da yawa, tsammãninku kunã cin nasara. . Kuma
ku yi ɗã'a ga Allah da ManzonSa, kuma kada ku yi jãyayya har ku raunana kuma karfinku
ya tafi, kuma ku yi haƙuri. Lalle ne Allah Yanã tãre da mãsu haƙuri.)
Ya ku matasa...
Ku
ne ruhin Al'uma kuma mahanganta , da ku ne zata rayu ta yi kyau, al'uma ta taso
a birni da kauye,daku ake karya logon
batattu da mabarnata,
To
ku kiyaye dukkan kiyayewa daga fitintinu, da kuma kai komo a cikinta da mara
mata baya, to addinin ku na da wajibi da ya hau kanku to ku bada shi,
magabatanku na da hakki a kanku to ku cika, kuma kasarku na da wajibi da ya
doru a kanku to ku kiyaye shi, ku ji tsoron Allah ku sani zaku hadu da shi.
(Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku karɓa wa
Allah, kuma ku karɓa wa Manzo, idan Ya kirãye ku zuwa ga abin da Yake rãyar da
ku; Kuma ku sani cewa Allah Yanã shãmakacewa a tsakãnin mutum da zũciyarsa,
kuma lalle ne Shĩ, a zuwa gare Shi ake tãra ku.
Kuma
ku ji tsõron fitina wadda bã ta sãmun waɗanda suka yi zãlunci daga gare ku keɓe,
kuma ku sani, lalle ne Allah Mai tsananin uƙũba ne).
Bayan haka yaku jama'ar musulmai
Musulmai gangan jiki ne guda kuma gini ne guda, ketare iyaka ga dayan su to ketare iyaka ne ga dukkaninsu, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi yace :Misalin mumini cikin kaunarsu da son junansu da tausayawa juna tamkar jiki ne idan wani gaba na ciwo sai sauran gabbai su amsa da rashin barci da zazzabi). Muslim ne ya rawaito
Musulmai gangan jiki ne guda kuma gini ne guda, ketare iyaka ga dayan su to ketare iyaka ne ga dukkaninsu, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi yace :Misalin mumini cikin kaunarsu da son junansu da tausayawa juna tamkar jiki ne idan wani gaba na ciwo sai sauran gabbai su amsa da rashin barci da zazzabi). Muslim ne ya rawaito
Lallai musibarku da musibar mu na ga abin da ya faru na yaudara da taaddancin da a ka nufi 'yan
uwanmu musulmai da zubar da jinin masallata da tsoratar da wadanda ke cikin
aminci, da keta alfarmar dakin Allah,
Kuma ba su tuhumce su ba, fãce
kawai domin sun yi ĩmãni da Allah, lalle musiba ce mai girma,babban abin
firgitarwa ne, muna neman ladanta a gurin Allah, kuma abin da ke gun Allah ya
fi alheri kuma ya fi wanzuwa.
To daga Allah muke kuma gare
shi za mu koma, Allah kyautata ta'aziyyar 'yan uwan mu, ya girmama musibarsu,
Allah ka yi gaggawan bawa marasa lafiyan cikinsu lafiya, Allah gafartawa
matattu ya daga darajojinsu cikin madaukaka,
Ya Allah ka daukaka musulunci
da musulmai
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق