الجمعة، 1 مارس 2019

BIYAN BASHI A MUSULUNCI


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Husain Al- Asshaikh 24-6-1440
Hudubar farko
Kiyaye hakkokin jama'a na daga cikin abubuwa na tushe kuma na kat da shariar musulunci ta karfafa, sawaun ta bangaren bata kariya ko kiyaye ta, na daga cikin abin da wasu mutane ke sakaci da shi akwai baiwa  masu hakki hakkokinsu musamman bashi, wanda ke kan mutum na rance,na farashin wani abu da ya saya ko rance da ya ranta, ko ladan wani dan kodago ya yi mishi aikin kodago,da makamantarsu.
To abin da ya ke wajibi ga musulmi ya yi kokarin sauke nauyin da ke kansa, ya biya abin da ke kansa na hakkin 'yan uwansa Allah Madaukakin sarki ya ce :(kada ku ci dukiyarku a tsakaninku ta hanyar barna).
Lalle abin da ya ke farilla akan kowane musulmi na dole ya bada gabadayan hakkokin halittu, cikakke ba tare da ya tawaye ba, na daga cikin bayyanannen laifi da zunubi mai girma akwai sulalewa daga biyan basuka ko gujewa masu hakkin, da kin biyan bashin da jinkirta shi sai gaba mai zuwa tare da halin biya, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(zalunci ne mawadaci ya jinkirta biyan bashi).Muslim ne ya rawaito.
Almadalu shine jinkirta biyan hakki da ya dace a biya tare da halin biya da iko, amma ya ki biya akan lokacin to ya aikata haramun ya kuma fada cikin  zalunci  ga ma'abota hakki na daga cikin halittu, karshen zalunci hasara ne kuma abin kunya ne duniya da lahira.
Ya 'yan Uwa Musulmi!
Bashi al'amarinsa babba ne, shaninsa mai girma ne a musulunci, sabo da haka ne Abu Huraira Allah kara yarda a gare shi yace zaa zo ga Annabi da mammaci wanda akwai bashi a kansa  sai ya ce :(Shin ya bar abin da zaa biya bashinsa da shi? In an bada bayanin cewa  ya bar abin biya sai ya mishi sallah,in ba haka ba sai yace : ku yi sallah ga sahibinku,) Hadisin Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
    To ya kai wanda bai damuwa da biyan bashi, bai kulawada hakkin mai hakki, ka ji tsoron Allah Ubangijinka !
Muslim ya rawaito a sahih na shi daga Abdullahi dan Amr Allah kara yarda a gare shi ya ce : (Ana gafartawa dukkan shahidi sai wanda akwai bashi a kansa)
Haka kuma a gun nasa cewa wani mutum ya zo ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi sai ya ce:ya Manzon Allah, shin yanzu in an kashe ni a tafarkin Allah zaa gafarta min dukkan zunubai na? ya ce :E a halin kana mai hakuri kana neman lada kana mai fiskanta ba mai juya baya ba, ban da bashi, dazu Jibrilu ya fada min haka.)
To ya kai Musulmi ka sauke hakkin wani da ke kanka, ka kiyaye jinkirta biyan bashin dukiyan mutane a halin kana da kuduran biyanta, to ka gaggauta kafin wucewan lokaci,sanda zai zama ba wani abu na hakkokin halittu sai daukan fansa da kyawawa ko munana, Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi sai ya ce:( Duk wanda ya ke da wani hakki akansa na zaluncin dan uwansa game da mutuncinsa ko wani abu to ya warware daga gare shi a yau kafin ya zama dinari ko dirhami, in ya lasance yana da ayyukan kwarai sai a dauka daga gare shi gwargwadon abin da ya zalunce shi, to idan bai da kyawawa sai a dauka daga laifukan sahibin nasa sai a dora mishi).
Nasa'i ya rawaito daga Muhammad dan Muhsin Allah kara yarda a gare shi ya ce"(Mun kasance zaune a gurin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai ya daga kansa zuwa sama, sai ya sanya tafin hanunsa akan goshinsa, sannan ya ce : (Tsarki ya tabbata ga Allah! Me aka saukar na tsanani? Sai sahabbai suka yi shuru suka firgita da gari ya waye sai na tambaye shi ya Manzon Allah  wani tsanani ne wanda ya sauka? Sai ya ce :  Na rantse da wanda  rai na ya ke hanun shi , da ace wani mutum   za a kashe shi a tafarkin Allah  sannan a raya shi sannan a kashe shi sannan a raya shi , sannan  a kashe shi alhali akwai bashi akan shi to da ba zai shiga Aljanna ba har sai anbiya mishi wannan bashin .)
YA DAN UWANA MUSULMI:
Ka kasance cikin himma na gaskiya wurin sauke nauyin halittu  kuma ka halarto da kyakkyawar niyya  a lokacin biya da cika alkawari  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce :- (Duk wanda ya karbi dukiyan mutane  da nufin zai biya to Allah zai biya mishi ) buhari ne ya rawaito
Kai kuma mai bin bashi ka kasance mai rangwame mai saukin hali mai kyauta , duk wanda ya kasance yana cikin matsanancin hali ka yi mishi rangwame  zuwa sanda zai samu , sabo da fadin Allah madaukakin sarki :-( Idan  ya kasance  matalauci ne  to a jinkirta mishi zuwa  lokacin da Allah zai hore  mishi )
Daga cikin ayuka masu falala  akwai  ;  yin hakuri ga wanda bai samu ba da yafewa wanda ya rasa ,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:(Wani attajiri ya kasance yana bawa mutane bashi  idan ya ga  wanda ya gagara biya sai ya ce wa yaran shi ku yafe mishi ko muma Allah zai yafe mana  to kuma sai Allah ya yafe mishi ).
A ruwayar musulim Allah madaukakin sarki ya ce :-(Mu muka fi dacewa da hakan bisa gare shi   to a yafe mishi ). Ya zo a hadisi kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:(Duk wanda ya saukake wa wanda ke mawuyacin hali  to Allah zai saukake mishi a duniya da lahira  ) Buhari da muslim ne suka rawaito.
  YA KAI   DAN UWA MUSULMI:
To ka ribaci    ladannan mai girma da falala mai auki ta hanyar tausayawa wanda ya rasa , kana mai  jinkirtawa  zuwa ga wani ajali   ko kuma ta hanyar yin rangwami da kubuta daga hakki  wannan shi ne lada mafi girma da sakayya mafi yalwa .
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:-( duk wanda  ke son Allah ya tsiratar da shi daga bakin ciki na ranar alkiyama  to ya yayewa matalauci     ) Muslim ne ya rawaito
HUDUBA TA BIYU
Yana daga cikin abin da musulunci ya wajabta akwai cika ladan mai kodago , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:-(ku bawa mai aikin kodago ladan sa kafin zufan sa ya bushe)  wasu malamai masu tantancewa sun ce hadisi ne  mai kyau .
To ya haramta a tawaye hakkin sa ko a rika cewa sai nan gaba , kan haka ne ma  Allah  madaukakin sarki  ya ce:-(mutum uku ni ne zanyi musu da su ranar alkiyama  sai ya ambata daga cikin su:- da mutumin da ya dauki hayan dan kodago,  ya nemi ya cikata mishi  ya nemi hakki daga gunshi bai bashi ladan shi ba)  Buhari ne ya rawaito


       

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق