الجمعة، 6 أبريل 2018

NI'IMAR ALJANNA


Hudubar juma'a na Masallacin Annabi  tare da sheikh Salah bin Muhammad Albudair 20-7-1439 AH.
Hudubar farko:
Ya ku Musulmai ! Ajali na kusantowa, Burace –burace na karewa, duk wani tsani ya yanke, lokacin tafiya da kaura ya zo, ya raba mutum da iyalai da sadawa da su,
Ba na ganin akwai abin da zai sha gaqban mutuwa ya tsallake ta, *
                                                                              Mutuwa ta katse jin dadi ga mawadaci da talaka.
Ka yi dubi ga duniya da idon mai ban kwana, *
                                                                      Domin hakika tafiyar ta kusa lokacin ban kwana ya yi.
Lallai Masoyi abin fizgewa ne daga masoyansa, *
                                                                                          Mai gadi ko mai tsaro bai hana  mutuwa.
Ta yaya zai yi farin ciki da duniya da jin dadin cikinta?*
                                                            mutumin da ana kidanya masa lafuzansa da numfashinsa.
Dukkan wata gida –wata rana-abar rushewa ce *
                                                         Komin dadewarta bisa ginshikinta.

Ya ku musulmai!
Yayin da duniya ta kasance gida ce ta fitintinu da jarabawa to mutum zai dandani wahalar neman abin rayuwa ,da gwagwarmaya da bala'i da cututtuka da nau'uka na musibu, da cin karo da abubuwa masu hanun riga, da kawatarwa irin na shaidan, da ma'abota barna.
Mai kyauta da karamci Mai jinkai,Mai girma ya yi kira ga bayinsa muminai zuwa ga Aljannarsa  gidan karamcinsa  gidan aminci da ni'ima, kubutacciya daga bakin ciki da bacin rai, wanda babu matsaltsalu da tashin hankali da bala'I,(kuma Allah na kira zuwa gidan aminci)
Idan duniya ta ma kunci gabadayanta *** ka zama baka da wani masauki sananne.
To ka yi gaggauto zuwa ga Jannatu Adnin  domin ita dinnan *** Masaukan mu ne na farko kuma cikinta akwai shemomi
sai dai fursunonin yaki ne na Magauda (Makiya) abin mamaki ya jama'a *** shin ko za mu koma gidajenmu mu samu aminci?
Gida ce da ni'imarta bai karewa , bai  halakewa,gidan da akwai dukkan alheri cikinta har da kari, an tanade ta an kusanto da ita an kawata ta domin karramawa ga masu tsoron Allah, ba su jin tsoron wani abu a ciki na bakin ciki ko hayaniya da gajiya,ba su tsoron talauci ko bashi a cikinta,ko fitarwa ko katsewa ko karewa ba. (Ba zaa fitar da su daga cikinta ba).
Duk wanda ya shiga Aljanna ba zai samu wata damuwa ba, tufafinsa ba zai ridddige ya tsufa ba,haka samartansa ba zai tsufa ba, mai yekuwa zai kira su : (lalle za ku samu  lafiya a cikinta ba za ku yi rashin lafiya ba har abada, kuma ku rayu ba za ku mutu ba har abada, kuma ku zama matasa ba za ku tsufa ba har abada, lalle kuma za ku samu ni'ima ba za ku samu wata damuwa ba har abada, sai a ce : Ya ku 'yan Aljanna ku dawwama ba mutuwa har abada, ya ku 'yan wuta ! ku dawwama ba mutuwa,  a cikin Aljanna akwai abin da ido bai taba gani ba, kunne bai taba ji ba,zuciyar dan Adam bai taba hararo shi ba,).
(Mala'iku na shiga musu ta kowace kofa, Amincin Allah ya tabbata a gare ku sabo da hakurin da ku ka yi, madalla da gida mai kyakkyawan karshe).
Allah Mai girma!! Mala'iku na shigo musu,!! Mala'iku su zo musu,Mala'iku  su gaishe su, Mala'iku na taya su murna!!
(To amincin Allah ya tabbata a gare ku, kun ji dadi, ku shige ta kuna masu dawwama.)
Abin mamaki da girman wannan kusancin da girmamawa a gidan aminci.
Lalle Allah Madaukakin sarki zai ce ga 'yan Aljanna,  :( ya ku 'yan Aljanna ! sai su ce : Mun amsa kirarka kuma mun rusuna, sai yace : ko kun gamsu? Sai su ce :  ta yaya ba za mu gamsu ba bayan ka bamu abin da baka baiwa wani ba daga cikin halittunka,sai yace : zan baku abin da ya fi haka.sai su ce Ya Ubangiji me ne ne ya fi hakan?, Sai yace : zan sanya yarda ta a gare ku bayan haka ba zan yi fushi da ku ba har abada).
(Kuma yardar Allah ya fi girma)
Ya fi girma bisa Aljannar da koramanta ya fi girma akan benayenta da tufafinta da guzurinta.
Amma ganin Allah a Aljanna shi ne abin da masu jan damara su ke jan damara akan shi, masu yin munafasa da rige –rige ke tsere a kan shi, ya hana shi ga wadanda aka musu shamaki da Ubangijinsu, kuma aka kore su daga kofarsa, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Wasu fiskoki a wannan rana suna mani'imta ne. masu dubi zuwa  ga Ubangijinsu) Al  kiyama 21-22
An karbo daga Abu Musa Allah kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Gonakai guda biyu na azurfa kwanukansu da abin da ke cikin su,da gonakai biyu na zinari  kwanukansu da abin da ke cikinsu, ba wani abu da yake tsanin mutanen da su ga Ubangijinsu  mai tsarki da daukaka face  rigar girmame –girmame a fiskarsa cikin Aljannar Adni) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
An karbo daga Suhaibu daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :: Idan 'yan Aljanna sun shiga Aljanna Allah Madaukakin sarki zai ce : Ko kuna son wani abu na kara muku? Sai su ce : Allah ba ka haskaka fusakanmu ba ka shigar da mu Aljanna ba kuma ka tseratar da mu daga wuta? Yace sai ya yaye hijabin  sai su ji dadin da  ba a taba basu wani abu da ya fi soyuwa a gare su ba kamar ganin Ubangijinsu  ba Mabuwayi da Daukaka).Muslim ne ya rawaito.
Ibnul Kayyim Allah ya mishi rahama ya ce :  To wannan kenan in ka tambayi ranar kari daga Mabuwayi  Abin godiya, da ganin fiskarsa tsarkakakka daga misali ko kamanci, kamar yadda kake ganin rana lokacin azahar, da kuma wata a daren sha hudu, kamar yadda aka karbo daga mai gaskiya abin gaskatawa,ta hanyoyi  masu dumbin yawa, hakan na nan cikin sahihai da sunann da musnadai, na daga riwayar Jarir da Suhaibu da Anas da Abu Huraira da Abu Musa da Abu Sa'id , Ka saurari ranar da mai kira zai yi kira ? Ya 'yan Aljanna Ubangijinku  zai nemi ziyartarku,, to ku zo , don ziyartarshi,  sai su ce : mun ji mun bi,sai su taso zuwa ga ziyara suna gaggautowa  har lokacin da suka isa kwarinmai fadi  wanda aka sanya musu magama, suka hadu a can ba wani guda da mai kiran ya bari, Ubangiji Allah sai ya yi umarni da a kafa masa kujerar sarautarsa, sai aka kafa, su kuma aka kafa musu  minbarai na haske, da minbarai na lu'ulu'u, da minbarai na zubarjadi, da minbarai na zinari da minbarai na azurfa, mafi karancin daraja a  cikinsu ya zauna,-  duk da ba wani makaskanci cikinsu- bisa wata turbaya na almiski, kuma basu ganin nan kan kujera sun fi su samu kyauta,
Har zuwa lokacin da kowa ya natsu a mazauninsa hankali ya kwanta, sai mai kira ya yi kira,: ya 'yan Aljanna  lalle kuna da wani alkawari a gurin Allah da yake so ya cika muku! Sai su ce : Mene ne shi? Ase ba an haskaka fisakanmu ba,a ka nauyaya mizaninmu ba, aka shigar da mu Aljanna ba, aka nesatar da mu daga wuta ba? Suna cikin haka sai wani haske ya bayyana  wanda Aljanna ta haskaka da shi, sai suka daga kawunansu, sai ga Aljabbaru (kasaitacce) Girmansa ta kasaita, sunayensa sun tsarkaka, ya fuskanto su daga ta samansu,yace : (ya 'yan Aljanna amincin Allah ya tabbata a gare ku) Ba a amsa wannan gaisuwar da sama da fadin cewa : ya Allah kai ne aminci, daga gun ka aminci ya ke, albarka ta tabbata a gare ka,ya Ma'abocin girma da karamci,sai Ubangiji ya yi tajalli a gare su(Ya bayyana) Albarka da daukaka sun tabbata a gare shi, ya musu dariya yace :  Ya 'yan Aljanna ! sai ya zama farkon abin da zasu ji daga gare shi shine : Ina bayi na da suka yi min biyayya a fake bisa halin ba su ganni ba? To wannan ne ranar kari , sai su yi tarayya a kalma guda: Mun yarda to  ka yarda da mu, sai ya ce ya 'yan Aljanna in da ban yarda da ku ba da ba zan saukar da ku a Aljanna  ta ba. Sai yace : wannan ne ranar kari ku roke ni! Sai duk su yi tarayya a kan kalma guda: ka nuna mana fuskar ka mu yi dubi zuwa gare shi, sai Ubangiji  Allah Madaukakin sarki ya yaye shamaki, Daukaka ya tabbata a gare shi, sai ya yi tajalli a gare su, sai ya lullube su da haskensa, sai su manta da duk wata ni'ima da su ka taba gani, badon Allah ya hukunta ba za su kone ba da sun kone, ba wani da zai rage a wannan majlisar har sai ubangiji ya mar lacca kai tsaye, har ma ya ce ya wane ko kana tuna ranar kaza ka aikata kaza da kaza,? Yana tunatar da shi wasu sashi na ha'ince –ha'incen da ya yi a duniya, sai ya ce ya Ubangiji ba ka yafe mini ba? Sai yace ai da gafara tawa ce ka kai wannan matsayin taka da ka ke kai.
Allah Mai girma! Abin mamaki  da girman irin wannan ni'imar, abin mamaki da irin wannan karramawar, zasu ga Ubangijinsu a Aljanna,  za su ga Allah Ma'abocin girma da kyau da kamala, za su ga abin bautan da sun dade suna bauta masa, suna mishi tasbihi,da halala da kabbarori, suka yi mishi  sujada kuma suka girmama shi.
Wani irin dadi ne da jin dadi, wace irin ni'ima ce, wani irin rayuwa ce wani irin walwala ce,wani irin zabi ne, zasu ga Allah wanda duniya  bata yi dadi ba sai da ambatonsa,lahira ma bata yi dadi ba sai da yafiyarsa, haka ma Aljanna ma bata yi dadi ba sai da kallo zuwa gare shi, wayyo kwadayinmu zuwa gare shi, wayyo shaukinmu zuwa ga gidan ni'ima, wacce a cikinta masu kadaita Ubangiji zasu , zai yi tajalli a gare su ya bayyana, kuma yayi dariya agare su,ya fiskanta zuwa gare su, kuma yana bayyana ga 'yan Aljanna a kowace juma'a, cikin wata turbaya na Alkafur sai su kasance kusa da shi gwargwadon gaggawar su zuwa Juma'a a duniya,ba su kara dubi zuwa ga Ubangijinsu sai hakan ya kara musu karama.
Zaka ga fiskar Ubangiji  madalla da fiska da ke cike da kauna da daukaka.
Ya ku bayin Allah!
Wannan dadin labari ina ga dadin ganin?
Ya Allah muna rokon ka dadin dubi zuwa fiskar ka, da kwadayin haduwa da kai, ba cikin wata cuta ko cutarwa ba, ko wata fitina mai cutarwa ba.
Huduba ta biyu
Ya ku musulmai !
Ku kimtsa kayanku ku gaggauta morar rayuwarku  ku ribaci lokacin ku, to me ke baya ni'ima da jin dadi da kawar rayuwa da walwalarta face mutuwa da kare wa da rididdigewa,
Mutuwa kofa ce kuma dukkan mutane zasu shige ta
Me zan ji bayan wannan kofar me ke cikin gidan?
Gidan Aljanna ne na dawwama  muddin ka yi aiki da abin da zai yardar da Allah
In ka gaarta sai wuta, sune gidaje biyu mutane basu da wasu gidan in ba su ba.
To ka duba wa kanka wanne zaka zaba.     



ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق