السبت، 10 فبراير 2018

TARBIYANTARWA DA KAUNA

Hudubar Masallacin Annabi  na shaikh Abdulbari subaiti 23-5- 1439 AH
Hudubar farko
Musulunci na raya tashi da nauyin mas'uliyya a cikin zuciyar musulmi: mafi girman mas'uliyya shine kula da yara da tarbiyantar da su bisa turba da ginshiki na  addini da kyawawan halaye, wanda addini ne mabubbuga na duk wasu halaye na mutunci, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( Dukkan ku Makiyaya ne, kuma zaa tambayi kowannenku abin da aka ba shi kiwo) Bukhari ne ya rawaito.
Idan tarbiya ta yi rauni zaa wayi gari  damuwar wanda  ake tarbiyantarwa  da tunanin shi  kawai  yadda zai kashe  yunwarsa  da kosar da sha'awarsa, yana tafiya duk inda zai kai shi ga holewa da morewa na jin dadin rayuwa. Allah Madaukakin sarki ya ce : (Lalle ne Allah na shigar da wadanda suka yi imani kuma suka aikata ayyukan  kwarai a gidajen Aljanna, kogunan ruwa na gudana  daga karkashinsu, kuma wadanda suka kafirta, suna jin dan dadi (a duniya)  kuma suna ci kamar yadda dabbobi ke ci, kuma wuta ita ce mazauni a gare su.) Muhammad:12
Abin da ya fi karfin tasiri a tarbiya ita ce zuciya, idan ta gyaru to sauran jiki ya gyaru, to idan ya lalace to sauran jiki ma ya baci, (Domin lalle ne idanun basu makanta, amma zukata wadanda ke a cikin kiraza su ke makanta.)   Al-Hajj 46
     Idan zuciya ta gyaru ta yi kyau sai hankula su nuna su kuma rayuwa ta haskaka jiki, gabbai kuma su rusuna, Allah Madaukaki ya ce : ( shin lokaci bai yi ba ga wadanda suka yi imani  zukatansu su yi tawalui ga ambaton Allah da abin da ya sauka daga gaskiya.) Al-Hadid:16
Lalle ba makawa kauna  wani tushe ne mai asali daga koyarwar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, shi ne zancen  ruhi kuma sako ne daga zuciya zuwa zuciya, gurin tarbiyya da gyara. Kuma hakika Allah ya kimtsa zukatan iyaye biyu bisa son 'ya'ya da suke bawa tarbiya, Usama Dan Zaid na cewa Manzon Allah ya kasance yana dauka na ya zaunar da ni akan cinyarsa ya kuma zaunar da Hasan kan daya cinyar sai ya game su sannan ya ce : (ya Allah ka tausaya musu ni ma ina tausaya musu) Bukhari ya rawaito, a wata riwayar : (ya Allah lalle ni ina son su to ya Allah  ka so su) Tirmizi ne ya rawaito da isnadi ingantacce.
Na daga cikin alamomin tarbiyantarwa na bayyane  da kauna akwai sumbatar yara da manna su a jiki, Manzon Allah ya sumbaci Hasan a tare da shi akwai Akra Bin Al-Habis zaune sai yace :Ina da yara goma amma ban taba sumbatarsu ba sai Manzon Allah ya ce : (Duk wanda ba ya tausayawa to ba zaa tausaya masa ba,Tirmizi ne ya rawaito da isnadi ingantacce,
Manzon Allah ya kasance yana cikin huduba ga sahabbansa sai ga Hasan da Husaini sun zo suna sanye da tufafi jajaye suna tafiya suna faduwa, sai Annabi ya sauka daga kan minbari ya daga su ya dora su kan hannayensa,sannan ya ce Allah ya yi gaskiya (Dukiyoyinku da 'ya'yanku fitina dai ne) na  kalli yarannan biyu kanana suna tafiya suna faduwa sai na gaza hakuri na yanke zance na na daga su. Tirmizi da Nasa'I ne suka rawaito da isnadi ingantacce.
Manzon Allah ya kasance yana raha da yara kuma yana musu tawali'u, tare da la'akari da abin da ya kebance su, yace da dayansu (kai mai kunnuwa biyu.) Nasa'I ne ya rawaito da isnadi ingantacce. Yana cewa ga wani yaron kuma :( Ya Baban Umair menene labarin kanarin ka)?Bukhari da Muslim ne suka rawaito.       
 Kada iyaye biyu su manta cewa na daga cikin abu mafi girma da amfani  da tasiri a hanyoyi na tarbiya da kauna a aikace akwai lazimtar  adu'a ta shiryuwa da datarwa da gyaruwa da kariya ga wanda ake tarbiyantarwa, to bayin Mai rahama cewa suke yi a aduarsu : (Ya Ubangijinmu ! ka bamu sanyin idanu daga matanmu da zuriyarmu) Al-Furkan 74
Ga Annabi Zakariyya yana cewa : (sai ka ba ni wani mataimaki daga wajenka, ya gaje ni kuma ya yi gado daga gidan yakubu, kuma ka sanya shi yardajje ya Ubangiji!) Maryam 5-6
Ga Annabi Ibrahim yana cewa :  (Ya Ubangiji ka ba ni (abokin zama) daga salihan mutane)Assaffat 100 (Ya Ubangiji ka sanya ni mai tsayar da sallah  kuma daga zuriyyata).Ibrahim :40
Amma yi musu mummunar adu'a hani ya zo kan hakan, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(kada ku yi mummunar adu'a a kanku, kuma kada ku yi mummunar adu'a ga  'ya'yanku, kuma kada ku yi mummunar adu'a ga dukiyarku, domin kar ku yi muwafaka da lokacin amsawa  sai a amsa muku) Muslim ne ya rawaito
Abin nkoyi mai kyau wani tushe ne na tarbiya, kuma haske ne na tsarkaka, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ka ce: idan kun kasance kuna son Allah to ku bi ni, Allah ya so ku, kuma ya gafarta muku zunubanku, kuma Allah Mai gafara ne Mai jin kai).Al-Imran :31
 Kuma abu ne da bai buya cewa kwaikwayo da koyi na da tasirin da ya fi fadi da karatu da  sauraro,
Sabo da muhimmancin koyi ne ma da hadarin da ke tattare da shi Allah ya ke cewa :(Ya ku wadanda  suka yi imani! Don me ku ke fadin abin da ba ku aikatawa? Ya girma ga zama abin kyama a wurin Allah. Ku fadi abin da ba ku aikatawa). Assaf : 2-3  
Kauna na wanzuwa da karfafuwa da dawwama har a lokacin zamewa (kuskure) da gajartawa, wannan ita ce koyarwar Manzon Allah , hakika wani mutum ya zo mishi sai ya ce: ya Manzon Allah na halaka ! sai ya ce : (Me ke gare ka?) sai ya ce : na aukawa mata ta a halin ina azumi, sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Ko kana da wuyaye da za ka 'yanta? Sai ya ce : A'a. sai yace :(To za ka iya yin azumin wata biyu a jere?) sai yace :A'a. sai ya ce :(To zaka iya samun ciyar da miskinai sittin ?) sai ya ce :A'a). sai manzon Allah ya dan zauna jim kadan muna halin haka sai i aka  kawo wa Annabi  kwando  a cikin shi akwai dabino, kwando wata tasa ce ta awu   sai ya ce ina mai tambaya? Sai yace : Ga ni sai Manzon Allah ya ce karbi wannan ka yi sadaka  da shi, sai ya ce : ga wanda ya fi ni talauci ya Manzon Allah? To na rantse da Allah! ai duk  kewayen madina a tsakanin duwatsunta biyu ba mutan gidan da  suka  kai iyalan gida na  bukata.sai Annabi yayi dariya har fikarsa suka bayyana sai yace : ka ciyar da shi ga iyalanka).Bukhari ne ya rawaito.
A yanayi na kauna mai tarbiyantarwa ba zai shakala yin amfani da hikima da kyakkyawan fadakarwa da tausasa zance, da saukin hali, tare da nesatan amfani da karfi da suka da walakantarwa,  Allah Madaukakin sarki ya ce: (Ka yi kira  zuwa ga hanyar Ubangijinka da hikima da wa'azi mai kyau, kuma ka yi jayayya da su da magana wadda take mafi kyau.)ANNAHL -125
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Lalle Allah Mai sauki ne,kuma yana son saukakawa, kuma ta hanyar sauki ya kan bada abin da bai bada shi ta hanyar karfi ko waninsa.) Muslim ne ya rawaito.
Ya ce da balaraben kauyen da ya yi fitsari a masallaci: (ku kyale shi, ku kwarara bokitin ruwa ko guga guda a kan fitsarin  nashi abin sani kawai an turo ku ne kuna masu sauki baa turo ku kuna masu tsanani ba).Bukhari ne ya rawaito.
Kamar yadda girmama wadda ake tarbiyantarwa da yi mishi maraba da nuna haba-haba da shi, koyarwa ne na Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. A'isha Allah kara yarda a gare ta ta ce : Fadima ta fiskanto tana tafiya, tafiyarta irin na Annabi sai Annabi yace : (Maraba da 'ya ta )sannan ya zaunar da ita a damansa ko hagunsa) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Jiki na da gudumawa da yake bada wa gurin tarbiyyantarwa da kauna; kamar murmushi da fara'a ta gaskiya, da shafa irin na shauki, da kalmomin kwantar da hankali, da tausayawa irin na zuci.
Mai bada tarbiya ba zai yi sakaci da dama da ya samu ba na halrtowar hankali zuwa gare shi face ya dasa kyawawan dabiu ba tare da kankantar da hankalin yaro ba ko renarwa.
An karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah kara yarda a gare shi da mahaifin shi yace : wata rana na kasance a bayan Annabi sai ya ce: ya kai yaro zan sanar da kai wasu kalmomi: ka kiyaye Allah zai kiyaye ka,ka kiyaye Allah za ka same shi a gaba gare ka)Tirmizi ne ya rawaito da isnadi ingantacce.
Tarbiyantarwa da kauna na bukatar yanayi  da iyalai zasu game su dukule,su so juna , ta inda zasu samu farinciki da  walwala su yi wasa da bai sabawa shariar wannan addini ba, Aisha Allah kara yarda a gare ta tana cewa :Na kasance a wata tafiya tare da Annabi  sai muka yi tsere  da shi sai na yi galaba a kan shi,da kafafuwa ta,a yayin da na yi jiki muka sake tsere da shi sai ya yi galaba a kai na, sai ya ce : (To da wannan ni ma na rama wancan galaba da aka yi a kai na.)Abu Dawuda ya rawaito da isnadi ingantacce.
An karbo daga gare –Allah kara yarda a gare ta- ta tace: (na ga Manzon Allah a kofar daki na ga habashawa suna wasa a masallaci Annabi ya kare ni da mayafinsa ina kallon wasar tasu.)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Tarbiyantarwa da kauna na bukatar kulawa da adalci wajen bayyana kauna ga yara, sai ya fadada  so da ya ke musu ya game su  gabadayansu ba tare da wariya ba,
Yayin da Annabi yusuf ya yi mafarki (lalle ne ni na ga taurari goma sha daya, da rana da wata na gan su suna masu sujada a gare ni) sai mahaifinsa Annabi  Yakub  -Amincin Allah ya tabbata a gare shi - ya ce da shi : (ya karamin da na! kada ka labarta mafarkinka ga 'yan uwanka har su kulla maka wani  kaidi,  lalle shaidan ga mutum makiyi ne  bayyananne.) yusuf 4 &5
Manzon Allah ya ki ya shaida kyautar da wani mahaifi ya bawa daya daga cikin 'ya'yansa yace : (Ni ba zan yi shaida na zalunci ba). Bukhari ne ya rawaito.
Tarbiyantarwa ta hanyar kauna da kosar da zukata da sosa mata inda ya ke mata kaikayi shiryarwa ne na Annabi kuma bukata ce aka halicci mutum a kanta,kuma ya fi karfi ta bangaren  'ya'ya mata Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Wanda aka jarabce shi   da wani abu na daga wannan 'ya'ya  matan , sai ya kyautata musu to za su kasance  kariya a gare shi daga wuta) buhari da muslim ne suka rawaito  lafazin na Buhari ne ,  : kyautatawa ga 'ya'ya mata ta hanyar koyar da su da  tada su akan kamun  kai, da nesantar da su daga abin da Allah ya haramta , na daga tsiraici da bayyana jiki   .
                 Da dora yara maza a tafarki tsayayya  na aiki mai amfani , da kuma  shirye-shirye na aikin alheri wanda zai daga manufar su  ya kuma  kare su daga fadawa  cikin abubuwa marasa muhimmanci  da yawon banza.
       Yana daga cikin abin da ke warware tarbiyantarwa da kauna ; akwai shagwabantar  da yara  ta hanyar amsa musu duk  abin da suka nema  da abubuwan  kwadaye-kwadayen  su da kuma yin sakaci ta bangaren ladabtar da su da gyara musu kusakuran su : to jajarcewa wani lokaci yana cikin kauna ,: musgunawa uwa a gaban 'ya'ya yana toshe kofar soyayya  amma bayyana zunubai da fandarewa da iyaye za su yi a gaban 'ya'yan su to hanya ne mai rusa tarbiya Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (  ya isa zunubi ga mutum da ya sarayar da  wanda yake ciyarwa ) Abu Dauda da Ahmad suka rawaito da isnadi ingantacce  .
           HUDUBA TA BIYU
Hakika hanyoyin tasiri na zamani sun habaka , kuma sun haifar da wani sanje- sanje na tushe  a tunani da fahimta da dabi'u, har a ka wayi gari suna  gogayya  da  gudumawar da iyaye suke bayarwa na tarbiyan 'ya'yayen su ,: to  a nan ne muhimmancin tarbiyantarwa  da kauna zata bayyana, da kuma bashi mafaka  da kuma  gina gada mai karfi na aminci  da sabunta salo,  da shuka kyawawan dabi'u da zaburantar da himmar kafafen ilmantarwa da tarbiyantarwa , don tashi da sakonnin su   wurin kiyaye   madosan al'uma da fatanta nan gaba , da kuma kiyaye arzikin kasa , ta hanyar bada kariya ga ginshiki na addini da kuma dabi'u  da bada kulawa ga matasa ,  da kuma  abin da suke burin zama nan gaba  da kuma kiyaye radadin su da damuwan su .
Allah Madaukakin sarki ya ce : ( Ya ku wadan da suka yi imani ku karewa kan ku da iyalan ku wata  wuta makamashinta  mutane da duwatsu ne.  


                 
   


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق