الجمعة، 23 فبراير 2018

KUNYA ALHERI NE DUKA


Hudubar Masallacin Annabi  na shaikh AbdulMuhsin Alkasim  7-6-1439AH
HUDUBAR FARKO :
  Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin sarki  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa , muna neman gafarar sa  , kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa  da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa .
Bayan haka

Ku ji tsoron Allah - ya ku bayin Allah – ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci .
Mabudin bautawa Allah da sirrin bauta masa na ga sanin sunayen Allah ne da sifofinsa.to sunayensa  Madaukaki duk kyawawa ne, sifofinsa duk Madaukaka ne.  Yana da  wata sifa ta bauta na musamman ga dukkan suna da sifa  tsarki ya tabbata a gare shi , yana daga cikin  abin da ke haifar da shi  da kuma abin da ya kumsa,  Allah yana son sunayensa da sifofinsa kuma  yana son bayyana alamomin su ga halittunsa , sai ya umarci bayinsa da su roke shi da su,  Allah Madaukakin sarki ya ce: (Kuma  Allah yana da sunaye masu kyau , sai ku roke shi da   su ). Kuma mafi soyuwan halitta zuwa ga Allah  shi ne wanda ya siffantu da sifofin da Allah ke kauna ,  wanda ya bautawa Allah da sifofin shi zai kusantu  zuwa ga rahamarsa , wanda ya kiyaye sunayen sa  zai saukar da shi a aljannarsa  daga cikin sunayen Allah   akwai ALHAYIYU wato mai kunya  kuma daga cikin sifofin sa akwai kunya ,  kuma Allah ya siffanta kan shi da ita   sai ya ce : (Lallai ne Allah ba ya jin kunyar ya bayyana wani misali,  kowane iri ne, sauro da  abin da yake  bisa gare shi ) .
  Manzon sa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ambace shi sai ya ce :( Lallai Allah mabuwayi da daukaka  mai kunya ne , kuma marufin asiri ne  yana son kunya da  suturcewa ) Abu Dauda ne ya rawaito .   Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( Lallai Ubangijin ku mai girma da daukaka Makunyaci ne, kuma mai karamci ne , yana jin kunyar bawansa  idan ya daga hannayensa biyu zuwa gare shi ya dawo da su haka banza ).Abu Dauda ne ya rawaito shi
             Ibn Alkayyim Allah ya mishi rahama ya ce : '' Kunyan Ubangiji Madaukakin sarki ga bawansa, abu ne da fahimta ba zai riske shi ba , hankali kuma ba zai gano yadda yake ba, domin shi wani kunya ne na karamci  da kyautatawa  da kuma kyauta da daukaka ''.
             Mafi girman kyawawan halaye cikin halittu kuma mafi daukakansu da kuma mafi girma a daraja da kima kuma mafi  yawan amfani; shi ne kunya , wata dabi'a ce  wadda ke sa  abar duk wani munanan dabi'u  kuma yana hana yin sakaci  a cikin hakkin  ma'abocin hakki , tushen sa da asalin  maddarsa daga rayuwa ne ,  kuma bisa iya gorgodon rayuwar zuciya  iya kasancewar kunaya a cikin ta  a duk lokacin da zuciya  ta fi rayuwa , sai kunya ta fi cika a cikinta   da karfi  kunya bata  gushe ba  al'amarin ta tabbatacciya ce , kuma amfani da  ita  wajibi ne tun  zamanin Annabawan  farko ,  kuma ba wani  Annabi face   ya kirayi al'umar sa zuwa gare ta kuma an turo shi da ita  ba a goge ta ba cikin abubuwan da a ka goge na shari'o'insu , kuma  ba a canza ta ba cikin abubuwan da ake canzawa , sabo da wannan al'amari  da ya bayyana karara  na daidai ne  an sanshi  kuma  falalar shi ya bayyana  dukkan hankula sun yi taraiyya bisa ga kyanta , duk wanda wannan ya kasance shi ne sifansa  bai  halatta a goge shi ko a canza shi ba, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lallai yana daga cikin  abin da mutane suka riska  na maganan Annabawa  shi ne idan baka ji kunya ba ka aikata abin da ka ga dama ) Buhari ne ya rawaito
      Mafificin halittu ya siffantu da ita kuma Allah ya kyautata yabo ga ma'abotanta   to kuma mala'iku ma sun siffantu  da ita  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  gare shi ya ce game da Usman : ( Ase ba zan ji kunyar mutumin da mala'iku suke jin kunyar sa ba ), Muslim ne ya rawaito  , Annabawa an san su a cikin mutanen su da haka,   halittu za su nemi ceto ranar alkiyama da Adamu da Nuhu Alaihimassalam , sai ko wannen su ya tuna zunuban shi sai ya ji kunya )  Musa amincin Allah ya tabbata a gare shi makunyaci ne , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce : ( Lallai Musa  ya kasance  mutum ne makunyaci  mai yawan suturcewa  ba a ganin wani abu na daga fatar jikin shi sabo da irin kunyar sa ), Buhari ne ya rawaito
      Annabinmu Muhammadu  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana da kaso mafi tsoka na daga kunya,  sabo da haka yakan  yi jirwayi da kamar wanka,  baya yin karara,   akan gane  kunyar sa daga fuskarsa,  Abu Sa'id Al khudri ya ce:  '' Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ( Ya kasance   mafi tsananin kunya  fiye da budurwar  da take cikin haudajin ta , kuma ya kasance idan ya tsani wani abu mukan gane a fuskar sa) Buhari da Muslim ne suka rawaito  shi 
       Ya kai ya komo a daren mi'iraji  tsakanin Musa da Ubangijinsa yana rokon a sassauta game da sha'anin sallah har zuwa lokacin da ya ce : " ( Hakika na ji kunyar Ubangiji na ") ,  a yayin da ya shiga da Zainab 'yar Jahash,  an kira mutane   don hakan, sai suka ci abinci suka fita  sai ya rage wasu mutane uku suna ta hira a dakin  sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ji kunyar ya ce  mu su wani abu ,  sai ya fita ya bar su  a dakin, sai Allah Mabuwayi da daukaka ya saukar da : (Ya ku wadanda suka yi imani kada ku shiga gidajen Annabi  face fa idan anyi izini a gare ku zuwa ga wani abinci ,   ba da kun tsaya jiran nunar sa ba , kuma amma idan  an kira ku, to , ku shiga   sa'annan idan kun ci, to ku watse , kuma ba da kun tsaya kuna masu hira da wani labari ba ,  lallai wannan  yana cutar da Annanbi,  to yana jin kunyar ku , alhali kuwa Allah baya jin kunya daga gaskiya) Ahzab 53  Buhari da Muslim ne suka rawaito
            Kuma Usman Allah ya yarda da shi ya zama abin buga  misali a  akunya cikin sahabbai,  watarana  ya shigo ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  sai  Manzon Allah ya zauna ya daidaita tufafin shi   sai aka tambaye shi game da haka sai ya ce : ( Lallai Usman mutum ne makunyaci  na ji tsoron kada na mishi izini a wannan yanayi ya ki isowa zuwa gare ni , cikin bukatar sa ) Muslim ne ya rawaito .
         Mace an halicce ta bisa kunya  , kuma kunya ce adon ta  kuma kariya ne a gare ta da aminci   Aisha Allah ya kara yarda a gare ta ta ce " Ya Manzon Allah  ai ita budurwa tana jin kunya sai ya ce yardan ta –da auren - ai shi ne yin shurun ta  " Buhari ne ya rawaito
      'yar ma'abocin madyana  tazo  kunya na lullube da ita ta suturce fiskanta da hanunnta da kuma tufafin ta Allah madaukakin sarki ya ce : ( Dayan su sai ta zo tana tafiya bisa kunya  sai tace lalle mahaifi na na kiranka don ya saka maka abin da ka yi na shayar da mu)   .Kuma Aisha uwar muminai  Allah ya yarda da ita,  kunya ya kaita da ta suturce kanta  a cikin dakinta sabo da Umar  Allah ya yarda da shi   bayan an binne shi ( a  dakin ta ) Allah ya kara yarda  a gare ta, ta ce: "Na  kasance ina shiga  daki na   wanda aka binne  Manzon Allah a cikinsa da mahaifi na sai na cire tufafi na,  sai na ce ai wannan mijina ne, wannan kuma mahaifina  ne , to amma a lokacin da aka binne Umar tare da su   to wallahi ban shiga dakin ba face sai ina daure da tufafi na  a jiki na sabo da kunyar umar  )Ahmad ne ya rawaito .
          Kuma ga wata mace da ta yi hakuri bisa jarabawa   amma bata yarda da cire rigar kunya  ba , sai sakayyar ta  ya kasance aljanna :  Abdullahi Dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su shi da mahaifin shi ya ce ga  Ada Dan Abi Rabah  Allah ya mishi rahama ya ce : " Ase   ba zan nuna maka mata 'yar aljanna ba ? sai na ce e;  sai ya ce : " wannan bakar matar  ta zo ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  sai ta ce : "   Lallai ni  ina da cutar  farfadiya  har nakan  yaye daga tufafi na,  to ka roka min Allah  ya raba ni da ita,  sai ya ce in kin so ki yi hakuri kina da aljanna  in kuma kin so in roka miki Allah ya baki lafiya " sai ta ce : "zan  yi hakuri,  sai dai nakan yi tsiraici , to ka rokamini  Allah kada na rinka yin tsiraici  sai ya roka mata Allah" ) Buhari da Muslim ne suka rawaito
       Kuma tana cikin dabi'u masu daraja wanda har mutanen jahiliyya ma sun wanzu a kan ta, Abu Sufyan Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : " a yayin nan da Hiraklu ya tambaye shi game da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,  kuma a lokacin yana kafurci : (Wallahi ba don kunya ba a wannan ranar kar mutane na su taba kama ni da karya a wannan ranar da na yi mishi karya , a lokacin da ya tambaye ni game da  shi, amma sai dai na ji kunya kar a same ni da karya sai na fada mishi  gaskiya).
      Da kunya ne a ke samun walwala   a riski kuma sabubanta, dukkan  ta alheri ne  , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Kunya alheri ne dukanta  ko kuma ya  ce  kunya  dukkan ta alheri ne )Muslim ne ya rawaito
      Karshen ma'abocinta alheri ne    har abada  kuma ba zai hadu da nadama ba har abada   , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  yana cewa : ( Kunya bata kawo wani abu sai alheri). Muslim ne ya rawaito
      Ibn Kayyim Allah ya mishi rahama ya ce :" kunya wani sinadari ne na rayuwar zuciya kuma ita ce tushen dukkan alheri ,  rasa ta kuma rasa alheri ne gaba dayan shi  )
Yana daga cikin mafi girman alherin da ke cikin ta akwai sabarwa rayi  da kyawawan dabi'u da kuma nisantar munanan dabi'u , idan kunayar mutum ta tsananta sai a kare mutuncin sa kuma sai a binne laifukansa a kuma yada kyawawansa.
          Yana daga cikin  akidar ahlussunna waljama'a ; cewa imani fadi ne  da kudiri da aiki,  kunya wani yanki ne daga gare shi   Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce:( Imani yanki ne sittin da dori kuma kunya wani yanki ne na imani )    Buhari da Muslim ne suka rawaito shi .
 Ibn Hibban Allah ya mishi rahama ya ce :"kunya  na daga cikin imani kuma mumini na aljanna, ba za a  zare kunya daga wani ba face an zare imanin shi  ".
       Manzon Allah ya wuce wani mutum yana zargin dan uwansa game da  kunya, yana cewa : " Lallai kai kana jin kunya  har kamar yana cewa  da shi  ya kai ma yana cutar da kai , sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( kyale shi, lallai  kunya na daga cikin imani) . Buhari da muslim ne suka rawaito
      Ba ukubar da Allah zai yi ga zuciya da tafi a kwashe kunya daga gare ta, Ibn Umar Allah ya kara musu yarda  ya ce : " Lallai kunya da imani an hada su tare  idan an dauke dayan su sai a dauke dayan ma "  .
       Kunya da'a ce da ke janyo wasu biyayya  da za su kai  ma'abocinta zuwa ga tsentseni wanda kuma ya barta to zai aikata abin da yake kishiyan haka , Umar Allah  ya kara yarda a gare shi ya ce: " wanda kunyar sa ta karanta to tsentseninsa zai karanta, wanda tsantsenin sa ya karanta zuciyar sa ta mutu.
       Kunya na daga cikin abu mafi girma da ke  shiga tsakanin mutum  da  aikata sabo , makunyaci na  katse ayyukan sabo da kunya kamar yanda imani ke katse sabo,  idan an tube kunya daga bawa to sai ya zama ba abin da  ya rage da zai hana shi aikata munanan abubuwa   da kuma halaye marasa kyau,  sai ya zama kamar bai da imani,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( Idan  mutum bai ji kunya ba to ya aikata abin da ya so). Buhari  ne ya rawaito
                  Ibn Abdulbar Allah ya mishi rahama ya ce : " Duk wanda bai da kunyan da zai katange shi daga abin da Allah ya haramta , to daya ne a gare shi aikata aikin karamin zunubi da babba,   a cikin hadisin akwai gargadi da narkon azaba game da karancin  kunya "
 Zunubai na raunana kunya daga bawa har ma ya tafi gaba daya daga gare shi ,  ya zamana ba zai dame shi ba don mutane sun san halin shi ko suka gane abin da ya ke aikatawa , kai hakika ma yakan bada labari bisa halin shi da munanan  ayukan shi .
                 A kunya akwai ado da kawa ga ma'abocinta   Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Batsa baya shiga cikin komai sai ya bata shi kunya kuma baya shiga cikin komai sai ya kawata shi – wato ya adonta shi )  Tirmizi ne ya rawaito shi
                  Kunya na kira zuwa ga izzar rayi da kare ta , ba zai tambayi mutane wani abu ba ko da ya bukaci hakan , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Ba miskini shi ne wanda ya ke kai komo a kan loma daya ko biyu ba, sai dai miskini shi ne wanda ba yi da wadata kuma yana kunya, ko kuma baya tambayan mutane bisa naciya ) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
                Kunya kamar wani adireshi ne na kyakkyawan dabi'a da ladabi.  Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya tambaya : ( Game da itaciyar da take kama da musulmi , sai Ibn Umar Allah ya yarda da su ya ce : ( sai ya fado a zuciya ta cewa bishiyar dabino ne sai na ga Abubakar da Umar ba su yi magana ba, sai   na ji nauyin  na yi magana. a wani lafazin kuma ya ce : " sai na ji kunya ) Buhari da muslim ne suka rawaito .
         Mutum ana sakanya mishi da irin aikin da ya yi,  na daga cikin amfanin kunya da kyakkyawan sakayyan ta Allah na  jin kunyan  ma'abotanta  , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ( Amma dayan sai ya ji kunya sai Allah ya ji kunyar sa ) Buhari da Muslim ne suka rawaito 
           Tushen kunya kuma shi ne a ji kunyar Allah madaukaki, ta yanda kar ya gan ka  a inda  ya hane ka,  kar ya rasa ka kuma a in da ya umarce ka ,    Allah ne ya fi cancanta da a ji kunyar sa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ( Ku ji kunyar Allah cancantar kunyar sa) Tirmizi ne ya rawaito  
    Kunyar  Allah shi ne Allah ya jefa wani haske a zuciya da zai sa ya rinka ganin Allah gaba gare shi lokacin da yake shi kadai ko a cikin jama'a,  jin kunyan Allah  na tabbatuwa ne  ta hanyar tsinkayar baiwar sa da girman ni'imominsa tare da halarto da laifuka na rayi tare da gazawanta , kuma da sanin cewa yana tsinkayan abin da yake na  sirri da wanda ya fi boyuwa: ((Allah) Ya san yaudarar idanu da abin da kiraza ke boyewa) sura Al-Gafir aya 19  Allah madukakin sarki ya ce : (  Suna neman boyewa daga mutane  kuma ba sa neman boyewa daga Allah  alhali kuwa shi yana tare da su ).
 Idan bawa ya san cewa Allah madaukakin sarki yana kallon shi ;  kuma cewa  yana   gaban idon sa ne kuma yana jin sa  kuma  ya kasance mai jin kunya to sai ya ji kunyar kada ya kutsa zuwa ga  abin da zai fusata  shi  tare da mutum akwai mala'ikun  da ba sa rabuwa da shi yana daga cikin karrama su ka ji kunyar su (  Lalle ne a kanku  hakika akwai  matsara . masu daraja marubuta . Suna sanin abin da kuke aikatawa )  .
      Ibnul  Kayyim  Allah ya mishi rahama ya ce : " Ai ku  ji kunyan wadannan matsara din ku karrama su   ku ga kimar su   , ku ji nauyin su ganku  kuna aikata abin da ku ke jin kunyar wasun ku su ga kuna aikatawa ". 
            Jin kunyan mutane yana haifar da mutunci da kyawawan dabi'u  kai ko da ma a ce  mutum musulmi   bai samu wani Abu daga dan uwan shi ba sai kunyar  sa da zai hana shi aikata  sabo to ya isar mishi, wannan wani  alheri ne da zai taimakawa ma'abocin shi bisa jin kunyar Allah , to duk wanda baya kunyar mutane  to baya kunyar Allah , haka kuma duk wanda   ya zauna da ma'abota kunya , kunyar shi za ta sabunta   .
         Wanda ya fi dacewa mutum ya girmama shi ne kansa , duk mutumin da ya aikata wani aiki a sirrace  wanda ake jin kunyar aikata shi a  bayyane to bai kimanta kan sa ba,  wanda ya ji kunyar mutane bai ji kunyar kansa ba  to kansa ta fi walakantuwa a gunshi fiye da wanin shi  wanda ya ji kunyan wani kuma ya ji kunyar kansa bai ji kunyar Allah ba to baisan Ubangijin sa ba,  wanda  kunya ya lullube masa tufafin shi to mutane ba za su ga aibin shi ba.
   Bayan haka ya ku Musulmai   to musulunci addini ne na kyawawan halaye da  kyawawan dabi'u , ya tattaro daga halayya mafi kyansu   da sifofi kuma mafi daukakan su  ba wani alheri face ya yi umarni da shi , ba wani sharri kuma face ya yi gargadi game da shi,  to wajibi ne gare mu muyi riko da shi  kuma muyi alfahari da shi  kuma mu kira  mutane zuwa ga shi , jin kunyar Allah shi ne ta hanyar bin umarninsa  da kuma nisantar saba mishi .
       INA NEMAN TSARIN ALLAH DAGA SHARRIN  SHAIDAN  ABIN  JEFEWA
(Kuma wane ne ya fi  kyau ga addini daga wanda  ya sallama fuskar sa ga Allah alhali kuwa yana mai kyautatawa kuma ya bi akidar Ibrahim yana mai karkata ga gaskiya )
 Allah ya sa mini albarka ni da ku cikin alkur'ani mai girma,  kuma Allah ya amfane ni da ku da abinda yake cikin sa na daga ayoyi da ambato mai hikima , ina fadin wannan magana tawa kuma ina mai neman gafarar  Allah  da ni da ku da dukkan musulmai  daga dukkan zunubai ku nemi  gafarar shi lallai shi mai gafara ne mai jin kai
 HUDUBA TA BIYU 
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawan sa  , godiya ta tabbata a gare shi bisa  datarwar sa da baiwarsa na shaida  ba abin bautawa da gaskiya  sai Allah shi kadai yake bashi da  abokin tarayya   muna mai girmama sha 'anin sa,  na shaida Annabinmu Muhammad bawan sa ne kuma mManzon sa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan sa da sahabbansa  da aminci tabbatacce mai yawa ,
 Ya ku Musulmai   :
  Kunyan da yake abin yabawa a maganan Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ita ce   wannan dabi'ar  da ke sanya mutum ya aikata kyakkyawan abu ya bar mummuna amma rauni da gazawa, Wanda ke sa gajartawa a wani abu na daga hakkokin Allah, ko hakkokin bayinsa,wannan ba su da alaka da kunya a wani abu, in ya hana ma'abocinsa wani alheri to bai zama abin a yaba ba. Aisha Allah ya kara yarda a gare ta ta ce : (Madalla da matayen Ansar kunya bai hana su neman fahimtar addininsu ba) Muslim ne ya rawaito.
Babu kunya cikin neman sanin addini, wanda ya bar ilimi don kunya to zai zauna cikin jahilci har abada ya hana kansa alheri.
Mujahid Allah ya masa rahama ya ce :  ( Mai kunya ko Mai girman kai ba zai samu ilimi ba)
Kuma ku sani Allah na umartanku da salati da aminci ga Annabinsa    
           ( lalle Allah da malaikunsa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi da aminci tabbatacce.)  
               
  










































ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق