HUDUBAR MASALLACIN
ANNANBI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU
TABBATA A GARE SHI NA SHAIK ABDULMUHSIN AL-KASIMI NA 13- 3-1439 AH
HUDUBAR FARKO :
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah
madaukakin sarki muna gode mishi kuma
muna neman taimakon sa , muna neman gafarar sa
, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunan mu , da munanan
ayyukan mu , duk wanda Allah ya shiryar da shi ba bu mai batar da shi , duk wan
da ya batar kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya
sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi
Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi da iyalan sa da sahabban sa da
aminci tabbatacce mai yawa .
BAYAN HAKA :
Ku ji tsoron Allah -ya ku bayin Allah- hakkin tsoron sa da tsoron Allah ne ake haskaka basira da
zukata kuma ake kankare kusakurai da zunubai ,.
YA KU MUSULMAI:
Allah mai tausayi ne ga bayinsa , yana tausaya musu ta inda ba su sani
ba, yana sanya musu sababi na maslahohin
su ta inda ba su zata ba , lalle shi mai
kyautatawa ne kuma mai rahama ne mai
kyauta kuma mai karamci, ya yalwata
ni'imomin shi a gare mu na bayyane da na boye, Allah madaukakin sarki ya ce : ( kuma idan
kun kidaya ni'imar Allah ba ku iya lissafa ta )
Akwai wata ni'ima
mutane basu isa su wadatu ga barin ta ba a ko wani hali, Allah ya sanya ta dalilai ne na tabbatar da rububiyyar sa Allah madaukakin sarki ya ce : ( Shin kuma ba su gani ba , cewa lalle mu muna
kora ruwa zuwa ga kasa kekasasshiya sa'annan mu fitar game da shi wata shuka , wadda dabbobin su , da su kansu ke ci daga gare ta
? ashe fa ba su gani ba ? )
Allah ya
gagari bayin shi da su kawo kwatankwacin ta ( Shin
kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha
shin ku ne kuke saukar da shi daga girgije ko kuwa
mu ne masu saukarwa ? Da mun so da mun mayar da shi ruwan zartsi to don
me ba ku godewa ) , gaibi ne, ba wanda ya san lokacin shi na tabbas da
gwrgodon shi da amfanin shi sai Allah ,
Allah madaukakin sarki ya ce : ( Lalle Allah a wurin sa ne kawai sanin sa'a yake , kuma yana saukar da girgije kuma yana sanin abin da yake a cikin
mahaifannai).
yana daga cikin hujjoji na tabbatar da uluhiyyar Allah da
cancantar shi da a bauta mishi shi kadan shi , akwai saukar da ruwa daga
sama Allah madaukakin sarki ya ce :( kuma ya saukar da ruwa daga sama sa'annan ya fitar da abinci daga 'ya'yan itace game da shi ) .
Kuma shi din
yana daya daga cikin dalilai na fitarwa daga kabari da tadawa, Allah madaukakin sarki ya ce:( Kuma akwai
daga ayoyin sa cewa lalle kai kana ganin
kasa kekasasshiya , to, idan mun saukar da ruwa a kanta sai ta girgiza kuma ta
kumbura, lalle wannan da ya raya ta hakika , mai rayar da matattu ne, lalle shi
mai ikon yi ne akan ko wani abu ) da shi ne Allah ya ke rahama yake kuma
azabtarwa , Allah madaukakin sarki ya
ce:( kuma da sun tsayu sosai akan hanya da lalle mun shayar da su daga ruwa
mai yawa) .
Ruwa daukaka ne
kuma da girma da izza ne, kuma al'arshin
mai rahama yana kan ruwa, Allah madaukakin sarki ya ce : ( Al'arshin sa ya
kasance a kan ruwa ) yana daga cikin
ni'imomin Allah masu yawa wanda Allah ya
yi shi har ga wadanda suka gabace mu ni'ima da shi
, wanda ya gode daga cikin su Allah sai ya kara mishi, wanda kuma ya butulce mishi sai Allah ya azabtar da shi , Allah
madakakin sarki ya ce : ( Shin ba su gani ba
da yawa muka halakar da wani karni daga gabanin su , mun mallaka musu, a
cikin kasa abin da ba mu mallaka muku ba
, kuma muka saki sama akan su tana ta
zuba ).
Sabo da kasancewar sa
ni'ima mai girma , Allah ya turo gaba
gare shi abin da ke albishir da zuwan
shi Allah madaukakin sarki ya ce : ( kuma shi ne ya aiko mana iskokin bushara gaba ga rahamar sa ) yana daga cikin rahamar Allah ga bayin sa ya jefa
farin ciki da annashuwa ga zukatan su ,
dalilin dubin su zuwa ga abin da suke kallo na daga ni'imomin shi abin sabontarwa , yana daga cikin abin da yake sanya walwala ga zukata jin dadin da suke yi na saukar
ruwan sama bisa kasa Allah madaukakin sarki ya ce : ( Kuma shi ne
ke saukar da girgije (ruwa) a bayan sun yanke kauna kuma
yana watsa rahamar sa alhali
kuwa shi ne majibinci mai godiya) .
Kuma kasa na
farin ciki da gabatowan sa , sai ta
girgigiza kuma ta kumburo ta fitar da adon ta Allah madaukakin sarki ya ce : ( Sa'annan
idan muka saukar da ruwa akan ta sai ta
girgiza kuma ta kumbura , kuma ta tsirar
da tsiri daga ko wani nau'I mai
ban sha'awa) da shi ne kasa ke
rayuwa bayan mutuwar ta , Allah madaukakin sarki ya ce : (
kuma muna saukar da ruwa daga sama
sai mu raya kasa da shi bayan mutuwar ta ) .
Kuma halittu
suna bishara ga junan su da gabatoawan
shi Allah madaukakin sarki ya ce : ( Sa'annan idan Allah ya sami wadan da ya so daga bayin
sa sai ga su suna bishara da shi ) kuma yana cikin sabuba na yardan Allah ga bawa
in ya gode mishi game da ita , Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lalle Allah na yarda game da bawa da ya ci
abinci ya gode mi shi game da shi ko ya sha abin sha sai ya gode mishi sabo da ta ) MUSLIM
NE YA RAWAITO .
Ruwa jinsin shi guda ne tare da babbancin lokuta da
kuma wurare, Allah ya halicce shi ba launi
ya samar da shi ba tare da dandano ba
kuma ya saukar da shi ba tare da wari ba , abu ne mai dadi da yake shiga cikin ciki mai
karfi yana zuwa ya cike kwarurruka
ya haura duwatsu , halitta ne mai girma
idan ya sauka a matsayin azaba babu mai yaye shi sai Allah , Allah
madaukakin sarki ya ce : ( Zan tattara zuwa ga wani dutse ya tare ni daga
ruwan ,(NUHU ) ya ce : babu mai tsarewa
a yau daga umarnin Allah face wanda ya yiwa rahama , sai taguwar ruwa ta shamakace a tsakanin
su sai ya kasance daga wadanda aka nutsar).
Amfaninsa ba shi
kididdiguwa mai yawan tsarki ne ga gardi ga dadi mai taimakawa Allah madaukakin
sarki ya ce : (kuma Muka saukar daga sama ruwa mai yawan tsarki ) yana tsarkake jiki da zukata, Allah Madaukakin Sarki ya ce : ( Alokacin da Allah ya ke rufe ku da
gyanngyadi domin aminci daga gare shi kuma yana saukar
da ruwa daga sama a kan ku domin ya tsarkake ku da shi kuma ya tafiyar da kazantar shaidan daga barin ku) .
Allah ya halicce
shi da albarka to sai ga 'yan kwayoyi
kadan kasa na rayuwa da su da wanda
suke cikinta Allah ya ce : (Kuma Muka
saukar da ruwa daga sama mai albarka),
da shi ne Allah ya ke tsirar da dukkan shuke-shuke Allah madaukakin sarki ya ce : ( Sa'annan muka fitar game da shi daga dukkan
'ya'yan itace ) Allah ya sanya shi mai kankara ne ga zunubai
da kusakurai a cikin alola Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce : ( Idan bawa musulmi
ya yi alola – ko mumini ya wanke fiskan sa
sai ya fita daga fiskarsa dukkan
kusakuran da ya kalla da idanuwan nasa tare da digon ruwan ko tare da digon
karshe na ruwan, to idan ya wanke
hannayen sa sai ya fita daga hannayen nasa dukkan kusakuran da hannayen
nasa suka aika ta tare da ruwan , ko tare da digon karshe na ruwan
- to idan ya wanke kafafuwan sa sai
dukkan kusakuran da yayi tafiya da wannan kafan zuwa gare ta ya fita tare da ruwan – ko tare da digon
karshe na ruwan- har ya fita tsarkakake
daga zunubai ) MUSLIM NE YA RAWAITO
Saukan sa zuwa doron kasa bisa gwargwado ya ke , ana kidanya adadin digon, Allah
madaukakin sarki ya ce : ( Muka
saukar da ruwa daga sama bisa gwargwado) karin sa daga gwargwadon sa wani azaba,
ne aya mai ban mamaki ana kiyayeshi
acikin kasa kuma yana da taskoki acikinta ba wanda yasansu sai Allah,
Allah madaukakin sarki yace: ( shin baka gani bane Allah ya saukar da ruwa daga sama sa'an nan ya gudanar dashi yana mare mari
acikin kasa ),wani sashin na fita daga dutse Allah madaukakin sarki yace( kuma
lallai ne daga duwatsu ,hakika akwai abin da maremari suke bubbuga daga gareshi
kuma lallai ne daga garesu hakika akwai abin da yake tsatsagewa har ruwa ya
fita daga gareshi )mai muujiza idan ya sauka a doron kasa, kasa keka sassa sai
ya canza launinta zuwa ga abin kallo mai ban kaye, Allah madaukakin sarki yace
: (Ashe ba ka gani ba lalle ne Allah ya saukar
da ruwa daga sama sai kasa ta wayi gari koriya ? lalle Allah mai tausayawa ne
mai kididdigewa )
Halittan Allah da ya yi ga ruwan
sama a matakansa alamari ne na ban mamaki Allah madaukakin sarki ya ce (Allah
ne wanda ke aika iskoki sai su motsar da giragizai sa'annan ya shin fida shi a cikin sama yadda
ya ke so kuma ya sanyashi wani babbake sannan ka ga ruwa na fita daga
tsakaninsa ,sa'annan idan Allah ya sami wadan da ya so daga bayinsa sai gashi
suna bushara da shi .)
Na daga cikin cikan ni'mar Allah a gare mu bayan saukarsa kiyaye shi a
kasa bayan saukarsa, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (sa'annan muka saukar da
ruwa daga sama sa'annan muka shayar da ku shi, kuma baku zama masu taskacewa a
gare shi ba.)
Ni'ma ce makusanciyar riska mai saukin samuwa, idan bayi sun sabawa Ubangijin su sai ya nesatar da su daga gare ta,
Allah Madaukakin sarki ya ce : (ka ce ko kun gani idan ruwanku ya wayi gari
fakakke to wane ne zai zo muku da ruwa wani mai bubbuga).
Kamar yadda wannan take ni'ima ce – to wannan iska mai taushi da kananan digo wanda ake ni'imta bayi da shi to
ta na iya sauyawa da umarnin Allah zuwa ga azaba, Allah ya halaka wasu mutane
da wannan ruwa sabo da juyawa Allah baya da suka yi, shi ne farkon azabar da aka
yi wa wata al'uma, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Mutanen Nuhu sun karyata a
gabaninsu ,sai suka karyata BawanMu ,kuma suka ce, Shi mahaukaci ne " kuma
aka tsawace shi)(Saboda haka ya kira ubangijinsa (ya ce),lalle ni
an rinjayeni sai ka yi taimako)
(sai muka bude kofofin sama da ruwa mai zuba ) (kuma muka bubbugar
da kasa ta zama idanun ruwa sannan ruwa ya hadu akan wani umarni da aka riga
aka kaddara shi. Kuma muka dauke Nuhu akan jirgi na alluna da kusoshi. Tana
gudana a cikin kiyayewarmu domin sakamako ga wanda aka yi wa kafircin).Alkamar
9-14
Fir'auna ya yi girman kai ga musa ya mishi alfahari da ruwa sai ya ce :
(Ashe mulkin Masar ba a gare ni ya ke ba , kuma wadannan kogunan suna gudana daga karkashi na?) Zukhruf 51
Sai Allah ya halaka shi sakamakon girman kai da ya yi, ya sanya shi abin
lura ga mutane,
Allah Madaukakin sarki ya ce : (Har a lokacin da nutsewa ta riske shi
yace : Na yi imani cewa Hakika babu abin bautawa face wannan da banu Isra'ila
suka yi imani da shi kuma kuma ni ina daga Musulmai). Yunus 90
Ya kasance malalin Arimi
(Dam) ga mutanen Saba'i ya yin da suka
kafurcewa ni'imar Allah sai Allah ya kekketa su da shi kekketawa, Allah
Madaukakin sarki ya ce :(sai suka bijire saboda haka muka saki malalin
arimi(dam) a kansu, kuma muka musanya musu gonakinsu biyu da wadansu gonaki biyu
masu 'ya'yan itace kadan : Talakiya da goruba da wani abu na magarya kadan ).
Saba'I 16.
Hakika Allah ya sanya shi nasara ga muminai a yakin badar, Allah
Madaukakin sarki ya yace : (A lokacin da Allah ya ke rufe ku da
gyangyadi domin aminci daga gare shi ,
kuma yana saukar da ruwa daga sama a kanku, domin ya tsarkake ku da shi, kuma ya tafiyar da
kazantar shaidan daga barinku, kuma domin ya daure akan zukatanku, kuma ya
tabbatar da kafafu da shi.) Anfal 11
Kuma shi yana daga cikin ni'imomin da idanuwa ke jin dadi da shi a cikin
aljanna mai ni'ima.
Allah Madaukakin sarki ya ce : (A cikin ta akwai wadansu koguna na
ruwa ba mai sakewa ba).
Kuma 'yan wuta suna neman agaji da shi
Allah Madaukakin sarki ya ce : (Kuma abokan wuta suka kirayi abokan
Aljanna cewa , ku zubo a kanmu daga ruwa ko kuwa daga abin da Allah ya azurta
ku, su ce : lalle ne Allah ya haramta su a kan kafurai) Araf 50
Bayan haka ya ku Musulmai!
To ruwa na daga cikin ayoyin Allah da ke wajabta imani, Allah Madaukakin
sarki yace : (Kuma muka sanya dukkan komi mai rai daga ruwa shin ba za su yi
imani ba? ) Anbiya' 30
Aya ce mai ban kaye ba wani da ke ja cewa daga Allah ne, ba kuma
wanda ke samar da shi koma bayansa.
Allah Madaukakin sarki yace : ( Kuma lalle idan ka tambaye su wane ne ya
saukar da ruwa daga sama har ya rayar da kasa,game da shi a bayan mutuwar ta
lalle suna cewa, Allah ne).
Kuma wani ni'ima ce mai girma
daga Allah,tana tare da mu a kowani wuri da
lokaci, to ya wajaba a gare mu mu yi godiya game da ita, da tunani cikin sha'aninta , da biyayya ga Mahaliccinta,
kuma kada mu rudu da falalar da Allah ya mana da ita, kar mu yi barna a
cikinta, kuma ya dace mu rike ta abin taimako don raya lahirar mu.
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa.
(sai nace ku nemi gafara daga Ubangijinku lalle ne shi ya kasance mai gafara ne, ya sako girgijen sama akan ku da
ruwa mai bubbuga).
Allah ya sanya mini albarka ni da ku a cikin Alkur'ani Mai girma.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawarsa , da
godiya bisa datarwarsa da baiwarsa, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai
Allah ina mai girmama sha'aninsa, na shaida Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma
Manzo sa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da
sahabbansa, da aminci tabbatace mai yawa,
Ya ku musulmai !
Allah Mai azurta bayinsa ne mai biyayyansu da fajirinsu, (Ba wata
dabba a cikin kasa face ga Allah
arzikinta ya ke)Hud 6
Kuma arzikin Ubangiji yana sauka
ne da biyayya a gare shi, da tuba zuwa a gare shi, Allah Madaukakin sarki ya ce
: (Kuma da lalle mutanen Alkaryu sun yi imani
suka yi takawa da mun bude Albarkoki a kansu daga sama da kasa)
Kuma godiya na kiyaye ni'ima yana shelanta karinta Allah Madaukakin sarki ya ce : (Kuma
a lokacin da Ubangijinku ya sanar, lalle ne idan kun gode,hakika ina kara muku,
kuma lalle ne idan kun kafirta, hakika azaba ta tabbas mai tsanani ce)
Ibrahim 7
Sannan ku sani Allah ya umarce ku da salati da aminci ga Annabin sa
….)
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق