HUDUBAR MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE
SHI NA SHAIK ABDULBARI ATHUBAITI NA 28-
2 1439.
HUDUBAR FARKO :
BAYAN HAKA:
Allah madaukakin sarki ya hore wannan duniya mai fadi ya sanya
ta farfajiya na burace-buracen Dan adam wanda
ba sa yankewa, mutane wasu a
cikinta na gajarta buri wasu kuma na
tsawaitawa Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Da
dan adam ya kasance yana da kwari na dabino da ya yi fatan ya sake samun
wani kamar sa sa'annan kuma ya sake samun wani kamar sa har ma ya yi fatan ya zama yana da
kwarurruka, ba abin da yake cika cikin Dan adam sai
turbaya ) Ibn Hibbana ya rawaito shi
a sahihin shi.
Dukkan wani
buri da ake fatan aikata aikin alheri
abun yabo ne, duk wani buri kuma da ake ja da abin da Allah ya
kaddara ko kuma ayi fatan samun abin da ba zai yiwu ba to
wannan abin zargi ne , shi buri yana
nuni ne da irin abin da mutum ke dauke da shi a zuciyar sa , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : ( Kuma rayi yana buri kuma yakan yi sha'awa). Akwai wanda yake wulgawa da burin sa zuwa ga
izza da daukaka wani kuma kan jefa burin sa zuwa ga cikin rami .
Ma'abota
himma da azama suna fadada burin su kuma su kawata rayuwan su da shi ga Umar Dan Khaddabi yana zaune cikin mutanen shi wata rana sai ya ce da su kowa ya fadi burinsa , sai wani mutumi ya ce : '' ina burin ace wannan gidan gaba daya a cike da zinari na
ciyar da shi a tafarkin Allah ''
, sai ya sake cewa:
'' kowa ya fadi burinsa'' sai wani mutumi ya sake cewa : '' ina fata a
ce wannan gidan a cike yake da
lu'u-lu'u , da Zubarjadi , da Jauhari na ciyar da shi a tafarkin Allah
kuma na yi sadaka da shi , sannan sai Umar ya ce : '' ku fadi burinku '' sai suka ce :
'' to, kai me kake gani ya Amiral muminin '' sai Umar ya ce : '' Ina fata
da ace wannan gidan a cike yake da mazaje irin su Abu Ubaida Dan Jarrah da Mu'azu Dan Jabal da Salim Maula Abi Huzaifa da
Huzaifatu Dan Yaman .
Kyakkyawan
buri na daga cikin kofofi ne na lada mai girma , Abu Kabshata Al anmari ya
rawaito daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi cewa ya
ambaci wasu mazaje guda hudu: ( Mutumin da Allah ya bashi dukiya da ilimi yana
aiki da ilimin sa a cikin dukiyar sa yana ciyar da ita bisa hakkin ta , da kuma mutumin da Allah ya
bashi ilimi bai bashi dukiya ba , to,
sai yana cewa ina ma da ina da irin wannan
( dukiyar) sai na yi aiki da ita kamar yanda yake aiki da shi Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : '' Duk ladan su iri daya ne da kuma mutumin da
Allah ya bashi dukiya amma bai bashi ilimi ba sai yana ta kwamacala a cikin
dukiyar tasa yana ciyar da ita ba a
cikin hakkinta ba , da kuma mutumin da Allah bai bashi ilimi ba bai bashi
dukiya ba to amma yana cewa ina ma da
ina da irin dukiyar da wane yake da shi
na yi irin aikin da yake yi da shi
, Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce : '' Dukan su biyu suna daidai a
alhaki ''). Ibn Maja ne ya rawaito shi.
Burace-burace shi
kadan shi ba yi da kima matukar bai hadu da aiki na kwarai ba tare kuma da
kyakkyawar niyya na gaskiya , da kuma
bin koyarwan Annabi tare da kuma juriya Allah
madaukakin sarki ya ce : ( Ku
yi gaggawa zuwa ga neman gafara daga Ubangijin ku) shi burace-burace wani nau'I
ne na addu'a wanda ke tabbatuwa idan an amsa shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : ( Idan dayan ku
zai yi adu'a to, ya roka da babban masaki
, domin Ubangijin shi yake tambaya) Haithami
ya rawaito
Albani ya ce marawaita hadisan amintattu ne kuma marawata ne na sahihi.
Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( idan dayan ku zai yi buri to, ya yi dubi zuwa
ga abin da zai burata , domin bai sani ba me za a rubuta mishi na
daga burin nasa . Ahmad ne ya rawaito
da isnadi ingantacce .
Kamar yan da mai hankali ba
zai yi fatan fitintinu ba ko haduwa da
makiya , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( kar ku
yi fatan haduwa da makiya , ku roki Allah
samun sauki idan kun hadu da su
to ku yi hakuri ).
Mus'ab da Urwa da
Abdullahi dan Zubair da Abdullahi dan Umar suka hadu a Hijir , sai suka ce kowa ya ambaci burinsa , sai
Abdullahi dan Zubair ya ce ni buri na in
samu kalifanci , Urwa kuma ya ce : '' ni kuwa buri na a dauki ilimi daga gare
ni , shi kuma Mus'ab sai ya ce na ga na rike Mulkin iraki na hada tsakanin
Aisha 'yar Dalha da sukaina 'yar Husain , shi kuma Abdullahi Dan Umar ya ce ni
kuma buri na in samu gafara , dukkan su kuma sai suka samu abin da suka nema, ta iya yiwuwa Ibn Umar din ma an gafarta
mishi .
Umar dan Abdul'aziz Allah
ya mishi rahama ya kasance yana da himma madaukakiya wanda kuma ya cimmata da falalan Allah , ana kuma fatan dayan ma ya cimmata yana cewa ina da rayi mai yawan shauki ya yi
shaukin Fadimatu 'yar Abdulmalik kuma na
aure ta, na yi shaukin zama gwamna kuma
na zama, na yi shaukin kalifanci(shugaban
kasa) kuma na riske ta , kuma na bukaci
Aljanna kuma ina fatan na same ta in
Allah mai girma da daukaka ya so.''
Musulunci na kira zuwa ga
yin fatan alheri da yada fata nagari da rayuwa, ba ya kira zuwa ga mutuwa da
abu mara kyau, bai dacewa da shi munanan fata da neman mutuwa ko da fitinu sun
tsananta, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Kada
dayanku ya yi fatan mutuwa sakamakon wani cuta da ya same shi, in har ba makawa
sai ya yi to ya ce : Ya Allah ka raya ni muddin rayuwar ta kasance alheri a gare ni, kuma ka kashe ni
idan mutuwa ta fi alheri gare ni) Buhari da Muslim ne suka rawaito.
Yin
fata nagari na nuni ne ga kyautata zaton bawa ga Ubangijinsa, ya zo cikin Hadisin Kudsi : '' Ni
ina gun da bawa na ya zace ni, to , ya zaci
duk abin da ya so game da ni '' ibn Hibbana ya rawaito shi a sahihin sa . Wato ni
ina da ikon na aikata da bawa na duk abin da ya zaci zan aikata da shi . To
idan bawa ya kyautata zato ga Ubangijin sa , sai hakan ya juyo cikin
Burin sa sai ya zame madaukaki a
kima da kuma manufa .
Mai hankali yana saka burace –buracen sa ne tare da
, jin ni'imar Allah a gare shi ba tare
da ya yi hasada ga 'yan uwan sa ba , ko fatan abin hanun su ba . Allah madaukakin sarki ya ce : (kuma kada ku yi burin abin da Allah ya fifita
shashenku da shi a kan sashe.)
Musulmi na da masaniyar cewa cin ma buri na hanun Allah ne shi kadansa,
sabo da haka ba zai yi raki ko yayi bakin ciki ba sabo da rasa cin ma burinsa
da ya ke fata ba, Alheri na cikin zabin
Allah da kuma godiyan bawa ga Ubangijin
sa a ko wani hali Allah madaukakin sarki ya ce : (Akwai fatar
cewa ku ki wani abu alhali shi ne
mafi alheri a gare ku kuma akwai fatar
cewa kuna son wani abu alhali kuwa shi ne mafi sharri a gare ku , kuma
Allah ne yake sani kuma ku ba ku
sani ba ) .
Iblisu shi ne
tushen burace-burace mara kan gado , kuma ya yi alkawarin ya nitsar da bayin Allah cikin kogin burace
–burace na karya na jin dadin gaggawa ( duniya ) da kuma sa'ada
mara tabbas kamar yanda yake kawatawa
dan Adam mummunan aikin shi sai ya gan shi kyakkyawa Allah madaukakin sarki ya ce : ( Kuma
wanda ya riki shaidan majibinci baicin Allah , to , hakika ya yi hasara
bayyananniya yana yi musu alkawari kuma
yana sanya musu guri alhali shaidan baya
yi musu wa'adin komai face rudi .)
Idan
burace-buracen mutum ya gajarta bisa ga kyala-kyalan duniya, ya zama babu na lahira to hakika ya kauce hanya ya bar tafarki
mikakke Allah madaukakin sarki ya ce : ( wanda
ya kasance yana nufin duniya sai mu gaggauta abin da muka ga dama ga wanda muka ga dama a cikin ta sannan mu sanya jahannama gare
shi a lahira ya shige shi abin zargi , abin korewa. wanda yake nufin lahira da aikin sa ya yi kokari ya aikata aiki irin nata a gare ta alhali shi yana mai bada gaskiya
ga Ubangiji , to, wadancannin ka aikin su ya kasance abin godewa) .
Wanda
burace-buracen sa ke nitso a kogin mafarkai yana fadake ko yana bacci ba tare
da wani aiki ba, ya kewaye jikin sa da kasala , to ba zai tsinkaya ba sai
kawalwainiya, an karbo daga Anas Dan Malik Allah ya kara yarda a gare shi ya ce
: daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Mai wayo shi ne wan da ya yi wa kan sa hisabi ya yi kuma aiki domin bayan
mutuwa , shi kuma gajiyayye shi ne wanda
ransa ya bi abin da ya ke so ya yi kuma gurace-gurace a wurin
Allah ).
Wanda ya bi hanyoyin da aka haramta domin
cimma burace-buracen sa ta hanyar komawa zuwa ga matsafa , ko 'yan
siddabaru , to hakika ya zalunci kansa Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Duk wanda ya je wurin boka ko matsafi
ya yarda da abinda ya ce to, hakika ya kafurce da abin da aka saukarwa Muhammadu ). Dabarani ne ya rawaito Ibn
Hajar kuma ya hassana isnadin sa.
HUDUBA TA
BIYU
A cikin kaburbura wanda ake fara
rayuwan barzaku akan samu gurace-gurace
masu tsananin kunci , burin mumini a
kabarin sa shi ne kiyama ta tsaya , sabo da irin abin da ya ke gani kuma yake
sauraro na daga ni'ima da farin ciki , amma
kafuri burin sa kada alkiyama ta tsaya sabo da abin da yake gani da daga
azaba mai tsanani .
Mamaci na fatan sake dawowa duniya don riskan abin da ya tsere mishi na daga
da'a ya samu ya yi sallah ko da raka'a
biyu ne
Annabi ya wuce wani kabari sai ya ce : ( Wane ne ma'aboci wannan
kabari ? sai suka ce wane ne , sai ya ce
: '' raka'a biyu ya fi soyuwa ga wannan
(mutumin kabarin ) akan duk sauran abin duniya) .
Matattu na fatan komowa
duniya domin su yi sadaka kuma su
ambaci Allah ko da da tasbihi guda ne ,
ko da hailala guda ne , Allah madaukakin sarki ya ce : ( KU CIYAR DAGA ABIN DA MUKA AZURTA MUKU TUN GABANIN MUTUWA BA TA ZO MUKU BA YA FARA
CEWA UBANGIJINA DON ME BA KA JINKIRTA MINI BA
ZUWA AJALI MAKUSANCI IN YI SADAKA DA ZAKKA , DON NA KASANCE DAGA
CIKIN SALIHAI ) .
Burin mai radadi wanda ba makawa
daga gare su , shi ne kiran hasara ga 'yan wuta ranar alkiyama don shi kafuri
mai sabo a yayin da ya karbi littafin
shi da hanun hagu , kuma ya ga makomarsa sai ya yi fatan ina ma da ya kasance turbaya Allah
madaukakin sarki ya ce : ( wancannin ka shi ne rana ta gaskiya wanda
ya ga dama zai riki komawa zuwa ga
Ubangijin sa . Lalle ne mu mun yi mu ku gargadin azaba
makusanciya ranar da mutum ke dubi zuwa
ga abin da hannayen sa suka aikata , kuma kafuri ya ce kaito na da dai
na zama turbaya ).
Mafi daukakan matsayi a tafiya na buri shi ne abin da 'yan aljanna
za su samu na ni'iman burace-burace , kuma Ubangijin su mai kyauta yana mai kyauta a gare su kuma yana musu kari da
karamcin sa, mafi karancin guri da
ma'abota sa'ada shi ne wanda zai shiga aljanna
a karshe , ta kammala kuma ta
adonta a gare shi sai Ubangiji ya ce mishi fadi burin ka sai bawan ya yi ta buri , har iya kurewar
burin sa sai Allah ya ce wa bawan na shi an baka abinda ka burata da
kwatankwacin shi guda goma tare da shi.
Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Idan 'yan aljanna sun shiga aljanna sai Allah
madukakin sarki ya ce shin ko kuna sha'awan
wani abu na muku kari sai su ce ya Ubangijin mu shin yanzu akwai
abun da ya fi alherin fiye
da abinda ka bamu sai ya ce e, yarda na ya fi girma ).
TA TIKE
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق