HUDUBAR MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN
ALLAH SU TABBATA A GARE SHI14-2-1439AH NA SHAIK SALAH BIN
MUHAMMAD AL- BUDAIR
Ya ku musulmai! dukiya ganima ce mai tafiya , kuma dukkan
wani dukiya na saya da sayarwa ana kwadayin shi ana haba-haba da shi ana kwallafa
rai a kan shi 'yan fashi da barayi na
sa ido gare shi.
Shi barawo fasiki yana likimo
da sa ido, da kirdadon lokacin
gafala a duk lokacin da masu dakon
dukiya suka gafala daga dukiyan su
; sai ya
lallabo ya awon gaba da ita a boye
mai mummunan dabi'a mara kima , kaskantacce mai bushewan ido, mai yawan
zalunci mai afkawa hakkin wanin sa , ba
mai tsallake gidaje da aka katange su ya keta alfarmar abin da aka adana , ya balle
kwado , ko ya yanke aljihu, ya keta
hannayen riguna ya saci dabinai da shuki da 'ya'yan itace daga ma'adanan su , ba mai yin haka sai
fasiki, masharraci , barawo maha'inci ,mayaudari kazantacce , tsinanne
bisa harshen Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi.
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara
yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :
( Allah ya tsinewa barawo ya
saci kwai a yanke hanun shi ya saci
igiya a yanke hanun shi ) Buhari da
Muslim ne suka rawaito
Barawo fasiki
an mishi alkawarin narkon azaba da ukuba. An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare
shi a Hadisin Kusufi ya ce: Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ( Ba wani abu da aka alkawarta mu ku shi face na
gan shi cikin wannan sallar tawa , hakika an zo da wuta , wannan kuma a yayin da
kuka ga na dan ja baya , tsoro na kada harshenta ta taba ni , har na ga a cikin ta wani ma'aboci sanda yana jan hanjin sa a cikin wuta , ya kasance yana yiwa Alhazai sata da sandan
shi idan an ankara sai ya ce sandar ce
ta makale da kayan , in an gafala sai ya
wuce da shi .) Muslim ne ya rawaito
Hanun barawo hanu ne mai kwace mai ketare iyaka
, shari'a ya wajabta a yanke shi a raba
shi da ita domin tsoratarwa da gargadi da kuma ukuba domin bada kariya ga
dukiya da kayan albarkatu da kadarori
, Allah mai girma da daukaka ya ce : (Kuma Barawo da barauniya sai ku yanke hannuwan su , sakamakon abin da
suka aikata a kan azaba daga Allah kuma Allah mabuwayi ne mai hikima )
An karbo daga Dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi shi da mahaifin shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata ya yanke hanu a kan
garkuwan da bai wuce dirhami uku
ba ,) BUHARI DA MUSLIM NE SUKA
RAWAITO SHI
Malamai suka ce game
da hanun barawo ; ya yin da ( Hanun) ya
kasance amintacce sai ya kasance yana da
kima amma lokacin da ya yi ha'inci sai ya walakanta , wanin su yana cewa ; izza ta amana tana da ban mamaki na tsada da kuma sauki
*** ha'inci kuma ya kaskanta to
ka fahimci hikimar mahalicci
YA BAWAN ALLAH :
Ka kame daga kiyayyanka
kar ka kasance bawa ga shaidaninka , domin alhurmar dan uwanka Musulmi kamar alhurmar kanka ne haka nan kuma alhurman dukiyan shi
kamar alhurmar dukiyar ka ne
kuma alhurman gidan shi da iyalan shi
kamar alhurmar gidanka ne da iyalan ka ne , shin za ka yarda wani ya yi ta'addanci da dukiyar ka da iyalan ka ne
da gidan ka da iyalan ka kamar yanda ka yi ta'addanci zuwa ga wani
? to idan har baka yarda da hakan ga
dukiyar ka ba , to mutane ma baza su yarda da hakan ga dukiyar su ba .
YA BAWAN ALLAH :
Ka tuna ranar bijirowa kuma ranar azaba ka tuna ranar da za ka tsaya a gaban
Ubangijin ka mai girma mai daukaka , ka
tuna ranar da dukiya ba zai yi amfani ba ko wadata , ka tuna ranar dauri da sarka da
ankwa.
YA KU MUSULMAI:
Kada dayan ku ya dauki dukiya ko kayan wani ba
tare da izinin shi ba kankani ne ko mai yawa ,
An karbo daga Abdullahi Dan Umar Allah ya kara masa yarda shi da
mahaifin shi, ya ce : Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Kada dayanku ya tatsi nonon akuyan wani ba
tare da izinin shi ba , shin dayan ku na so a zo wurin shansa a fasa ma'adanan ruwan sa? Sabo da nonon awakin na su na adana musu
abincin su ne to, kar dayan ku ya tatsi
nonon wani sai da iziznin shi .) BUHARI
DA MUSLIM NE SUKA RAWAITO
An karbo daga Abu
Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : wata rana muna tare da Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi a halin tafiya sai muka ga rakuma
an tirka ta da wasu kayoyin itace sai muka tafi zuwa gare ta don mu kama ta ,
sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
kira mu , sai muka dawo zuwa gare shi , sai ya ce : '' wannan rakumar na mutanen
wani gida ne na musulmai shi ne
abincin su, yanzu zai muku
dadi ku koma zuwa ga sulken
ku ku same shi ba komai a cikin shi an tafi da shi? shin
kuna ganin hakan adalci ne ? sai suka ce : '' A'a'' sai ya ce : '' to, ai shi ma wannan kamar haka
ne .) AHMAD NE DA IBNU MAJA'
suka rawaito shi
An karbo daga Abu Humaid
Assa'idi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : ( Kada
dayan ku ya dauki sandan dan uwan shi ba
tare da yardan shi ba ). Wannan sabo da
tsananin abin da Annabi ya haramta ne na
dukiyan musulmi bisa ga musulmi ) Ahmad ne da Ibn Hibban ya rawaito
shi
To idan wannan akan kananan abubuwa ne wanda basu taka kara sun karya ba a gun ma'abotan shi kamar sanda da makamantar ta, to abin da ke sama da wannan shi ya fi dacewa a yi gargadi a kan su .
Duk wanda ya kwace
kasan wanin sa bisa karfi ba tare da hakki ba , ko ya riki taki a na
daga hanyan musulmi ko zira'i ko kuma
ya taba cikin dukiyar al'uma ba tare da hakki ba , to ya kai kansa ne ga azaba mai tsanani da kuma
ukuba mai karfi . An karbo daga Hakam dan Haris Assulami Allah ya yarda da shi ya ce : Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce : ( Duk wanda ya dauki taki
a hanyar musulmai zai zo ranar alkiyama yana dauke da shi , daga kassai guda
bakwai ) Abu ya'ala ne ya rawaito shi
An karbo daga Abu
Humaid assa'idi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi ya ce : ( Wallahi dayan ku ba zai riki wani abu ba na
hakkin wani ba tare da izinin shi ba face ya
hadu da Allah yana mai dauke da wannan abun ranar alkiyama to lalle zan san dayan ku da zai hadu da
Allah yana dauke da rakumi yana kuka ko
saniya na kara , ko akuya na kara , sannan ya daga hanun shi har a ka ga hasken
hamatan shi , yana cewa ya Allah na isar da sako ) BUHARI NE YA RAWAITO
An karbo daga Abu
malik Al-Ashja'I Allah ya kara yarda a
gare shi ya ce : Annabi tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi
ya ce : ( Mafi girman
sata a wurin Allah shi ne satan
zira'i na kasa , za ka samu mutum biyu ne makwabta a kasa ko a gida , sai
daya ya yanka zira'I guda na daga na dan'uwan shi idan ya yanka za a nade shi da kassai bakawai
ranar alkiyama )
Idan barawo ya tuba daga sata da aikata laifi
, to , Allah ya karbi tuban shi na abin
da ke tsakaninsa da shi , amma dukiyan
mutane dole ne ya mayar zuwa gare su , idan abin da a ka satan na nan to ya
wajaba a maida shi zuwa ga mai shi ko kuma a bada wani abu da ke a
madadin sa ko farashin sa da yake
dai-dai da shi , ko kuma a nemi yafiya daga gare shi.
Allah ya kare ni da ku daga
fadawa zuwa ga cin abin da yake mai
halakarwa , da abubuwa masu shigowa
kazantattu da kuma dukiyan haramun ,
Allah ya kare ni da ku ya wadatar da mu da halal , domin shi mai kyauta
ne mai karamci , ina neman gafarar Allah
kuma ku nemi gafarar sa domin shi
ya kasance mai yawan gafara ne ga masu komawa gare shi .
HUDUBA TA BIYU
YA KU MUSULMAI :
Wanda ya shiga daga cikin
mu - ya ku jama'ar Masulmai - garin wadanda ba musulmai ba da
alkawari da aminci, wato wannan biza da ake bada wa a gare shi don ya
samu daman shiga garin su to, ya haramta ya ha'ince su , ko ya musu sata ko
ya ketare iyaka gare su ga amincin su
da rayukan su , da mutuncin su da
kadarorin su , wanda ya saci wani abu na su to ya wajaba ya mayarwa masu shi
sabo da dukiya ne katangagge .
Sabo da haka ne yayin da
Annabi ya yi hijira zuwa ga madina ya umarci Aliyu da ya maida ajiyan Quraishawa da ke gunsa , Ibn Sa'ad ya
kawo a cikin littafin shi ADDABAKAT AL KUBRA
: cewa Aliyu dan Abi dalib Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Yayin
da Manzon Allah ya fita; zuwa
hijira ya umarce ni da na tsaya bayan
tafiyar sa don na sauke ajiyan mutane da
ke gun sa , Annabi ya zauna a Makka har shekaru sha uku tare da shi akwai
musulmai bai taba yiwa wani umarni ba,
da ya kwace dukiyar mutane ko ya
je ya zubar da jini , ko ya keta mutunci , sannan Annabi ya yi hijira ya bar
musulmai suna cikin rauni ko suna cikin buya a makka bai
bada izini ga dayan su ba ya yi wani abu makamancin haka .
Musulunci na umarni da cika
alkawura da gaskiya wurin mu'amala , kuma yana hani da ha'inci da cin
amana da gaba da kiyayya.
Allah ya sanya ni da ku cikin
shiryayyu wadanda aka shiryar, ya kare mu daga hanyar masu ketare iyaka batattu ,
ku yi salati da aminci bisa ga
Ahmad mai shiryarwa mai ceto ga bayi gaba daya .
Ta tike
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق