الجمعة، 3 نوفمبر 2017

SATAR DUKIYA A MUSULUNCI

 HUDUBAR MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI14-2-1439AH NA SHAIK SALAH  BIN  MUHAMMAD AL- BUDAIR
Ya ku musulmai!  dukiya ganima ce mai tafiya , kuma dukkan wani dukiya na saya da sayarwa ana kwadayin shi ana haba-haba da shi ana kwallafa rai a kan shi   'yan fashi da barayi na sa ido gare shi.
                 Shi barawo fasiki yana likimo da sa ido, da kirdadon  lokacin gafala  a duk lokacin da masu dakon dukiya suka gafala  daga dukiyan su ;  sai ya  lallabo ya  awon gaba da ita    a boye  mai mummunan dabi'a mara kima , kaskantacce mai bushewan ido, mai yawan zalunci mai afkawa hakkin wanin sa  , ba mai tsallake gidaje  da  aka katange su  ya keta alfarmar abin da aka adana , ya balle kwado , ko ya yanke aljihu,  ya keta hannayen riguna ya saci dabinai da shuki da 'ya'yan itace   daga ma'adanan su , ba mai yin haka sai fasiki, masharraci , barawo maha'inci ,mayaudari kazantacce , tsinanne bisa  harshen Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
                             An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce :  ( Allah ya tsinewa  barawo ya saci  kwai a yanke hanun shi  ya  saci igiya  a yanke hanun shi ) Buhari da Muslim ne suka rawaito
                                 Barawo fasiki an mishi alkawarin narkon azaba da ukuba.  An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare shi a Hadisin Kusufi ya ce:  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (  Ba wani abu da aka alkawarta mu ku shi face na gan shi cikin wannan sallar tawa  ,  hakika an zo da wuta , wannan kuma a yayin da kuka ga na dan ja baya , tsoro na kada harshenta ta taba ni ,  har na ga a cikin ta wani ma'aboci sanda  yana jan hanjin sa a cikin wuta ,  ya kasance yana yiwa Alhazai sata da sandan shi   idan an ankara sai ya ce sandar ce ta makale da kayan , in an gafala  sai ya wuce da shi .) Muslim ne ya rawaito
         Hanun barawo hanu ne mai kwace mai ketare iyaka ,  shari'a ya wajabta a yanke shi a raba shi da ita domin tsoratarwa da gargadi da kuma ukuba domin bada kariya ga dukiya  da kayan albarkatu da kadarori ,  Allah mai girma da daukaka ya ce : (Kuma  Barawo da barauniya  sai ku yanke hannuwan su , sakamakon abin da suka aikata  a kan azaba  daga Allah kuma Allah mabuwayi ne mai hikima )
 An karbo daga Dan Umar Allah ya kara yarda a gare shi  shi da mahaifin shi  ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata ya yanke hanu a kan  garkuwan  da bai wuce dirhami uku ba ,)  BUHARI DA MUSLIM NE SUKA RAWAITO SHI
                         Malamai suka ce game da hanun barawo ;  ya yin da ( Hanun) ya kasance amintacce  sai ya kasance yana da kima amma lokacin da ya yi ha'inci sai ya walakanta , wanin su yana cewa  ; izza ta amana  tana da ban mamaki na tsada  da kuma sauki  *** ha'inci kuma ya kaskanta to  ka fahimci hikimar mahalicci
 YA BAWAN ALLAH :
Ka kame daga kiyayyanka kar ka kasance bawa ga shaidaninka , domin alhurmar dan uwanka Musulmi  kamar alhurmar kanka ne    haka nan kuma alhurman dukiyan shi kamar   alhurmar dukiyar ka  ne  kuma alhurman gidan shi da iyalan shi  kamar alhurmar gidanka ne da iyalan ka ne ,  shin za ka yarda wani ya  yi ta'addanci da dukiyar ka da  iyalan ka ne  da gidan ka   da iyalan ka  kamar yanda ka yi ta'addanci zuwa ga wani ?  to idan har baka yarda da hakan ga dukiyar ka ba ,  to mutane ma  baza su yarda da hakan ga dukiyar su ba .
YA BAWAN ALLAH :
 Ka tuna ranar bijirowa kuma ranar  azaba ka tuna ranar da za ka tsaya a gaban Ubangijin ka mai girma mai daukaka ,   ka tuna ranar da dukiya ba zai yi amfani ba ko wadata ,  ka tuna ranar dauri  da sarka da  ankwa.
           YA KU MUSULMAI:
 Kada dayan ku ya dauki dukiya ko kayan wani ba tare da izinin shi ba kankani ne ko mai yawa ,  An karbo daga Abdullahi Dan Umar Allah ya kara masa yarda shi da mahaifin shi,  ya ce : Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (  Kada dayanku ya tatsi nonon akuyan  wani  ba tare da izinin shi ba ,  shin  dayan ku na so a zo wurin shansa  a fasa ma'adanan ruwan sa?    Sabo da nonon awakin na su na adana musu abincin su ne  to, kar dayan ku ya tatsi nonon   wani sai da iziznin shi .) BUHARI DA MUSLIM NE SUKA RAWAITO
                            An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : wata rana muna tare da Annabi tsira da amincin Allah su  tabbata a gare shi   a halin tafiya sai muka ga  rakuma  an tirka ta  da wasu  kayoyin itace sai muka  tafi zuwa gare ta don  mu kama ta ,  sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare  shi  ya kira mu , sai muka dawo zuwa gare shi , sai ya ce : '' wannan rakumar na  mutanen  wani gida ne  na musulmai  shi ne  abincin su,  yanzu zai muku dadi  ku koma zuwa  ga sulken  ku  ku same shi ba komai  a cikin shi an tafi da shi?  shin  kuna ganin  hakan adalci ne ?  sai suka ce : '' A'a''  sai ya ce : '' to, ai shi ma wannan kamar haka ne .)  AHMAD NE DA IBNU MAJA' suka  rawaito shi
                    An karbo daga Abu Humaid Assa'idi  ya ce:  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (  Kada dayan ku ya dauki sandan dan uwan  shi ba tare da  yardan shi ba ). Wannan sabo da tsananin abin da Annabi ya haramta ne  na dukiyan musulmi bisa ga musulmi ) Ahmad ne da Ibn Hibban ya rawaito shi
                 To idan wannan akan kananan abubuwa ne wanda   basu taka kara sun karya ba  a gun ma'abotan shi kamar sanda  da makamantar ta,  to abin da ke sama da wannan shi ya fi  dacewa a yi gargadi a kan su .
                Duk wanda ya kwace kasan wanin sa bisa karfi ba tare da hakki ba , ko ya riki taki  a  na daga hanyan musulmi   ko zira'i ko kuma ya taba cikin dukiyar al'uma ba tare da hakki ba , to ya kai kansa ne  ga azaba mai tsanani  da kuma  ukuba mai karfi . An karbo daga Hakam dan Haris Assulami  Allah ya yarda da shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce : (  Duk wanda ya dauki taki a hanyar musulmai zai zo ranar alkiyama yana dauke da shi , daga kassai guda bakwai ) Abu ya'ala ne ya rawaito shi
               An karbo daga Abu Humaid assa'idi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (   Wallahi dayan ku ba zai riki wani abu ba na hakkin wani ba tare da izinin shi ba face ya  hadu da Allah yana mai dauke da wannan abun  ranar alkiyama   to lalle zan san dayan ku da zai hadu da Allah yana dauke da rakumi yana  kuka ko saniya na kara  , ko akuya na kara ,   sannan ya daga hanun shi har a ka ga hasken hamatan shi , yana cewa ya Allah na isar da sako )  BUHARI NE YA RAWAITO
              An karbo daga Abu malik Al-Ashja'I Allah ya kara yarda  a gare shi ya ce :  Annabi  tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya ce : (     Mafi girman  sata   a wurin Allah shi ne satan zira'i  na kasa ,  za ka samu mutum biyu ne makwabta  a kasa ko a gida  ,  sai daya ya yanka zira'I  guda na daga  na dan'uwan shi  idan ya yanka za a nade shi da kassai bakawai ranar alkiyama )
           Idan barawo ya tuba daga sata da aikata laifi , to ,  Allah ya karbi tuban shi na abin da ke tsakaninsa da shi ,  amma dukiyan mutane dole ne ya mayar zuwa gare su , idan abin da a ka satan na nan  to ya  wajaba a maida shi zuwa ga mai shi ko kuma a bada wani abu da ke a madadin sa ko farashin sa da  yake dai-dai da shi , ko kuma a nemi yafiya daga gare shi.
  Allah ya kare ni da ku daga fadawa  zuwa ga cin abin da yake mai halakarwa ,  da abubuwa masu shigowa kazantattu  da kuma dukiyan haramun  ,  Allah ya kare ni da ku ya wadatar da mu da halal , domin shi mai kyauta ne mai karamci , ina neman gafarar Allah  kuma ku nemi gafarar sa  domin shi ya kasance mai yawan gafara ne   ga  masu komawa gare shi .
          HUDUBA TA BIYU
YA KU MUSULMAI :
       Wanda ya shiga daga cikin mu  - ya ku jama'ar Masulmai -  garin wadanda ba musulmai ba  da  alkawari da aminci, wato wannan biza da ake bada wa a gare shi don ya samu daman shiga  garin su to,  ya haramta ya ha'ince su , ko ya musu sata ko ya ketare iyaka gare su  ga amincin su da  rayukan su , da mutuncin su da kadarorin su , wanda ya saci wani abu na su to ya wajaba ya mayarwa masu shi sabo da dukiya ne katangagge .
                   Sabo da haka ne yayin da Annabi ya yi hijira zuwa  ga madina  ya umarci Aliyu da ya maida  ajiyan Quraishawa da ke gunsa , Ibn Sa'ad ya kawo a cikin littafin shi ADDABAKAT AL KUBRA  : cewa Aliyu dan Abi dalib Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Yayin da Manzon Allah ya fita;  zuwa hijira  ya umarce ni da na tsaya bayan tafiyar sa don na sauke  ajiyan mutane da ke gun sa , Annabi ya zauna  a  Makka har shekaru sha uku tare da shi akwai musulmai bai taba yiwa wani umarni ba,   da ya kwace dukiyar mutane ko  ya je ya zubar da jini , ko ya keta mutunci , sannan Annabi ya yi hijira ya bar musulmai suna cikin rauni ko suna cikin buya a makka  bai  bada izini ga dayan su ba ya yi wani abu makamancin haka .
 Musulunci na umarni da cika alkawura da gaskiya wurin mu'amala , kuma yana hani da ha'inci da cin amana  da gaba da kiyayya.
  Allah ya sanya ni da ku cikin shiryayyu wadanda aka shiryar, ya kare mu daga hanyar masu ketare iyaka  batattu ,  ku yi salati da aminci bisa ga  Ahmad mai shiryarwa mai ceto ga bayi gaba daya .
 Ta tike

   


   

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق