الجمعة، 15 ديسمبر 2017

MASALLACIN AKSA (KUDUS) A MUSULUNCI

Hudubar Masallacin Annabi  na shaikh Husain Al- Asshaikh  27-3- 1439 AH
Batu mai girma na cikin zuciyar kowani Musulmi : shine  batun Masallacin Aksa Kiblar farko na Musulmai kuma masallaci mai daraja na uku, kuma gurin da aka yi ISRA'I (Tafiyan dare ) da Shugaban Halittu.
shine batu mafi muhimmanci a yanzu wanda ba zai  gushe ba daga zuciyar  kowani musulmi daidaiku da al'uma, a duk yadda kalu bale ke fiskantar musulmai , da duk yadda musulmai suka samu kansu a ciki na fitintinu.
Kudus da abin da kasarta ta kumsa na masallacin Aksa batu ne na akida a gurin musulmai, kuma RIBADI ne mai  zurfin tarihi ba za a manta shi ba a a kowani yanayi ko a goge shi daga  kundin Musulunci, sabo da wani Alami ne daga cikin  alamomi na musulmai , kuma ginshiki ne daga ginshikanta da ba a sauya su, kuma guri ne mai tsarki daga cikin gurare masu alfarma a musulunci.
Ta yaya zai yiwu bayan ga littafin Ubangijinmu na tunatar da mu safiya da maraice da fadinsa Mai tsarki (Tsarki ya tabbata ga wanda yayi tafiyar dare da bawansa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa masallacin Aksa wanda muka sanya albarka a gefensa domin mu nuna masa daga Ayoyinmu lalle ne shi shi ne Mai ji Mai gani ) Al'isra 1
Masallacin Aksa daya ne daga cikin Masallatayya guda uku ne da ba ya halatta a nika gari zuwa ga wasu  sai zuwa gare su da sunan neman kusanci ga Allah da neman kari daga falalansa  kamar yadda hadisai suka zo daga Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi.
Kasar baitul Makdis nan ne kasar da za a hada halittu a tada su a ranar alkiyama , An karbo daga Maimuna baiwar Annabi ta ce : Ba mu labari game da baitul Makdis sai ya ce : (kasa ce na tattarowa da tadawa ).Ibnu Maja ya rawaito shi da isnadi Ingantacce.
Baitul Makdis na da matsayi mai girma a musulunci da falala na musamman, an karbo daga Abu Zarri Allah kara yarda a gare shi ya ce : (Muna tattaunawa a gaban Manzon Allah ko wanne ya fi falala Masallacin Annabi ko Masallacin Baitul Makdis, sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Salla guda a Masallaci na ya fi salloli hudu a cikin shi kuma madalla da  Masallaci, Yana dab da ya kasance mutum ya zama bai da abinda ya kai  igiyar dokinsa na daga kasa wanda zaa ga Baitul Makdis daga can  hakan ya fi mishi duniya da abin da ke cikinta) Hakim ne ya rawaito ya inganta shi Kuma Imam Azzahabi ya mara mishi baya wurin ingantawar.
Na daga cikin falalolin shi a musulunci shi ne gurin da aka yi tafiyar dare da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi kuma daga nan ne aka tafi sama da shi,
An karbo daga Anas Dan Malik Allah ya kara mishi yarda cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : An kawo min Alburak wata dabba ce fara mai tsawo ya fi jaki bai kai alfadari ba, yana sanya kofoton sa iya makuran ganinsa, ya ce Na hau shi har na zo baitul Makdis, sai ya ce sai na daure shi a tirken da Annabawa ke daure wa. Yace sai na shiga Masallaci na yi raka'a biyu a cikinsa, sai na fita sai Jibrilu ya zo min da kwano daya na giya daya kuma na nono sai na zami nono, sai Jibrilu ya ce ka zabi FIDIRA (Musulunci)  sai ya haura da mu zuwa sama.) Muslim ne ya ya rawaito.
Na daga cikin falalolin shi akwai hadisin Abdullahi Dan Amr Dan As  daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Yayin da Sulaiman dan Dawud ya kammala gina Baitul Makdis sai    ya roki Allah abu uku;  hukuncin da zai yi daidai da hukuncin sa, da mulkin da ba wanda ya dace ya samu irin shi a bayan sa ,  kada kuma wani ya zo wannan masallacin da ba abin da ya nufa sai salla a cikin shi face ya  fita daga zunuban shi kamar ranar da  mahaifiyar shi ta haife shi ) ,  sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :  - Amma biyun hakika an bashi su ina fatan  an bashi na uku) Nasa'i ya rawaito shi   da Ibn Maja Albani ya inganta shi .
           'YAN UWA A MUSULUNCI :
                    Kuma Baitul makdis da Masallacin Aksa na da falaloli masu girma  a Musulunci  wanda ya sanya malaman musulunci  tun a karnoni da suka shude ,  sukan ware su da talifi  daban-daban masu bin juna da rubutu daya bayan daya , game da falalan shi da girman hakkin shi ,    hakika  dunbin malamai na wannan al'umma    sun yi  rubutu takanas  akan shi:  Daga cikin su akwai Baha'uddin Ibn Asakir   a cikin littafin shi   ( Aljami'ulmustakasa fi  fada'ilil masjidi aksa )  . Daga cikin su akwai Aminuddin Ibn Hibatillah asshafi'I  a littafinsa (Kitabul Uns fi Fada'ilil Kudus),  a cikinsu  akwai Burhanuddin Alfazari  a littafin sa ( Ba'isul nufus ila ziyaratilkudus almaharus)    daga cikin su akwai Shihabuddin Ahmad Dan Muhammad  Almakadisi  a littafin shi  (  Musirulgaram ila ziyaratil kudus wa sham )  , daga cikin su akwai  Alhussainul Husaini a littafin shi ( Alraudulmugris fi fada'ilu baitilmakadis ) daga cikin su akwai  Ibnul jauzi  a cikin littafin sa ( Fada'ilul kudus )  daga cikin su akwai suyudi   a cikin littafin sa ( Ithafu Al'akhissa   bi fada'ili Almasjidil aksa) .
                    Da wannan ne ya sa musulmai gaba dayan su   ba za su yarda   su tabbatar da duk wani mataki da zai  taba batun kudus da  Masallacin Aksa ba  abu ne da yake mai tsarki a musulunci  baya halatta da kowani  irin hali  a taba shi  kai sai dai ma irin wannan tasarrufin ,  ba  abin da zai karawa musulmai  sai tsayuwa da jajarcewa da  dogewa   bisa ga neman hakkokin su tabbatattu  wanda ya yi daidai da   ginshikai  tabbatattu  don tantance gaskiya  da  tsawatarwa  ga zalunci , da kuma yiwa wanda a ka zalunta  adalci, kamar yanda  shari'o'i na sammai  da dokokin kasa da kasa suka tabbatatar .
               Kai duniya ma gaba daya a yau  ,  yana daukan duk wani mataki    irin wannan  abu ne da yake na keta dokokin da aka yi tarayya a kai na kasa da kasa, na cewa kudus   birnin tarayya    ne  na musulunci  ,  kuma gu ne mai tsarki daga  cikin tsarkakan gurare na musulmai .
     Lalle  batutuwa na al'uma ba a yin nasara ta hanyar huduba kawatacciya  ko kalmomi   masu   amsa amo ba ,   ba yi da wani amfani   ya- ma'abota musulunci  na nuna   bakin ciki da bacin rai  , ko kuma   daga  abubuwa na nuna   Allah wadarai da yawaita jerin gwano a titi don bayyana manufa , sau nawa  hakan ya faru da musulmai , da suka yi haka abin ya zo ya wuce ba a cimma manufa ba  tare da hakan  bai wuce ya zama wani abu na maida martani irin wanda ba zai tunkude zalunci ba ko ya kauda cuta ba , kuma ba zai hana tokobin mai ketare iyaka ba ko ketan mai keta ba,  to fa lalle mu sani ba makawa sai an ko ma ga Allah mai girma da daukaka  komawa na gaskiya ,  tare da kankan da kai da ikhlasi zuwa ga  Allah mai girma  da kasaita tabaraka wata ala .
         Al'uma tana samun nasara ne kawai idan ta taimaki al'uma ciki da waje ,  tana mai amsa kira  a waki'I, a duk lokacin da al'uma ta kasance mai riko da addinin Allah  tana mai girmama umarnin shi da shari'an shi  tana tunkuduwa  a  harkokin ta  daga addini na gaskiya  wan da  batun Masjidul Aksa ya tsayu a kai, to, a wannan lokacin ne za a samu waraka   da kuma nasara tabbatacce  , sa kuma samu mafita mai amfani , Allah madaukakin sarki ya ce : ( Idan kun taimaki Allah( wato addinin sa) zai taimake ku ( akan magautan ku ) Muhammad 7 .
        YA JAMA'AR MUSULMAI:
        Duk ranar da tsoratarwa na kur'ani da sunna ke galaba a kan zuciya ,  sannan hujjoji na waki'i suka gaskata haka a fagage na rayuwa  da lokutan ta , to musulmai ba za su taba fadawa cikin rauni ba , da walakanci  ba, kuma wani abu da zai same su na kaskanci da walakanci ,            Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma kada ku yi rauni kuma kada ku yi bakin ciki alhali kuwa, ku ne mafiya daukaka idan kun kasance masu imani ) Ali Imrana 139    
            Hakika lokaci ya yi ga musulmai musamman   ga 'yan uwa da suke FALASDIN a halin suna tinkaran  kalubale mai hadari , wanda ta shafi amincin  al'iumman su gaba daya , da su hadu a kan da'a da tsoron Allah , kuma su yi sulhu bisa ga maslahohi na addini da lahira  kuma su  hadu don kauda  duk wani abin da zai kawo sabani  da rarrabuwa a tsakanin su,  su fita daga  dabar   gaba  zuwa ga farfajiya ta 'yan uwantaka , su fita daga wutan kiyayya , zuwa ga  haske na  zuciya  su kuma fita daga juyawa juna baya da  rarrabuwar kawuna , zuwa ga yafiya da hadin kai , su yi watsi da kungiyanci da bangaranci , su gudo zuwa ga ruhi na 'yan uwantaka na musulunci ,  da kauna na imani   A llah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma ku yi da'a ga Allah da Manzon sa , kuma kada ku yi jayayya har ku raunana , kuma karfin ku ya tafi, kuma ku yi hakuri lalle ne Allah yana tare da masu hakuri ) Anfal 46
         A duk lokacin da musulmai suka tabbatar da   cikakken sako  na musulunci a waki'in su ba tare da sun tawaye ba kuma suka hakimantar da shi  hakimantarwa cikakke gamamme ,  kuma suka yi aiki da shi ciki da waje  , kuma suka rayu da musulunci don musulunci, to Allah ba zai tozartar da aikin su ba duk yadda wahala ta kai wahala  , ba za su taba ganin duhu ba  a kan hanyar su ta tafiya da kuma mafita  duk yanda musiba ta  yi girma  muddin  akan tafarki na musulunci suke tafiya  , kuma suna masu bin  hukunce –hukuncen shi  , kuma suna masu koyi  da  riko da   sunnan Annabi,   Allah madaukakin sarki ya ce : (  Lalle ne Allah yana   bada kariya ga wadanda suka yi imani ,) Hajj 38  .
             Amma fa muddin al'uma ta kasance   ta dauwama  wutan sha'awe-sha'awe na haramun na  kadawa  ,  ya yi awun gaba da ita  , abubuwa na shagaltarwa na bata na fisganta     taguwar son rai na fandarewa da shubuhohi na dibanta   to a wannan lokacin  za ta tinkari   ambaliyar fitintinu da jarabawowi  da nau'uka na bala'o'I masu yawa , Allah madaukakin sarki ya ce : (   Kuma abin da ya same ku na wata masifa  to, game da abin da hannayen ku suka sana'an ta ne ,  kuma ( Allah) yana yafewa ( wadan su laifuffuka ) masu yawa)  Shura 30 .
      Allah madaukakin sarki ya ce game da  yakin uhud : (  Shin kuma a lokacin da wata masifa hakika ta same ku, alhali kuwa kun samar da  biyun ta kunce : ( daga ina wannan yake  ka ce daga wurin rayukan ku ya ke )     lalle ne Allah akan dukkan komai mai ikon yi ne) Ali Imran 165.
       YA KU JAMA'AR MUSULMAI :
        Ba makawa  al'uma ta sakankance da wasu martabobi na yakini dukkan su  ba za su tsiratar da ita daga matsatsi da ta shiga ba ko kuma ta kawar da ita daga yanayi da ta shiga ba na bakin ciki face musulunci na gaskiya akan akida na tauhidi tacecce da bin sunna ingantacce ,  wanda yake shi ne tafarki na dai-dai   a littafi da  sunna bisa fahimtar magabata na al'uma  to wannan shi ne tushe na asali kuma shi ne ginshiki mai karfi na samun  daukaka da jagoranci , da kuma samun taimako da daukaka Allah madaukakin  sarki yana cewa : ( Wadan da sukayi imani kuma basu gauraya imanin su da zalunci ba wadan nan suna da  suna da aminci kuma su ne shiryayyu) . An'am 82
           Alkawari ne na tabbas  kuma labari ne na gaskiya ( Kuma ya kasance tabbatacce, taimakon Muminai wajibi ne a kan mu) ARRUM 47
        ( Rinjaye ga Allah ya ke kuma da manzon sa  kuma da muminai  kuma amma munafukai ba su sani ba ).  Munafikun 8  ( Hakika muminai sun rabauta ) muaminun 1

         YA KU JAMA'AR MUSULMAI:
    Lallai wajibi ne ga dukkan musulmai   bisa sabanin matsayin su    su tsaya bisa batu mai tushe  wato batun masallacin Aksa da kuma  Baitul makdis  da kasar FALASDIN  su tsaya tsayuwan daka a irin mahanga na musulunci   ba wanin sa ba  ta hanyar hadin kai mai tasiri , da kyakkyawan  motsi wanda zai kai ga samar  da da mai ido da cimma manufofi   Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma ka ce ku yi aiki sa'annan Allah zai ga ayukan ku  da Manzon sa da muminai ) Tauba 105 .
            Ba makawa sai an yi amfani da basira mai karfi da cikakkiyar hikima   wanda da ita ne al'umar musulmi za su iya tinkarar kalubale   daban-daban kuma ko wani iri  wanda zai yi daidai da hadin kai  da kuma da'iran taimakekeniya da karfafan juna ,   da taimakon juna ba rikici  ko fada ko zage-zage ,  ko neman wani laifi  da wannan ne za a toshe zaluncin masu zalunci al'uma ta kai ga nasara  mai karfi  .
         Ba makawa sai anyi dubi bisa batu na al'uma da dubi wanda  yake akwai hangen nesa a ciki,  wanda zai tashi daga  motsi na zahiri  zuwa ga  bigire  mai tasiri  da kuma ayyuka  da aka auna su  wanda za su kai ga rinjayi  cikin jerin gwanon hada karfi da karfe  da kyakkyawan tsari don a kai ga matsaya na gaskiya wanda ya taso daga   tuta na addinin musulunci mai hikima , , da kuma abin da shari'ar shugaban Annabawa da Manzanni ta kebanta da shi, wanda ita ce za ta iya jan ragamar duniya gaba daya  zuwa ga wayewa da aminci da walwala da hadin kai da zaman lafiya .
        Dole ne al'uma ta tafi  akan kokari gurin hada karfi da karfe  don fiskantar kalubale  da salo da ya dace  da kuma  tattaunawa  mai kaiwa ga manufa nesa daga salo na cece ku ce da kuma   kalmomi na bangaranci  da ife-ife da ta'assubanci  ko agender  na wata kasa  , to wadan nan wasu abubuwa ne da ba za  su haifar  da wani abu ga al'uma ba sai sharri da bala'I  Allah madaukakin sarki ya ce : ( Sai ( al'umar) suka yayyanke al'amarin su  a tsakanin su guntu-guntu  kowace kungiya suna masu farin ciki da abin da yake a gare su ) Muaminun 53 .
    Ba makawa wurin amsa kiran fadin  Allah madaukakin sarki ( Lalle ne wannan ita ce al'ummar ku , ta zama al'umma guda kuma ni ne Ubangijin ku sai ku bauta mini )
                HUDUBA TA BIYU
     Kasar haramaini masu mulkin su kuma da talakawan su a ko yaushe suna tsaye tsayin daka   wurin bada kariya ga dukkan batutuwa na musulunci da kuma na larabci musamman batun FALASDINU , to matsayan wannan kasar da mahukuntan ta   game da batun FALASDINU  abu ne da yake tabbatacce ba za su girgiza  ko su sauka  daga kanta ba  batu ne dake cikin abu mafi muhimmanci  da suke iya kokarin su  ta fiskoki daban-daban , musamman  bangarorin da suka shafi bangarorin tattalin  arziki da na siyasa.
     A zamanin mai hidimawa masallatayya biyu masu alfarma sarki Salman  duniya ta shaida  ba da kulawa da cigaba da wannan tafiya  karkashin kulawan mai girma Allah ya kara kiyaye shi  sabo da la'akari da yayi da ita batu ne na musulunci   kafin ta zama batu ne na larabawa ,  wannan kasan tana ganin wani nauyi ne da ke kanta  kuma tana bautawa Ubangijinta da shi , kuma tana samun daukaka da ita da kuma hukuncin sakon ta na musulunci  da matsayinta a duniyance ,  sabo da haka  ba wani gurbi na neman kari ga duk wani mai kin gaskiya  bisa ga kokarin wannan kasa     haka kuma da mai  musanta hakan , da kuma  'yan sashi-fadi ,  da kuma mai kawo shakku   cikin   jinsin mu (na larabawa)  bisa ga kokarin da wannan kasa  take tashi da shi , to, ya wajaba a gare su da su ji tsoron Allah su sani cewa  duk wani dauki ba dadi  da ake yi don taba wannan kasa    mai alfarma to lalle fa suka ne ga fadar musulunci  da kuma suka ga wadanda suke rike da tutar bada kariya a gare shi , to, yin haka  kamar wata tawaga ne  da suna yaudarar kawunan su  kuma suna makirtar al'umar su .
      Allah madaukakin sarki ya ce : ( Suna yaudarayya da Allah da wadan da suka yi imani alhali ba su yaudarar kowa face kansu ,  kuma basu sakankancewa ) Bakara 9.
Kuma su sani wannan kasan tana tafiya ne  a kan tsari na musulunci  wanda ba ya bukatan  kari sabo da yabon mai yabo  ko kuma  jafa'i  sabo da farfagandan makiya masu fatan sharri  ga kasan,  Allah na sane kuma yana ganin nufin su.  

                        

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق