الجمعة، 6 أكتوبر 2017

FARAUTAR MATA DA KAI MUSU FARMAKI

HUDUBAR JUMA'A NA MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI NA  16-1-1439 NA SHAIKH ABDULBARI AL-SUBAITI
HUDUBAR FARKO:
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI
Bayan haka:
Musulunci ya karrama dan Adam  da  cikakken rayuwa ta natsuwa  da aminci da zaman lafiya da duk abin da ya kumsa,  shari'ar Musulunci ta siffantu da siffa ta kamala da gamewa na hukunce –hukuncenta ,  ta kuma kewaye al'umma da dukkan wata katanga da kyawawan halaye da dabi'u wanda zai kare ta daga dukkan bangarorin ta  ya janyo ta  zuwa ga kyawawan dabi'u  da ayyuka  nagari ,  wanda zai kauda ta ta yi nesa daga  munanan halaye da siffofi marasa kyau,  Allah madaukakin sarki ya ce : (( A yau na kammala muku addininku kuma na cika ni'ima ta a kan ku , kuma na yarda da Musulunci ya zamo addini a gare ku ))
   Koyarwar Musulunci  ya iyakance dukkan wasu laifuka ,   ta hanyar toshe sabubanta ,  da kuma hana abubuwan da za su janyo ta   , ya gama da ita tun tana karamarta ,  domin kariya da amincin al'umma ,  domin  kulawa  da hakkin daidaiku,  kamar yanda Musulunci   ya toshe kofofin bullan laifuffuka  ta hanyar bada tarbiya ga al'umma  bisa ga kyawawan dabi'u da halaye na gari  da kuma gina  kariya na fadawa ga tabarbarewan halaye ,  shari'a ta wajabta dokoki da kisasi  ,  da kuma   hukunci na horo don amincin al'umma gaba daya  Allah madaukakin sarki ya ce ((kuma kuna da rayuwa a cikin kisasi,ya ma'abuta hankula;   tsammaninku, za ku yi takawa)).
Na daga cikin manyan laifuka   da al'umma ke dandanan azabanta,  dukkan masu hankali sun yi tarayya bisa ga muhimmancin yaki da ita ko hana faruwanta  akwai  laifin  farautar mutunci 'yan mata da firgita su wanda zai kai   zuwa ga abin da aka haramta  ta hanyar batarwa ko cutarwa da yaudara ;  shi din wani banzan dabi'a ne   kuma barna ne  abin kyama ,  ana  amfani da shi wurin tafiyar da zuciya da tada sha'awa , wannan laifin na da illoli da suka kai makura ;  cutarwan ta mafi girma ya boyu ne cikin fadawa ga abin da Allah ya haramta , da kuma tada hankulan al'umma da kuma cututtuka irin na zuci  ga wanda abu ya shafa , wanda hakan yakan kai  zuwa ga fadawa   ga kololuwan sharri,   yakan zamar da mutum ya gangara da shi zuwa ga sharri mafi zurfi  ,  ko ma ya kai ga kashe kan shi .
 Tsawatarwa masu farautar mata da kai hari da farmaki  don keta mutuncinsu, masu isgilanci masu wasa , abu ne  da  ya ke na wajibi a shari'a  ,  kuma abu ne  da yake na tilas a zamantakewa . Allah Madaukakin sarki ya ce: (( Kuma wadan da suke cutar muminai maza da muminai mata, ba da wani abu da suka aikata ba , to lalle sun dauki  kiren  karya da zunubi bayyananne)).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Lalle mafi sharrin mutane matsayi  a ranar alkiyama a wurin Allah  shi ne wanda mutane suka kyale shi ko suka guje shi  don tsoron alfashan shi )).
Rikan farautar mata da kai musu  farmaki a matsayin laifi , da kuma yakansa  aiki ne mai daraja , kuma akwai tsaida hukunci na Allah  ta hanyar tsoratar  da duk wanda ya ke so ya kawo barna a doron kasa  ,  da kuma kunna wutar fitina , da kawo tashin tashina  ga aminci  ya kuma doge cikin bata ,  hukuncin Allah na kiyayewa mutane mutuncin su  da sum'ar su da kuma karamar su ; Nasa'I da Ibn Maja sun rawaito daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi  , cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce : (( Haddi da za a tsaida a doron kasa ya fi alheri ga mutanen bisa a musu ruwa na kwana arba'in))
  Ga kira na Alkur'ani mai girma ga muminai , da su yi nesa da bin hanyoyin shaidan  Allah madaukakin sarki ya ce (( Kuma kada ku kusanci abubuwan alfasha  abin da ya bayyana daga gare ta  da  abin da ya boyu))
 (( ya ku wadanda suka yi imani kada ku bi hanyoyin shaidan ,    Kuma wanda ke bin hanyoyin shaidan ,  to, lalle ne shi  yana umurni da yin alfahasha da abin da  aka ki )).
Dukkan wannan domin a toshe kofofin sharri ne  da kuma wanda  da ya ke kokarin yada alfahasha   a cikin wadan da suka yi imani .
 Kai farauta da farmaki ga mata  mummunar sifa  ce  da a ke samun su daga wadanda suke masu raunin hankali kuma wawaye , marasa lafiyan zukata ,  masu illa a dabi'u  kuma marasa mutunci , wadan da suke aikata ayyukan assha.
Laifi irin na kai farauta da farmaki ga mata   yana da salo daban-daban masu yawa , da hanyoyi  iri-iri  wanda ana fara shi ne da lafuza na batsa , da maganganu na fitsara , wanda masu aikata shi  ke yin shi,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Ina muku gargadi da ku nisanci batsa  domin lalle Allah baya son masu batsa, da kuma masu neman ayi alfasha))  kuma ya ce:  (( Mumini bai zama mai yawan zagi ba ko yawan tsinuwa ko alfasha ko kuma batsa ba )).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ((  Ga ko wani dan Adam akwai wani kaso na daga zina ,  idanuwa biyu suna yin zina ;  zinan su kuma shi ne kallo,  hannaye biyu suma suna zina; zinan su kuma shi ne damka , kafafuwa biyu suma suna zina ; zinan su kuma shi ne tafiya , baki ma yana zina ; zinan shi kuma shi ne sumba, zuciya kuma na dimauta cikin fatan hakan, farji kuma sai ya gaskata ko kuma ya karyata shi )). Ahmad ne ya rawaito da isnadi ingantacce bisa sharadin Muslim
Idan mutum ya sakarwa  harshen sa linzami , da ya yi wasa  to, zai kai kansa ne bisa ga saraya a duniya    da kuma tsiyacewa  a lahira, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Ba ya lafazi da wata magana face a like da shi akwai mai tsaro halartacce)
Kuma ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah  ku fadi magana madaidaiciya).
Kai farauta da harin taba mutuncin mata ; wani ciwo ne mai game dukkan guri, ya ke kwankwasa dukkan kofa, kuma yana kara bazuwa a sararin samaniya, ba iyaka na wuri ko zamani,  da wasu  irin dabaru da ba a saba  da su ba, da makircin da ba a sansu ba  sai ya  ratsa cikin zuciya yana barna ya kuma gurbata hankali , ya bata kyakkyawan tunani .
 Daga cikin nau'uka na kai hari akwai amfani da  wasu hotunan bidiyo  na batsa ,  a kafafen sada zumunta  na yanar gizo, wanda a ciki akwai yada sharri  da  alfasha,  da kwadaitarwa mai ban tsoro zuwa gare ta  da cutarwa mai tsanani wanda ba za a iya siffanta shi ba , ((Lalle ne wadan da ke son alfasha ta watsu  ga wadan da suka yi imani , suna da azaba mai radadi a cikin duniya da lahira . kuma Allah shi ne ya sani , alhali kuwa ku ba ku sani ba  )).
  Masu yada wadan nan hotunan bidiyo kuma  suna masu tashi da  tallata  ta , makomar su ba kyau  , kuma karshen su abin bakin ciki ne  mai radadi : Allah ya kare mu da ku daga mummunan karshe ,   Allah madaukakin sarki ya ce: (( Domin su dauki zunuban su cikakku aranar kiyama , kuma daga zunuban wadan da suke bautarwa ba da wani ilimi ba .  to, abin da suke dauka na zunubi ya munana )).
Allah madaukakin sarki ya ce : (( Kuma lalle suna daukan kayan nauyin su ,  da wadan su nauyayan kaya , tare da kayan nauyin su , kuma lalle za a tambaye su a ranar kiyama ,  game da abin da suka kasance suna kirkirawa  na  karya   )).
Hakika cutan kai hari ga mutuncin mata da farautarsu ya yadu ne sakamakon bayyana sabo da sakaci da alfahari da kawata mummunan  abu,   kamar yanda  rashin kwanciyar hankali a gida ya ke saka 'yan mata  da yara  da mata  su zama abin farauta , mafi sauki a gun  masu kai farmaki da hari ga mutuncin mata .
Ma'abota shari'a da tunani da ra'ayi mai kyau sun san cewa lalle mafificin hanya na  kariya daga wannan mugunyar cutan, shi ne a dasa  kariya na addini  da kuma karfafan imani  da kuma bin koyarwar kur'ani , da lazimtar tsoron Allah a fadi da kuma  dabi'a da kuma runtse ido da sanya tufafi mai suturcewa , da tsarkake rayi  ta hanyar kamewa da kuma tsoron Allah. Baya boyuwa  cewa matasa suna da wani karfi  da fisgan kai na samartaka , to, amma idan ya samu saiti da nusarwa  da jan ragama , sai ya dawo kan hanyar da ya dace , tunanin shi da natsuwan shi sai su daidaita, sai ya zama cikin masu kawo gyara da gini ga al'umma , wannan kuma yana taimakawa wurin bada kariya ga al'uma daga aikin  kai farmaki ga mutuncin mata .
 Kamar yanda aure da  wuri yana kosar da bukatu, ya kan hana zaman banza kuma yana bada kariya daga munanan halaye , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Ya ku taron matasa  wanda yake da ikon yin aure  a cikin ku , to, ya yi aure , domin shi din ya fi bada kariya ga runtsa ido da katange farji )).
Gina alaka mai karfi da amincewa tsakanin iyaye da yara ,  yana gina mutum akan halin da yake kai nakwarai  ya kuma ba shi karfin gwuiwa  akan kyawawan dabi'un sa , kuma ya  gina mishi mazantakan shi ya cire mishi irin  dabi'un  mata , yana tarbiyantar da 'yan mata bisa ga kamun kai da suturcewa  da hijabi , amma iyalan gidan da ba su damu da  dulmuya acikin matsalolin zamani da  cin karon al'adu  da rarrabuwa kawuna ba , to   kamar wani sarari ne na shanya da masu farautar mata da kai farmakin suka samu  don kai farmakin  



    HUDUBA NA BIYU:
 Yana daga cikin abin da ya dace   a yi tsokaci a kai  kula da ba da muhimmanci kan tarbiyan yara  da kuma  rashin sakaci da su , musamman  lokacin da a ka hangi wasu munanan halaye da ake shakku a kansu.
  lalle yaki da farauta  ko farmaki ga mata da dukkan laifuka nauyi ne da ya rataya a kan kowa ,  a cikin al'uma ,  duk wanda bai ji tsawatarwan kur'ani ba da kira na imani ba to fa dole ne a wannan lokaci  ayi anfani da bulala ta hukuma.
 Hakika ya zo daga Usmanu Allah ya kara yarda a gare shi, ya ce : Lalle Allah na tsawatarwa da karfin mulki irin tsawatarwan da baya yi da kur'ani

        
    

.
  

   

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق