HUDUBAR JUMA'A NA MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A
GARE SHI NA 16-1-1439 NA SHAIKH
ABDULBARI AL-SUBAITI
HUDUBAR
FARKO:
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI
Bayan
haka:
Musulunci ya karrama dan Adam da
cikakken rayuwa ta natsuwa da
aminci da zaman lafiya da duk abin da ya kumsa,
shari'ar Musulunci ta siffantu da siffa ta kamala da gamewa na hukunce
–hukuncenta , ta kuma kewaye al'umma da
dukkan wata katanga da kyawawan halaye da dabi'u wanda zai kare ta daga dukkan
bangarorin ta ya janyo ta zuwa ga kyawawan dabi'u da ayyuka
nagari , wanda zai kauda ta ta yi
nesa daga munanan halaye da siffofi
marasa kyau, Allah madaukakin sarki ya
ce : (( A yau na kammala muku addininku kuma na cika ni'ima ta a kan ku ,
kuma na yarda da Musulunci ya zamo addini a gare ku ))
Koyarwar Musulunci ya iyakance dukkan wasu laifuka , ta hanyar toshe sabubanta , da kuma hana abubuwan da za su janyo ta , ya gama da ita tun tana karamarta , domin kariya da amincin al'umma , domin kulawa da hakkin daidaiku, kamar yanda Musulunci ya toshe kofofin bullan laifuffuka ta hanyar bada tarbiya ga al'umma bisa ga kyawawan dabi'u da halaye na
gari da kuma gina kariya na fadawa ga tabarbarewan halaye
, shari'a ta wajabta dokoki da
kisasi ,
da kuma hukunci na horo don
amincin al'umma gaba daya Allah
madaukakin sarki ya ce ((kuma kuna da rayuwa a cikin kisasi,ya ma'abuta
hankula; tsammaninku, za ku yi
takawa)).
Na daga cikin manyan laifuka da
al'umma ke dandanan azabanta, dukkan
masu hankali sun yi tarayya bisa ga muhimmancin yaki da ita ko hana faruwanta akwai
laifin farautar mutunci 'yan mata
da firgita su wanda zai kai zuwa ga
abin da aka haramta ta hanyar batarwa ko
cutarwa da yaudara ; shi din wani banzan
dabi'a ne kuma barna ne abin kyama ,
ana amfani da shi wurin tafiyar
da zuciya da tada sha'awa , wannan laifin na da illoli da suka kai makura ; cutarwan ta mafi girma ya boyu ne cikin
fadawa ga abin da Allah ya haramta , da kuma tada hankulan al'umma da kuma
cututtuka irin na zuci ga wanda abu ya
shafa , wanda hakan yakan kai zuwa ga
fadawa ga kololuwan sharri, yakan zamar da mutum ya gangara da shi zuwa
ga sharri mafi zurfi , ko ma ya kai ga kashe kan shi .
Tsawatarwa masu farautar mata da
kai hari da farmaki don keta mutuncinsu,
masu isgilanci masu wasa , abu ne
da ya ke na wajibi a shari'a , kuma
abu ne da yake na tilas a zamantakewa .
Allah Madaukakin sarki ya ce: (( Kuma wadan da suke cutar muminai maza da
muminai mata, ba da wani abu da suka aikata ba , to lalle sun dauki kiren karya da zunubi bayyananne)).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ((
Lalle mafi sharrin mutane matsayi a
ranar alkiyama a wurin Allah shi ne
wanda mutane suka kyale shi ko suka guje shi
don tsoron alfashan shi )).
Rikan farautar mata da kai musu farmaki a matsayin laifi , da kuma
yakansa aiki ne mai daraja , kuma akwai
tsaida hukunci na Allah ta hanyar
tsoratar da duk wanda ya ke so ya kawo
barna a doron kasa , da kuma kunna wutar fitina , da kawo tashin
tashina ga aminci ya kuma doge cikin bata , hukuncin Allah na kiyayewa mutane mutuncin
su da sum'ar su da kuma karamar su ;
Nasa'I da Ibn Maja sun rawaito daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare
shi , cewa Annabi tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce : (( Haddi
da za a tsaida a doron kasa ya fi alheri ga mutanen bisa a musu ruwa na kwana
arba'in))
Ga kira na Alkur'ani mai girma
ga muminai , da su yi nesa da bin hanyoyin shaidan Allah madaukakin sarki ya ce (( Kuma kada ku
kusanci abubuwan alfasha abin da ya
bayyana daga gare ta da abin da ya boyu))
(( ya ku wadanda suka yi imani
kada ku bi hanyoyin shaidan , Kuma
wanda ke bin hanyoyin shaidan , to,
lalle ne shi yana umurni da yin alfahasha
da abin da aka ki )).
Dukkan wannan domin a toshe kofofin sharri ne da kuma wanda
da ya ke kokarin yada alfahasha
a cikin wadan da suka yi imani .
Kai farauta da farmaki ga
mata mummunar sifa ce da
a ke samun su daga wadanda suke masu raunin hankali kuma wawaye , marasa
lafiyan zukata , masu illa a dabi'u kuma marasa mutunci , wadan da suke aikata
ayyukan assha.
Laifi irin na kai farauta da farmaki ga mata yana da salo daban-daban masu yawa , da
hanyoyi iri-iri wanda ana fara shi ne da lafuza na batsa , da
maganganu na fitsara , wanda masu aikata shi
ke yin shi, Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Ina muku gargadi da ku
nisanci batsa domin lalle Allah baya son
masu batsa, da kuma masu neman ayi alfasha)) kuma ya ce:
(( Mumini bai zama mai yawan zagi ba ko yawan tsinuwa ko alfasha ko
kuma batsa ba )).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (( Ga ko wani dan Adam akwai wani kaso na daga
zina , idanuwa biyu suna yin zina ; zinan su kuma shi ne kallo, hannaye biyu suma suna zina; zinan su kuma
shi ne damka , kafafuwa biyu suma suna zina ; zinan su kuma shi ne tafiya ,
baki ma yana zina ; zinan shi kuma shi ne sumba, zuciya kuma na dimauta cikin
fatan hakan, farji kuma sai ya gaskata ko kuma ya karyata shi )). Ahmad ne
ya rawaito da isnadi ingantacce bisa sharadin Muslim
Idan mutum ya sakarwa harshen sa
linzami , da ya yi wasa to, zai kai
kansa ne bisa ga saraya a duniya da
kuma tsiyacewa a lahira, Allah
Madaukakin Sarki ya ce : (Ba ya lafazi da wata magana face a like da shi
akwai mai tsaro halartacce)
Kuma ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah ku fadi magana madaidaiciya).
Kai farauta da harin taba mutuncin mata ; wani ciwo ne mai game dukkan
guri, ya ke kwankwasa dukkan kofa, kuma yana kara bazuwa a sararin samaniya, ba
iyaka na wuri ko zamani, da wasu irin dabaru da ba a saba da su ba, da makircin da ba a sansu ba sai ya
ratsa cikin zuciya yana barna ya kuma gurbata hankali , ya bata
kyakkyawan tunani .
Daga cikin nau'uka na kai hari
akwai amfani da wasu hotunan bidiyo na batsa ,
a kafafen sada zumunta na yanar
gizo, wanda a ciki akwai yada sharri
da alfasha, da kwadaitarwa mai ban tsoro zuwa gare
ta da cutarwa mai tsanani wanda ba za a
iya siffanta shi ba , ((Lalle ne wadan da ke son alfasha ta watsu ga wadan da suka yi imani , suna da azaba mai
radadi a cikin duniya da lahira . kuma Allah shi ne ya sani , alhali kuwa ku ba
ku sani ba )).
Masu yada wadan nan hotunan bidiyo kuma suna masu tashi da tallata
ta , makomar su ba kyau , kuma
karshen su abin bakin ciki ne mai radadi
: Allah ya kare mu da ku daga mummunan karshe , Allah
madaukakin sarki ya ce: (( Domin su dauki zunuban su cikakku aranar kiyama ,
kuma daga zunuban wadan da suke bautarwa ba da wani ilimi ba . to, abin da suke dauka na zunubi ya munana
)).
Allah madaukakin sarki ya ce : (( Kuma lalle suna daukan kayan nauyin
su , da wadan su nauyayan kaya , tare da
kayan nauyin su , kuma lalle za a tambaye su a ranar kiyama , game da abin da suka kasance suna
kirkirawa na karya )).
Hakika cutan kai hari ga mutuncin mata da farautarsu ya yadu ne
sakamakon bayyana sabo da sakaci da alfahari da kawata mummunan abu, kamar yanda
rashin kwanciyar hankali a gida ya ke saka 'yan mata da yara
da mata su zama abin farauta ,
mafi sauki a gun masu kai farmaki da
hari ga mutuncin mata .
Ma'abota shari'a da tunani da ra'ayi mai kyau
sun san cewa lalle mafificin hanya na
kariya daga wannan mugunyar cutan, shi ne a dasa kariya na addini da kuma karfafan imani da kuma bin koyarwar kur'ani , da lazimtar
tsoron Allah a fadi da kuma dabi'a da
kuma runtse ido da sanya tufafi mai suturcewa , da tsarkake rayi ta hanyar kamewa da kuma tsoron Allah. Baya
boyuwa cewa matasa suna da wani
karfi da fisgan kai na samartaka , to,
amma idan ya samu saiti da nusarwa da
jan ragama , sai ya dawo kan hanyar da ya dace , tunanin shi da natsuwan shi
sai su daidaita, sai ya zama cikin masu kawo gyara da gini ga al'umma , wannan
kuma yana taimakawa wurin bada kariya ga al'uma daga aikin kai farmaki ga mutuncin mata .
Kamar yanda aure da wuri yana kosar da bukatu, ya kan hana zaman
banza kuma yana bada kariya daga munanan halaye , Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Ya ku taron matasa wanda yake da ikon yin aure a cikin ku , to, ya yi aure , domin shi din
ya fi bada kariya ga runtsa ido da katange farji )).
Gina alaka mai karfi da amincewa tsakanin iyaye da yara , yana gina mutum akan halin da yake kai nakwarai
ya kuma ba shi karfin gwuiwa akan kyawawan dabi'un sa , kuma ya gina mishi mazantakan shi ya cire mishi
irin dabi'un mata , yana tarbiyantar da 'yan mata bisa ga
kamun kai da suturcewa da hijabi , amma
iyalan gidan da ba su damu da dulmuya
acikin matsalolin zamani da cin karon
al'adu da rarrabuwa kawuna ba , to kamar wani sarari ne na shanya da masu farautar
mata da kai farmakin suka samu don kai
farmakin
HUDUBA NA BIYU:
Yana daga cikin abin da ya
dace a yi tsokaci a kai kula da ba da muhimmanci kan tarbiyan
yara da kuma rashin sakaci da su , musamman lokacin da a ka hangi wasu munanan halaye da
ake shakku a kansu.
lalle yaki da farauta ko farmaki ga mata da dukkan laifuka nauyi ne
da ya rataya a kan kowa , a cikin al'uma
, duk wanda bai ji tsawatarwan kur'ani
ba da kira na imani ba to fa dole ne a wannan lokaci ayi anfani da bulala ta hukuma.
Hakika ya zo daga Usmanu Allah ya
kara yarda a gare shi, ya ce : Lalle Allah na tsawatarwa da karfin mulki irin
tsawatarwan da baya yi da kur'ani
.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق