الخميس، 21 سبتمبر 2017

RIBATAR DAMA A RAYUWA TA HANYAR BIYAYYA GA ALLAH

Hudubar Masallacin Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi 2/1/1439 H
Na Sheikh Abdullah Bin Abdurrahman Albuaijan
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda sammai da kasa na shi ne, gare shi al'amura ke komawa, godiya da yabo da kyakkyawan ambato da wanzuwa nashi ne, kuma gare shi zaa koma, tsarki ya tabbata gare shi ya horar da rana da wata suna karbar juna ya kuma hore muku dare da wuni kome gare shi a kaddare ya ke.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya mulki da godiya na shi ne, yana rayawa kuma yana kashe wa kuma shi rayayye ne ba ya mutuwa, alheri na hanunsa kuma mai iko ne ga dukkan komai.
Na shaida Annabi Muhammadu cikamaki ne na Annabawansa  da Manzanninsa, an turo shi a lokacin da ba Manzanni  sai ya isar da sako ya kuma bada amana ya yi nasiha ga al'umma, ya yi jahadi don Allah hakkin jahadi har mutuwa ta zo mishi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da iyalansa da sahabbansa  wadanda suka yi hijira daga gidajen su da dukiyoyinsu suna neman falala na Allah da yarda.
 Da Ansar da da suka mallaki gida da imani suna son wadanda suka yi hijira zuwa gare su, basu jin wani bukata daga ransu cikin abin da su bada ko sun kasace mabukata.
Da kuma wadanda suka bi sawunsu su ka bi su da kyautatawa,da aminci tabbatacce mai yawa har zuwa ranar alkiyama.
Bayan haka! Lalle mafi gaskiyan zance shi ne littafin Allah mafi karfin abin riko shi ne kalmar takawa, mafi alherin addini shi ne addinin Ibrahim, mafi kyan kissoshi shine Alkur'ani, kuma mafi kyan shiryarwa shine shiryarwar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, mafi al'amura shi ne fararrunta, dukkan bidiah bata ne.
Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah hakkin tsoronsa, kar ku mutu face kuna musulmai)
Ya ku bayin Allah!
Duniya gidan jarabawa ne da karewa  ita kuma lahira gida ce na sakayya da wanzuwa, duniya jindadi ne na rudi, wasu sa'oi ne da kwanaki da watanni da shekaru  da zama shekaru na karewa  wasu zamuna n su zo su riska, ranaku su shude, watanni su zo su wuce, Allah na juya dare da wuni, a hakan akwai abin lura ga masu basira.
Zamani na karewa  gurace gurace na karewa , kuma ajali na cika ( kuma duk wanda ke kan ta na kare wa, fiskan Ubangijinka ne zai wanzu ma'aboci daraja da daukaka ).
*Wallahi duniya ba gidan wanzuwa ba ne* A'a ko da mutane sun gina benayenta
*Shekaru na shan banban sai dai * suna mai tsawon kwana da gajere na  daidaita  a yayin mutuwa.
Nesa ba kusa ba gidan duniya ba gidan da ake  fatan wanzuwa ba ne , farin- cikinta bai cika, mutuwa abin buri ne ga dukkan rayuka * ga mai hankali ba banbanci tsakanin benayenta da kaburanta
Yaku Musulmi!
Shekara ta kare, kuma shekarun duniya na raguwa, ga ajali na kusantowa , an rufe ayyukanta,  an nade takardunta, Madalla da barka ga wanda ya ribaci damanta, ya ribaci lokacinsa. Ya gyara ayyukansa.
Ku saurara ga mu mun shigo  farkon sabuwar shekara , wanda zai  tattara mu zuwa kabari  ya tunkuda mu zuwa ga ranar tadawa da tattarowa.
To ya dace ga duk mai zuciya da wanda ya kasa kunnen shi, ya ribaci dama ta rayuwarsa kafin nadama da da na sani, da zubar da hawaye ya riske shi, (Kada wani rai ya ce ya nadama ta akan abin da na yi sakaci a cikin  sashen Allah, kuma lalle na kasance hakika daga masu isgili,ko kuma (kada) ya ce ; da Allah ya shiryar da ni da na kasance daga masu takawa, ko kuma (kada) ya ce, a lokacin da ya ke ganin azaba da lalle ace ina da wata komawa zuwa duniya.) domin in kasance daga masu kyautatawa).
 Ya ku bayin Allah!
Lalle lokaci na shudewa rayuwa na ta tafiya, kuma rayuwar lokaci ne kankani, ga wajibabbu sun taru, ga hakkoki sun cunkushe mutum abin tambaya ne game da rayuwarsa  yadda ya tafiyar da ita da samartarsa yadda ya gudanar da ita. Kuma zaa yi mar bincike game da yadda ya sarayar da rayuwarsa, da zamanin da ya daidaitar, duk yadda shekuru ya  tsawaita to lokaci ne kankani,  ( Ya ce nawa ku ka zauna acikin kasa na kidayar shekaru? Suka ce , mun zauna a yini daya ko rabin yini sai ka tambayi masu kidanyawa. Ya ce ba ku zauna ba face kadan da dai kun kasance kuna sani, shin to kun yi zaton cewa mun halitta ku ne da wasa  kuma lalle ku zuwa gare mu ba za ku koma ).
Ya ku bayin Allah !
Lalle Allah bai halicce ku don wasa ba , kuma bai bar ku haka kawai ba, hakika ya halicci mutuwa da rayuwa domin ya jarraba ku. Ya nuna waye daga cikinku ya fi kyawun aiki.
Ku saurara! Lalle  mafi girman musiba , kuma mafi tsananin wahala  da kuma abu mafi tada hankali da bakin ciki mafi firgitawa  , shi ne ; hasara bisa sarayar da lokaci  ,  da kwacewan ajali   da cudewan sa'o'I na zamani ba tare da aiki ba ,  hasararta na farawa ne da nadamar tata  tun daga lokacin halartowar magagin mutuwa , (   Har idan mutuwa ta je wa dayan su sai ya ce : '' Ya Ubangijina ku mayar da ni ( duniya). Tsammani na  in aikata aiki na kwarai cikin abin da na bari , kayya , lalle ne! ita kalma ce shi ne  mafadinta alhali kuwa a baya gare su akwai shamaki har ranar da za a tayar da su''.
''Ya     ku wadanda suka yi imani kada dukiyoyin ku da 'ya'yan ku su shagaltar da ku daga ambaton Allah , kuma wanda ya yi haka , to wadannan  shu ne masu hasara , kuma ku ciyar daga abin da muka azurta ku daga gabanin mutuwa  ta je wa dayan ku har ya ce ya Ubangijina  don me ba ka yi min jinkiri ba zuwa wani ajali makusanci, domin in gaskata kuma in kasance daga salihai !    kuma Allah ba zai jinkirtawa wani rai ba idan ajalin sa  ya zo kuma Allah masani ne bisa abin da kuke aikatawa ''.
     To lokacin rayuwa -bayin Allah- wata dama ce na aiki  kuma  ni'ima ce da take wajabta yin godiya   ( Idan za ku kidaya  ni'imomin Allah ba za ku iya lissafa ta ba)     
Mafi alherin cikin ku shi ne wanda shekarun shi  ya tsawaita kuma ayyukansa suka kyautata, Mafi sharrin ku shi ne wanda ya yi tsawon rayuwa kuma ayyukansa  ya munana.
Ku saurara ! lalle na daga cikin godiya ga ni'ima ribatan ni'ima na lokuta , da rayuwa cikin da'a wa Allah  mabuwayi da daukaka daidai  yanda ya shasr'anta wa Annabin sa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
 A daya bangaren kuma yana daga cikin kafurcewa ni'ima ,  da sababi na bala'I da  azaba  da  hasara da kuma nadama   akwai tafiyar da lokaci da ruwa cikin sabawa Allah , ko kuma cikin abin da Allah bai shar'anta ba , (  To wanda ya aikata (wani aiki) gorgodon nauyin zarra   na alheri zai gan shi .  kuma wanda ya aikata    gorgodon nauyin zarra zai ganshi .
 Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma.
    HUDUBA  TA  BIYU
Dukkan yabo da godiya  sun tabbata ga Allah  Ubangijin talikai ya kammala mana addini  kuma ya cika mana ni'imomi ,  kuma ya yardar mana da Musulunci a matsayin addini , na shaida ba  abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya , wanda ya hada Allah da wani hakika ya bata ,   bata mabayyani.
 Na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne , tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi da aminci tabbatacce mai yawa.
 YA KU MUSULMAI
Lalle farkon wata na hijira na shekara shi ne watan Almuharram kuma wata ne mai alfarma  Allah madaukakin sarki  ya ce:  ( lalle   ne kidayan watanni a wurin Allah wata goma sha biyu ne a cikin littafin Allah ,  a ranar  da ya halicci sammai da kasa , daga cikin su  akwa hudu masu alfarma , wannanne addini madaidaici    sabo da haka  kada ku zalunci kawunan ku a cikin su )
 An karbo daga Abu bakrata Allah ya kara yarda a gare shi  daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ''  Lalle zamani ya juyo kamar siffan shi a ranar da Allah ya halicci sammai da kasa  shekara watanni goma sha biyu , cikin su akwai guda hudu masu alfarma  uku a jere su ke :- Zulkada, Zulhijja da Almuharram,  da Rajab  na MUDAR  wanda ke tsakanin Jimada da sha'aban) Bukhari da Muslim ne su ka rawaito.
Ya ku Bayin Allah!
Na daga cikin koyarwar Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma na daga cikin masu kankare  zunubai da kuma  godiya ga Allah , da kuma girmama shi , akwai azumtar ranar ashura  , shi ne goma  ga watan Almuharram .
 An karbo daga  Dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su, ya ce: '' Ya yin da  Annabi ya  zo garin madina ya sami yahudawa  suna azumin ashura sai ya tambaye su game da hakan sai suka ce ; wannan rana ne da Allah ya bawa  Annabi musa nasara da Banu Isra'ila a kan Fir'auna , kuma mu muna azumtar shi don girmamawa gare shi   sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi  ya ce: '' mu muka fi dacewa da musa akan ku , sai  Manzon Allah ya yi umarni da azumtar shi ''. Buhari da Muslim ne su ka rawaito shi
 Kuma daga gare shi ya ce :'' ban taba ganin Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana kirdadan azumin watarana ba ,  wanda ya fifita shi akan wanin shi ba face wannan ranan    na ashura da wannan wata  yana nufin watan ramadan ''.  Buhari ne ya rawaito
 Ya zo a cikin sahihu Muslim Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : '' azumin   ranar Arfa ina fata Allah ya kankare  zunuban shekaran kafin shi ,  da kuma shekaran da take bayan shi, da azumin Ashura ina fatan Allah ya kankare shekaran da take kafin shi''.
 Ya yin da  labari ya sami  Annabi   a  karshen rayuwan shi  , kan cewa yahudawa na rikan ashura a matsayin idi  , sai ya nufi  ya azumci  tara da  goma a shekara  mai zagayowa ,  sai mutuwa ta shiga tsakani , 
An karbo daga Abdullahi dan Abbas  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: a yayin da Annabi ya yi azumin ashura   ya yi  umarni da azumtar shi sai suka ce  :'' ya Manzon Allah Yahudu da Nasara su na girmama shi  ,  sai Manzon Allah tsira da  amincin Allah su tabbat a gare shi ya ce  : idan Allah ya kai mu badi za mu azumci tara ''. yana nufin tare da goma   .  ya ce : shekaran bata kewayo ba har Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya rasu.''   Muslim ne  ya rawaito
 Abin da ya fi falala shi ne a yi azumi  guda kafin shi, sabanin na yahudawa  in hakan  bai samu ba to a yi azumin ranar goma.
Ya Ku Musulmai !
Bidia fitina ce, fitina kuma jarabawa ce,  mafi sharrin al'amura su ne fararrunta , dukkan bidi'a bata ce    dukkan bata na wuta , to ku yi riko da igiya mai karfi da tafarki mikakke,  kada ku bi hanyoyi ,  sai su kawar da ku daga tafarkin 
ku yi riko da littafin ku da shiryarwar Annabin ku , to hakika an isar mu ku,.
 (Sabo da haka ka yi riko ga abin da aka yi  wahayi da shi zuwa gare ka, lalle ne kai kana kan hanya madaidaiciya. Kuma shi (Abin wahayin ) ambato ( na daukaka ) ne a gare ka da kuma ga mutanenka, kuma za a tambaye ku.)
Ya ku Musulmai !
 Lalle abin nan da mabarnata  suke shiryawa, mujirimai ke tsarawa, makirai da mahassada ke gudanarwa, na daga makiyanmu da makiya addinin mu da garuruwanmu  wasu tawaga ne na 'yan jarida da farfaganda irin na shaidan, da kai wa mummunan hari , da wani kazamin makirci suna yi ne don karanbawul ga zaman lafiyanmu, da wargaza hadin kanmu, da kunna fitina a garuruwanmu, a tsakanin sahun mu, da keta alfarmar watanni  masu  alfarma, da warware alkawari,da janye mubaya'a da fita daga da'a da barna a doron kasa, mun gani da idanuwarmu  yadda kasashe makwabta suka koma,  na daga rugujewa, to  ku yi lura ya masu basira!
Ya Allah ka kiyaye wannan gari ya zama cikin aminci da zaman lafiya, ya Allah ka kiyaye garin daga fitintinu, ya Allah ka kiyaye shi daga makircin masu makirci, da sharrin mabarnata, da  sharrin makiya da mahassada,
Ya Allah ka kiyaye garin da sauran garuruwan musulmai, ya Ubangijin talikai,
Ya Allah ka taimaki musulmai a Borma ka kare jinin su kuma ka suturce al'auran su , ka basu aminci a abin da suke tsoro  ka yi gaggawan yaye musu bakin ciki .
 Allah ka datar da jagoran al'amarin mu mai hidima ga masallatayya biyu masu alfarma   da datarwarka , ka karfafe shi da karfafanka.
Ya  Allah ka datar da shi da mataimakin shi , da abin da a cikin shi akwai gyaran garuruwa da bayi  da abin da  a cikin shi akwai alheri ga musulunci da Musulmai , ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka kiyaye mana iyakan mu , ka bawa sojojin mu  nasara  ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka warkar da marasa lafiyan su , ka karbi matattun su, ka kiyaye su da kiyayewarka, ka kare su da kariyarka .
BAYIN ALLAH  ( Llle Allah  na yin  umurni da kyautatawa,  da  bai wa ma'abucin  zumunta , kuma yana hani da alfasha  da abin da aka ki , da rarrabe jama'a . Ya na yi muku gargadi,  dammaninku,  kuna tunawa.
(Kuma ku cika da alkawarin  Allah idan kun yi alkawari,  kuma kada ku warware rantsuwoyin ku a bayan karfafa su,  alhali kuma hakika kun sanya  Allah mai lamuncewa a kanku .  Kuma lalle Allah ne  ya ke sanin abin da kuke  aikatawa) .  


  

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق