الخميس، 7 سبتمبر 2017

TUSHEN KARBAR AIKI IKHLASI

Hudubar Jumaa a Masallacin Annabi  na Sheikh Abdul Muhsin Alkasim 17 ga zulhijja 1438 AH
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da kuma munanan ayyukanmu, Duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatace mai yawa.
Bayan haka!
Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah hakkin tsoronsa,ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.
Kadaita Allah da bauta shine manufa na halittawa da umarni, Allah Mai tsarki da daukaka ya ce :(Ban halicci Aljani da mutane ba face su bauta min) Da hakan ne za a raya kasa, kuma dan Adam ya samu walwala, Allah Madaukakin sarki ya ce :  (wanda ya yi aiki na kawarai na daga na miji ko mace  yana mumini to zamu raya shi rayuwa na jin dadi  kuma mu sakanya mishi da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa )
Yana yarda da aiki na kwarai ya amince da shi, Allah Mai tsarki ne bai karba sai mai tsarki,
Tushen karbar aiki shi ne Imani da Allah da yin aiki don neman yardarsa, Allah Mabuwayi da daukaka ya ce : (kuma wanda ya nufi lahira kuma ya yi aiki sabo da ita irin aikinta alhali kuwa yana mumini, to wadannan aikin su ya kasance godadde.)
 Aikin kafiri a lahira abin mayarwa ne ko da wani irin aiki ya yi, Allah Madaukakin sarki ya ce :(kuma muka gabata zuwa ga abin da suka aikata daga aiki sai muka sanya shi kura watsattsiya )
A duniya zaa ciyar da shi da kyakkyawan ayyuka da ya aikata, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Amma shi kafiri zaa ciyar da shi da kyakkyawan abin da ya aikata don Allah a nan duniya, har idan ya koma lahira sai ya zama bai da wani aikin lada guda da zaa saka mishi.) Muslim ne ya rawaito.
Aisha Allah kara yarda a gare ta ta ce :Ya Manzon Allah! Dan Jud'an ya kasance a lokacin Jahiliyya ya na  sada zumunci kuma yana ciyar da miskinai ko wannan zai amfane shi? Sai ya ce : Ba zai amfane shi ba,sabo da bai taba cewa :" ya Allah ka gafarta min kusakurai na a ranar sakayya"  ba ko da rana daya )  Muslim ne ya rawaito.
Wanda ya bayyana Musulunci ya boye sabanin haka a zuciyarsa ba zai amfana ba da abin da ya bayyana ba kuma zaa maida masa da aikinsa ba zaa karba ba. Allah Madaukakin Sarki ya ce game da halin munafukai : (Ku ciyar bisa kuna so ko akan tilas ba za a karba daga gare ku ba lalle ne ku kun kasance ne mutane fasikai. Kuma ba bu abin da ya hana a karbi ciyarwarsu daga gare su face domin su sun kafirta da Allah da Manzon sa.)
Kaiwa da komowar ibada ya dogara ne a kan niyya da aiki, kuma sharadin karbarta ita ce tsarkake niyya da kyautata aiki, da Ikhlasi ne manufa ke yin kyau  da bin sunna ne ayyuka ke daidaituwa, Allah Madaukakin sarki ya ce : (sabo da haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da Ubangijinsa to sai ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bautawa Ubangijinsa).
Kuma addinin Musulunci an gina shi a kan tushe ne guda biyu, : da a bauta wa Allah shi kadai ba shi da abokin taryya, kuma mu bauta masa da abinda ya shar'anta, shi ne abin da Manzon Allah ya zo da shi, tsira da amincin Allah sau tabbata a gare shi. Kuma wannan shine hakikanin shahada biyu, kuma sune rukunai biyu na karbabbun aiki.
Jarabawa a duniya ya doru ne bisa tabbatar ikhlasi da bin sunna, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Allah wanda gudanar da Mulki ya ke ga hannunsa, ya tsarkaka kuma shi mai iko ne akan kome. Shi ne wanda ya halitta mutuwa da rayuwa domin ya jarraba ku, ya nuna waye  daga cikin ku yafi kyawun aiki) wato wanda ya fi ikhlasi da yi daidai, Fudail dan Iyad Allah ya mishi rahama : " Lalle aiki idan ya kasanceAllah kadai aka nufa amma ba a kawo shi daida da koyarwar sharia ba to ba zaa karba ba, haka kuma idan an yi shi daidai amma ba ikhlasi to ba za a karba ba, ba za karba ba har sai ya hada ikhlasi da bin sunna, Taceccen aiki shi ne wanda aka yi don Allah, shi kuma daidai: shi ne idan an yi shi bisa koyarwar Annabi.
Hakikanin ikhlasi shi ne bawa ya nufi yardar  Allah a biyayyarsa, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Ka bauta wa Allah kana mai tsarkake addini a gare shi)
To duk abin da musulmi  ya ke yi na da'a  an umarce shi  ne da ya aikata shi tare da tsarkake shi ga Allah Ubangijin talikai,ba zai nemi sakayya ko godiya daga wani halitta ba, Gyaruwan zuciya shi ne tushe gurin karbar aiki, aiki na gyaruwa ne idan niyya ta yi kyau, niyya ce uwa uba na wadannan aiki ita ce niyya , kuma mutum niyyarsa na kai shi inda aikin shi ba zai kai shi ba, ta iya yiwuwa aiki karami amma niyya sai ta maida shi babba, ko kuma aiki babba amma niyya ta mai da shi karami.
Yahya Bin Abi kasir Allah ya mishi rahama ya ce : (ku koyi niyya don tafi tasiri bisa aiki)
Dukkan ibadar da baa yi ikhlasi ba da kyakkyawar badini ba to ba a karbar ta, ikhlasi bai haduwa a zuciya tare da kaunar yabo da kyakkyawan ambato, da kwadayin abin da ke hanun mutane, bin Annabi sharadi ne a gun karbar aiki, in an rasa shi to aikin abin maidawa ne ga mai shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya aikata aiki ba umarnin mu a ciki to an maida mishi da kayansa).Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Sa'id Bin Jubair Allah ya mishi rahama  ya ce : (Ba a karbar fadi sai da aiki, ba za a karbi aiki ba sai da fadi, ba za a karbi fadi da aiki da niyya ba sai da bin sunna )
Sanya tsoron Allah a cikin ayyuka na daga sababi na karbar ayyuka Allah Madaukakin sarki ya ce : (Allah na karba ne daga masu takawa) 
Musulmi na da tsananin tsoro ga kan sa,kada ya zama bai cikin su,ba za a karbi aikinsa ba,wannan shi ne halin magabata, Abu Darda Allah ya kara yadda a gare shi ya ce : (Da na samu yakinin Allah ya karba sallah ta guda   yafi min duniya da abin da ke cikinta sabo da Allah na cewa : " Allah na karba ne daga masu takawa".
Wanda  ya ji tsoron Allah da ikhlasin aikinsa  da kuma bin sunna, to ya dace Ubangiji  mai karamci ya karbe shi.)  Sheikhul Islam Allah ya mishi rahama ya ce : (A gun Ahlussunna waljama'a ana karbar aiki daga wanda ya ji tsoron Allah a cikinsa  ya yi da ikhlasi don Allah yana bin daidai da umarnin Allah,duk wanda ya ji tsoronsa a wani aiki to zai amsa masa ko  da yana sabo a waninsa, wanda bai ji tsoron shi ba a cikinsa ba zai karba masa ba ko da yana mishi biyayya a waninsa.)
Yin da'a bayan da'a alama ce ta karbarta, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Kuma wadannan da suka nemi shiryuwa (Allah) ya kara musu shiryuwarsu kuma ya basu (sakamakon takawarsu).
Alhasan AlBasri Allah ya mishi rahama ya ce : (Na daga sakayyar kyakkyawa a bi ta da kyakkyawa, na daga ukuba ta mummuna a bi ta da mummuna,  abin mamaki da kyakkyawa  ta biyo mummuna don za ta goge ta, tir da aikata mummuna bayan kyakkyawa don zata lalata ta, ta debe albarkarta. Wanda bai kasance cikin kari na da'a ba to kuwa yana cikin ragi
Saukin ibada ga ma'abocin shi  da kaunan aikin alheri albishir ne na duniya,Allah Madaukakin sarki ya ce: (To amma wanda ya yi kyauta kuma ya yi takawa, kuma ya gaskata kalma mai kyau, to za mu saukake masa har ya kai ga sauki)
Tsayuwa a kan aiki da tabbatuwa akan da'a dalili ne na alheri da dace,Ibnu kasir Allah ya yi mishi rahama: ( Allah na tafiyar da al'adarsa cikin karamcinsa bisa wanda  ya rayu a kan abu zai mutu a kai,in har ya mutu a kan wani abu to  za a tashe shi a kai ranar Alkiyama.)
Na daga koyarwar Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai  dawwama a kan aikin alheri  ya kasance yana cewa : (Mafi soyuwar aiki a gun Allah shi ne wanda aka dawwama akai ko dan kadan ne.)Bukhari da Muslim ne suka rawaito
Gyaruwar gabbai da daidaituwarta na daga cikin fa'ida na karbuwar aikin daa , da kaunar ma'abocinta, Allah Madaukakin sarki ya ce  a hadisin Alkudsi : (Ba abin da bawa na  zai kusance ni da shi da ya fi soyuwa a gare ni kamar abin da na  farlanta mishi bawa na ba zai gushe yana kusanta na da nafila har na so shi,idan na so shi sai na zama jin shi da ya ke ji da shi da ganin shi da ya ke gani da shi da hanun shi da yake damka da shi da kafarsa da ya ke tafiya da ita kuma idan ya roke ni zan ba shi, in ya nemi tsari na zan bashi tsari )Bukhari ne ya rawaito.
Shanin mumini kokari cikin ibada da ganin aikin shi kankani, idan ya kammala wani biyayya sai ya sadar da wata ibada,bai nunawa ga Ubangijin shi yawan aikin sabo da in an kwatanta da abin da ya yi mar na ni'ima ya bashi kadan ne,) Allah ya ce : (kada ka yi kyauta kana neman kari) Duk wanda ya shaida hakikanin rububiya da hakikanin Ubudiyya, ya san Allah Ubangijinsa zai bayyana a gare shi, shi ,ba kome ba ba ne, ba wanin mu da shiga Aljanna a cikin mu don aikin shi sai dai da falalar Allah da karamcin sa da rahamarsa. Ibnu Abu Mulaika Allah ya mi shi rahamayace : " na riski  talatin daga cikin sahabbai kowannen su na tsoron munafunci a kansa, ba wani daga cikinsu da ke cewa yana da imani irin na Jibrilu da Mika'il "
Istigfari bayan da'a da bayyana gajartawa hali ne na bayin Allah masu ikhlasi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Sun kasance a lokaci na dare kadan su ke yin barci,kuma alokacin asuba suna ta yin istigfari)
Ibnul kayyim Allah ya mishi rahama ya ce : (Alamar karbar aikin ka shi ne ka rena aikin naka ka kankantar da shi, ka kalle shi karami a zuciyarka har ya kai wanda ya san Allah zai rika neman gafara a karshen aikin sa na daa).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya kasance  idan ya sallame daga sallah yana neman gafarar Allah sau uku"
Kuma Allah ya umarci bayin sa bayan aikin hajji da neman gafara, ya kuma ya yabe su sabo da neman gafara a karshen tsayuwan dare, Manzon Allah ya shar'anta a karshen Alola tuba da istigfari, duk wanda ya shaida wajibin Ubangijinsa da gwargwadon aikinsa,da laifin kansa to dole ne  ya nemi  gafarar Ubangijinsa daga gare shi ya kuma rena kansa da aikinsa ya dauke su ba komai ba  ya rena kansa.
,    Allah ya yabi bayinsa da fadinsa  :( Da wadanda ke bayar da abin da suka bayar alhali kuwa zukatarsu  suna tsorace domin suna komawa  zuwa ga Ubangijinsu  )
Aisha ta ce ya Manzon Allah ! shin su ne su ke shan shan giya suna sata, sai yace a'a ya 'yar siddik sai dai su ne wadanda suke azumi suna sallah suna sadaka amma suna tsoron kar baa karba musu ba (Wadancan suna gaggawar tsere a cikin ayyukan alheri  alhali kuwa suna masu tserewa zuwa gare su(Ayyukan alheri)Tirmizi ne ya rawaito
Shi Mumini yana hada Ihsani da tsoro, Abdul'Aziz Dan Abi Rawad (Na riske su su na kokari cikin ayyukan kwarai idan su aikata shi sai su shiga damuwa na shin ko za'a karba musu ko a'a,)
Na daga cikin abu mafi girma na sababin karbar aiki da samun biyan bukata akwai rokon Allah hakan, to Ibrahim daIsma'il Amincin Allah ya tabbata a gare su a halin suna daga tubalin dakin ka'aba kuma suna rokon Allah, (Ya Ubangijin Mu ka karba daga gare mu lalle ne kai kai ne Mai ji Mai sani,)
To 'yar Imrana ta yi bakancen abin da ke cikin ta don hidima ga Masallacin Aksa, ta kasance tana adu'a  tana cewa : ( ya Ubangiji na lalle ne ni na yi bakancen abin da ke cikin ciki na gare ka ya zama 'yantacce, sai ka karba daga gare ni.lalle ne kai kai ne mai ji , masani ).
Annabi ya yi laiha sai ya ce : Ya  Allah ka karba daga Muhammad da Iyalan Muhammad    da kuma daga Al'umar Muhammad) Muslim ne ya rawaito.

 Godiya tafarki ne na karbar aiki, kuma kofa ne na kari Allah ya ce : (kuma alokacin da Ubangijinku ya sanar Lalle ne idan kun gode ina kara muku)
Kuma bayin Allah na cewa  :( Ya Ubangiji na ka kange ni domin in godewa ni'imar wadda ka ni'imta a kai na da kuma a kan Mahaifa na biyu, kuma domin in aikata aikin kwarai, wanda ka ke yarda da shi, kuma ka kyautata mini a cikin zuriya ta, lalle ni na tuba zuwa gare ka kuma lalle ni ina daga masu sallamawa  (ga umarninka)
Sai Allah ya musu alkawari da fadinsa  ( Wadancan ne wadanda muke karba daga gare su, mafi kyawun abin da suka aikata kuma muke gafarta mafi munanan ayyukansu,(suna ) a cikin 'yan Aljanna akan wa'adin gaskiya wanda suka kasance ana yi musu alkawari (da shi).
 Musulmi na kodayin a karba masa aikinsa kuma ya na kokari don  tabbatar da haka kuma yana taka tsantsa don tsananin  tsoron lalacewan aikin da rushewansa,  ba wai ya tsaya a aiki kadai ba a'a amma al'amarin ya hada da kiyaye aikin  bayan gama shi daga abin da zai bata shi ya rusa shi, mafi girman shi shi ne hada Allah da wani, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Da sun yi shirki da hakika abin da su ka kasance suna aikatawa ya lalace )
Mutuwa cikin ridda na rusa aiki, Allah Mabuwayi da daukak :(Kuma wanda ya yi ridda daga gare ku ga barin Addinin sa,har ya mutu alhali kuwa yana kafiri to wadannan ayyukansu sun baci a cikin duniya da lahira)
Kuma kin addini na rusa aikin mai shi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (wannan sabo da lalle su sun ki abin da Allah ya saukar domin haka ya bata ayyukansu).
Kafirci da Allah da haduwa da shi na sanya laacewar aiki Allah Madaukaki ya ce : (kuma wadanda suka karyata game da ayoyin mu da gamuwa da lahira ayyukansu sun baci )
Duk wanda ya bi abin da zai fusata Allah ya ki neman yardarsa Allah zai saka masa da ga irin aikin sa sai ya rusa aikinsa Allah Madaukakin sarki ya ce : (wannan domin lalle su sun bi abin da ya fusatar da Allah kuma sun ki yardarsa sabo da haka ya bata ayyukansu)
Kuma munafunci aiki ne mai mummunan karshe da sharri, Allah ya ce : (wadannan basu yi imani ba sabo da haka Allah ya bata ayyukansu ).
A cikin sabawa Manzo Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ta hanyan saba umarninsa akwai bata aiki da rusa shi Allah Madaukakin sarki  ya ce : ( Lalle ne wadanda suka kafirta kuma suka kange daga tafarkin Allah kuma suka sabawa Manzonsa abayan shiriyar ta bayyana a gare su ba za su cuci Allah da kome ba kuma zai baita ayyukansu.)
Kuma daga sauti a gaban Annabi na bata ayyuka. (yaku wadanda suka yi imani kada ku daukaka saututtukanku bisa sautin Annabi kuma kada ku bayyana sauti gare shi a magana kamar bayyanawar sashin ku ga sashe, domin kada ayyukanku su bacialhali kuwa ku baku sani ba)
Alfahari da aiki da shisshigi  ga Allah,  yana suka ne ga bangare rububiya Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace ga da wanda yace da wani Wallahi Allah ba zai gafarta ma wane  ba, sai Allah ya ce   : wane ne ya ke yi min shisshigi  kan cewa ba zan gafarta wa wane ba to ni lalle na gafarta masa kai kuma na rusa aikin ka).Muslim ne ya rawaito
Riya na lalata aiki Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisi kudsi: (Ni na wadatu daga abokan tarayya duk wanda ya yi wani aiki ya hada ni da wani na a ciki to na bar shi da shirkarsa)Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya zo gurin boka  ya tambaye shi wani abu to ba za a karba mishi sallan kwana arba'in ba) Muslim ne ya rawaito.
(Duk wanda ya bar sallar la'asar to aikin ka ya rushe) Bukhari ne ya rawaito
(Zalunci duhu ne ranar alkiyama).
Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce : ( Tsiyatacce wanda aka yi wa wasoso shi ne wanda zai zo ranar Alkiyama da sallah da azumi da zakka kuma ya zo yazagi wannan ya yi kazafi ga wane ya ci dukiyan wane, ya zubar da jinin wane ya duki wane, sai a bawa wannan dag kyawawan shi wancan ma daga kyawawan shi, idan kyawawan shi sun kare kafin a biya bashin da ke kansa, sai a dauki kusakuransu sai a dora mishi sannan a jefa shi a wuta.) Muslim ne ya rawaito.
Zunuban  boye na goge kyawawa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Na san wasu mutane magana cikin al'umata za su zo ranar alkiya ma da kyawawa  sun kai girman dutsen tihama   da hasken sa sai Allah ya maida shi Turbaya tarwatstse
Sauban Allah ya yarda da shi ya ce : ya Manzon Allah siffanta su gare ka fayyace mana su ka mu kasance cikinsu ahalin ba mu sani ba, sai ya ce : ( Ai su 'yan uwanku ne masu irin fatar jikin ku, suna rikan kamar yadda ku ke yi na daga dare, sai dai su mutane ne da idan sun kebanta da abin da aka haramta sai su keta alfurmarta) Ibnu Maja ne ya rawaito.
(Wanda ya riki kare inba na kare dabbobi ba ko farauta ko kare shuka ba za a rage a kowani rana ladan sa da ya kai kiradi.)Bukhari ne ya rawaito.
(Duk wanda ya sha giya to Allah ba zai karba masa salla ba na safiya na arba'in ) Ahmad ne ya rawaito.
Makurar hasara shi ne mutum ya zaci yana kan aiki mai kyau a halin yana kan sabanin hakan. Allah Madaukakin sarki ya ce : (kace ko mu gaya muku game da mafifita hasara ga ayyuka?(wadanda aikinsu ya baci a cikin rayuwar duniya ,alhali kuwa suna zaton lalle ne su suna kyautata (abin da suke gani)aikin kwarai?)
Bayan haka ya ku musulmai :
To Ita ibada da  kiyaye ta abin nema ne a musulunci, dawwama akanta har zuwa mutuwa tushe ne a sharia, Allah Madaukaki ya ce : ( Kuma ka bautawa Ubangijinka har mutuwa ta zo ma)
Ya wajaba akan musulmi kada ya guji duk wani aikin alheri,ko da dan kadan ne, ya kuma nesanci dukkan munana ko da karama ce don bai san wace kyakyawan ce Allah zai jikan shi a dalilinta.bai kuma san wace mummunar ce Allah zai yi fushi da shi akan ta ba, ya wajaba ga Musulmi da ya tafi cikin ibadar sa yana mai tsakanin fata da tsoro, yana raya zuciyar sa da kaunar Allah da kyautata masa zato,
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa.
(Ka ce lalle ne salla ta da yanka na da rayuwa ta da mutuwa ta na Allah ne Ubangijin talikai, babu abokin tarayya a gare shi, kuma da wancan aka umarce ni, kuma ni ne farkon masu sallamawa)
Allah ya sanya min albari ka ni da ku a cikin Alkurni Mai girma,
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawarsa.godiya ta tabbata bisa datarwarsa da baiwarsa, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya muna girmama shaninsa, kuma na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzon sa ne, tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa,
Ya ku Musulmai!
Ku kasance kun fi kula da karbar aikin akan shi kan shi aikin, ku kiyaye abin da zai tafiyar muku da da'a  daga abin da zai lalata shi ko ya rage shi, duk wanda yayi aiki mai kyau to ya godewa Allah da ya datar da shi zuwa ga aikata  wannan aiki, kuma ya roke shi tabbatuwa da dogewa a kai,kuma kiyaye da'a ya fi aikata ta. Kuma bin lura shine na karshe, shi wanda ya san Allah yana kuma bauta masa zai sanya a cikin biyayyar sa wani abu da zai rika tsarkake mishi rayinsa ta hanyar lazimtar ibada,
Da gaskiya da kubutaciya kuma  da kankan da kai lafiyayyar zuciya,da kyawawan dabiu zai so alheri ga waninsa kamar yadda ya ke so wa kansa, kada ya aminta daga Makru na Allah kuma kada ya yanke kauna daga rahamar Allah.

Sannan ku sani Allah ya  umarce ku da salati ga Annabinsa.   

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق