Hudubar Jumaa a Masallacin Annabi
na Sheikh Abdul Muhsin Alkasim 17 ga zulhijja 1438 AH
Hudubar farko
Dukkan
yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa
muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da kuma
munanan ayyukanmu, Duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya
batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,
shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne
kuma Manzonsa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da
sahabbansa da aminci tabbatace mai yawa.
Bayan
haka!
Ku
ji tsoron Allah ya ku bayin Allah hakkin tsoronsa,ku yi riko da igiya mai karfi
na musulunci.
Kadaita Allah da bauta shine manufa na halittawa da umarni, Allah Mai
tsarki da daukaka ya ce :(Ban halicci Aljani da mutane ba face su bauta min)
Da hakan ne za a raya kasa, kuma dan Adam ya samu walwala, Allah Madaukakin
sarki ya ce : (wanda ya yi aiki na kawarai na daga na miji ko
mace yana mumini to zamu raya shi rayuwa na jin dadi kuma mu
sakanya mishi da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa )
Yana yarda da aiki na kwarai ya amince da shi, Allah Mai tsarki ne bai
karba sai mai tsarki,
Tushen karbar aiki shi ne Imani da Allah da yin aiki don neman yardarsa,
Allah Mabuwayi da daukaka ya ce : (kuma wanda ya nufi lahira kuma ya
yi aiki sabo da ita irin aikinta alhali kuwa yana mumini, to wadannan aikin su
ya kasance godadde.)
Aikin kafiri a lahira abin
mayarwa ne ko da wani irin aiki ya yi, Allah Madaukakin sarki ya ce :(kuma
muka gabata zuwa ga abin da suka aikata daga aiki sai muka sanya shi kura
watsattsiya )
A duniya zaa ciyar da shi da kyakkyawan ayyuka da ya aikata, Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Amma shi kafiri
zaa ciyar da shi da kyakkyawan abin da ya aikata don Allah a nan duniya, har
idan ya koma lahira sai ya zama bai da wani aikin lada guda da zaa saka mishi.)
Muslim ne ya rawaito.
Aisha Allah kara yarda a gare ta ta ce :Ya Manzon Allah! Dan Jud'an
ya kasance a lokacin Jahiliyya ya na
sada zumunci kuma yana ciyar da miskinai ko wannan zai amfane shi? Sai
ya ce : Ba zai amfane shi ba,sabo da bai taba cewa :" ya Allah ka gafarta
min kusakurai na a ranar sakayya"
ba ko da rana daya ) Muslim ne ya
rawaito.
Wanda ya bayyana Musulunci ya boye sabanin haka a zuciyarsa ba zai
amfana ba da abin da ya bayyana ba kuma zaa maida masa da aikinsa ba zaa karba
ba. Allah Madaukakin Sarki ya ce game da halin munafukai : (Ku ciyar bisa
kuna so ko akan tilas ba za a karba daga gare ku ba lalle ne ku kun kasance ne
mutane fasikai. Kuma ba bu abin da ya hana a karbi ciyarwarsu daga gare su face
domin su sun kafirta da Allah da Manzon sa.)
Kaiwa da komowar ibada ya dogara ne a kan niyya da aiki, kuma sharadin karbarta
ita ce tsarkake niyya da kyautata aiki, da Ikhlasi ne manufa ke yin kyau da bin sunna ne ayyuka ke daidaituwa, Allah
Madaukakin sarki ya ce : (sabo da haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da
Ubangijinsa to sai ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bautawa
Ubangijinsa).
Kuma addinin Musulunci an gina shi a kan tushe ne guda biyu, : da a
bauta wa Allah shi kadai ba shi da abokin taryya, kuma mu bauta masa da abinda
ya shar'anta, shi ne abin da Manzon Allah ya zo da shi, tsira da amincin Allah
sau tabbata a gare shi. Kuma wannan shine hakikanin shahada biyu, kuma sune
rukunai biyu na karbabbun aiki.
Jarabawa a duniya ya doru ne bisa tabbatar ikhlasi da bin sunna, Allah
Madaukakin sarki ya ce :(Allah wanda gudanar da Mulki ya ke ga hannunsa, ya
tsarkaka kuma shi mai iko ne akan kome. Shi ne wanda ya halitta mutuwa da
rayuwa domin ya jarraba ku, ya nuna waye
daga cikin ku yafi kyawun aiki) wato wanda ya fi ikhlasi da yi
daidai, Fudail dan Iyad Allah ya mishi rahama : " Lalle aiki idan ya kasanceAllah
kadai aka nufa amma ba a kawo shi daida da koyarwar sharia ba to ba zaa karba
ba, haka kuma idan an yi shi daidai amma ba ikhlasi to ba za a karba ba, ba za
karba ba har sai ya hada ikhlasi da bin sunna, Taceccen aiki shi ne wanda aka
yi don Allah, shi kuma daidai: shi ne idan an yi shi bisa koyarwar Annabi.
Hakikanin ikhlasi shi ne bawa ya nufi yardar Allah a biyayyarsa, Allah Madaukakin
sarki ya ce :(Ka bauta wa Allah kana mai tsarkake addini a gare shi)
To duk abin da musulmi ya ke yi
na da'a an umarce shi ne da ya aikata shi tare da tsarkake shi ga
Allah Ubangijin talikai,ba zai nemi sakayya ko godiya daga wani halitta ba,
Gyaruwan zuciya shi ne tushe gurin karbar aiki, aiki na gyaruwa ne idan niyya
ta yi kyau, niyya ce uwa uba na wadannan aiki ita ce niyya , kuma mutum
niyyarsa na kai shi inda aikin shi ba zai kai shi ba, ta iya yiwuwa aiki karami
amma niyya sai ta maida shi babba, ko kuma aiki babba amma niyya ta mai da shi
karami.
Yahya Bin Abi kasir Allah ya mishi rahama ya ce : (ku koyi niyya don
tafi tasiri bisa aiki)
Dukkan ibadar da baa yi ikhlasi ba da kyakkyawar badini ba to ba a
karbar ta, ikhlasi bai haduwa a zuciya tare da kaunar yabo da kyakkyawan
ambato, da kwadayin abin da ke hanun mutane, bin Annabi sharadi ne a gun karbar
aiki, in an rasa shi to aikin abin maidawa ne ga mai shi, Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya aikata aiki ba
umarnin mu a ciki to an maida mishi da kayansa).Bukhari da Muslim ne suka
rawaito.
Sa'id Bin Jubair Allah ya mishi rahama
ya ce : (Ba a karbar fadi sai da aiki, ba za a karbi aiki ba sai da
fadi, ba za a karbi fadi da aiki da niyya ba sai da bin sunna )
Sanya tsoron Allah a cikin ayyuka na daga sababi na karbar ayyuka Allah
Madaukakin sarki ya ce : (Allah na karba ne daga masu takawa)
Musulmi na da tsananin tsoro ga kan sa,kada ya zama bai cikin su,ba za a
karbi aikinsa ba,wannan shi ne halin magabata, Abu Darda Allah ya kara yadda a
gare shi ya ce : (Da na samu yakinin Allah ya karba sallah ta guda yafi min duniya da abin da ke cikinta sabo
da Allah na cewa : " Allah na karba ne daga masu takawa".
Wanda ya ji tsoron Allah da
ikhlasin aikinsa da kuma bin sunna, to
ya dace Ubangiji mai karamci ya karbe
shi.) Sheikhul Islam Allah ya
mishi rahama ya ce : (A gun Ahlussunna waljama'a ana karbar aiki daga wanda
ya ji tsoron Allah a cikinsa ya
yi da ikhlasi don Allah yana bin daidai da umarnin Allah,duk wanda ya ji
tsoronsa a wani aiki to zai amsa masa ko
da yana sabo a waninsa, wanda bai ji tsoron shi ba a cikinsa ba zai
karba masa ba ko da yana mishi biyayya a waninsa.)
Yin da'a bayan da'a alama ce ta karbarta, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Kuma
wadannan da suka nemi shiryuwa (Allah) ya kara musu shiryuwarsu kuma ya basu
(sakamakon takawarsu).
Alhasan AlBasri Allah ya mishi rahama ya ce : (Na daga sakayyar
kyakkyawa a bi ta da kyakkyawa, na daga ukuba ta mummuna a bi ta da
mummuna, abin mamaki da kyakkyawa ta biyo mummuna don za ta goge ta, tir da
aikata mummuna bayan kyakkyawa don zata lalata ta, ta debe albarkarta. Wanda bai
kasance cikin kari na da'a ba to kuwa yana cikin ragi
Saukin ibada ga ma'abocin shi da
kaunan aikin alheri albishir ne na duniya,Allah Madaukakin sarki ya ce: (To
amma wanda ya yi kyauta kuma ya yi takawa, kuma ya gaskata kalma mai kyau, to
za mu saukake masa har ya kai ga sauki)
Tsayuwa a kan aiki da tabbatuwa akan da'a dalili ne na alheri da
dace,Ibnu kasir Allah ya yi mishi rahama: ( Allah na tafiyar da al'adarsa cikin
karamcinsa bisa wanda ya rayu a kan abu
zai mutu a kai,in har ya mutu a kan wani abu to za a tashe shi a kai ranar Alkiyama.)
Na daga koyarwar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai
dawwama a kan aikin alheri ya kasance yana cewa : (Mafi soyuwar aiki
a gun Allah shi ne wanda aka dawwama akai ko dan kadan ne.)Bukhari da Muslim ne
suka rawaito
Gyaruwar gabbai da daidaituwarta na daga cikin fa'ida na karbuwar aikin
daa , da kaunar ma'abocinta, Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin Alkudsi : (Ba abin da bawa na zai kusance ni da shi da ya fi soyuwa a gare
ni kamar abin da na farlanta mishi bawa
na ba zai gushe yana kusanta na da nafila har na so shi,idan na so shi sai na
zama jin shi da ya ke ji da shi da ganin shi da ya ke gani da shi da hanun shi
da yake damka da shi da kafarsa da ya ke tafiya da ita kuma idan ya roke ni zan
ba shi, in ya nemi tsari na zan bashi tsari )Bukhari ne ya rawaito.
Shanin mumini kokari cikin ibada da ganin aikin shi kankani, idan ya
kammala wani biyayya sai ya sadar da wata ibada,bai nunawa ga Ubangijin shi
yawan aikin sabo da in an kwatanta da abin da ya yi mar na ni'ima ya bashi kadan
ne,) Allah ya ce : (kada ka yi kyauta kana neman kari) Duk wanda ya
shaida hakikanin rububiya da hakikanin Ubudiyya, ya san Allah Ubangijinsa zai
bayyana a gare shi, shi ,ba kome ba ba ne, ba wanin mu da shiga Aljanna a cikin
mu don aikin shi sai dai da falalar Allah da karamcin sa da rahamarsa. Ibnu Abu
Mulaika Allah ya mi shi rahamayace : " na riski talatin daga cikin sahabbai kowannen su na
tsoron munafunci a kansa, ba wani daga cikinsu da ke cewa yana da imani irin na
Jibrilu da Mika'il "
Istigfari bayan da'a da bayyana gajartawa hali ne na bayin Allah masu
ikhlasi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Sun kasance a lokaci na dare kadan
su ke yin barci,kuma alokacin asuba suna ta yin istigfari)
Ibnul kayyim Allah ya mishi rahama ya ce : (Alamar karbar aikin ka
shi ne ka rena aikin naka ka kankantar da shi, ka kalle shi karami a zuciyarka
har ya kai wanda ya san Allah zai rika neman gafara a karshen aikin sa na daa).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya kasance idan ya sallame daga sallah yana neman gafarar
Allah sau uku"
Kuma Allah ya umarci bayin sa bayan aikin hajji da neman gafara, ya kuma
ya yabe su sabo da neman gafara a karshen tsayuwan dare, Manzon Allah ya
shar'anta a karshen Alola tuba da istigfari, duk wanda ya shaida wajibin
Ubangijinsa da gwargwadon aikinsa,da laifin kansa to dole ne ya nemi gafarar Ubangijinsa daga gare shi ya kuma rena
kansa da aikinsa ya dauke su ba komai ba
ya rena kansa.
, Allah
ya yabi bayinsa da fadinsa :( Da
wadanda ke bayar da abin da suka bayar alhali kuwa zukatarsu suna tsorace domin suna komawa zuwa ga Ubangijinsu )
Aisha ta ce ya Manzon Allah ! shin su ne su ke shan
shan giya suna sata, sai yace a'a ya 'yar siddik sai dai su ne wadanda suke
azumi suna sallah suna sadaka amma suna tsoron kar baa karba musu ba (Wadancan
suna gaggawar tsere a cikin ayyukan alheri
alhali kuwa suna masu tserewa zuwa gare su(Ayyukan alheri)Tirmizi ne ya
rawaito
Shi Mumini yana hada Ihsani da tsoro, Abdul'Aziz Dan
Abi Rawad (Na riske su su na kokari cikin ayyukan kwarai idan su aikata shi
sai su shiga damuwa na shin ko za'a karba musu ko a'a,)
Na daga cikin abu mafi girma na sababin karbar aiki da
samun biyan bukata akwai rokon Allah hakan, to Ibrahim daIsma'il Amincin Allah
ya tabbata a gare su a halin suna daga tubalin dakin ka'aba kuma suna rokon
Allah, (Ya Ubangijin Mu ka karba daga gare mu lalle ne kai kai ne Mai ji Mai
sani,)
To 'yar Imrana ta yi bakancen abin da ke cikin ta don
hidima ga Masallacin Aksa, ta kasance tana adu'a tana cewa : ( ya Ubangiji na lalle ne ni
na yi bakancen abin da ke cikin ciki na gare ka ya zama 'yantacce, sai ka karba
daga gare ni.lalle ne kai kai ne mai ji , masani ).
Annabi ya yi laiha sai ya ce : Ya Allah ka karba daga Muhammad da Iyalan
Muhammad da kuma
daga Al'umar Muhammad) Muslim ne ya rawaito.
Godiya tafarki
ne na karbar aiki, kuma kofa ne na kari Allah ya ce : (kuma alokacin da
Ubangijinku ya sanar Lalle ne idan kun gode ina kara muku)
Kuma bayin Allah na cewa :( Ya Ubangiji na ka kange ni domin in
godewa ni'imar wadda ka ni'imta a kai na da kuma a kan Mahaifa na biyu, kuma
domin in aikata aikin kwarai, wanda ka ke yarda da shi, kuma ka kyautata mini a
cikin zuriya ta, lalle ni na tuba zuwa gare ka kuma lalle ni ina daga masu
sallamawa (ga umarninka)
Sai Allah ya musu alkawari da fadinsa ( Wadancan ne wadanda muke karba daga gare su,
mafi kyawun abin da suka aikata kuma muke gafarta mafi munanan ayyukansu,(suna
) a cikin 'yan Aljanna akan wa'adin gaskiya wanda suka kasance ana yi musu
alkawari (da shi).
Musulmi
na kodayin a karba masa aikinsa kuma ya na kokari don tabbatar da haka kuma yana taka tsantsa don
tsananin tsoron lalacewan aikin da
rushewansa, ba wai ya tsaya a aiki kadai
ba a'a amma al'amarin ya hada da kiyaye aikin
bayan gama shi daga abin da zai bata shi ya rusa shi, mafi girman shi
shi ne hada Allah da wani, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Da sun yi shirki
da hakika abin da su ka kasance suna aikatawa ya lalace )
Mutuwa cikin ridda na rusa aiki, Allah Mabuwayi da
daukak :(Kuma wanda ya yi ridda daga gare ku ga barin Addinin sa,har ya mutu
alhali kuwa yana kafiri to wadannan ayyukansu sun baci a cikin duniya da lahira)
Kuma kin addini na rusa aikin mai shi, Allah Madaukakin
sarki ya ce : (wannan sabo da lalle su sun ki abin da Allah ya saukar domin
haka ya bata ayyukansu).
Kafirci da Allah da haduwa da shi na sanya laacewar
aiki Allah Madaukaki ya ce : (kuma wadanda suka karyata game da ayoyin mu da
gamuwa da lahira ayyukansu sun baci )
Duk wanda ya bi abin da zai fusata Allah ya ki neman
yardarsa Allah zai saka masa da ga irin aikin sa sai ya rusa aikinsa Allah
Madaukakin sarki ya ce : (wannan domin lalle su sun bi abin da ya fusatar da
Allah kuma sun ki yardarsa sabo da haka ya bata ayyukansu)
Kuma munafunci aiki ne mai mummunan karshe da sharri,
Allah ya ce : (wadannan basu yi imani ba sabo da haka Allah ya bata
ayyukansu ).
A cikin sabawa Manzo Tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ta hanyan saba umarninsa akwai bata aiki da rusa shi Allah
Madaukakin sarki ya ce : ( Lalle ne
wadanda suka kafirta kuma suka kange daga tafarkin Allah kuma suka sabawa
Manzonsa abayan shiriyar ta bayyana a gare su ba za su cuci Allah da
kome ba kuma zai baita ayyukansu.)
Kuma daga sauti a gaban Annabi na bata ayyuka. (yaku
wadanda suka yi imani kada ku daukaka saututtukanku bisa sautin Annabi kuma
kada ku bayyana sauti gare shi a magana kamar bayyanawar sashin ku ga sashe,
domin kada ayyukanku su bacialhali kuwa ku baku sani ba)
Alfahari da aiki da shisshigi ga Allah, yana suka ne ga bangare rububiya Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace ga da wanda yace da wani
Wallahi Allah ba zai gafarta ma wane ba,
sai Allah ya ce : wane ne ya ke yi min shisshigi kan cewa ba zan gafarta wa wane ba to ni lalle
na gafarta masa kai kuma na rusa aikin ka).Muslim ne ya rawaito
Riya na lalata aiki Allah Madaukakin sarki ya ce a
hadisi kudsi: (Ni na wadatu daga abokan tarayya duk wanda ya yi wani aiki ya
hada ni da wani na a ciki to na bar shi da shirkarsa)Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya zo gurin boka ya tambaye shi wani abu to ba za a karba
mishi sallan kwana arba'in ba) Muslim ne ya rawaito.
(Duk wanda ya bar sallar la'asar to aikin ka ya
rushe) Bukhari ne ya rawaito
(Zalunci duhu ne ranar alkiyama).
Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi,ya ce : ( Tsiyatacce wanda aka yi wa wasoso shi ne
wanda zai zo ranar Alkiyama da sallah da azumi da zakka kuma ya zo yazagi
wannan ya yi kazafi ga wane ya ci dukiyan wane, ya zubar da jinin wane ya duki
wane, sai a bawa wannan dag kyawawan shi wancan ma daga kyawawan shi, idan
kyawawan shi sun kare kafin a biya bashin da ke kansa, sai a dauki kusakuransu
sai a dora mishi sannan a jefa shi a wuta.) Muslim ne ya rawaito.
Zunuban boye na
goge kyawawa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (
Na san wasu mutane magana cikin al'umata za su zo ranar alkiya ma da
kyawawa sun kai girman dutsen tihama da
hasken sa sai Allah ya maida shi Turbaya tarwatstse
Sauban Allah ya yarda da shi ya ce : ya Manzon Allah
siffanta su gare ka fayyace mana su ka mu kasance cikinsu ahalin ba mu sani ba,
sai ya ce : ( Ai su 'yan uwanku ne masu irin fatar jikin ku, suna rikan kamar
yadda ku ke yi na daga dare, sai dai su mutane ne da idan sun kebanta da abin
da aka haramta sai su keta alfurmarta) Ibnu Maja ne ya rawaito.
(Wanda ya riki kare inba na kare dabbobi ba ko
farauta ko kare shuka ba za a rage a kowani rana ladan sa da ya kai
kiradi.)Bukhari ne ya rawaito.
(Duk wanda ya sha giya to Allah ba zai karba masa
salla ba na safiya na arba'in ) Ahmad ne ya rawaito.
Makurar hasara shi ne mutum ya zaci yana kan aiki
mai kyau a halin yana kan sabanin hakan. Allah Madaukakin sarki ya ce : (kace
ko mu gaya muku game da mafifita hasara ga ayyuka?(wadanda aikinsu ya baci a
cikin rayuwar duniya ,alhali kuwa suna zaton lalle ne su suna kyautata (abin da
suke gani)aikin kwarai?)
Bayan
haka ya ku musulmai :
To Ita
ibada da kiyaye ta abin nema ne a
musulunci, dawwama akanta har zuwa mutuwa tushe ne a sharia, Allah Madaukaki
ya ce : ( Kuma ka bautawa Ubangijinka har mutuwa ta zo ma)
Ya wajaba
akan musulmi kada ya guji duk wani aikin alheri,ko da dan kadan ne, ya kuma
nesanci dukkan munana ko da karama ce don bai san wace kyakyawan ce Allah zai
jikan shi a dalilinta.bai kuma san wace mummunar ce Allah zai yi fushi da shi
akan ta ba, ya wajaba ga Musulmi da ya tafi cikin ibadar sa yana mai tsakanin
fata da tsoro, yana raya zuciyar sa da kaunar Allah da kyautata masa zato,
Ina
neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa.
(Ka
ce lalle ne salla ta da yanka na da rayuwa ta da mutuwa ta na Allah ne
Ubangijin talikai, babu abokin tarayya a gare shi, kuma da wancan aka umarce
ni, kuma ni ne farkon masu sallamawa)
Allah
ya sanya min albari ka ni da ku a cikin Alkurni Mai girma,
Huduba
ta biyu
Dukkan
yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawarsa.godiya ta tabbata bisa
datarwarsa da baiwarsa, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi
kadai yake ba shi da abokin tarayya muna girmama shaninsa, kuma na shaida
Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzon sa ne, tsira da amincin Allah ya tabbata
a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa,
Ya
ku Musulmai!
Ku kasance
kun fi kula da karbar aikin akan shi kan shi aikin, ku kiyaye abin da zai
tafiyar muku da da'a daga abin da zai
lalata shi ko ya rage shi, duk wanda yayi aiki mai kyau to ya godewa Allah da
ya datar da shi zuwa ga aikata wannan
aiki, kuma ya roke shi tabbatuwa da dogewa a kai,kuma kiyaye da'a ya fi aikata
ta. Kuma bin lura shine na karshe, shi wanda ya san Allah yana kuma bauta masa
zai sanya a cikin biyayyar sa wani abu da zai rika tsarkake mishi rayinsa ta hanyar
lazimtar ibada,
Da
gaskiya da kubutaciya kuma da kankan da
kai lafiyayyar zuciya,da kyawawan dabiu zai so alheri ga waninsa kamar yadda ya
ke so wa kansa, kada ya aminta daga Makru na Allah kuma kada ya yanke kauna
daga rahamar Allah.
Sannan
ku sani Allah ya umarce ku da salati ga
Annabinsa.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق