الخميس، 24 أغسطس 2017

Gyaran zahiri da badini (Ciki da Waje

Hudubar  Juma'a na Masallacin Annabi na sheikh Abdulbari Bin  Awad  Assubaiti 3/12/1438 AH

Hudubar farko
Allah ya halicci mutum a cikin mafi kyawun tsayuwa, ya mar ni'ima da sura ta bayyane mai kyau, da na ciki daidaitacce mai daraja.
Allah Madaukaki ya ce : (Ya kai mutum me ya rude ka game da ubangijinka Mai karimci ? wanda ya halitta ka sa'annan ya daidaita ka ya kuma tsakaita ka. A cikin kowace irin sura ya so gina ka a kanta)
Cikan kyan dan Adam na daga gyaruwan badinin shi, wanda ke bayyana kyan wajen shi. Tsabtatuwan ciki na bayyana  amfanin  tsarkin waje.
Ko da ya ke mutane sun fi damuwa da abu na bayyane don shi ne makurar sanin su, amma shi Allah ya fi la'akari da na badini game da dan adam, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Allah bai dubi ga surorin ku ko dukiyarku, sai dai yana dubi  ne ga zukatanku da ayyukanku)
A duk lokacin da aka fi kyautata  badini wurin karfin  alaka  da Ubangiji sai a samu kauna da karbuwa, ba wani bawa da ya kyautata cikinsa da son Allah Madaukaki face ya samu karbuwa  ta zuci a sama da kasa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle idan Allah ya so bawa sai ya kira Jibrilu yace : Lalle ina son wane ta ka so shi! Sai Jibrilu ya so shi, sannan ya yi yekuwa a sama, ya ce : Allah na son wane to ku so shi! Sai na cikin sama su so shi, sai a sanya mishi karbuwa a doron kasa.)
A ranar Alkiyama ; za a kwalkwale hisabi ciki da waje na bayi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma kada ka bi abin da ba ka da ilimi game da shi, lalle ne ji da gani da zuciya dukkan wadancan (Mutum) ya kasance daga gare shi wanda ake tambaya,)
Wannan fahimta mai zurfi zai sanya musulmi ya gyara badinin shi, wanda ya ginu a kan tsarkaki niyya ga wanda ake bautawa, don niyya ne sirrin bauta , kuma ginshikin bautawa Allah na zahiri yana ga kyautatuwan bin Manzo da koyi da shi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ka ce idan kun kasance kuna son Allah to ku bi ni Allah ya so ku, kuma ya gafarta muku)
 Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Dukkan al'uma ta zasu shiga aljanna sai wanda ya ki, sai suka ce ya Manzon Allah wa zai ki? Sai ya ce : Wanda ya bi ni zai shiga aljanna wanda ya saba mini to hakika ya ki.)
Ibada na tarbiyantar da  musulmi a zahiri da badini, wanda ya lura da koyarwar Annabi zai ga akwai kulawa da ciki da waje, na daga cikin haka akwai tsayuwar musulmai gaba ga Ubangijinsa da daidaita sahu da la'akari da ita na da ga cikin tsaida sallah, hakika ya tabbata daga gare shi ya kasance ya na umartan mutane da daidaita sahu  ya na cewa ya ku bayin Allah ko dai ku daidaita sahun ku ko Allah ya rarraba fiskoki.
Muna gani cikin ayyukan hajji kulawa da tsarkake zahiri da tsaftace badini, to fitan musulmi yana nufan yin hajji ya dumfari dakin Allah mai alfarma yana nuna mana mafi girman sura na amsa kiran Allah ciki da waje, tufafi da niyya da talbiya da ambaton Allah na dada tabbatar mana da hakan.
 Allah Madaukakin sarki ya ce : (Hajji watanni ne sanannu cikinsu to babu jima'I kuma babu fasikanci  kuma babu jayayya a cikin hajji kuma abin da kuka aikata daga alheri Allah  ya san shi kuma ku yi guzuri to mafi alherin guzuri yin takawa kuma ku bi ni da takawa ya ma'abuta hankula  سورة البقرة 197
 Kamar yadda Manzon Allah Almusdafa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fito da hakan a fili a hudubarsa ta hajjin ban kwana inda ya bayyana mana matsayin abubuwa na badini a musulunci, kuma shine abin da Allah ke sa ido akai, yana cewa : (Ya ku mutane ! ku saurara  lalle Ubangijinku guda ne kuma mahaifinku daya ne, ku sani ba fifiko tsakanin balarabe da ba'ajame  haka farin fata bai fi bakar fata ba haka jar fata bai fi bakin fata ba kuma bakin fata bai fi jar fata ba sai da tsoron Allah)
Musulmi an umarce shi da ya nesaci sabo na bayyane da na boye Allah Madaukakin sarki ya ce : (  Ka ce abin sani kawai Ubangijina ya hana abubuwan al-fasha abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya boyu ) سورة الاعراف 33
Lalle tsaftar zahiri da tsarkake badini na kai wa ne ga tsaftace matattarar al'umar musulmi da kuma sifantuwa da kyawawan halaye da kyautata dabi'u, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Kuma Allah ne ya fitar da ku daga cikunan iyayenku ba da kuna sanin kome ba kuma ya  sanya muku ji da gannai da zukata tsammaninku za ku gode  سورة النحل 78
     Duk wanda ya gyara zahirinsa ya tsaftace badininsa  to zai yi kokari kar ya saba abin da yake kira a kansa na shiriya da halaye na mutunci da alheri, Allah Madaukakin sarki ya ce :( Shin kuna umurnin mutane da alheri kuma ku manta da kanku alhali kuwa kuna karatun littafi ? shin ba za ku hankalta ba)  سورة البقرة 44
Cikin alakar musulmi da dan uwansa musulmi a zahiri da badini akwai ya fiskance shi da fara'a da runguma sa'annan ya ya yi mishi adua na alheri a boye cikin tsarkin zuciya, ya so wa 'yan uwansa alheri  ya kuma bayyana kauna tare tsarkake zuciya game da shi, Manzon  Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Ba wani bawa musulmi da zai yi adu'a ga dan uwan shi musulmi a boye face Mala'ika ya ce : Kai ma kana da kwatankwacin hakan)
Musulmi shi ne wanda musulmai suka kubuta daga sharrin harshensa da hanunsa a bayyane kuma  suka aminta daga hasadarsa da  kullinsa a zuci, Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(kar ku yi hasada kar ku yi munajasha (cinikin ingiza mai kantu ruwa) kar ku yi gaba da juna, kar ku yanke wa juna, kada wanin ku ya yi ciniki a kan cinikin wani, ku zama bayin Allah 'yan uwan juna, Musulmi dan uwan musulmi ne ba zai cuce shi ba, ba zai tabar da shi ba, ba zai yi mishi karya ba, ba zai rena shi ba)
'Yan Uwantaka  na hukunta taimakawa musulmi ga dan Uwansa  Musulmi da harshe da rubutu a bayyane, a boye kuma a zuciya da tunani.
Ya wajaba ga dukkan musulmi ya taimaka game da al'amuran musulmi da dukiya da matsayi da shawari da adua,  (Kuma lalle Mun aika zuwa ga al'ummai daga  gabaninka sai muka kama su da tsanani da cuta tsammaninsu za su kankan da kai) سورة الانعام 42
 Idan musulmi zai zartar da wani hukunci bai dace a gare shi ya yi ta bibiyan sirrin mutane ba ko ya dora wa kansa nauyin haka ba ko farauto abin da ya boyu daga gare su ba, to Allah shi ne mafi sanin abin da ya boyu, kuma hisabin su na kan wanda ba abin da ke boyuwa a gare shi,   Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( An umarce ni da na yaki mutane har sai sun shaida ba abin bauta da gaskiya sai Allah kuma Muhammadu Manzo ne na Allah su kuma tsaida sallah su bada zakkah, to idan sun yi hakan to kare jininsu daga gare ni, sai da hakki na musulunci, kuma hisabin su na kan  Allah Madaukai).
Neman kutsawa cikin badinin musulmai da hukunci game da abin da ke zukatansu  keta alfarmansu ne, wanda hakan zai kai ga sakaci game da mutunci musulmi da halasta jinin su, Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Gushewar duniya wallahi ya fi sauki gurin Allah a kan kashe mutum musulmi,)
Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana muamalantar munafukai  da ke bayyana musulunci irin muamalar musulmai kuma yana gudanar musu da hukunci  na musulunci a zahiri duk da cewa ya san wasun su a boye munafukai ne.
Alamu na imani na bayyana a lokacin jarrabawa: ta hanyar  hakuri a zahiri da neman lada a badini, gabbansa ba za su wuce gona da iri ba ko ya yi rashin ladabi ga Ubangijinsa kuma Majibincinsa. Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lalle idanu na zubar da hawaye kuma zuciya na bakin ciki amma ba za mu fadi wani abu ba sai abin da Ubangiji ya yarda da shi, kuma lalle ya kai Ibrahim muna bakin cikin rabuwa da kai)
A wurin tsere zuwa ga aljanna ba a yin nasara sai an gyara ciki tare da muhimmancin waje, to da gyaruwan badini ne masu cin nasara suka yi fintinkau, masu isa suka haye suka kai gaci, Allah Madaukakin Sarki ya ce :  (Lalle wadannan da suka ce Ubangijinmu shi ne Allah sa'an nan suka daidaitu mala'iku na sassauka a kansu (a lokacin saukar ajalinsu suna ce musa ) kada ku ji tsoro kuma kada ku yi bakin ciki kuma ku yi  bushara da Aljanna wadda kun kasance ana yi muku wa'di da ita   سورة فصلت 30

Huduba ta biyu
Bayan haka ! na daga cikin yelwar rahamar Allah ya hore wa mutum  tasha ta karin imani da zai yi guzuri da abin da zai tsarkake badininsa ya kuma habaka zahirinsa, na daga ciki akwai wadannan ranaku masu girma masu albarka wanda lada ke ribanyuwa a ciki wato ranaku goma na zulhijja wanda ke da nunanun fa'idoji ga daidaiku da al'uma, ya zo a falalansu fadin Allah Madaukakin sarki  (Ina rantsuwa da Alfijri  da daruruwa goma) da fadin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ( Ba aikin da ya fi kamar na wadannan ranaku goma ) sai aka ce har jihadi? Sai yace ( ko jihadi ne sai dai mutumin da ya fita da ransa da dukiyarsa bai dawo da komai ba)Buhari ne ya rawaito
Kamar yadda kabar bari na saki waiwai sunna ne a goman zulhajji da sauran ranakun Sallah (Tashrik) tun daga shigar watan zulhajji  har zuwa  ranar karshe na Attashrik, shi kuma kabarbari kayyadaddu na fara wa ne tun daga asubahin ranar arafa har zuwa faduwar rana  na ranar karshe na ranaku Attashrik.
Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu akbar La'ilaha illallahu Allahu akbar wa lillahil Hamd
Na daga cikin ayyuka da a ke kusantar  Allah da  shi akwai yanka dabbar  laiha, hakika Imam Attirmizi da Ibnu Majah daga A'isha tana mai jingina shi ga Annabi (Ba wani aiki da dan adam zai yi a ranar babbar sallah da ya fi soyuwa ga Allah da ya  kai zubar da jini( wato yanka dabba ) don zai taho a ranar alkiyama da kahonsa da abin alamarsa da kofotonsa, kuma jinin na zuba a gurin Allah a wani wuri kafin ya zuba a kasa, to ku tsarkake kawunanku da shi) Hakim ya inganta shi a Almustadrak.

Ya tike.

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق