الجمعة، 11 أغسطس 2017

KUNYA A MUSULUNCI

Hudubar Juma'a  a Masallacin Annabi  19-11-1438AH sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albuaijan
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya raba halaye a tsakaninku kamar yadda ya kasa arziki a tsakaninku ya sanya kyakyawan hali shine ma'uni na fifiko a tsakaninku                                                             na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya yana da kyawawan sunaye da kuma siffofi madaukaka.
Na shaida Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bawansa ne kuma Manzonsa ne, ya isar da sako, kuma ya sauke amana, ya yi nasiha wa alumma, ya yi jahadi don Allah yadda ya dace a yi jahadi har lokacin da mutuwa ta zo mishi .
Ya Allah ka yi dadin tsira da aminci a gare shi da iyalansa da sahabbansa da wanda  ya bi shiryarwarsa  ya kuma yi riko da sunnarsa har zuwa ranar sakayya.
Ya ku bayin Allah ku ji tsoron Allah, Mabuwayi da daukaka,domin takawa daukaka ne a nan duniya kuma guzuri ne a lahira.
(ya ku wadanda suka yi imani! In kun ji tsoron Allah zai sanya muku mararraba kuma ya kankare kananan zunubanku kuma ya gafarta muku. Kuma Allah ne Ma'abucin falala Mai girma)
Lalle duk da sabawan harshen su da launin su ko da kuwa sun kasance daga  Uba guda,to su kamar ma'adinai ne (da ake tonowa a kasa) wani na da fifiko kan wani haka wani nau'in ya dara wani, sabo da dabiu ne maauni na kyawawan halaye, kuma shi ne mizani na al'umu, kuma tsani zuwa ga daukaka, da kaiwa kololuwa, Manzon Allah ya yi gaskiya da ya ce :(Lalle zababbun ku su ne mafi kyan halaye a cikinku) Bukhari ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah ! Lalle addinin da muke dangantuwa gare shi addini ne na kyawawan dabiu. Kuma AnnabinMu Muhammad an turo shi ne don ya cika kyawawan dabiu, kuma biyu bisa ukun farfajiya na duniyan musulmai sun karbi musulunci ne ta hanyar kyawawan dabiu.
      kunya ne sarkin halaye nagari kuma, ba sabani kan  kunya ne abu mafi kyau da ado  a cikin kyawawan dabiu,                                                                                                                                                                                                             ya ku bayin Allah  kunya ita ce tushen kyawawan dabiu'kuma ita ce mabubbugan kyawawan halaye dukk wata falala ta boyu a cikin kunya wanda ya siffantu da ita  musuluncinsa ya yi kyau, haka nan kuma dabiu'.
Ita  za ta daukaka mutum ta sa ya  yi nesa daga sabo domin jin kunyan ubangijin shi dabia' ce mai daraja wanda ke haifar da aikata dukkan wani aiki mai kyaw ya hana mutun aikata aiki dukkan mara kyaw yasa mutun ya yi nesa daga dukk wani  aiki na kunya muna na da kuma ya yi nesa da abubuwa na minkari lalle shi din nan dalili ne da ke nuna girman hali da tsarkakan zuciya ga mutun kunya na tunkude mutun daga  aikata aikin ashshakuma kuma ya kare mai mutuncin shi ya dasa mishi kame kai a zuciyan shi shi kama wani ma'dini ne  mai tsada wanda ba mai siffantuwa da shi sai zukatanda suke na ayaba kuma kaman wani ado ne na annabawa an karbo daga abu masu'd Allah ya kara mishi yarda  ya ce: manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce''Na daga cikin abinda mutane suka riska na maganganun Annabawan farko  akawai " in baka ji kunya ba to ka aikata abin da ka so ) Bukhari ne ya rawaito   
 kunya  alami ne na musulunci ko wani addini yanada wasu dabiu'                                       
Na daga cikin dabi'u na musulunci  akwai kunya,Ibnu maja ya rawaito kuma Albani ya inganta shi a cikin sahihuhu aljami 
Imani  yanki saba'in da dori ne kuma kunya  daya daga cikin yanki  ne na imani muslim ne ya rawaito
 Manzon Allah ya wuce wani mutumi yana zargin dan uwan shi sabo da yawan   kunya sai ya ke cewa lalle kai din nan kana jin kunya sai yana cewa har kaman hakan ya maka illa sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yake cewa kyale shi domin lalle kunya na daga cikin imani kuma babu imani ga wanda ba yi da kunya Bukhari ne ya rawaito
Kuma na daga cikin sirri ya ku bayin Allah da ke sanya kunya ta zama  a cikin imani saboda dukkan imani da kunya sun kasance suna kira ne zuwa ga alheri kuma suna kusantarwa zuwa gare shi kuma suna tunkudarwa daga sharri kuma suna  nesatarwa daga gareshi  kunya kofa ne daga cikin kofofin alheri.
An karbo daga Imran dan Husain Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Annabi tsira da amicin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Ita kunya bata kawo wani abu sai alheri ) kuma ya ce (kunya alherine dukkaninta ) muslim ne ya rawaito
Ya ku bayin Allah hakika manzon Allah ya tattaro dukkan siffofi  na mutanen farko da na karshe ya siffantu da dukkan sifa mafi daukaka da daraja har Allah ma ya ke ce da shi (lalle kai din nan kana kan dabiu' masu girma).
Manzon Allah ya  kasance mafi jin kunya a kan budurwa da ta ke cikin kafunta idan yaga wani abu da ya ki sai  a ga kin a fuskar shi ta hanyan kunya  ya lullubeshi
 ya ku musulmai lalle kunya daya daga cikin surori ne da darajoji mafi kololuwa a wurin Allah ta inda za ka ji kunyan a ganka wurinda ya haneka hakika kuma shi ya halicceka kuma ya daidaita ka kana jin kunyan ka yi amfani da ni'marsa da ya baka wurin saba mishi , Manzon Allah ya kwadaitar bisa ga kunya kuma cewa kunya daga Allah ne sai ya ce (ku ji kunya ya ku bayin Allah yanda ya dace a ji kunya sai suka ce ya manzon Allah dukkan mu muna jin kunya Ahamdu llillahi sai ya ce ba shi a ke nufi ba ana nufin jin kunya daga Allah yanda ya dace da  cancancin jin kunyarsa) wato kayi ya kiyaye abunda ya tattara ciki ya kiyaye abinda ya kumsa kuma a tuna mutuwa da karewa duk wanda ya nufi lahira zai bar kawan rayuwan duniya wanda ya yi haka to hakika ya ji kunyan Allah bisa cancancin kunyarsa  ) Hakim ne a mustadrak ya rawaito kuma ya inganta shi zahabi ya mar muwafaka kunya daga malayiku masu daraja da kuma masu kiyayewa masu rubutu da su shaida a gareka wato daga dama da hagu suna zaune ba abin da zai ambata  ko ya furta na fadi face  akwai mai kulawa tare da shi kunya na mutane shi ne ka keta dokan Allah da ya suturta a gare ka ka bayyana sabo a gabansu Annabi ya ce dukkan alummana ana basu lafiya suna kubuta sai wadanda su ke masu bayyana sabo kunya daga rayi daga gabbai domin su din nan sune zasu zama shaida a gareka sun yi musu da kai ranar alkiyama Allah ya ce ( ranarda harsunansu  za su shaida musu da hannayensu da kafafuwansu da abinda suka kasance suna aikatawa a wannan ranar ne Allah zai cika musu addininsu na gaskiya kuma su san cewa lalle Allah shi ne gaskiya kuma bayyananne )




 HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah mai kunya kuma mai suturcewa ya sanya daga cikin dabiu' masu daraja da kuma ya cika kyawawan dabiu' ta hanyan turo mai albishir kuma mai gargadi wato fitila mai haskakawa annabin mu muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi da aminci tabbatacce mai yawa ya ku musulmai lalle muna rayuwa acikin wata marhala na halaye wanda suke na kunci muna karshen zamani wanda wadan nan munanan dabiun sun yi rinjaye kuma sun yawaita shubuhohi dabin soye soyen rayuka sun yadu abunda da ya kasance  a jiya sanennen abune a yau ya zama shi ne  abin ki abunda kuma ya kasance abin ki a jiya ya zama shi ne abin so abinda aka saba da shi munanan dabi' sun sulale su shigo cikin gidaje ta hanyoyin nau'urorin  sadarwa  na zamani a wannan yanayi gashi ana fiskantanmu to ya wajaba mu  tarbiyyantar da masu tasowa kuma mu katangesu da akida na musulunci kyawawan dabiu' daga Allah ne kuma su din nan katanga ne daga cikin katanga wanda suke masu bada kariya kuma da aminci ga tarbiyya da tsarkake zukata da kuma murakaban Allah .
Ya ke musulma ya ke yar uwata mai daraja lalle kunya ko da ya kasance abu ne da ake nema a hakkin maza sai de kuma ya fi wajabta a kan hakkin mata a bangarenta yafi karfi domin lalle matanda ta ke bautawa  Allah da kyawawan dabiu'nta tana neman lada kuma tana jin tsoron ukubarsa  lalle kunya na daga cikin kyawawan dabiu' na addini kuma da ake tada mutane a kansu wanda ke lullube mace a cikin kafunta da shi tana ci tana sha kuma tana tufata shi kuma ta ke kai komo fita ta tafi tare da shi lalle kunya ga mace musulma shine hanun jarinta kuma kuma shi ne daukakanta kuma shi ke kiyaye karamarta kunya na janyo wa ya mace aminci da kuma daukaka da kuma kawa dalili ne kuma na nuna cewa ita kamemmiya ce haka nan kuma wani katanga ne mai katangewa mai karfi ya ke musulma Allah ya yi nuni a cikin littafinsa da kunya mace a kissan musa alaihi assalam ayayinda ya zo diba daga ruwan madyana  ta inda wata mace daya daga cikin diyar shua'ibu ta zana mana mana siffa daga cikin siffofi na kunya na daga ciki abinda annabi musa ya yi la'kari da shi na irin kame kanta da kunyanta da rashin cakudedeniyansu da mutane sai ya shayar da su Allah madaukakin sarki ya ce game da annabi musa  (kuma a lokacin da ya isa mashayar madyana ya sami wata jam'ar mutane suna shayarwa kuma a bayansu ya sami wadansu mata biyu suna korar (tumakinsu ).ya ce menene sha'ninku ? su ka ce ba za mu iya shayarwa ba sai makiyaya sun fitakuma uban mu tsoho ne mai daraja ) (sai ya shayar da su )
Shi kunya da kame wana daga cikin abubuwa ne na kunya kuma alamane na musulma kuma  dalili ne na kyakyawan tarbiyya ayan nan mai girma ta nuna mana misali daga cikin kyawawan dabiu shi wato kunya da kuma nitsuwa a dukkan kai komo  da zance Allah ya yabi daya daga cikinsu  , lokacin da ta dawo gare shi , sabo da abin da ta siffantu da shi na kunya, ba ta yi wani rangaji ko kwarkwasa ba , ba ta bayyana kwalliyanta ba kuma bata  rausaya murya ba, (  sai dayansu ta je masa  tana tafiya akan jin kunya ta ce: Ubana yana kiran ka domin ya sakanya  maka  ladan abin da ka shayar )

 YA KE MUSULMA :
Ga mahaifiyarki kuma abin koyin ki Aisha uwar muminai tana buga misali mafi kaye game da kunya , don ta kasance tana jin kunya har ma ta suturce daga rayayye da matacce ,  tana cewa :- na kasance na kan shiga dakin da aka binne Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata agare shi tare da Abubakar a cikin shi, ba tare da tufafi ba ,  sai nake cewa wannan  miji na  ne wannan kuma mahaifi na  ,   to a yayin da aka binne Umar wallahi ban shiga dakin ba face da tufafi na a daure a kai na sabo da kunya da nake ji na Umar .
 Kuma ta kasance idan ta zo daura da mahaya  a halin tana ihrami sai ta  sake jalbabinta a kan fiskanta .
Kuma ta kasance tana dawafi a dakin ka'aba  kamar  yanda ya zo a cikin littafi mai inganci  ba ta cakudaidainiya da su , a yayin da wata 'yar gidan ta take cewa da ita , na yi dawafi bakwai a dakin ka'aba kuma      na taba rukuni sau biyu ko uku sai Aisha ta ce, kar Allah ya baki lada , kina tuttunkude maza, ase ba za ki yi kabbara ba kawai ki wuce .
 YA KE MUSULMA :
Hijabin mace da kamun kanta na cikin addininta kuma yana cikin kyawawan  halayen ta , to, idan har fidiranta ya juya , ta shakala yin addinin ta sai ta yada kwarjallenta , ta yi wurgi da mayafinta , ta bayyana adonta  wuraren da za ta sa a fitinu da ita , tofa ta yi hasarar addinin ta kuma ta sarayar da amananta , an karbo daga Abu Huraira ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (nau'I biyu na mutane suna cikin 'yan wuta ban gansu ,   sai ya ambata daga cikin su , Matayen da suke sanya sutura amma suna cikin tsiraici , suna kuma jan hankalin mutane , masu karkatarwa ne kuma karkatattu, kayukan su kamar tozon rakumi , wanda suka karkace ,  ba za su shiga Aljanna ba ba za ma su ji kamshin ta ba , kuma a hali kamshinta a na jin shi tun daga tafiyan kaza da kaza ).

YA KU MUSULMAI :
(Dukkan ku masu kiwo ne , kuma dukkan ku abun tambaya ne bisa ga kiwonsu ,  na miji me kiwo ne akan iyalan gidan shi  kuma  abin tambaya ne game da  su ,  haka ma mace mai kiwo ne a kan gidan mijinta da kuma 'ya'yan shi ,   kuma ita abin tambaya ne game da su ,  ku saurara ! dukkan ku masu kiwo ne kuma dukkanin ku abin tambaya ne bisa ga kiwon da aka ba ku) Muslim ne ya rawaito
 Ya  Allah ina rokonka kunya da zai tsare ni daga saba maka ,
Ya Allah ka shiryar da mu bisa ga mafi kyan halaye ba mai shiryarwa  zuwa gare su sai kai , ka tunkude mana munanansu daga  gare mu , domin  ba mai tunkude munanan daga gare mu sai kai.
 Ya Allah muna rokon ka shiriya da takawa da kame kai da wadata .
 Ya Allah ka daukaka Musulunci ga musulmai ka kaskantar da shirka da mushrikai, ka taimaki bayinka masu Tauhidi ,    


















    

  


هناك تعليقان (2):