Hudubar Juma'a a Masallacin Annabi 20 shawwal 1438 AH Na
Sheikh Abdul-Bari Bin Awad Al- subaiti
Allah ya sanya kasa ga mutum
shimfida da makwanci ,ya sanya a cikin shi Matabbata da kuma jin dadi
zuwa wani lokaci, sannan ya sa albarka kuma ya kaddara abin cinta a ciki Allah ya hore abin da ke cikin sammai da kasa, ya sanya dare
da wuni da rana da wata da sauran halittu don amfanin bayi da kuma nau'uka
na maslahohinsu.
Na daga cikin hikimar samar da amfani shine a bawa musulmi daman jin dadi da abin da Allah ya halatta, mutun ya ji dadi da rayuwa ta duniya da jin dadinta, Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Ubangijinka
yana da hakki a gare ka haka nan jikinka na da hakki a gare ka kuma iyalan ka
na da hakki a gare ka haka nan shi ma mai ziyaranka yana da hakki a gare ka to ka bawa kowanne hakkinsa.)
Allah Madaukakin sarki yana cewa
: (ka ce: wa ya haramta kawa na Allah wanda ya fitar ga bayinSa da dadada na daga arziki? ka ce : su din nan ga wadanda suka yi imani ne a wannan rayuwa ta
duniya sannan kuma yana kebanta a gare su
ranar alkiyama haka nan ne muke bayanin ayoyi daki daki ga mutanen da suke sani).
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi kira da
bayyana abin da ke cikin addinin Allah na hutu da shakatawa ta rayuwar duniya
don jin dadi da ke kawo karsashi ga rai da ingizawa zuwa ga aiki, a lokacin da Annabi
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya ga mutanen Habashawa suna wasa
sai ya ce: (Domin ku sani a cikin Addininmu akwai sauki da sassauci, domin
ni an turo ni ne da addini mai sauki wato Alhanifiyya Assamha)
Aliyu Dan Abu Dalib Allah ya kara yarda a gareshi ya ce: (Lalle
zukata na kosawa kamar yanda jiki ke kosawa to ku nema mata abubuwa da kalaman
hikima na jin dadi )
kuma yake cewa : (ku hutar da zukatanku na wani lokaci bayan lokaci domin
zuciya idan an takura mata sai ta makance).
Abu darda' Allah ya kara yarda a gareshi yana cewa (lalle ni ina dan
zuwa yawo na shakatawa da zuciyata da wasa na halal domin ya dada samun karfi don tsayuwa a kan gaskiya.
Manzon mu tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi mai karamci
yana cewa ya kai Hanzala haba dan lokaci bayan lokaci mana )(Wato a huta)
Umar dan kaddab yace:( mutanen (sahabbai) sun kasance suna dariya a
halin imani a cikin zukatansu yafi karfi da kafuwa akan dutse.)
To wan nan wasan da jin dadin baya raunana imaninsu kuma baya bata
dabiunsu sannan kuma ba ya sa su ketare
lokaci na sallarsu da ambaton Allah da karatun alkur,ani.
Jin dadin musulmi daga cikin abin da Allah ya samar madaukakin sarki na
daga abubuwa na amfani da alheri ana gina shi ne akan daidaito tare da saiti,
sai mutum ya rayu da fidira irin wanda Allah ya halicci dan adam akai sannan
mutum yaji dadin abin da Allah ya halatta a gare shi tare da yalwata jin dadi
da annashawa musamman alokacin idi wato da kuma bukukuwa ana bawa mutum lada
alokacin da yake jin dadi a rayuwarsa na duniya in bai fita cikin dokoki na
sharia ba da ka'idoji na addini ba Manzo Allah tsira da aminci Allah su tabbata
a gare shi yace: (A cikin tsokan dayanku akwai sadaka (wato agurin tarawa da
iyali) sai suka ce ya Manzon Allah mutum zai biya bukatarsa ya more shaawarsa kuma kasance
yana da lada? Annabi yace: E yanzu in da
zina ya yi shin bai da alhaki? sai suka
ce e yana da shi. yace to haka ne idan
ya sanya shi ahalal to shima yanada lada.
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: ( An
sanya min kaunar turare da mata, sannan an sanya sanyin idanuwana acikin sallah).
Dadin
rayuwan duniya da ni'marta na daga cikin nau'uka na gabatar da lada da Allah ke
yi wa bayinsa mu'minai kari a kan abin da ya tattala musu a ranar sakayya na daga ni'ma na madawwamiya, Allah Madaukakin sarki ya ce :(To domin men
wata alkarya bata kasance ta yi imani ba har imaninta ya amfane ta, face mutanen Yunus? A lokacin da suka yi imani mun janye azabar
wulakanci daga gare su a cikin rayuwar duniya kuma muka jiyar da su dadi zuwa
wani lokaci )
A duk lokacin da bawa ya dada
kusantan majibincin shi ya kuma koma
zuwa gareshi to zai yi rayuwa na jin dadi da morewa kuma abin da ke wurin Allah
yafi alheri kuma yafi wanzuwa : shi jin dadi da morewa na daga cikin
amfanin ne ayyuka na kawarai, Allah madaukakin sarki ya ce :(wanda ya yi
aiki na kawarai na daga na miji ko mace
yana mumini to zamu raya shi rayuwa na jin dadi kuma mu sakanya mishi da mafi kyan abin da
suka kasance suna aikatawa ) mafi
girman abu mai kawo jin dadi shi ne
lazimtan istigfari wanda da shi ne alheri ke tabbatuwa da albarkoki kuma da shi
a ke tunkude bala'i kuma a duddulo da arziki sannan muna sha daga albarkatun
sama a fitar mana kuma da albarkatun
kasa kuma a taimaka mana da dukiya da
y'ay'a sai na ce ku nemi gafara daga
ubangijinku lalle ya kasance mai gafara ne0 ya sako (girgijen) sama a kanku da
ruwa mai bubbuga . kuma ya yalwata muku game da dukiya da diya ,( kuma ya sanya
muku albarka kuma ya sanya muku gonaki
kuma ya sanya muku koguna )
walwala da jin dadi a rayuwan
mutun musulmi abu ne mai fadi da yalwar
ma'ana ya taso ne daga wasu manufofi masu daraja kuma ya ta'allaka da sako na
wannan addini da halayensa da ladubansa , kai lalle jin dadi wani hanya ne na
sauke sako ba ita ce ma kura ba da ake so a nemi jin dadin ta, to
idan ba haka ba kuma to sai mutun ya dulmuye ya samu rauni da fandarewa.
jin dadi a rayuwan musulmi
be iyakance shi a kyalakyalan rayuwan duniya ba bai kuma tsakaita a kantaba,
sai dai ma ya zarce zuwa ga ni'ma na aljanna wanda ke mantar da dukkan gajiya
da wahalhalu na duniya :to shi musulmi
yana riskan cewa wannan rayuwan na duniya duk yadda ta tsawaita to zata gushe
kuma jin dadinta duk yadda ya girmama to na dan wani lokaci ne, Allah madaukakin
sarki ya ce ( ka ce jin dadin duniya dan kadan ne )
kuma Allah ya ce:(kuma alhali kuwa rayuwan duniya bata zama ba
dangane da duniya face jin dadi kadan ) (kuma kuna da a cikin kasa matabbata da
kuma jin dadi zuwa wani lokaci )
Aduk lokacin da musulmi ya dandani dadi na rayuwan duniya da
walwalanta )
zai yi gaggawan faduwa a
tunaninshi jin dadi na aljanna da ni'mar lahira sai ya yi gaggawa saboda
kwadayi da shawki zuwa gareta da kuma fatan samun daraja mafi kololuwa
Allah madaukakin sarki ya ce: (sabo da
haka abin da aka ba ku, ko mene ne, to, jin dadin rayuwan duniya ne kuma abin da
ke wurin Allah shi ne mafifici kuma shi ne mafi wanzuwa ga wanda suka yi imani
kuma suna dogara a kan ubangijinsu kawai )
imani da Allah da dogaro a gare
shi tsarki ya tabbata a gare shi rangwame da afuwa da yafiya da sa farin ciki a
zukatan masu rauni da sanya musu hoton shi a fiskan su da idanuwan su da
tsayuwa don biyawa mutane bukatunsu shine dukkan jin dadi,
wani mutumi ya zo gun Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi sai ya ce ya manzon Allah
wani aiki ne yafi soyuwa a wurin Allah? sai ya ce farin ciki da zaka jefa wa
musulmi ko kuma ka yaye mishi bakin ciki,
ko kuma wani bashi da zaka biya masa ko
ka kore mishi yunwa ,da na tashi na tafi ga dan uwana musulmi da bukata yafi
soyuwa a gare ni a kan na yi itikafi a
wannan masallaci :yana nufi
masallacin madina .
Na daga cikin jindadin duniya
akwai ni'ima ta 'ya'ya da 'yan Uwa maza da mata, don samuwarsu akwai debe kewa,
gyaruwarsu kamar wata ganima ce da karfi, su kawa ce ta rayuwar duniya da
kyalakyalanta, da kuma cikar walwala da annashawa ne,su ne ma tushenta,
Farinciki da walwala na karuwa a lokacin da ka yi shi tare da 'yan Uwanka da
wadanda ke kewaye da kai, ka yi farin ciki da farincikinsu, kuma ka samu
walwala da debe kewa a dalilin nasu walwalar,ka yi tarayya da su a jin dadi da
annashawa,
Rayi na kara samun jin dadi a
lokacin da mutum ya cinma wata manufa ya yi nasara a aiki ya tsinkayi daukaka da fa'idojinta, kamar yadda ya ke shiga rayuwa
mafi sa'ida idan ya kammala wata
ibada,zai yi murna da azumi yayin da ya sha ruwa, zai yi murna da sallah yayin
da ya ya yi ta, haka kuma da hajji bayan ya sauke ayyukanta.
Dadi na kai wa makura idan
mutum ya yarda da kaddara ta Ubangiji,
ya zama ya samu yakini da Allah Madaukaki a dukkan abin da ya hukunta na al'amari, Abu Addarda ya
ce : ( Lalle Idan Allah ya kaddara hukunci to yana so bayi su yarda da shi)
Ibnu Mas'ud ya ce : (Allah
cikin adalcinsa ya sanya hutu da farinciki a yakini da yarda, ya kuma sanya
bakin ciki da bacin rai a shakku.)
Umar dan Abdul'Aziz Allah ya
masa rahama ya ce :( Na wayi gari ba abin da ya rage na ke jin dadinsa sai
cikin yarda da abin da Allah ya hukunta)
Huduba ta biyu
Mai hankali ya na baiwa rayuwar
duniya matsayinta, bai kwace wa a tunanin sa alkawarin Allah duk yadda kyala
kyalan duniya da kawannta ke ci da
habaka, Allah Madaukakin sarki ya ce :(
kuma wannan rayuwa ta duniya ba ta zamo ba face abar shagala da wasa, kuma
lalle lahira tabbas ita ce rayuwa, da sun kasance suna sani,)
Mai hankali zai yi taka
tsantsan da jindadi na boge, wanda ke haifar da hasara da nadama, domin sabo
karshen sa kaskanci ne da bakin ciki da radadi, ba wata ni'ima da zata gushe wa
mutum face sabo da shu'umci irin na sabonsa, domin idan Allah ya yi ni'ima ga
bawansa sai ya kiyaye ta gare shi ba zai
sauya ta gare shi ba har sai idan shin ne da kansa ya yi aiki don canja ta, (Lalle
ne Allah bai canja abin da ya ke ga mutane sai sun canja abin da ya ke ga zukatansu
kuma idan Allah ya yi nufin wata azaba game da mutane to babu mai mayar da ita
kuma ba su da wani majibinci baicin shi ).
Wace hasara ce ta fi jin dadin
da zai haifar da fushin Allah da azabarsa? Allah madaukakin sarki ya ce :(wancan
domin abin da ku ka kasance ne kuna farin ciki da shi a cikin kasa ba da hakki
ba kuma da abin da kuka kasance kuna yi na nishadi).
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق