الخميس، 13 يوليو 2017

JIN DADIN RAYUWAR DUNIYA GA MUSULMI

Hudubar  Juma'a  a Masallacin Annabi 20 shawwal 1438 AH Na Sheikh Abdul-Bari Bin Awad Al- subaiti
Allah ya sanya kasa ga mutum  shimfida da makwanci ,ya sanya a cikin shi Matabbata da kuma jin dadi zuwa wani lokaci, sannan ya sa albarka kuma ya kaddara abin cinta a ciki  Allah ya hore  abin da ke cikin sammai da kasa, ya sanya dare da wuni da rana da wata da   sauran halittu don amfanin bayi da kuma nau'uka na  maslahohinsu.
Na daga cikin hikimar   samar da amfani shine a bawa musulmi  daman jin dadi  da abin da Allah ya halatta, mutun ya ji dadi  da rayuwa ta duniya da jin dadinta, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Ubangijinka yana da hakki a gare ka haka nan jikinka na da hakki a gare ka kuma iyalan ka na da hakki a gare ka haka nan shi ma mai ziyaranka  yana da  hakki a gare ka to ka bawa kowanne hakkinsa.)
  Allah Madaukakin sarki yana cewa : (ka ce: wa ya haramta kawa na Allah wanda ya fitar ga bayinSa da dadada  na daga arziki? ka ce : su din nan  ga wadanda suka yi imani ne a wannan rayuwa ta duniya sannan kuma yana  kebanta a gare su ranar alkiyama haka nan ne muke bayanin ayoyi daki daki  ga mutanen da suke sani).
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi kira da bayyana abin da ke cikin addinin Allah na hutu da shakatawa ta rayuwar duniya don jin dadi da ke kawo karsashi ga rai da ingizawa zuwa ga aiki, a lokacin da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ga  mutanen Habashawa suna wasa sai ya ce: (Domin ku sani a cikin Addininmu akwai sauki da sassauci, domin ni an turo ni ne da addini mai sauki wato Alhanifiyya Assamha)
Aliyu Dan Abu Dalib Allah ya kara yarda a gareshi ya ce: (Lalle zukata na kosawa kamar yanda jiki ke kosawa to ku nema mata abubuwa da kalaman hikima  na jin dadi )
kuma yake cewa : (ku hutar da zukatanku na wani lokaci bayan lokaci domin zuciya idan an takura mata sai ta makance).
Abu darda' Allah ya kara yarda a gareshi yana cewa (lalle ni ina dan zuwa yawo na shakatawa da zuciyata da wasa na halal domin ya dada  samun karfi don tsayuwa a kan gaskiya.
Manzon mu tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi mai karamci yana cewa  ya kai  Hanzala haba dan lokaci  bayan  lokaci mana )(Wato a huta)
Umar dan kaddab yace:( mutanen (sahabbai) sun kasance suna dariya a halin  imani a cikin zukatansu  yafi karfi da kafuwa  akan dutse.)
To wan nan wasan da jin dadin baya raunana imaninsu kuma baya bata dabiunsu sannan  kuma ba ya sa su ketare lokaci na sallarsu da ambaton Allah da karatun alkur,ani.
Jin dadin musulmi daga cikin abin da Allah ya samar madaukakin sarki na daga abubuwa na amfani da alheri ana gina shi ne akan daidaito tare da saiti, sai mutum ya rayu da fidira irin wanda Allah ya halicci dan adam akai sannan mutum yaji dadin abin da Allah ya halatta a gare shi tare da yalwata jin dadi da annashawa musamman alokacin idi wato da kuma bukukuwa ana bawa mutum lada alokacin da yake jin dadi a rayuwarsa na duniya in bai fita cikin dokoki na sharia ba da ka'idoji na addini ba Manzo Allah tsira da aminci Allah su tabbata a gare shi yace: (A cikin tsokan dayanku akwai sadaka (wato agurin tarawa da iyali) sai suka ce ya Manzon Allah mutum zai  biya bukatarsa ya more shaawarsa kuma kasance yana da lada? Annabi yace: E  yanzu in da zina ya yi  shin bai da alhaki? sai suka ce e yana da shi.  yace to haka ne idan ya sanya shi ahalal to shima yanada lada.
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: ( An sanya min kaunar turare da mata, sannan an sanya sanyin  idanuwana acikin  sallah).
   Dadin rayuwan duniya da ni'marta na daga cikin nau'uka na gabatar da lada da Allah ke yi wa bayinsa mu'minai kari a kan abin da ya tattala musu a ranar sakayya  na daga ni'ma na madawwamiya,  Allah Madaukakin sarki ya ce :(To domin men wata alkarya bata kasance ta yi imani ba har  imaninta ya amfane ta, face mutanen Yunus?  A lokacin da suka yi imani mun janye azabar wulakanci daga gare su a cikin rayuwar duniya kuma muka jiyar da su dadi zuwa wani lokaci )
A duk lokacin da bawa ya  dada kusantan majibincin shi  ya kuma koma zuwa gareshi to zai yi rayuwa na jin dadi da morewa kuma abin da ke wurin Allah yafi alheri kuma yafi wanzuwa : shi jin dadi da morewa na daga cikin amfanin  ne ayyuka na kawarai,  Allah madaukakin sarki ya ce :(wanda ya yi aiki na kawarai na daga na miji ko mace  yana mumini to zamu raya shi rayuwa na jin dadi  kuma mu sakanya mishi da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa ) mafi girman abu mai kawo  jin dadi shi ne lazimtan istigfari wanda da shi ne alheri ke tabbatuwa da albarkoki kuma da shi a ke tunkude bala'i kuma a duddulo da arziki sannan muna sha daga albarkatun sama a  fitar mana kuma da albarkatun kasa kuma a taimaka mana  da dukiya da y'ay'a  sai na ce ku nemi gafara daga ubangijinku lalle ya kasance mai gafara ne0 ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai bubbuga . kuma ya yalwata muku game da dukiya da diya ,( kuma ya sanya muku albarka  kuma ya sanya muku gonaki kuma ya sanya muku koguna )
walwala da jin dadi a rayuwan mutun  musulmi abu ne mai fadi da yalwar ma'ana ya taso ne daga wasu manufofi masu daraja kuma ya ta'allaka da sako na wannan addini da halayensa da ladubansa , kai lalle jin dadi wani hanya ne na sauke sako  ba ita ce ma kura ba  da ake so a nemi jin dadin ta,   to idan ba haka ba kuma to sai mutun ya dulmuye ya samu rauni da fandarewa.    
jin dadi a rayuwan musulmi be  iyakance shi a  kyalakyalan  rayuwan duniya ba bai kuma tsakaita a kantaba, sai dai ma ya zarce zuwa ga ni'ma na aljanna wanda ke mantar da dukkan gajiya da wahalhalu na duniya  :to shi musulmi yana riskan cewa wannan rayuwan na duniya duk yadda ta tsawaita to zata gushe kuma jin dadinta duk yadda ya girmama to na dan wani lokaci ne, Allah madaukakin sarki ya ce ( ka ce jin dadin duniya dan kadan ne )
kuma Allah ya ce:(kuma  alhali kuwa rayuwan duniya bata zama ba dangane da duniya face jin dadi kadan ) (kuma kuna da a cikin kasa matabbata da kuma jin dadi zuwa wani lokaci )
Aduk lokacin da  musulmi ya dandani dadi na rayuwan duniya da walwalanta )
zai yi gaggawan faduwa a tunaninshi jin dadi na aljanna da ni'mar lahira sai ya yi gaggawa saboda kwadayi da shawki zuwa gareta da kuma fatan samun daraja mafi kololuwa
 Allah madaukakin sarki ya ce: (sabo da haka  abin da aka ba ku, ko mene ne,  to, jin dadin rayuwan duniya ne kuma abin da ke wurin Allah shi ne mafifici kuma shi ne mafi wanzuwa ga wanda suka yi imani kuma suna dogara a kan ubangijinsu kawai )
imani da Allah da dogaro a gare shi tsarki ya tabbata a gare shi rangwame da afuwa da yafiya da sa farin ciki a zukatan masu rauni da sanya musu hoton shi a fiskan su da idanuwan su da tsayuwa don biyawa mutane bukatunsu shine dukkan jin dadi,
wani mutumi ya zo gun Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi sai ya ce ya manzon Allah wani aiki ne yafi soyuwa a wurin Allah? sai ya ce farin ciki da zaka jefa wa musulmi  ko kuma ka yaye mishi bakin ciki, ko kuma wani bashi da zaka biya masa  ko ka kore mishi yunwa ,da na tashi na tafi ga dan uwana musulmi da bukata yafi soyuwa a gare ni  a kan na yi itikafi a wannan masallaci :yana nufi masallacin madina .
Na daga cikin jindadin duniya akwai ni'ima ta 'ya'ya da 'yan Uwa maza da mata, don samuwarsu akwai debe kewa, gyaruwarsu kamar wata ganima ce da karfi, su kawa ce ta rayuwar duniya da kyalakyalanta, da kuma cikar walwala da annashawa ne,su ne ma tushenta, Farinciki da walwala na karuwa a lokacin da ka yi shi tare da 'yan Uwanka da wadanda ke kewaye da kai, ka yi farin ciki da farincikinsu, kuma ka samu walwala da debe kewa a dalilin nasu walwalar,ka yi tarayya da su a jin dadi da annashawa,
Rayi na kara samun jin dadi a lokacin da mutum ya cinma wata manufa ya yi nasara a aiki ya tsinkayi daukaka  da fa'idojinta, kamar yadda ya ke shiga rayuwa mafi  sa'ida idan ya kammala wata ibada,zai yi murna da azumi yayin da ya sha ruwa, zai yi murna da sallah yayin da ya ya yi ta, haka kuma da hajji bayan ya sauke ayyukanta.
Dadi na kai wa makura idan mutum ya yarda da  kaddara ta Ubangiji, ya zama ya samu yakini da Allah Madaukaki a dukkan  abin da ya hukunta na al'amari, Abu Addarda ya ce : ( Lalle Idan Allah ya kaddara hukunci to yana so bayi su yarda da shi)
Ibnu Mas'ud ya ce : (Allah cikin adalcinsa ya sanya hutu da farinciki a yakini da yarda, ya kuma sanya bakin ciki da bacin rai a shakku.)
Umar dan Abdul'Aziz Allah ya masa rahama ya ce :( Na wayi gari ba abin da ya rage na ke jin dadinsa sai cikin yarda da abin da Allah ya hukunta)
Huduba ta biyu
Mai hankali ya na baiwa rayuwar duniya matsayinta, bai kwace wa a tunanin sa alkawarin Allah duk yadda kyala kyalan duniya da kawannta  ke ci da habaka, Allah  Madaukakin sarki ya ce :( kuma wannan rayuwa ta duniya ba ta zamo ba face abar shagala da wasa, kuma lalle lahira tabbas ita ce rayuwa, da sun kasance suna sani,)
Mai hankali zai yi taka tsantsan da jindadi na boge, wanda ke haifar da hasara da nadama, domin sabo karshen sa kaskanci ne da bakin ciki da radadi, ba wata ni'ima da zata gushe wa mutum face sabo da shu'umci irin na sabonsa, domin idan Allah ya yi ni'ima ga bawansa  sai ya kiyaye ta gare shi ba zai sauya ta gare shi ba har sai idan shin ne da kansa ya yi aiki don canja ta, (Lalle ne Allah bai canja abin da ya ke ga mutane sai sun canja abin da ya ke ga zukatansu kuma idan Allah ya yi nufin wata azaba game da mutane to babu mai mayar da ita kuma ba su da wani majibinci baicin shi ).
Wace hasara ce ta fi jin dadin da zai haifar da fushin Allah da azabarsa? Allah madaukakin sarki ya ce :(wancan domin abin da ku ka kasance ne kuna farin ciki da shi a cikin kasa ba da hakki ba kuma da abin da kuka kasance kuna yi na nishadi).
                                                                                                                                                                                        









ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق