الخميس، 29 يونيو 2017

CI GABA DA AYYUKAN DAA BAYAN WATAN AZUMI

Hudubar masallacin Annabi  6-shawwal 1438AH na sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albuaijan
Dukkan yabo da godiya  sun tabbata ga Alllah, wanda da ni'marsa ce ayyuka na  kwarai ke kammala, na shaida babu abin bawtawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya, Ubangijin kasa da sammai na shaida lalle Annabin mu Muhammadu bawansa ne kuma manzonsane, shine mafi darajan wadanda su ka yi gaggawa zuwa ga alkin alheri,
 Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka a gare shi da iyalansa da sahabbansa masu tsoron Allah da ayyuka na kwarai.
 Baya haka:
lalle mafi alherin zance shine littafin Allah kuma mafi alherin koyarwa shine koyarwan Annabi muhammadu tsira da  amincin Allah su tabbata a gareshi,  mafi sharrin al'amura shine fararrunsu dukkan bidi' a kuma bata ce dukkan bata kuma yana wuta .
ya ku bayin Allah ina muku wasiyya da ni kaina da tsoron Allah Mabuwayi da daukaka domin ita ce wasiyyan Allah ga mutanen farko da na karshe (kuma lalle ne hakika mun yi wasiyya daga wanda aka baiwa littafi a gabaninku da ku cewa kubi Allah da takawa
ya jama'r musulmi:
cikin shudewan zamanunnuka akwai abin lura mafi girma haka  cikin jujjuyawar ranaku akwai gargadi mafi girma (lalle ne a cikin sabawan dare da yini da abin da Allah ya halitta a cikin sammai da kasa akwai ayoyi ga mutane wadanda su ke yin takawa).
Ya ku bayin  Allah!  hakika munyi bankwana da wata mai girma kamin wasu yan kawana ki kadan kum wani lokaci ne mai girma daga cikin lokutan alheri da albarka ya kasance yana cike da riba da kyawtuttuka da gafara da rahama wanda ke ratsa zuciya ga idanuwa kuma na zubar da hawaye ga zukata sun  rusunawa Ubangijinsu kuma suna cikin tsoro, da gabbai sun himmatu suna fiskantan Allah da wurin ambaton shi kuma ana raya masallatai da ambaton Allah da karatun alkura'ni ga natsuwa ta sauko kuma rahama ta lullube.
Allah ya karrama mu da azumi a wuninsa da abin da ya sawwaka na  tsayuwa a darensa, ya kuma  datar da mu a cikinsa da da yawa daga nau'uka  na da'a da ibadoji da zikiri da adduao'i da sadakoki, to dukkan yabo da godiya da baiwa na Allah ne to muna godiya a gare shi bisa wadannan ni'momi to   ya Allah ka karba .
Ba wani abu bane face wasu ranaku kididdigaggu da awowi iyakantattu da wasu  'yan lokuta da ke shudewa hakika gajiyansu da wahalansu sun tafi saura ladarsu da ribarsu in Allah ya yarda .
Watan ramadana ya kare kuma ya nade tabarmarsa wanda ya rabauta a cikinsa ya rabauta wanda aka haramtawa kuma an haramta mishi Allah sarki wanene aka karbi aikin shi a cikin mu yi mishi murna! kuma wanene aka maida mishi mu mishi jaje! .



 Ya ku bayin Allah
Ibada na da tasiri a halayen ma'abotanta Allah madaukakin sarki ya ce:
 (lalle salla tana hani ga alfahasha da munkari ).
Na daga cikin alamomin karban ayyuka akawai gyaruwan halaye daga wani halin zuwa halin da yafi kyau  (lalle da'a  na shiryarwa zuwa ga aljanna )
Ta daya bangaren kuma na daga cikin alamomin  tsiya da kuma rashin karban aiki akwai komawa baya zuwa ga munanan ayyuka bayan shudewan ramadana  da canjawan hali zuwa mafi muni domin shi sabo sashinsa na jan sashi (madalla da aikata kyakkyawa bayan mummuna don zata gogeta wanda yafi kyau kuma shine mutum  ya aikata kyakkyawa bayan kyakyawa,  mafi muni kuma aikata mummuna bayan kyakkyawa domin zata shafe albarkanta kuma ta gogeta . zunubi guda daya bayan tuba yafi muni akan zunubai da yawa kafin  tuba, juyawa zuwa ga munanan halaye yafi wuyan  sha'ani akan cuta watakila ma ta halakar, roki Allah tabbatuwa akan da'a har zuwa mutuwa , kuma mu nemi  tsarinsa daga juyawan zukata  da kuma lalacewa bayan gyaruwa, abin mamaki da dabbancin kaskancin sabo bayan daukaka irin na da'a, abin mamaki kuma da abkawa cikin talaucin kwadayi bayan wadatan zuci).
Ya ku musulmai
Lalle hanyoyin alheri na da yawa ina masu binsa haka kuma kofofin nasa a bude suke ina masu shigansu  lalle gaskiya a bayyane take ba mai baude wa daga gare ta sai halakakku,  to ku yi riko ya ku bayin Allah da kaso dagsa dukkan biyayya  (ya ku wadanda suka yi imani ku yi rukui kuma ku yi sujjada kuma ku bautawa ubangijinku kuma ku aikata alheri saboda ku samu babban rabo )
Kuma lalle hakuri a kan dimantan da'a da tsayuwa a kan tafarki da tabbatuwa na daga cikin mafi girman ayyukan da'a, tabbatuwa da dogewa dalili ne na ikhlasi  da  karban aiki , (mafi soyuwan  ayyuka a wurin Allah su ne wadanda aka dawwama a kansu )
(aikin manzon Allah ya kasance dimamme )
To ku tabbatu akan  da'a, ku tabbatu a kan da'a  kuma  ku tsayu a kan biyayya, to ku tsayu a kan biyayya kuma ku dawwama a kan ayyuka .
Ya ku bayin Allah !
Ku yi kwadayin karban ayyuka kuma ku kiyayi talauci da gushewa ,lalle mafi girman hasara   shine ka bawa waninka mafi girman abinda ka samu na daga lada, to wannan shi ne talauci na gaskiya.
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara masa yarda ya ce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( shin kun san wanene matalauci ?  sai suka ce matalauci shine wanda bai da dirhami ko kaya sai ya ce: matalauci daga alumma ta  shine wanda zai zo ranar alkiyama da salla da azumi da zakka, ya zo ya zagi wannan kuma ya yi wa wannan kazafi kuma ya ci dukiyan wannan kuma ya zubar da jinin wannan kuma ya daki wannan  sai abawa wannan daga ayyukan shi  kyawawa  wannan ma daga ayyukan shi kyawawa in ayyukansa  kyawawa sun  kare kafin a gama masa hisabi  Sai a dauki  zunuban wannan sai a dora mishi sai a hurgashi cikin wuta )muslim ne ya rawaito

Bayin Allah!
Kuma rena sabon Allah da bushewar ido wurin keta alhurmarsa na daga cikin sababi mafi girma na tsiyacewa da hasara  da bata da tabewa, an karbo daga Sauban  Allah ya kara yarda  a gare shi cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lallai zan san wasu mutane acikin al'umata za su zo ranar alkiyama da ayuka misalin duwatsun Tihama farare  sai Allah ya maishe su  tarwatsatssen kura ,  Sauban ya ce: ya Manzon Allah siffanta mana su don kar mu kasance cikin su a halin ba mu sani ba ,  sai ya ce  ai su dinnan lalle 'yan uwan ku ne  kuma wadanda fatar ku iri daya, kuma suna riko cikin dare  kamar yadda ku ke riko,  sai dai su din wasu mutane ne da idan sun kebanta da ababen da Allah ya haramta sai su keta alfarmarsa,  sun kasance suna azumi kuma suna salla kuma suna rikan wani lokaci cikin dare  sai dai basa murakabar Allah  a lokacin yalwa,  to idan sun kebanta da abin da Allah  ya haramta sai su keta alfarmarsu  sai Allah ya ruguza ayukan su ( Kuma abin da  ba su kasance suna  zato ba daga Allah ya bayyana a gare su) .
 Idan ka kadaita a wani zamanin wata rana  to kar ka ce *
                                                     Na kadaita sai dai ka ce ina da mai mini murakaba
Kada ka zaci Allah yana gafala na wani lokaci  * 
                                                    ko kuma abin da ake boyewa   yana fakuwa a gare shi.
ku saurara  ku tsayu akan da'a wa Ubangijinku ku  amsa kiransa ku bi umarnin sa  a dukkan  matakan rayuwanku za ku samu rabauta da ganima   da walwala da tsira   ( Lalle ne wadan da suka ce '' Ubangijin mu Allah ne''     sa'annan suka daidaitu to, babu wani tsoro a kan su , kuma baza su yi bakin ciki ba  . to wadannan su ne ma'abota aljanna suna masu dauwama a cikinta sakayyan abin da suka kasance suna aikatawa  ).


                            HUDUBA NA BIYU
Lalle dukkan yabo da godiya sun tabata ga Allah  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa , muna neman shiriyarsa , kuma muna neman gafararsa , muna tuba zuwa gare shi , muna neman tsarin Allah daga kawunan mu da kuma munanan ayukanmu   wanda Allah ya shiryar da shi ba mai batar da shi  wanda kuma Allah ya  batar da shi babu mai shiryar da shi , na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai  yake bashi da abokin tarayya , na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne  kuma Manzon sa ne , tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabansa  , da  wadanda suka bisu da kyautatawa har zuwa ranar sakayya da aminci tabbatacce mai yawa.

 Ya ku Musulmai  ku ji tsoron Allah   ku  gaggauta  ribatan ayukanku kafin karewar rayuwarku   ku tabbatar da maganganun ku ta hanyar ayukan ku   domin lalle hakika  rayuwar mutum  shi ne abinda  ya tafiyar da shi a cikin da'a  wa  Allah ,  lalle mai wayo shi ne wanda  ya yi hisabi  da kansa ya yi aiki don bayan mutuwarsa   shi kuma  wanda ya gajiya  shi ne wanda ya bi son ran shi ya yi ta gurace – gurace  a wurin Allah .
 Ya ku bayin Allah      watanni dukkan su lokuta ne na ibada  ko da sun  saba a wurin falala.  rayuwa dukkanin ta dama ce ta aiki da kuma da'a , ko wanne yana wayan gari  yana mai saida kansa, wani ya 'yanta ta wani kuma  ya halakata , sannan kowa ana saukake mishi abinda a ka halicce shi don shi   .
 To ya wanda ya cika a ramadana ya kyautata   bisa mafi kyawun kyautatawa , maganganun shi da ayukan shi suka    kawata,  to ka tabbatu kada ka canza a bayan shi a cikin shauwal.
 Ya wanda mutane suka tsere maka   aka barka a baya mafi yawan rayuwa ya tafi   sai zanyi , bai yin ba , dama ta Ramadan ta tsere maka baka ci riba ba , taho  , to, kofofin basu gushe ba suna bude ,  kuma tuba ana karbanta   Allah madaukakin sarki ya ce :( Ka ce , (Allah ya ce) '' ya ku bayi Na  wadan da suka yi barna  akan rayukansu ! kada ku yanke kauna   daga rahamar Allah . Lallai Allah na gafarta zunubai  gaba daya .  Lallai shi ,  shi ne mai gafara , mai jin kai .
  Ya ku  jama'ar Musulmai :
Lallai na daga  cikin hanyoyi na shiriya da kuma aikin Musdafa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  akwai azumtar   azumi shida na watan shauwal,  an karbo daga Abu Ayuba Al'ansari Allah ya kara yarda a gare shi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare shi ya ce : ( Wanda ya yi azumin Ramadana ya bi shi da guda shida a shauwal  yana dai-dai  da ya yi azumin shekara)
 Hakika Allah ya sanya  lada goma ga kyakkyawa   daya wato wata  daya na da ladan watanni goma ,   ranaku shida kuma na bayan salla na da ribin su sau goma wato kwana sittin wannan shi ne shekara guda cikakkiya .
Ba laifi , a yi azumin su a jere ko a rarrabe  kada dayan ku yayiwa kanshi rowa  na wannan kwanaki shidan ta iya yiwuwa a rubuta  shi  cikin wadanda suka yi azumin shekara,  lallai kuwa wannan babban ganima ce wanda ke sa mutum yayi kokari don ya same shi.
  Ya ku Musulmai :
  Lallai abin da 'yan ta'adda suka tashi da shi a cikin azumi kuma  a makka  a kusa da ka'aba  na daga cikin ayyuka na ta'addanci   wanda shari'a da hankali duka zai kyamace shi ,  basu kiyaye alfarmar Ramadana ba  ko alfarmar daki mai alhurma ba  ,  ko kuma alhurmar jinin muminai ba ,  ma su azumi , lallai wannan na daga cikin kaidi na makiya musulunci  da kuma bushewar ran mahara  wanda suke aikin barna a doron kasa  .
 Lallai dakin na da Ubangijin da zai kiyaye shi , hakika Allah yayi alkawarin narkon azaba   ga wanda ya keta alhurmar sa, Allah ya ce : (Lallai wadanda suka kafurta kuma suka taushe''  mutane'' daga hanyar Allah da masallaci mai alhurma     wanda muka sanya shi ga mutane alhali kuwa` mazauni a ciki da bakauye dai-dai suke kuma wanda ya yi nufin karkatar da gaskiya a cikinsa da zalunci  za mu dandana masa daga wata azaba mai radadi).
Allah  ya kiyaye  shi daga dukkan mai ketare iyaka azzalumi , maha'inci , mai laifi , shaidani abin jefewa , mai girman kai la'imi (mai dakon mummunan abu)  ya faru da musulunci ,  to, mugunyan musifa  mai kewayewa ta tabbata akansa ,Allah ya maida mishi kaidinsa a mokoshinsa , ya sanya mummunan shirinsa  ya zama  halakarwa a gare shi , kuma Allah ya yanke karshensa .
Ya ku bayin Allah:
 Lallai Allah mabuwayi da daukakaa ya umarce mu da al'amari mai girma , ku saurara! Wanda shi ne salati da aminci ga Annabi mai girma ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da  albarka bisa  ga shugabanmu Annabin mu Muhammad.
 Ya Allah ka yarda da kalifofi shiryayyu Abubakar da Umar  da Usman da Ali da iyalai baki daya da wanda ya bi su da kyautatawa  har zuwa ranar sakayya .
 Ya Allah ka sanya mu cikin wadanda ka karbi azuminsu  da tsayuwansu da sauran ayukan su .
 Ya Allah ka maimaita mana Ramadan shekaru masu yawa   muna cikin lafiya da aminci da imani    .
Ya Allah ka tsawaita rayuwarmu ka kyautata ayukanmu  ka bamu kyakkyawan karshe .
Ya Allah ka gyara halayen Musulmai a ko ina  ya Ubangijin talikai  .
Ya Allah ka kiyaye shugabanmu kadimul haramaini sharifaini da kiyayewan ka ka ba shi kulawa da kulawarka .
 Ya Allah ka datar da mataimakin shi cikin abin da kake so kuma ka yarda da shi , ka riki makwarkwadan su  da da'a da takawa .
 Ya Allah ka datar da su cikin abinda akwai alheri ga Musulunci da musulmai  , da kuma abin da cikin shi a kwai gyaruwar gari da bayi .
Ya Allah ka azurta shi da abokan sirri na kwarai, masu nasiha wanda za su  nusar da su zuwa ga alheri kuma su taimaka musu a kanshi , ya Ubangijin talikai.
 


ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق