الخميس، 25 مايو 2017

GODIYA GA ALLAH



Hudubar juma'a na masallacin Annabi tare da sheikh Salah Bin Muhammad Al Budair
16/sha'aban/ 1438 AH
Ya ku musulmai!
Godiya hanya ce ta kari da takawa da dace.
Rabiu dan Anas yace: lallai  Allah na ambaton wanda ya ambace shi kuma yana kari ga wanda ya gode mishi kuma yana azabtar da wanda ya kafurce mishi
Na gode maka lalle godiya wata igiyace ta takawa* kuma ba dukkan wanda ka yiwa ni'ma bane yake biya.
Allah madaukakin sarki yace (kuyi godewa ni'mar Allah in kun kasance shi kadai kuke bawtawa ) 
(ku godemini kada ku kafurce mini).
An karbo daga Mu'azu dan Jabal Allah yakara yarda a gare shi yace lalle manzon Allah yayi riko  da hanun shi sai yace ya Mu'azu  wallahi ni lalle ina sonka wallahi lalle ni ina sonka, sai yace ;ina ma wasiyya ya kai Mu'az kar ka bar fadin cewa bayan kowani sallah : ya Allah ka taimakeni bisa ambatonka da godiya a gare ka da kyautata bauta a gare ka) Abu dauda ne ya fitar da shi.
Dukkan yabo da godiya naka ne ya ubangiji sa'annan dukkan yabo naka ne muddin baki na furuci, falalarka ta kebance ni kuma ta game, daga gun ka ne gani da ji da dandano,  da shakan ga wuni ma haske ga dare mai duhu ga kuma dutse mai tudu da tsirrai wanda suke tsaye akan makyangamansu da wadanda suke akasin haka.
Yaku musulmai
Lalle ku kuna rayuwa a cikin aminci mai yawa da arziki mai yalwa da rayuwa na jin dadi da ci da sha, ga wasu a kewayenku matsanancin yunwa na kashe su ga mutuwa na bi ta kansu a kashe   akamasu amasayin bayi a riki matayensu kuyangi suna kuma fama da bala'i da annoba suna kuma fiskanta tsadan abinci ga kuma fitar da su da aka yi daga gidajensu ba abin da za kagani sai uwa cikin yunwa yara cikin  kuka ga alummu raunuka  ya illantasu to ku kiyaye wasa da ni'mar da Allah ya yi muku kar ni'man ya mantar da ku godiyan Allah a gare ku, ku  yi dubi da abin da Ubangijinku ya yalwata a gareku na daga ni'momi ku san hakkin shi ne mai muku ni'man
Ku kasan ce daga cikin wadanda suka jawu gare shi ta hanyar godiya bisa ga ni'imominsa,
Kar kuyi amfani da kyauta  da ya muku cikin saba masa kada shaidanu su rudekukada makiyanku su yaudareku da bata ,karku bayyana sabo bayan samuwan arziki da aminci da bayani da baiwa,ku kyautata muamala da ni'imomi, ku kiyaye ni'imomin da ke tare da ku, sai kuma ku nemi ni'imomin da kuka rasa ,ku nemi dawwamar kyautar Allah da karamcinsa ni'ima ba ta juya baya idan ta fiskanto, ba a dauke ta bayan ta sauka ba a dauke wata karama bayan an bada ta ,sai dai  kasancewarta kyauta da ba a gode ba ,ko sakamakon kusakurai da aka aikata kuma ita ni'ima idan an yi godiya sai ta tabbata, idan an butulce saita guje.
ya wanda ke tafiya akan koyin kafirci ya sanya kafarsa cikin tawagar matafiya na kafirci da fasikanci da sharri, abin da ya rudeka shine hakurin Allah sararawarsa harka juya baya da fiskanka ka yi watsi da hakkin Allah.
Ya kai dan' adam lallai ka gafala,  sai  kace ba zaka kare ba ko ba zaka halaka, ba ya wanda yayi sharri da dagawa da sabo da fasikanci da fajirci ,shin ko kana zaton kyautar bata halake ba ne, ko ni'imar ba a amsarta ne,dako da jinkiri da rashin gajiyawa ukuba ke diban ka, ka gajarta daga barnarka Allah bai taba kama mutane ba face a yayin da suke mayensu suka shagaltu cikin rudunsu da walwalansu, sau da yawa Allah kan bawa mutane arziki da yalwa da ni'ima, sai suka riki ni'imar Allah tamkar wani tsani ne da zasu haura su tsallaka zuwa ga saba mishi suka rike shi matakala zuwaga abin da Allah ya hana sai suka zaci wannan kyautar da ni'ima wata girmamawa ce da daukaka da darajanta su kan saura da fifitasu da zabansu basu san hakan ba wani abu bane sai daurin talala, sau barkatai akan yiwa wasu daurin talala ta hanyar ihsani, sau da yawa wani kan fitinu in an yabe shi, wani kuma ya rudu in Allah suturce shi bai tona masa asiri ba.
 Ya ku musulmi!
 ka kiyaye fadawa cikin sabon Allah da nuta a cikinsa, da kwankwada daga gare shi da yin sakaci gurin keta laduba, da yin karan tsaye ga tauhidi da sharia da addini, ku kiyaye daga mataimakan shaidan da abokansa dake kokarin batar da ku ta hanyar yaudara kuyi nesa da mummunar fahimtarsu da bataccen tafarkinsu, ku kauda kai daga kiranye kiranyesu, ku kaurace wa tawagarsu, ku wofantar da hanyarsu  ku shakala yinsu, kar kubi soye soyen rayu kansu da sha'awe sha'awensu, kar kuyi biyayya ga mai zunubi ko mai yawan sabo mai yawan kafurci, (kada ka bi wanda muka rabkanar da zuciyarsa ga barin  ambatonmu,alhali kuwa al'amarinsa ya kasance yin barna)
( ku kauda kai daga wanda ya juya bayadaga ambatommu bai nufin komai sai rayuwar duniya)
Makhlad dan Husain yace: An kasance ana cewa : (Godiya shi ne barin sabo)
Mai lura mai hankali yakan banbance tsakanin tsaki da tsakuwa, kuma ya rabe tsakanin zare da abawa domin rogo ba kitse bane.
Yaku musulmai!
 ku janyowa kanku kari ta hanyar  godiya daga kyauta kuyi nesa daga sifa ta butulci da afkawa ga sabo, kuyi nesa daga abin da aka haramta, kar kuyi sabuban da za su kai ku ga fadawa cikinta, don godiya ga Allah bisa ga ni'imominsa masu yawa  da ya baku, duk wanda ya tsallaka halall ya fada ga haram to ya ketare iyaka kuma yayi zalunci,
 Allah yace:(wadancan iyakokin Allah ne, sabo da haka kada ku ketare su, to duk wanda ke ketare iyakokin Allah wadan nan sune azzalumai)
 yaku musulmai ku kiyaye yin dabaru don bata hukunce- hukunce na sharia don ku isa zuwa ga abubuwa da aka haramta munana, don aikata hakan baya cikin aikin masu tauhidi masu godiya, aa yana cikin sifofi na fasikai batattu ) Al hiyal wato dabaru jam'i ne na dabara hanya ce ta boye da zata isar dakai ga manufa.
Imamun Nasafi yace acikin Al kafi daga Muhammad dan Alhasan yace: Baya cikin dabi'ar mumini gujewa hukunce- hukuncen Allah ta hanyar dabaru da zasu kai mutum ga bata gaskiya .
 Allah ya sanya ni da ku cikin masu godiya a halin yalwa ya tabbatar da mu akan addininsa  ba tare da baudewa ba .
HUDUBA TA BIYU:-
Ya ku Musulmai :  Yarda da kadan sifa ce ta masu godiya,  ba sa rena ni'imar Allah  ko da ta karanta,  a duk yayin da wani abu na al'amarin duniya ya wuyata a gare su,  sai su wadatu da abin da ya ke koma bayansa , kuma su yarda ,  hakika ya daukaka duk wanda ya yi wadatan zuci ,  kuma ya kaskanta duk wanda ya sa kwadayi,   daga cikin mutane akwai wanda baya yarda da abin da Allah ya kasa mishi na  arziki ,  za ka ganshi  yana fushi yana raki  yana kuma fatan abin da ke hanun wanin shi na daga matsayi da  dukiya da hali ,  

Yaro na neman girma  *   tsoho kuwa na neman  ya koma yaro
 Me zaman banza na neman aiki   *  Ma'abocin aiki kuma ya kosa
Ma'aboci dukiya kuma na cikin gajiya  *  Matalauci kuma na cikin wahala
Mai yara kuma na cikin bacin rai   *  mai neman su kuma gashinan ya jikkata
 Mutumin da aka yi galaba akan shi kuma yana cikin  tsiya  *  wanda  kuma ya yi nasara shi kuma bai da  hutu
Zai rika neman daukaka  cikin tsoron hasara   *  idan ya yi nasara da ita kuma  sai jikin sa ya mutu .
Arziki kaso ne daga Allah  wanda ya fito bisa hikima  da gudanarwa da ilimi game da halin bayi,  kada ku yi hasada, kada ku yi fatan abin da Allah ya fifita wasunku akan wasu da shi  , kada dayanku ya yi burin  dukiyan wanin shi  da iyalan shi,   ku roka mishi Allah albarka , kuma  ku roki Allah daga taskar sa da bata karewa , a cikin mutane akwai wanda yake rokan mutane don ya bunkasa dukiyan shi, zai rika bijiro musu a masallatayya da kuma wuraren tarurruka  ,   da kuma lokuta masu daraja  kamar juma'a  da ramadan,  watakila ma ya rike dan yaro  ya koya mishi kaskanci da roko  domin neman tausayin mutane   da kuma neman yawaita kyautan su .
An karbo daga Abu Huraira  Allah ya kara yarda a gare  shi ya ce :  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :''  Wanda ya roki mutane dukiyan su  don neman ya yi kudi  to hakika garwashin wuta yake rokan su  to ya roki dan kadan ko da yawa  '' . Muslim ne ya rawaito shi.
 Ya ku Musulmai :
 Almabazzaranci da dukiya  da ciyar da shi a gurin da ba hakkinsa ba   hakanan a wurin alfahari da neman suna,  da tinkaho  da shi   kishiyan godiya ne .
Mujahid ya ce:  da mutum zai ciyar da dukiyan shi gaba daya a cikin hakki , to, da bai zama  almabazzaranci ba  .
 Ciyar da abinci  falala ne mai girma  da kuma ciyar da masu azumi abincin buda baki   a Ramadan  kusanci ne mai daraja , kuma  ibada ne mai girma  da ya dace  duk wani  wanda ya yi dace   ya yi kwadayin ta,
 Muna gargadi game da barna cikin fadada  shinfidar cin abinci  ba tare da bukata ba      da zuba dabino da biredi da abinci ba tare da iyaka ba,  wanda karshe makomansu ya zama abin jefarwa a wurin tara shara , ku tuna 'yan uwanku talakawa da wadanda suke cikin jarabawa a kasar fari   , da tsananin talauci  da yunwa  da  yake -yake  .
Ku nemi abin da yake dai-dai, ku kusanto , ku yi bishara, kuma ku yi fatan alheri, lallai Allah baya sarayar da ladan wanda ya kyautata aiki,
 lalle Allah bai lalata ladan masu kyautatawa.            

هناك تعليق واحد: