Hudubar Masllacin Annabi na 11-10
-1440AH/14-6-2019 AD na Sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albu'aijan.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah,
muna gode masa muna neman taimakonsa muna neman gafararsa, muna neman tsarin
Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar
da shi babu mai batar da shi duk wanda ya batar da shi ba zaka sama mishi
majibinci mai shiryarwa ba.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah
shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ya halitta kuma ya daidaita abin
halitta ya kaddara (abin da ya so) ya shiryar, na shaida Annabi Muhammad
bawansa ne kuma manzon sa ne, wanda ya turo shi da gaskiya da shiriya, tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da duk wanda ya
bi sawun shi,ya bi tafarkinsa da kyautatawa har zuwa ranar sakayya,
Bayan haka: Lallai mafi alherin zance shi ne
littafin Allah, kuma mafi alherin shiryarwa shine shiryarwa Muhammad dan
Abdullah, Mafi sharrin al'amura sune fararrunta, dukkan fararrun abubuwa bidiah
ne, dukkan bidiah bata ne dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah … ku ji tsoron Allah cikin
abin da ya umarta, ku hanu daga abin da ya hana ya tsawatar, ku sani dukkan
karami da babba ana rubuta shi, (ya ku wadanda suka
yi mani ku bi Allah da takawa, kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe,
kuma ku bi Allah da takawa lalle Allah mai kididdigewa ne ga abin da ku ke
aikatawa,)
Ya ku bayin bayin Allah!
Lokaci na albarka da falala da alheri da da'a
ranakunsa ya kare an nade ayyukansa, lalle wata ne mai girman falala, tasirin
sa a cikin Al'uma na da ban mamaki, masu nasara cikin shi sun ribata,masu
kokari cikinsa sun samu ganima,ina ma da mun san wanda aka karbi ayyukansa mu
mishi barka! Wane ne baa karba mishi ba mu jajanta mishi,
Madalla da farincikin wanda suka rabauta, Allah
ya musu ilhamar tuba, ya datar da su ga biyayya, muna roka musu Allah da ya
karba musu ya dora su kan daidai.
Ya kaiton hasarar wadanda suka rasa wannan alheri
aka katange su daga Ubangijin su,
damammaki a rayuwa suka kwace musu.ga lokutan alheri basu ribaci komai ba sai
hasara da nadama,
Sai dai ya jama'ar musulmi ! kofofin tuba basu
gushe ba suna bude ba a rufe su ba bayan watan ramadan,Ubangijinmu mabuwayi da
daukaka yana karbar tuba daga bayin sa a kowane zamani da guri (Shi ne yake karbar
tuba daga bayin sa kuma yana yafe munana, kuma ya san abin da kuke aikatawa).
Ya tabbata daga Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi yace :Lalle
Allah ya fi farinciki da tuban bawansa
mumini akan mutumin da yake cikin kasa ta sahara wacce ke da ababan halakarwa yana tare da dabbarsa abin cin shi da abin shan sa na kanta sai ya yi bacci , da ya farka sai ya ga ta
tafi ya yi ta nemanta har sai da
kishi ya cimmasa sai ya ce bari
na koma wurina da na kasance a cikin shi
sai na je na yi bacci har ma na mutu
sai ya dora kanshi a bisa damtsen
shi don ya mutu yana halin haka sai ga
dabbarsa a kan sa tare da ita ga guzurin
shi da abin cin shi da abin shan sa sai ya
rike linzamin ta yayi kuskure don tsananin farin ciki yana mai cewa ya Allah
kai ne bawana ni ne Ubangijin ka .
An karbo daga
Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare
shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:(Idan wani yanki na
dare ya shude ko kuma wani sulusin shi ,
Ubangijin mu mai tsarki da daukaka zai sauko
zuwa ga sama na duniya
sai ya ce:-
Ko shin akwai mai tambaya na ba
shi , ko shin akwai mai roko na amsa mishi , shin akwai mai neman gafara a
gafarta masa har gari ya waye . Muslim
ne ya rawaito)
Zuwa ga wanda
daman ramadan ya kwace mishi to ka yi
gaggawa zuwa ga tuba kafin lokaci ya
tsere da kuma shammatan ajali kada ka
yanke tsammani don duk dan adam mai kuskure ne
abin zargi na ga wanda ya
doge kuma alhali yana da Ubangiji mai
gafarta zunubai kuma bai nemi gafarar sa ba , ba don kun kasance kuna kusakurai
ba kuma kuna neman gafara da Allah ya
tafiyar da ku ya kawo wasu mutane wadan da suna kuskure kuma suna neman gafara
sai Allah ya gafarta musu .
YA KU BAYIN
ALLAH:
Ku ji tsoron
Allah kuma ku nemi gafarar sa kuma ku
koma zuwa gare shi ku mar da'a kada ku
jinkirta tuba domin mutuwa na zuwa
bagtatan .
Allah
madaukakin sarki ya ce :-(Ku tuba suwa ga Allah gaba dayanku ya ku muminai ko za ku
rabauta)
Kuma ya ce :-( Ka ce ya ku bayi na wadanda suka barnatawa kawunan su kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah
lallai Allah yana gafarta zunubai baki daya
lallai shi mai gafara ne kuma mai jin kai . Ku koma zuwa
ga Ubangijinku ku mika wuya gare
shi kafin azaba ya zo muku sa'annan ba za a taimaka muku ba , ku bi mafi
kyaun abin da aka saukar gare ku daga
Ubangijin ku tun kafin azaba ya zo
muku bagtatan a halin kuna baku sani
ba kada rayi ta ce ya hasara ta
bisa abin da na yi sakaci a
janibin Allah , ko da na kasance
cikin wadan da suke masu isgili ko kuma ta ce ina ma da Allah ya shirye
ni da na
kasance cikin masu takawa , ko
kuma ta ce ya yin da ta ga azaba ina ma
da ina da kome da na kasance cikin masu kyautatawa
YA KU MUSULMAI:
Lallai ibada na da tasiri cikin halayen ma'abocinta Allah madaukakin
sarkiya ce :-(Lallai sallah na hani ga
alfasha da munkari)
Na daga cikin
alamomin karban ayyuka akwai canzawan
halayen zuwa mafi kyan hali a daya
bangaren kuma yana daga cikin alamomi
na rasa alheri da rashin karban
aiki akwai komawa baya daga da'a
bayan shudewan ramadana yanayin
halaye ya canza zuwa mafi muni domin
sabo sashi na janyo sashi , madalla da kakkyawa bayan mummuna sai ta goge ta mafi kyaunta kuma shi ne kyakkyawa bayan
kyakkyawa tana mai binta , ku roki Allah
tabbatuwa akan da'a har zuwa mutuwa kuma
ku nemi tsarin Allah daga juyawar zukata
haka nan kuma daga warwarewa bayan
daurewa .
Abin mamaki da munin kaskanci
na sabo bayan izza ta da'a tir da
talauci na kwadayi bayan wadatuwa
da wadatan zuci ku roki Allah tabbatuwa
, ya tabbata daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce :-( Lallai
dayanku zai yi aiki irin na 'yan
aljanna har sai ya kasance tsakanin shi
da ita face zira'I sai littafin sa ya rigaya , sai ya yi aiki irin na 'yan wuta sai ya
shige ta , kuma lallai dayan ku zai yi
aiki irin na 'yan wuta har sai ya
kasance tsakanin shi da ita face zira'I sai littafin shi ya rigaya sai ya
shigeta Buhari ne ya rawaito)
Ina fadin abin
da kuke ji ……….
HADUBA TA BIYU
Dukkan yabo da
godiya sun tabbata ga Allah
wanda yake karban tuba daga bayin
sa kuma yake yafe kusakurai kuma ya san
abin da kuke aikatawa , kuma yana amsa
kiran wadan da suka yi imani kuma suka
yi aiki na kwarai kuma yana kara musu
daga falalar sa .
YA KU MUSULMAI :
Watanni dukan
su lokuta ne na ibada ko da sun sha
banban sun saba a wurin fifiko da ayyuka
rayuwa dukkanta dama ce ta aiki da biyayya
ko wanne yana wayan gari yana mai saida kan sa akwai mai 'yantata akwai
kuma mai halakata , kuma kowa ana
yassare mi shi abin da aka halicce shi
akanta , .
To ku sabarwa
kawunan da da'a ku nemi taimako game da ita da tuba da neman gafara da komawa zuwa gare shi da marairaicewa da kuma murakaban Allah guda mai rinjayi a sirri kuma da bayyane a dare da wuni .
(Ku bar sabo
na zahiri da na badinin sa lallai wadanda suke aikata laifi za a sakanya
musu da abinda suka kasance suna aikatawa)
YA KU BAYIN
ALLAH:
Ku rantawa
Allah rance kyakkyawa , ku kaddamarwa kawunan ku abu mai amfani , (Duk wani abu da za ku
kaddamar wa kawunan ku na alheri za ku same shi a wurin Allah).
(Wane ne zai rantawa Allah
rance mai kyau sai ya ribanya mishi ribanyawa mai yawa).
Sannan ku sani
cewa azumi garkuwa ne , dukkan aikin dan adam
na shi ne sai azumi to shi na
Allah ne zai sakanya game da shi , to duk wanda zai iya a cikin ku ya azumci azumi shida a
shauwal to lallai hakan na daga cikin
sunna kuma aiki ne na musdafa tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi
An karbo dga
Abu ayubal Ansari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbataa agare shi ya ce :-(Duk wanda ya yi azumin ramadana sannan ya bi da guda shida a shauwal
zai kasance kamar ya yi azumi na shekara ne )Muslim
ne ya rawaito
Sabo da
kyakkyawa guda na da lada goma kamarta,to ramadana na da ladan wata goma, guda
shidan kuma ladan wata biyu, kuma adadin watanni a gurin Allah goma sha biyu
ne,
Ba laifi mutum
ya yi azumin a jere ko a rarrabe, muddin dai a cikin watan shauwal ne, tamkar
tana matsayin sunnoni ne na ratibi game da sallolin farilla,tana cike gurbin
tawaya ne da aka samu a farilla.
YA KU MUSULMAI :
Ku ji tsoron
Allah,iya iyawanku,ku yi riko da addininku,ku kankame sunnar Annabinku, ku kuma
gyara tsakaninku,ku kiyaye hadin kanku, da garinku, ku zama hanu guda kan
abokin gabanku, ku roki Allah da ya tabbatar da ku ya datar da ku,
Bayan haka YA KU MUSULMAI :
Lallai abin da
masu ketare iyaka suka suka aikata na harbi kan 'yan kasa da mazauna, da
tsorata amintattu, da zubar da jinin wanda bai ci ba bai sha ba.da yara da
mata, da keta alfarman wurare masu tsarki manya da gari mai alfarma, na daga
cikin manyan laifuka abin ki ga dukkan addinai, kuma yana cin karo da ginshikai
na musulunci, Alla maida musu sharrinsu a kan su.ya sanya yakinsu a tsakaninsu,
kuma ya yanke karshensu.
Ya Allah ka
kare wannan kasa da kariyarka.
ليست هناك تعليقات:
إرسال تعليق