الجمعة، 17 مايو 2019

ka yi sujada ka kusanto


Hudubar Masllacin Annabi na sheikh Abdulbari Bin Awad Assubaiti 12 Ramadan 1440Ah
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, tsira da amincin Allah su tabbata ga  mafificin halittun Allah,
Bayan haka !
A kalmomi biyu na karshen farkon sura da aka saukar a Alkur'ani Allah yana cewa:(Kuma ka yi kujada ka kusanto ) an karbo daga  Abu Huraira  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( lokacin da bawa ya fi kusanci da Ubangijin shi shi ne a halin yana sujjada , to ku yawaita adu'a ) Muslim ne ya rawaito
Sujada shi ne mafi daukakan hali na bawa , a cikin shi ne mutum zai ji dadin rusunawa mabuwayi mai girma  da kuma  kawa irin na kankan da kai ga mai rahama mai jin kai , wasu lokuta ne na karamci da albarka  wanda ba su da iyaka .
 Acikin sujada ne a ke jin dadin da baya misaltuwa   da yaye walwalan zuciya  wanda ba alkalamin da zai iya iyakance shi  yana  kaurar da musulmi daga kunci ,  zuwa ga yalwa mai fadi  na kasa  cikin sararin samaniya  sabo da haka ne  (Aisha Allah ya kara yarda a gare ta  ta sifanta tsayuwan daren Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da cewa; yana sujjada  guda da zai kai dayan ku ya karanta aya hamsin  kafin ya dago)  Buhari ne ya rawaito .
Sujada na kara wani haske na imani   daga ma'abocin shi ya jefa wani walwala a zuciya da natsuwa  ya bashi wani  gairmamawa , Allah madaukakin sarki ya ce :-(Muhammadu Manzon Allah ne , kuma  wadan da suke tare da shi  suna masu  tsanani ga kafurai  masu tausayi a junan su  za ka gansu suna masu yawan ruku'u da sujada  suna neman falala daga wurin Allah  da yarda  alamun su  na fiskan su na gurbin sujada )
Asujada ne Ubangiji ke kasancewa kusa da wanda ya roke shi  , Ubangiji mai tsarki    yana kusa da wanda ya roke shi  , mai amsawa ne ga wanda ya nemi ganawa da shi   mai badawa ne ga wanda yayi fata gare shi  duk wanda ya kusanci Allah to lallai zai riski kyauta mafi yalwa daga Ubangijin shi, kuma ya samu matsayi mafi
aminci da yakini da kariya mai karfi  ,  Allah madaukakin sarki ya ce (To amma (  idan mai mutuwan ya kasance daga makusanta   sai hutawa  da kyakkyawan abinci da aljanna mai ni'ima )
Makusantan suna da Rauhun shi ne;  hutu  da natsuwa da farin ciki  da kuma annashawa , Raihan   shi ne suna da ya tattaro dukkan  wani jin dadi na  jiki  na daga abinci ne ko abin sha  da makamantan su ,  da  (aljanna mai ni'ima) wanda a cikin ta akwai abinda ido bai gani ba kuma kunne bai ji ba kuma bai halarto a tunanin wani dan adam  ba yana yiwa makusantan shi albishir yayin  halartowan mutuwan su da wannan albishir din  wanda  rayuka ke kusa da su fire sabo da tsabar jin dadi da farin jiki , (ka yi sujada kuma ka kusanto )      
A ko wani sujada kana da daukaka na daraja   da kusanci na matsayi  da kuma kusanci na wuri  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Ba wani bawa da zai yi sujada  don Allah face an rubuta mishi kyakkyawa da ita , an kankare mishi mummuna da ita  an kuma daga darajar ku da  ita  , to ku yawaita yin sujada ) Ibn Maja ne ya rawaito da isnadi ingantacce
To kyautan Allah bai  karewa duk wanda ya kusance shi sai ya saukar da shi bisa falalan sa daraja irin na Annabawa  da siddikai da shahidai  da salihai , Manzon Allah tsira  da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da Rabi'ata Dan Ka'ab Al-Aslami a lokacin da ya nemi kusanci da Manzon Allah a aljanna  sai  ya ce da shi:-(  ka taimaka mini akan kanka da yawan sujada)   Muslim ne ya rawaito

     (ka yi sujada kuma ka kusanto ) a cikin sujada ne alamomi na gaskatawa da imani ke bayyana alamomin yakini da mika wuya ke fitowa fili , an karbo daga Aliyu dan Abi Dalib  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :-  ya kasancen  daga  cikin adu'o'in manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a sujadan sa  Allahumma laka sajadtu , Aya Allah don kai na yi sujada , wabika amantu , da kai ne kuma na yi imani  wa laka aslamtu, kuma da kai na mika wuya  ,  fiska ta ta yi sujada ga wanda ya halicce ta ya sauwara ta  ya tsagi jinta da ganin ta  tsarki ya tabbata ga Allah mafi kyaun masu halitta )Muslim ne ya rawaito
(ka yi sujada kuma ka kusanto ) lalle sujada na    cikin ibada  wanda dukkan halitu suka yi tarayya suka tattaru a kanta (Kuma ga Allah abinda yake cikin sammai da kasa na dabba da mala'iku suke yin sujada , kuma basu kangara .  Suna tsoron Ubangijin su daga bisan su  kuma  suna aikata abinda ake umarnin su )
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ni ina ganin abinda bakwa gani kuma ina jin abinda bakwa ji , sama ta yi  kara kuma ta cancanci ta yi karan sabo da  babu wani bigirea na yatsu fa ce mala'ika yana daure da fiffigen shi yana mai sujada ga Allah , wallahi da kunsan  abinda na sani da kunyi dariya dan kadan kunyi kuka mai yawa . Da ba ku ji dadi da mata ba akan shimfidi  da kun fita kwararo –kwararo  kun yi kururuwa  kuna kara  zuwa ga Allah ) Nasa'I da Ibn Maja ne suka rawaito  da Ahmada.
1.   (ka yi sujada kuma ka kusanto ) ka yi sujada kana mai rokon Ubangijin ka kana mai kiran mahaliccin ka  , kana mai kankan da kai zuwa ga masoyin ka , kai din nan kana aljanna ne daga cikin aljannoni na duniya , ka yi sujada sujudan mai tsoron Allah   a duk lokacin da ka ji ayoyin alkur'ani , bayanansa suka ratsa ma zuciya.

 Allah madaukakin sarki yana cewa (Kuma yana abun karatu  mun rarraba shi domin ka karanta shi ga mutane akan jinkiri,  kuma mun sasaukar da shi sassaukarwa  ka ce ku yi imani da shi ko kuwa  kada  ku yi imani ,   lalle ne  wadan da  aka  baiwa  ilimi  gabaninsa  idan ana  karatun sa  akan  su   suna   faduwa   ga habobin  su  suna masu sujada )
(Kuma suna cewa tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu lallae ne wa'adin Ubangijin mu ya kasance hakika abin aikatawa , kuma suna faduwa ga habobin su  suna  kuka  kuma  yana  kara  musu  tsoro  )
(ka yi sujada kuma ka kusanto ) kuma duk lokacin da ka tuna jinkirin ayukan ka kuma ka ji zafin zunuban ka da gafalar ka  ka rinka kwankwasa kofar tuba da neman gafarar ka  to Allah  madaukaki yana cewa  yana mai siffanta Annabin sa Dauda  Amincin Allah ya tabbata a gare shi
(Dauda ya tabbatar da cewa mun fitine shi ne, sabo da haka,  ya nemi Ubangijin sa gafara  kuma ya fadi yana mai sujada  kuma ya mayar da al'amari ga Allah , sabo da haka muka gafarta masa wancan .  Kuma lallai yana da wata  kusantar daraja a wurin mu da kyawun makoma )
(ka yi sujada kuma ka kusanto ) Idan bakin ciki ya tananta a gare ka , matsaltsalu sun kyawaye ka   ga fitintinu sun dame ka , to lalle sujada  yayewa ne ga dukkan wani bakin ciki   duk wanda zuciyar sa  ya kuntata   mutane suka bata mishi rai to, ya yawaita salla da sujada da adu'a   Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Hakika mun sani cewa  zuciyan ka na kuntata   sakamakon abinda suke  fadi to ka yi  tasbihi da godiy a ga Ubangijin ka  ka kasance cikin masu sujada  )
 Sujada na kashe fushin Uabangiji mai rahama kuma  yana  haifar da yardan sa  tsarki ya tabbata ga Allah  madaukaki :- Ya zo a sahihi ingantacce  na Annabi tsira da aminci su tabbata a gare shi (kan cewa idan mutane sun tsaya a farfajiyan ranar alkiyama  aka tafi neman  ceto   wurin Annabawa, har suka kai ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,sai suka ce ya Muhammad ba ka ga halin da muke ciki ba? Ba ka ga musibar da ta same mu ba? Sai yace "Da ma neman ceton tawa ce" sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya tafi ya yi sujada a karkashin Al'arshi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace : sai na nemi izinin Ubangiji na sai ya ban izini,shi na gode mi shi,da wasu yabo da ba zan iya su yanzu ba, wanda Allah zai min ilhamar su, sai na fadi ina mai sujada sai a ce ya Muhammad daga kanka, ka fada za a saurare ka, ka roka zaa baka, ka nemi ceto za a baka.) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Sai Allah ya sanya sujada a matsayin ceto kuma tsani don fita daga azabar matattarar kiyama.
A duk lokacin da ka samu wasu alheri da kyauta mai yawa daga Mai rahama to ka fadi ka yi sujada ga  Allah    don godiya  bisa ni'imarsa.
An karbo daga Abu bakrata yace a duk lokacin wani abu na farin ciki ya samu Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai ya fadi ya yi sujada ga Allah)Su biyar suka rawaito banda Nasa'i
An karbo daga Abdurrahman Bin Auf  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya yi sujada sai ya tsawaita sujadan sannan sai ya daga kansa sai ya ce " Lalle Jibrilu ne ya zo ya mini albishir sai na yi sujada don godiya ga Allah" Ahmad ne ya rawaito Hakim kuma ya inganta shi.

Huduba ta biyu
Bayan haka!
Mamakin da kyaun sauyawan mutumin da zai kwankwadi dadin sujada a dararrakin ramadana da falalarsa,Allah Madaukakin sarkin yace :(Daga wani sashe na dare ka yi masa sujada kuma ka masa tasbihi dare mai tsawo,)   
Allah Madaukakin sarkin yace :(Da wadanda suke kwana suna sujada da tsayuwan dare) Allah Madaukakin sarkin yace (Shin wanda yake mai tawaliu tsawon dare  yana mai sujada ku yana mai tsayuwa ga sallah yana tsoron lahira kuma yana fatan rahamar Ubangijinsa(yana daidai da waninsa?)
Ya kai mai tsere zuwa ga aikin alheri a ramadan, ka yi gaggawa  a tafiyarka zuwa ga ubangijinka.
Hasara dukkan hasara shine a haramtawa bawa ni'imar sujada gaba ga Ubangiji.
Idan dan'adam ya karanta sajada sai yayi sujada sai shaidan, sai shaidan  ya kebe yana kuka yana cewa : ya bonenSa- A riwayar Abu kuraib "ya bone na"
An umarci dan Adam da sujada sai yayi to yana da Aljanna.
An umarce ni da sujada sai na ki to gashi zan shiga wanda) Muslim ne ya rawaito
Duk wanda ya yi girman kai bai yiwa Ubangiji sujada  ba a duniya ba, to ba  zai   iya yin haka a lahira ba in an kiraye shi da haka.
An karbo daga Ada'u dan yasar daga Abu Said Allah ya kara yarda a gare shi yace  :Na ji  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:UbangijinMu zai yaye kwabrinsa sai dukkan wani Mumini da mumina, su yi sujada  sai yasaura kawai wanda ya kasance mai yin sujada don riya da neman a ji. Sai ya je don yayi sujada sai bayansa ya zamza  shinfida guda).Bukhari ne ya rawaito


  



الجمعة، 3 مايو 2019

Ayyukan Biyayya a Watan Ramadan


Hudubar Masallacin Annabi 28-8-1440AH Sheikh Abdulmuhsin Alkasim
Hudubar Farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacciya mai yawa.
Bayan haka,
 ku ji tsoron Allah yadda ya dace a ji tsoron shi, ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.
Ya ku Musulmai!
Ranaku da dararraki na ta tafiya da sauri,ga shekara na kokarin nade tabarmarsa da gaggawa,.bayi na tafiya zuwa ga Allah ! kuma su riski ayyukansa.
Na daga falalar Allah da karamcinsa ya zaba mana wasu lokuta na da'a, ya zabi wasu ranaku da dararraki da wasu sa'o'i, domin kwadayin rahamar Allah ya yawaita a samu karin kaimi da masu zage damtse,da gasar masu gasa cikin ayyukan alheri, a duk lokacin da jinjirin watar ramadana ya kada sai ya buso mana da wasu albarka masu yawa, sai musulmai su fiskance shi da annashawa, zukatarsu su cika da farinciki sabo da shi,ta iya yiwuwa sa'a guda da zaa riska ta daga darajan mutum ta sa Allah ya yarda da shi ya kuma samu walwala,
Ga wata mafi daraja ta dumfaro mu,lokaci ne mai girma da Allah ya kebance ta da daukakawa da girmamawa, sai ya turo manzonsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya sauke littafinsa a cikinta,ya wajabta azumtarta, sa'ointa na da albarka, lokutan cikinta ana raya su da ayyukan alheri, alheri na bibiyan juna a ciki,albarka na gamewa a ciki,lokaci ne na kyautatawa da bada sadakoki, lokaci ne na gafara da kankare laifuka, wuninta azumi darenta kuma tsayuwan dare ana nafila, ana raya ta da sallah da karatun Alkur'ani,Ana bude kofofin Aljanna,ana kulle kofofin wuta,ana daure shaidanu a cikinta, a cikinta akwai dare guda da ya fi watanni dubu, wanda ya rasa alherinta lalle ya yi hasara.
Ramadana fage ne mai fadi na gasa cikin ayyukan da'a,  kuma wani kyauta ne na tsarkake rayuka daga kazanta da laifuka,wata ne mai girma ana ribanya ayyukan Alheri, ana kankare kusakurai da laifuka, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Salloli guda biyar da juma'a zuwa juma'a da Ramadan zuwa ramadan kankara ne ga abin da ke tsakanin su muddin aka nesaci manyan zunubai)Muslim ne ya rawaito
A cikin ta musulmai ke sauke rukuni daga cikin rukunan musulunci, kuma wani abu ne na aiki bayyananne da ke nuna girman wannan addini da hadin kan musulmai, a cikinta ne fadin Allah Madaukakin sarki ke bayyana na cewa : (Lalle wannan Al'umarku ce Al'uma guda Ni kuma Ubangijinku ne to ku bauta mini).
Ribatan lokutan alheri budi ne daga Allah ga wanda ya so na daga bayinSa, a cikin Ramadan tushen ibadoji  kuma mafi girma ke haduwa ga musulmai, sallah sadarwa ne tsakanin bawa da Ubangijinsa, bata rabuwa da musulmi a dukkan rayuwarsa,sallan mutum cikin jam'I farilla ne ta fi sallarsa a gidansa da kasuwansa da lada ashirin da bakwai.
Ya dace ga musulmi da ya nemi taimako da azuminsa bisa sallarsa, kuma ya zama yana kaso mafi girma na sallah To ( wanda ya yi tsayuwan Ramadan bisa imani da neman lada zaa gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa)Bukhari da muslim ne ya rawaito. Duk ( wanda ya yi tsayuwan dare  tare da liman har aka tashi  za a rubuta mishi cikakken tsayuwan dare ) Tirmizi ne ya rawaito.
Zakka da sadaka tsarkaka ne da habaka ga dukiya kuma  wadata ne ga zuci da tsarkaka, tasirinta a bayyane yake ga rayi da dukiya da   da, tana tunkude bala'I, tana janyo yalwa, wanda ya yi wa bayin Allah kyauta Allah zai yi masa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Allah Mabuwayi da daukaka ya ce: Ya kai dan Adam ka ciyar zan ciyar da kai)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Dukkan mutum na karkashin inuwar sadakarsa ranar alkiyan, to ku yi sadaka ko da da dan kadan ne, ka jiyar wa kanka dadi, ka sadar da zumunci da shi ga wanda bai da shi, Duk wanda ya shayar da mai azumi to yana da kwatankwacinsa na lada, kuma na daga cikin kyautarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai ciyarwa da kuma kyauta, yana bada kyautar mutumin da bai tsoron talauci, in ya ciyar zai bada da yawa, in ya bada kyauta zai yawaita , ba ya maida mai tambaya. Baa tambayarsa wani abu ba face sai ya bada,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance mafi kyauta a cikin azumi to shi yafi iska mai busawa.
Azumi shi ne   alami mafi girma cikin alamomin addini  a cikin wannan wata mai falala  musulmai na guzurin tsoron Allah a cikin shi,  Allah madaukakin sarki ya ce :-(Ya ku wadanda suka yi imani  an wajabta muku yin azumi kamar yanda aka wajabtawa wadanda suka gabace ku ko za ku samu tsoron Allah)
Ladan shi ba yi da kididdiga ko iyaka, Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin Alkudsi:  ( Dukkan aikin dan adam na shi ne sai azumi, lalle shi nawa ne kuma ni nake sakanya wa game da shi)  Buhari da Muslim ne  suka rawaito.
Kuma ( wanda ya yi azumin ramadana yana mai neman lada an gafarta mishi zunuban sa)
Azumi kan yi shamaki tsakanin ma'abocin shi da sharrace-sharrace  da laifuka  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- ( azumi garkuwa ce   ).
Umra na daga cikin ayukan da ake riba ta a wannan wata  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (yin umra a watan Ramadan na dai-dai da Hajji )Buhari da muslim ne suka rawaito
Kuma kur'ani maganan Allah ne madaukaki kuma hujjan sa ne kan halittun shi , kuma shi wani mabubbuga ne na hikima  , kuma aya ne na sako  babu hanya zuwa ga Allah sai ta hanyar shi   babu tsira gare mu ba tare da shi ba  haske ne  na basira  da kuma gani  wanda ya kusance shi zai samu daukaka , wanda ya yi riko da shi kuma zai samu buwaya  karanta shi lada ne da kuma shiriya , bitar sa kuma ilimi ne da tabbatuwa akan tafarki  aiki da shi kuma wani katanga ne da kuma aminci , koyar da shi kuma da kira zuwa gare shi kambi ne  akan kawunan masu da'a ,  a cikin ramadana ne kur'ani ya sauka  sabo da haka ake karfafa yawan karanta shi a cikin sa da lura da ma'anonin shi  da  koya da koyar da shi  da kuma aiki da shi da riko da koyarwar sa , Allah mabuwayi da daukaka ya ce:- (watan  ramadan wanda aka saukar da kur'rani acikinta  shiriya ne ga mutane,  kuma da bayyanannu na daga shiriya da kuma rarrabewa).
Jibrilu alaihissalatu wassalam  ya kasance yana bitar alkur'a ni da Annabin mu tsira da amincin Allah su tabbata a gare  shi  sau daya a ko wani  shekara , a shekaran da ya rasu kuma ya yi bita da shi  sau biyu  amincin Allah ya tabbata a gare shi .
Adu'a ibada ce kuma kusanci ne   wani garabasa ne ba tare da wahala ba ,  kuma riba ne da ba  tsiya tare da shi  kuma shi yana janyo yalwa , kuma makiyi ne ga dukkan wani bala'i   mutum ba zai taba halaka ba muddin yana tare da adu'a  da shi ne bawa  zai kai ga burin shi ya kuma  riski bukatar shi , sau dayawa yakan kusanto da abin da ke nesa kuma sau dayawa yakan saukake abin da ke da tsanani , sau dayawa yakan yaye bakin cikin abin da akwai bakin ciki a ciki,  kuma mafi karbuwan adu'a  shi ne wanda ya kasance a cikin  yankin karshe na dare  idan bawa ya marairaice gaba ga  Ubangijin shi to, Allah zai amsa rokon shi ,  idan rayi ta ji  yunwa sai zukata su yi taushi , mai azumi ba'a maida adu'ar sa  Ibn Rajab Allah ya kara mishi rahama ya ce :-(Mai azumi yana cikin bauta ne a daren sa da wunin sa  ana kuma amsa mi shi adu'a a azumin shi ya yin shan ruwan shi  , to, a haka shi   mai azumi ne kuma mai hakuri  a daren shi kuma yana mai ci kuma mai godiya ) .
Wanda aka yiwa dace shi ne wanda ya yawaita kwankwasa  kofar sama  ya sanyawa kanshi cikin wadannan kwanaki da dararraki   hyana mai adana .
  Ambaton Allah ibada ce mai girma kuma mai sauki  wanda ya ambaci Allah Allah zai ambace shi , bawa idan harshen shi bai shagaltu da zikiri ba to maganganu marasa amfani za su shagaltar da shi   da kuma sabonnin su .
  Addini mu'amala ne mafi dacewan halittu da kyautatawan ka shi ne wanda  Allah ya hada hakkinsa da na su ,  to iyaye biyu aljannan ka ne  kuma wutan ka  su suka fi dacewa a cikin mutane wurin kyautata mu'amala da su   , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- ( Hancin shi ya dumbuli kasa , kuma hancin shi ya dumbuli kasa kuma hancinsa ya dumbuli kasa! Sai aka ce :wanene ya Manzon Allah? Sai yace : duk wanda ya riski iyayensa a halin girma dayansu ko dukansu biyu kuma bai shiga Aljanna ba)Muslim ne ya rawaito. kuma (Zumunci na danfare da Al'arshi yana cewa: duk wanda ya sada mini Allah zai sada mishi, wanda ya yanke min Allah zai yanke mishi, wanda zai burge shi a yalwata mi shi arzikin shi a kuma jinkirta mishi  a bayan shi to ya sada zumuncin shi .) Buhari da Muslim ne suka rawaito
 Yan daga cikin cikan da'a a  kiyaye ta daga dukkan abin da zai tawaye ta ko ya warware ta  mai azumi yana da tsananin bukatan  kiyaye ibadar sa da kiyaye azumin shi daga abubuwan da za su kyata shi  ko bata shi  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce:- (Idan ranar da dayan ku ke azumi ne kada ya yi batsa  kada kuma ya yi hayaniya  , idan wani ya zage shi ko ya nemi   fada da shi   to ya ce lallai ni mutum ne mai azumi) Buhari da Muslim ne suka rawaito .
Ya kasance daga cikin koyarwan magabata Allah ya musu rahama  idan sun yi azumi sai su zauna a masallatai sai su ce :- za mu kiyaye azumin mu ba za mu ci naman wani ba Imamu Ahmad Allah ya mi shi rahama ya ce :- ( Ya dace ga mai azumi ya kula da azumin shi  daga harshen shi kar ya yi musu ).
BAYAN HAKA YA KU  MUSULMAI:
Biyayya baya  cika  kuma baya tsayuwa a kan kafan sa  ya zauna da gindin sa face da kauna  wanda za ta yi riko da ma'abocinta zuwa ga ikhlasi ,  da kuma gaskiyan da zai yi nuni da kyakkyawan  bi, kuma  aiki baya kasancewa kusanci sai idan har abin da ya sa a ka yi shi imani ne ba al'ada ba ko son rai  ba kuma neman suna ba ko  don  riya ba ,  har sai ya kasance babban manufan yin shi shi ne neman lada a wurin Allah  da kuma neman yardan sa ,  idan imani da neman lada ya hadu a aiki  , sai karbuwan aikin da kuma gafara ya tabbata.
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa
(Ku yi gaggawa zuwa ga neman gafara daga Ubangijin ku  da aljanna wanda fadin ta   sammai da kasa an tanade shi ga masu takawa).
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo sun tabbata ga Allah bisa kyautatawan sa  godiya kuma ta tabbata a gare shi bisa datarwan sa  da baiwan sa , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya  ina mai girmama sha'anin sa , na shaida Annabin mu Muhammad bawan sa ne kuma Manzon sa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da iyalan sa da sahabban sa da aminci tabbatacce mai kari .
YA KU MUSULMAI
Duniya za ta kare da farin cikinta da  bakin cikin ta  shekaru kuma su kare da tsawon su da kuma gajartan su , kowa ya hadu da Ubangijin shi  to anan ne fa dukiya ba zai yi amfani ba ko da  sai wanda ya zo wa Allah da zuciya  lafiyayye , to ku fiskanci watan ku da tuba na gaskiya , ku kulla azama  bisa ribatan shi da raya lokutan shi da da'a  rayuwan duniya fa ba wani abu ba ne sai wani 'yan numfasawa ne kididdigaggu da kuma ajali iyakantacce  to ku ribaci lokuta mafi daukaka , kuma hasararre shi ne wanda ya riski watan azumi ba a gafarta mishi ba .
 Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Hancin shi ya dumbuli kasa, hancin shi ya dumbuli kasa , mutum da ya riski ramadan har ya fita ba a gafarta mishi ba)  Tirmizi ne ya rawaito
(Duk wanda bai bar fadin  zur ba da  aiki da shi ba , to Allah baya bukatan   ya bar abin cin sa da abin  shan sa ) buhari da muslim ne suka rawaito
Mafi girman Abin da ke gyara  zuciya ambaton Allah, da lazimtar kur'ani mai girma, da tsayuwan dare , da zama da salihai.
Sannan ku sani hakika Allah ya umarce ku da salati da aminci ga Annabin shi.