Tarjamar
Hudubar Masllacin Annabi Na shaikh Abdullah bin Abdurrahman Albuaijan
14-8-1440AH/19/4/2019AD
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah
wanda ya halicci sammai da kasa, ya sanya duhu da haske, mai sauya ranaku da
watanni, mai karar da shekaru da zamuna.
Ina gode masa ga dukkan al'amura,muddin iskar gabas
da ta yamma na kadawa.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,
shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, bisa gaskiya da yakini. Ina adana ta
ga Allah ranar da rai bai mallaki wani
abu ba ga wani rai, kuma al'amari a wannan rana na Allah ne.
Kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma
ManzonSa ne, ya isar da sako ya sauke.amana, ya yi jahadi a tafarkin Allah har
yakini ya zo mishi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi
da sahabban shi baki daya.
Bayan haka !Lalle Alkur'ani shine zance da
magana mafi kyau,Addini a gurin Allah shine musulunci,Mafi alherin shiriya
shine koyarwar Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,(Ya ku mutane ku ji tsoron Ubangijinku ku tsoraci wata
rana da mahaifi ba zai fanshi danSa ba, ko shi da ya fanshi mahaifinSa da wani
abu, lalle alkawarin Allah gaskiya ne kada rayuwar duniya ta rude ku, kada wani
mai rudi game da Allah ya rude ku.)
Ya Ku jama'ar musulmi!
Lalle Allah ya sanya lokuta tamkar wata
ma'adana ce ga aiki, (To duk wanda ya yi wani
aiki da ya kai kwayar zarra na alheri zai gan shi. To duk wanda ya yi wani aiki
da ya kai kwayar zarra na sharri zai gan shi)
Wanda ya yi hasara shi ne wanda ya hasarar da
lokuta mafi alheri, mahrumi shine wanda aka hana shi ribatar lokutan da'a,
hakika Allah ya sanya zamani ya zama hanya ne ga muminai zuwa ga biyayya ga
Ubangijinsu, hasara ce ga wasu mutane da zai zama gafala ne ga kawunan su, to
ku raya kawunanku,ta hanyar yin biyayya ga Allah, domin zukata na rayuwa ne da
ambaton Allah (Abin da ku ka gabatar na alheri don
kawunanku zaku same shi a gurin Allah).
Ya ku bayin Allah!
Lalle zamani na da fifiko kan sashi bisa ranaku
ko watanni ko sa'oi, mafi alherin abin da mutum zai raya shekarunsa da shi ya
raya lokacinsa sune ayyuka masu falala da abin da zai kusanto da kai ga
ubangiji, da aikata ayyukan alheri da da'a, Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma shine wanda ya sanya dare da yini akan mayewa ga
wanda ya ke son ya yi tunani ko kuwa ya yi nufin ya gode,)
Ku saurara! Lalle kuna cikin wata mai girma wanda
da yawa daga cikin mutane na gafala daga shi tir da gafala kason wadanda aka
hana alheri,kayan hajan lalatatu,
Ku saurara! Lalle kuna cikin wata mai girma da
ake daga ayyuka a cikinsa zuwa ga Ubangijin talikai, to ku cike karshensa da
tuba, da ayyuka na kwarai,ko Allah zai bamu kyakkyawan karshe,
Ku saurara! Lalle kuna cikin wata mai girma da
manzon Allah ke kokarin yin azumi a cikin shi.
An karbo daga Usama dan Zaid yace
da Manzon Allah tsira amincin Allah su tabbata a gare shi, ban ga kana yawaita
azumi a wani wata ba kamar yadda naga ka ke yawaita wa a wannan watan na sha'abana
ba, sai yace :( Ai wannan wata ne da mutane ke gafala daga shi yana tsakanin
rajab da ramadan kuma wata ne da ake daga ayyuka zuwa ga Ubangijin talikai to
sai na so a daga ayyuka na ina mai azumi.
An karbo daga Aisha Allah kara
yarda agare ta tace : Manzon Allah ya kasance yana azumi har muce ba zai sha
ba, wani sa'i kuma yana sha har muce ba zai yi azumi ba,ban taba ganin manzon
Allah ya cika wani wata yana azumi ba
sai ramadan ba watan da naga yana yawaita azumi acikin shi kamar sha'aban,)Muslim ne ya rawaito
An karbo daga gare ta ta ce: ya
kasance mafi soyuwan watanni a gurin manzon Allah da ya azumce shi shine
sha'aban) Abu Dawuda ne ya rawaito shi a sunan nashi kuma Albani ya inganta
shi.
Ya Ku jama'ar musulmi!
Lalle a daren tsakiyan sha'aban Allah na da gafara da take
game muminai amma ana haramtawa masu gaba da kiyayya da kullin juna da kafurai,
An karbo daga Abu Musa Al'ash'ari Allah ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: (Lalle Allah na tsinkaya a tsakiyar daren sha'aban sai ya
gafartawa dukkan halittun shi banda mushriki ko mai gaba da wani,)Ibnu Majah ne
ya rawaito da waninsa,Ibnu Hibban da Albani sun inganta shi
Ku yafe
ku yi rangwame ku dauke kai ku tausayawa
juna, ku yi afuwa, ku sada zumunci, kar ku yi hasada, kar ku yi munajasha, kar
ku yi kiyayya kar ku juyawa juna baya, ku zama bayin Allah 'yan uwan juna.
An karbo
daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi, yace: (Lalle
ana bude kofofin Aljanna ranar litini da ranar Alhamis, sai a gafartawa dukkan
bawan da bai hada Allah da wani face mutumin da akwai kiyayya da dan'uwan shi,
sai ace : ku dakanci wadannan biyun har sai sun yi sulhu! ku dakanci wadannan
biyun har sai sun yi sulhu! ku dakanci wadannan biyun har sai sun yi sulhu!)
Muslim ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah!
Sha'aban sha gaban daya daga cikin rukunnen
musulunci ne, shine Azumin watan ramadan da aka saukar da Alkur'ani a cikinsa.
To shi fage ne na sabo da koyo, da kimtsawa da
shiryawa, da shigowan watan imani don fiskantar watan ramadan,
Sha'aban da ramadan kamar sunnoni ne na
ratibi ga sallolin farillah. Shi kamar
wani gwaji ne don sabo da watan ramadan don rage wahalansa da nauyin sa da
dandana zakin azumi da dadinsa sai mutum ya shiga azumin ramadana da kuzarinsa
da karsashinsa.
Ya Ku
jama'ar musulmi!
Duk wanda akwai biyan azumin watan ramadana da
ya gabata a kansa to ya gaggauta azumtarsa kafin shigowan watan ramadan, don
jinkiri game da haka zai iya zama sababi daga cikin sabuba na sakaci,
An karbo daga Aisha Allah kara
yarda a gare ta tace : Azumi na kasancewa a kai na ba na samun daman biyansa har
sai sha'aban sabo da matsayin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi,)
To ku gaggauta ayyukan alheri –Allah ya muku rahama-
kafin ajali ya zo, (ku gaggauta zuwa
ga gafara daga Ubangijinku, da Aljanna wanda fadinta ya kai sammai da kasa an
tanade shi ga masu takawa.)
Huduba ta biyu.
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah bisa
kyautatawarsa godiya ta tabbata a gare shi bisa datarwarsa da baiwarsa, na shaida ba abin bautawa da
gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, ina mai girmama
shaninsa,na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzon sa ne, mai kira zuwa
ga neman yardarsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi
da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.
Ya ku musulmai!
Lalle Allah madaukakin sarki, ya
farlanta azumin watan ramadan a wannan wata, wato ina nufin sha'aban a shekara ta uku bayan hijira: Manzon Allah ya
yi azumi
Ramadan sau tara, sannan ya koma ga
Ubangijinsa.
Allah madaukakin sarki yace; (Ya ku wadanda suka yi imani An wajabta muku azumi kamar
yadda aka wajabta shi ga wadanda suka gabace ku ko zaku ji tsoron Alla)
. Ranaku ne kididdigaggu
to duk wanda ya ke maralafiya a cikinku ko yana matafiyi to gwargwadon abin da
ya sha na daga kwanaki a wadansu kwanaki yana kansa. Fidiya yana kan wadanda ke
da ikon yin azumi tare da wahala ita ce abincin miskinai, duk wanda ya yi tadauwa'i
na alheri to ya fi alheri a gare shi, ku yi azumi shi ya fi amfani a gare ku,
in kun kasance kun san hakan yafi ( watan ramadan shine wanda aka sauke
Alkur'ani a cikinsa mai shiryar da mutane daga bata, ayoyi na shiriya mabayyana
da rarrabewa tsakanin karya da gaskiya. Duka wanda ya ga wata daga cikin ku to
ya azumce shi, wanda ya kasance mara lafiya ko a kan tafiya to gwargwadon abin
da ya sha na kansa na wasu kwanaki, Allah na nufin sauki gare ku bai nufin
tsanani gare ku, sabo da ku cika adadin kuma ku girmama Allah bisa shiryarwar
da ya muku kuma don ku gode masa bisa wannan ni'ima,)
An karbo daga Abdullahi dan umar Allah
ya kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi, yace: (Lalle An gina musulunci
akan abubuwa biyar :Bisa a bautawa Allah
a kafurcewa waninsa, ya tsaida salla ya bada zakka da hajji dakin Allah da
azumin ramadan )Muslim ne ya rawaito.
An karbo daga Abu huraira Allah ya
kara yarda a gare shi, yace :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi, yace: (wanda ya yi azumin ramadana
yana mai imani da neman lada zaa gafarta masa abin da ya gabata na daga
zunubansa kuma wanda ya yi tsayuwan dare na ramadan bisa imani da neman lada to
zaa gafarta mishi dukkan abin da ya gabata na daga zunubansa) Bukhari ne ya
rawaito
Ya ku bayin Allah!
Ba abin da ya rage a wannan wata sai
ranaku kididdigaggu, to ya dace ga musulmai da su shirya wa wannan wata,da su
kimtsa masa, kuma su yi gaggawa su yi
tsere da rigegeniya bisa biyayya ga Allah . to sam barka ga wanda ya riski
ramadan,barka da duk wanda aka datar da shi zuwa ga alheri da ayyukan kwarai,
ya mai neman alheri ka fiskanto ya mai neman sharri ka gajarta,
To ku nuna wa Allah alheri daga
kawunanku, don matsiyaci shine wanda aka haramta mishi biyayya ga ubangijinsa, kuma lokutan alheri suka tsere
mishi bai fadaku ba. Ya yiwa kansa barna har mutuwa ta shammace shi bai tuba
daga zunubansa ba.