Hudubar Masallacin
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi na shaikh Abdulmuhsin
Alkasim 19-5-1440
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun
tabbata ga Allah, muna gode masa kuma muna neman taimakonsa
Muna neman tsarin Allah daga
sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu,
duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar kuma babu mai
shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke
ba shi da abokin tarayya,kuma na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma
ManzonSa. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da
sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa.
Bayan haka, ku ji tsoron Allah
-ya ku bayin Allah- cancancin tsoronSa, don cikin tsoron Allah akwai karuwar ni'ima da tunkude azaba.
Ya ku musulmai! Addinin
musulunci addini ne na fidira yana kira zuwa ga kyakkyawan kuduri da kyawawan
dabiu, da sifofi abin yabawa, yana lura da yanayin halin da mutum ke ciki, kuma
ya faranta masa rai a yanzu, kuma ya kwadaitar da shi fatan alheri a nan gaba,
da yi wa halittu albishir da abin da zai dadada musu rai, a matsayin bauta ga
Allah da kusanci, Allah ya ce : (ka yi albishir
ga muminai). Hakika Allah ya siffanta kanSa da hakan sai yace: (wancanninka shine abin da Allah ke albishir ga
bayinSa) sabo da girman matsayi irin na albishir a
cikin zukata mala'iku ke zuwa da shi, Allah Mabuwayi da daukaka ya ce:(Hakika manzanninMu sun zo wa Ibrahim da bushara). Yin
bushara ga bayin Allah muminai na daga cikin manufa na turo manzanni, Allah
Madaukakin sarki ya ce :(Ba mu turo manzanni ba face
masu albishir masu gargadi)
Isa amincin Allah su tabbata a
gare shi ya zo da albishir sai Allah ya ce : (Kuma
ina mai albishir da wani manzo da zai zo a bayana sunansa Ahmad)
Kuma yana cikin siffofi mafi
kyau na mutanen farko, (A yayin da mai albishir ya
zo sai ya jefa ta (rigar) akan fiskarsa sai ya koma mai gani)
Allah ya turo Annabinmu
Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da bushara na falaloli da
gidajen aljanna masu ni'ima ga
Al'umarsa,Allah madaukakin sarki ya ce : (Ba mu
turo ka ba face mai albishir kuma mai gargadi)
Annabi tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya kasance mai yawan Albishir ne ga sahabbansa, dukiya ya
zo mishi daga kasar Bahrain sai ya ce da su (Ku
yi bushara da fatan alheri na abin da zai dadada muku rai) Bukhari da Muslim ne
suka rawaito.
Na daga cikin koyarwarsa ya
kan tura masu da'awa ga sassa na duniya don su yi wa mutane bishara da ni'ima
ta musulunci, sai yace da Mu'az dan Jabal da Abu Musa Allah kara yarda a gare
su a yayi da ya tura su yaman :(ku saukaka kada
ku tsananta, ku yi bushara kada ku kore mutane,) Bukhari da Muslim ne suka
rawaito,
Hakika Allah ya bada labari
cewa na daga cikin siffofin muminai albishir ga junansu, (kuma idan aka saukar da wata sura to daga cikinsu akwai
wadanda suke cewa: wanene a cikin ku wannan sura ta kara masa imani? To amma
wadanda suka yi imani, to ta kara musu imani, kuma su suna yin bushara (da
ita). Wato sashe na yi wa
sashe albishir da baiwa da Allah ya yi musu.
A addinin musulunci akwai
albishir masu yawa daya bayan daya ga
mabiyansa, bushara mafi girma ga wanda ya tabbatar da tauhidi (kuma wadan da suka nesanci shaidanu ga bauta musu
kuma suka maida al'amari ga Allah,suna da
bushara , To ka bayar da bushara ga bayi na)
To idan bawa ya tsayu a kan
biyayya ga Allah da kadaita shi to yana da albishir da gidajen Aljanna na
ni'ima, (Lalle wadannan da suka ce Ubangijinmu
shine Allahm sa'annan suka daidaitu Mala'iku na sauka a gare su(lokacin zuwan
ajalinsu) suna ce musu) kada ku ji tsoro kuma kada ku yi bakinciki, kuma ku yi
bushara da aljanna.wanda kun kasance ana yi muku wa'adi da ita.
Duk wanda ya hadu da Allah bai hada shi da wani
to albishirinsa Aljanna ne, Mala'ika jibrilu amincin Allah ya tabbata a gare
shi ya ce da Manzon Allah (ka yi albishir ga
Al'umarka cewa Duk wanda ya mutu bai hada Allah da wani to zai shiga Aljanna.)Bukhari
da muslim ne suka rawaito
To duk wanda ya bi Alkur'ani
da sunna Allah na mishi albishir da gafara da lada mai girma, (kana yin gargadi kawai ga wanda ya bi Alkur'ani ne kuma ya
ji tsoron Mai rahama a fake, to ka yi masa bishara da gafara da wani sakamako
mai karamci ).
Tushen shiriya shine ilimin da
ya hadu da aiki Allah madaukakin sarki
yace :(wadan da suke sauraron magana sa'annan su
bi mafi kyaunta, wadancan sune Allah ya shiryar da su, kuma wadancan su ne masu
hankali).
Kuma shi musulmi mai kankan da
kai ga Ubangijinsa mai mika wuya ga umarninSa, mai tawaliu ga halittunSa zai
samu bushara, Allah madaukakin sarki ya ce : (Kuma
ka yi bushara ga masu kankantar da kai)
Duk wanda wata musiba ta same
shi sai ya maidawa Allah lamarin shi ya yi hakuri bisa ga abin da Allah ya
hukunta ya kaddara, to yana da albishir daga Ubangijin talikai. Allah
madaukakin sarki ya ce : (ka yi albishir ga masu
hakuri wadan da idan musiba ta same su sai su ce :lalle ne mu daga Allah
muke kuma gare shi za mu koma. Wadannan akwai kyakkyawan yabo daga ubangijinsu
da wata rahama kuma wadannan su ne shiryayyu.)
Kyautayi ga Allah da
halittunSa alheri ne a duniya da lahira Allah ya ce :
(ka yi albishir ga masu kyautatawa).
Kuma muminai ana musu albishir
da daddadan rayuwa da sakayya mai girma. Allah
madaukakin sarki ya ce: (ka yi albishir ga muminai
suna da wani falala mai girma daga Allah).
Na daga cikin falalarSa gare
su yi musu bushara da abin da Allah ya alkawarta musu na gidajen Aljanna masu
ni'ima da dukkan abin da suke fata a cikinta. Allah madaukakin sarki ya ce : (Wadanda suka yi imani kuma suka yi ayyukan kwarai suna cikin fadamun aljanna suna abin da suke
so, a wurin Ubangijinsu waccan fa ita ce falala mai girma. Wancan shi ne Allah
ke bayar da bushara da shi ga bayinSa wadanda suka yi imani kuma suka aikata
ayyuka na kwarai).
Bisharori masu yawa na bin
juna cikin rayuwar duniya har bayan mutuwa. Allah madaukakin sarki ya ce : (To lalle masoyan Allah babu tsoro a gare su kuma ba
bakinciki. Wadanda suka yi imani kuma suna jin tsoron Allah. Suna da bushara a
cikin rayuwar duniya da ta lahira babu musanyawa ga kalmomin Allah, wancan
shine babban rabo mai girma ).
Idan mutuwa ta zowa mumini sai
a mishi bushara da mafi daukakan masaukai Manzon Allah tsira amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce :(Mumini Idan mutuwa ta
zo mishi zaa mishi albishir da yardar Allah da karamarSa sabo da haka ba wani
abu da ya fi soyuwa a gare shi fiye da abin da ke gaba gare shi, sai ya so
haduwa da Allah to Allah ma ya so haduwa da shi,) Bukhari ne ya rawaito.
Malaiku na cewa
ka fita ya kai rai mai tsarki, ana maka albishir da hutawa da kyakkyawan
abinci, da Ubangiji wanda ba zai yi fushi ba, sannan a haura da shi zuwa sama,
sai a bude mishi sai a ce :wanene wannan sai su ce wane ne, sai a ce maraba da
rai mai tsarki wanda ya kasance cikin jiki mai tsarki, ka shiga kana godiya,ana
ma bushara da hutu da abinci, da Ubangiji ba zai yi fushi ba, ba zaa gushe ba
ana fada mishi haka har a kai ga saman da Allah Mabuwayi da daukaka ke cikinta,)Ahmad
ne ya rawaito.
Idan kiyama ta tsaya bishara zata bayyana a
fiskar muminai, Allah madaukakin sarki ya ce : (wasu
fiskoki a wannan ranar masu haske ne, masu dariya masu bishara)
Suna da bushara a yanayi mafi tsanani, lokacin da mutane zasu kasance a
kan siradi bisa jahannama, Allah mai tsarki da dauka ya ce : ( Rãnar da zã ka ga mũminai maza da mũminai mãtã haskensu nã
tafiya a gaba gare su, da kuma dãma gare su. (Anã ce musu) "Bushãrarku a
yau, ita ce gidajen Aljanna." Ruwa na gudãna daga ƙarƙashinsu sunã mãsu
dawwama a cikinsu. Wannan, shĩ ne babban rabo maigirma. )
Idan sun shiga aljanna suna da sakayya mai yawa a wurin Ubangijinsu.( kuma ka yi bushãra ga waɗanda suka yi ĩmãni da cewa: Lalle ne sunã da abin gabãtarwar gaskiya a wurin Ubangijinsu.)
Idan sun shiga aljanna suna da sakayya mai yawa a wurin Ubangijinsu.( kuma ka yi bushãra ga waɗanda suka yi ĩmãni da cewa: Lalle ne sunã da abin gabãtarwar gaskiya a wurin Ubangijinsu.)
Musulmi na so wa 'yan'uwansa abin da ya ke so wa kan sa, kuma yana
kokari don ya faranta musu, bishara da alheri na cikin kofofi mafi sauki na ribatar
zukata, idan wata ni'ima ta sabunta ga dan'uwanka na addini ko duniya, to ka mishi Albishir da
ita,kamar yadda mala'iku suka yi wa Annabi Ibrahim albishir da Isma'il Amincin
Allah su tabbata a gare shi, Allah madaukakin sarki ya ce : ( Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri)
Sun yi mishi bishara da Ishak Amincin Allah ya tabbata a gare shi Allah
madaukakin sarki ya ce : ( Kuma Muka yi masa bushãraDa Is'hãƙa ya zama Annabi
daga sãlihan mutãne.)
An yi albishir ga zakariyya da Da bayan ya yanke tsammani (Allah Ya karɓa) "Yã zakariyya! Lalle ne Mũ, Munã yi
maka bushãra da wani yãro, sunansa Yahaya. Ba Mu sanya masa wani takwara ba a
gabãni).
Wani Malaika ya sauka ga Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi wanda bai taba sauka ba :(Bushara gare ka da haske biyu da aka baka ba wani Annabi
da aka bawa su kafin kai, fatiha da karshen suratul bakara ba za ka karanta su
ba sai an baka su.)Muslim ne ya rawaito.
Na daga cikin koyarwarsa
Manzon Allah su tabbata a gare shi,Albishir ga wanda wani bakinciki ya yaye a
gare shi, ya ce da Aisha Allah kara yarda a gare ta:
(Albishirinki ya A'isha, amma Allah ya barrantar dake)
Mace tagari mai biyayya ga
mijinta sakayyarta Aljanna ne,Jibrilu amincin Allah su tabbata a gare shi ya
sauka ga Annabi sai yace :(Ya Manzon Allah ga
khadija nan tana zuwa da kwano acikin shi akwai miya ko abinci ko abin sha, to
idan ta zo ma to ka isar mata da gaisuwa daga Ubangijinta kuma daga gare ni,
kuma ka mata bushara da gida a Aljanna na Zinari ba hayaniya a ciki ko gajiya,)Bukhari
da Muslim ne suka rawaito.
Kaifin hankali na ga rarrashin
wanda halinsa ya kyautata idan wani abu ya dame shi sai a mishi bushara da
fatan alheri, a farkon saukan wahayi ga Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi, sai ya shiga gun khadija Allah kara yarda a gare ta sai ya
ce da ita :(Hakika na tsoracewa kai na, sai ta
ce da shi:, A'a albishir na rantse da Allah, Allah ba zai taba kunyata ka ba
har abada). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Duk wanda ya lazimci gaskiya
ba tare da ketare iyaka ba, ko jafa'i to yana da bushara ta lada mai yawa,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (ku kirdadi daidai ku kusanto ku yi bishara) Bukhari da
Muslim ne suka rawaito.
Allah na farinciki da tuban
bawa sabo da falala da karamci irin nashi, kuma ranar da bawa zai tuba zuwa ga
Allah shine mafi alherin ranaku a gare shi a duniya, sabo da abin da tuba ke
janyowa ga bawa na maslaha a duniya da lahira, Ka'ab dan Malik bai halarci yakin
tabuka ba,Allah ya yarda a gare shi, shi
da abokan nasa biyu ba tare da wani uzuri ba, sannan Allah ya karbi tubansu,
sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana mai albishir
ga ka'ab, sai yace : (Bushara a gare ka da rana mafi alheri a gare ka tun daga randa
mahaifiyarka ta haife ka),
Kuma duniya kan kuntata ga wanda ajalinsa ya kusato, amma kuma yana jin
dadin kalamai masu dadi, da zai ji ta sabo da kusacin kaurarsu ga gidan lahira
bai san ina ya nufa ba, Mutuwa ta zo ga Amru dan As, sai ya yi kuka mai tsawo, sai
dansa na cewa : Ya baba na a se Annabi bai ma
albishir da kaza ba)Muslim ne ya rawaito.
Mafi girman abin da musulmi zai yi albishir da
shi shi ne daukakan wannan addini da isan sa duk inda dare da rana ya isa,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce: (Yi wa wannan al'uma bishara da daraja da daukaka, da addini da nasara da samun mulki a doron kasa)Ahmad ne ya
rawaito). Ahmad ne ya rawaito
Duk wanda aka mar albishir da alheri ya zama
mustahabbi ne a gare shi da yayi wa Allah sujada na godiya, kuma ya saka wa
wanda ya mishi albishir da abin da zai iya,Ka'ab dan Malik Allah ya kara yarda
a gare shi ya ce a hadisin kissarsa da
sahibansa : (A yayi da ina zaune a halin da
Allah ya ambata game da mu, hakika raina ya kuntata, kasa ta min kunci da duk
fadinta, sai na ji mai yekuwa ya cika dutse da sautin sa yana cewa :ya ka'ab dan
Malik Albishirinka, sai yace :sai na fadi ina mai sujada, sai na san cewa
yayewan bakinciki ya zo, wasu masu albishir suka tafi ta gun sahibai na, wani
mutun yayi gudu haye kan doki zuwa gare ni, wani mai kokari daga kabilar Aslama ya hauro dutse to
sautin nasa har ya fi dokin sauri, yayin
da wanda na ji sautin nasa ya iso sai ya min albishir,sai na tube tufafi na
biyu na tufatantar da shi su sakayya ga albishir da ya yi min, Wallahi ban
mallaki waninsu ba,sai na ari wasu tufafi biyu na sanya su, sai na tafi zuwa ga
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ,sai ga mutane suna
ta tara na tawaga tawaga suna mini barka da karbar tuba, suna cewa: Barkanka da
tubar da Allah ya amsa ma).Bukhari da Muslim ne ya rawaito.
Bayan haka ya ku musulmai:
Ba wani addini da ya fi addinin musulunci kyau,
don shi addini ne na farinciki da jindadi, yana kwadaitarwa gurin cusa walwala ga al'uma, mafi
dacewan mutane da alherin musulunci sune musulmai, Bushara tushe ne cikin kiran
halittu zuwa ga addini, da kwadaitar da shi cikin zukatarsu.
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan
abin jefewa,
(Yã kai Annabi!
Lalle Mũ Mun aike ka kanã mai shaida, kuma mai bãyar da bushãra kuma mai
gargaɗi.
Kuma mai kira zuwa ga Allah da izninSa, kuma fitila mai haskakãwa.
Kuma ka yi bushãra ga mũminai cħwa, sũnã da falala mai girma daga Allah.)
Allah sa mini Albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma.
Kuma mai kira zuwa ga Allah da izninSa, kuma fitila mai haskakãwa.
Kuma ka yi bushãra ga mũminai cħwa, sũnã da falala mai girma daga Allah.)
Allah sa mini Albarka ni da ku cikin Alkur'ani mai girma.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa
kyautatawarsa, godiya ta tabbata agare shi bisa taufikinsa da datarwarsa, na
shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin
tarayya, sabo da girmama sha'aninSa, kuma na shaida Annabinmu Muhammad bawanSa
ne kuma Manzonsa ne,tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da
sahabbansa da karin aminci tabbatace mai
yawa.
Ya ku Musulmai:
Mafi girman mai albishir a musulunci shine
Alkur'ani mai girma, dukkan shi shiryarwa ne da albishir Allah madaukakin
sarki ya ce : ( kuma Mun saussaukar da Littãfi a gare ka dõmin
yin bãyani ga dukkan kõme da shiriya da rahama da bushãra ga mãsu mĩƙa wuya
(Musulmi).
Kuma da Kyautata yabo ga wanda ya kyautata ba
tare da ya nemi hakan ba, na daga cikin albishir na kusa ga mumini, an ce da
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,(bani labarin mutumin da yana aikata aikin alheri kuma
mutane na yabonsa bisa haka, sai manzon Allah yace : Ai bushara ce ta mai
gaugawa ga mumini.)Muslim ne ya rawaito.
Mafarki na kwarai na farantawa ba ya korewa
kuma yana cikin masu bishara, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce : (Ba abin da ya rage na
annabtaka sai masu bushara, sai suka ce: menene masu bishara? Sai yace :
Mafarki nagari,) Bukhari ne ya rawaito.
Allah na turo iska ne da bushara ta ruwan sama
don ya farantawa mutane rai kafin
saukarsa da bayan saukarsa.
( Kuma akwai daga ãyõyinSa, ya aika iskõki mãsu bãyar da
bushãra)
Daddadan lafazi na bishara ne da alheri, kuma
yana cikin kyakkyawan fata, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce : (Ba rabuwar cuta ko camfi kuma
kyakkyawan fata na burge ni sai suka ce : menen kyakkyawan fata ? sai yace
daddadar kalma).Bukhari da muslim ne ya rawaito.
Sannan ku sani lallai Allah ya yi muku umarni
da salati da aminci bisa ga Annabinsa