HUDUBAR MASALLACIN
ANNABI NA SHAIKH ABDUL BARI ASSUBAITI 10-2-1440AH
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah,tsayayye Rayayye, ina gode mishi tsarki ya tabbata a gare
shi,bacci ba ya daukan shi ko gyangyadi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya
sai Allah Shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya,Madaukaki Mai girma, na
shaida Annabinmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne,ya nusar da mu zuwa ga
tafarkin Allah mikakke, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi,da sahabbansa masu tafiya akan
tafarki mikakke, bayan haka,
Ina muku wasiya da ni
kai na da ku ji tsoron Allah ,Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku wadan da
ku ka yi imani ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa, kar ku mutu face kuna
musulmai)
(Manzon Allah tsira
da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ya Abul Munzir ! ko kasan wace
aya ce mafi girma ka ke da ita a cikin littafin Allah? Yace sai na ce :Allah da
Manzonsa ne suka fi sani, sai yace: ya Abul Munzir ! ko kasan wace aya ce mafi
girma ka ke da ita a cikin littafin Allah? Yace sai na ce : (Allahu La'ilaha
illa huwal Hayyul Kayyum) sai ya buga kirji na yace " Madalla da ilimi
irin naka ya Abul Munzir",
Ayatul kursi ta zama
aya mafi girma ne sabo da ta tattaro tushen sunayen Allah da sifofinsa, ta
bayyana kudura na Allah Mai girma.
(ALLAHU LA'ILAHA ILLAHUWA) :- Allah
ba abin bautawa da gaskiya sai shi ) ,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Imani kashi saba'in da dori ne ko sittin da
dori mafi girmanta shi ne fadin LA'ILAHA'ILLALLAH
; ) shi ne mai gaskiya tsarki ya tabbata a gare
shi , fadin sa kuma shi ne gaskiya alkawarin shi ma gaskiya ne addinin shi ma
shi ne na gaskiya , kuma littafin shi ma gaskiya kuma duk abin da ya bada labari gaskiya ,
kuma duk abin da ya yi umarni da shi gaskiya ne
a zatin sa da sifofinsa mai
cikakken sifofi , shi ne wanda bai gushe ba kuma ba zai gushe ba ya siffantu da daukaka da kyau da kamala haka nan kuma bai gushe ba kuma ba zai gushe ba wanda aka san shi da ihsani .
( ALHAYYUL –KAYYUM) :-Rayayye
tsayayye shi dinnan shi ne rayayye
wanda baya mutuwa ko ya halaka ; yana da rayuwa na dindindin da wanzuwa wanda
bayi da farko ko karshe da za a
iya iyakance shi kuma (ALKAYYAUM) ya kunshi
kamalar wadatuwar sa da kamalar kudurar sa domin shi tsayyayye ne a kan kansa sannan kuma
yake dawainiya da wasu ,
wanin sa ba zai iya tsayuwa ba sai da tsayuwar sa wadan nan sunayen biyu sai suka kintsu wajen tabbatar da kamalar sa to, sai ya kasance shi ne abin neman
agaji da wadannan sunaye biyun kuma ana neman agaji da dukkan suna daga
cikin sunayen Ubangiji madaukaki da kuma
dukkan siffa daga cikin siffofin shi ,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance maiyana
yawan adu'a da wadannan sunaye biyun ,
idan wani abin bakin ciki ya same shi sai ya ce :- (YA HAYYU-YA KAYYUM BI RAHMATIKA ASTAGIS) Rayayye tsayayye da rahamarka nake neman agaji . Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce duk wanda ya ce Astagfirulllahal
lazi la'ilaha illahuwal hayyul kayyum wa
atubu ilaik) ina
neman gafaran Allah wanda ba abin bautawa da
gaskiya sai shi rayyayye tsayayye
kuma ina tuba zuwa gare shi ,
to, za a gafarta mi shi zunuban
shi ko da ya gudu daga fagen yaki ne .
Idan Musulmi ya lura ya san cewa Ubangijin shi dinnan rayayye ne
tsayayye ( sai zuciyan shi ya samu natsuwa da kwanciyan hankali ; hakika an
isar mishi daga bakin cikin duk
wani shiri , kuma an bashi kariya daga dukkan wasu sharrace-sharrace da laifuka
.
( LATA'AKUZUHU
–SINATUN WALA NAUM) Gyangyadi ko bacci bai daukan shi to shi mabuwayi mai daukaka ya tsarkaka daga
dukkan wata nakasa ko gajiyawa ko
aibi irin wanda ke tattare ga bayin sa :
- Yanda duniya ke gudana cikin tsari shaida ne akan haka , haka nan yanda rayuwa ke tafiya , da kuma yanda halittu ke rayuwa ( LATA'AKUZUHU
–SINATUN WALA NAUM) Gyangyadi ko bacci bai daukan shi, in ba don haka
ba kuwa da wannan duniyan ta rikirkice ,
tafiyar sa ya baci , tsarin sa
ya rikirkice ,,(Bai dace ga rana ba ta riski wata ko kuma dare ya sha gaban yini ) da kuma ruwan koguna sun rinka ambaliya da koramai .
A lokacin da idanuwa suka yi bacci taurari suka bayyana to lallai wasu mutane cikin
muminai hakarkarin su na yin nesa daga
makwanci :- suna ganawa da wanda
gyangyadi ko bacci bai kama shi , sai ya
amsa musu Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Ubangiji
mu mabuwayi da daukaka na sauka a dukkan dare
zuwa ga saman duniya daidai
sulusin karshe na dare sai ya ce :- wa
zai roke ni na amsa mishi kuma wa zai
tambaye ni na bashi kuma wa zai nemi gafara ta na gafarta mishi).
Abin da ke cikin sammai da
kassai duka na shi ne dukkan komai da ke
cikin su yana karkashin mulkin sa ne da
kudurar sa da kuma kaddarawan sa da falalan sa
da fifikon sa da hukuncin sa da
hikimar sa falakoki da duniyoyi masu
girma : shi ne mahaliccin su,Mai mallakansu abin bautansu,ba abin bauta da
gaskiya koma bayanSa basu da wani
Ubangiji koma bayanSa,
(wanene zai yi
ceto gaba gare shi in ba da izininSa ba)? Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce : (Wanda ya fi samun ceto na ranar Alkiyama shi ne
wanda ya ce La'ilaha illallah yana mai ikhlasi daga zuciyarsa).
(yasan abin da ke
gaban su da abin da ke bayansu, ba su iyakance wani abu na iliminsa sai abin da
ya so) Shi ne wanda
tsarki ya tabbata a gare shi Mai ji Mai gani Masani kuma Gwani, yana ganin
tafiyan bakar tururuwa akan
sandararren dutse a cikin dare mai
duhu yana ganin abin da ke damfare da
jijiyoyin ta da gudun abinci a cikin
gabbanta .
( Yana da mabudan gaibi ba wanda ya san su
sai shi kuma ya san abin da ke tudu da
kogi , ba wani abu da ke faduwa na ganyen itaciya face ya sani ko kwaya a cikin
duhun kasa , ko danyen abu ko busasshe
face yana rubuce a littafi bayyananne )
ba abin da ya kewaye ilimin sa Mala'ika
ne na kusa ko wani Annabi manzo , to, ta
yaya masu duba da bokaye da 'yan
tsubbu za su iyakance ilimin shi , wadanda
suke da'awan sanin abin da zai faru nan gaba Allah madaukakin sarki ya ce :- (Ba wanda ya san gaibi cikin wanda suke
sammai da kasa face Allah ) .
(wasi'a kursiyyuhussamawati wal ardi
) kujerarSa ta fi fadin sammai da kasa abin mamaki da girman Allah abin bauta maigirma madaukaki kudurarSa ta bayyana tsarki ya tabbata a gare
shi , idan wannan shi ne girman kujerarSa
na cewa ya fi fadin sammai da kasa duk da girman sunnan da girman wanda ke cikin su to ina ga girman mahaliccin su da
kuma wanda ya kirkire su , to shi
ne; tsarki ya tabbata a gare shi mai
yalwa a iliminSa , kuma mai yalwa a wadatarSa
kuma mai yalwa a falalar sa da
ni'imtarwanSa da kyautarSa shi ne kuma mai yalwa a karfinSa da kasaitarSa kuma shi ne mai yalwa a ikon sa,
kuma mai yalwa a hikimarSa kuma mai yalwa a gafararSa da rahamarSa .
To Musulmi yana bautawa Ubangiji wanda kyautarSa na da
yalwa a dukkan komai , falalarSa kuma ta ketare dukkan abin da ake
fata Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya yi umarni game da rokon mai adu'a ga UbangijinSa ba tare da ya ga cewa ya yawaita mishi ba sai ya ce , (idan dayan ku ya zo roko to ya yawaita domin
Ubangijinsa fa ya ke roko).
Manzon Allah tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Idan za ku roki Allah to ku
roke shi Aljannar firdausi don ita ce tsaka –tsakin Aljanna kuma mafi
daukakanta, kuma samanta Al'arshin Mai rahama yake daga nan ne koramun Aljanna
ke bubbugowa).
(Kiyaye su ba zai
nauyayi Allah ba) Dukkan
wani abu da ke duniya na cikin kiyayewa na Allah ne, shine Alhaafiz kuma
Alhafeez) shi ne mai kiyaye ayyukan Mukallafi, kuma shi ne mai
kiyaye sharri da cuta da bala'i ga wanda ya so.
Na daga ciki aduar da
Annabi ya koyar da mu ita (Ya Allah ka kiyaye ni ta gaba na da ta baya na da
ta dama na da ta hagu na, kuma da ta sama na, ina neman tsarinka da kasaitarka
da a mini kisan gilla ta kasa ta.)
Allah- Mai tsarki -shi
kadan shi ne mai kiyaye mutum in ya kiyaye dokokin Allah ya nesaci abin da ya
haramta.
Allah Madaukakin sarki
ya ce :(To managartan mata masu bi ne
ga mazajensu masu kiyayewa ne a fakuwa, sabo da Allah ya kiyaye su
da yiwa maza wasiyya dasu )
Ayatul kursi : ganima
ce ga musulmai kuma ni'ima ce daga cikin ni'imomin Allah mafi girma, tana daga cikin zikiri mafi karfi
na safiya da maraice , wanda da ita ake samun kiyayewa mai karfi na Allah, game
da ita ne manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Duk
wanda ya karanta ayatul kursi karshen kowace sallah ba abin da zai hana shi shiga Aljanna
sai mutuwa) kuma idan ka karanta yayin da ka zo barci (Bai zai gushe ba
kana samun kariyan Allah kuma ba wani
shaidan da zai kusance ka har ka wayi gari)
HUDUBA TA BIYU
Alokacin da magana ta
yawaita kuma tashoshin watsa labarai suka cika da naji ance(kila da kala) to
wajibi a kan musulmi shi ne ya auna abin da yake gani da abin da ya ke ji da
abin da yake fada bisa mizani na sharia da hankali,idan ka samu kalma da zata
kashe fitina ta sanya fata na gari ta kawo zaman lafiya ta karfafi kwanciyan
hankali, ta kuma binne balbali ta rufe kofar fitina kuma ta rinjayar da
maslahar kasa kuma zata taimaka guri dunkulewar Al'uma ta kuma kiyaye wa
jagororin Addini hakkokinsu, to wannan ita ce kalma mai kyau.
To idan kalma na kara
wutan fitina ne, ta na gusar da zaman lafiya kuma tana tada balbalin bala'i tana girgiza aminta da jagororin Addini, tana
taba mutuncin malamai tana kawo rarrabuwar al'uma kuma tana cin karo da
maslahar kasa, to wannan ita ce kazantacciyar kalma, to binne ta tun tana
karama ya fi dacewa, kuma kaurace mata shine tafarki mafi daukaka.
Kasar saudiya tana da
gini mai karfi wanda ta kafu a zuciya, taba darajarta kaskanci ne, duk wanda ya
yi gaba da ita zai fadi ya kaskanta, yin kokarin kawo mata zaman lafiya da
amincin masallatayya biyu masu alfarma,kuma tare Masun da aka nufe ta da su, da
karfafa dunkulewarta abu ne na wajibi a sharia, kuma abu ne da ya dace duk wani
maihankali ya nema, (To su bautawa Ubangijin wannan daki. Wanda ya ciyar da
su daga yunwa, ya amintar da su daga tsoro.)