الجمعة، 19 أكتوبر 2018

FALALAR AYATUL KURSI


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI NA SHAIKH ABDUL BARI ASSUBAITI 10-2-1440AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah,tsayayye Rayayye, ina gode mishi tsarki ya tabbata a gare shi,bacci ba ya daukan shi ko gyangyadi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya,Madaukaki Mai girma, na shaida Annabinmu Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne,ya nusar da mu zuwa ga tafarkin Allah mikakke, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da iyalan shi,da sahabbansa masu tafiya akan tafarki mikakke, bayan haka,
Ina muku wasiya da ni kai na da ku ji tsoron Allah ,Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku wadan da ku ka yi imani ku ji tsoron Allah cancancin tsoronSa, kar ku mutu face kuna musulmai)
(Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ya Abul Munzir ! ko kasan wace aya ce mafi girma ka ke da ita a cikin littafin Allah? Yace sai na ce :Allah da Manzonsa ne suka fi sani, sai yace: ya Abul Munzir ! ko kasan wace aya ce mafi girma ka ke da ita a cikin littafin Allah? Yace sai na ce : (Allahu La'ilaha illa huwal Hayyul Kayyum) sai ya buga kirji na yace " Madalla da ilimi irin naka ya Abul Munzir",   
Ayatul kursi ta zama aya mafi girma ne sabo da ta tattaro tushen sunayen Allah da sifofinsa, ta bayyana kudura na Allah Mai girma.
 (ALLAHU LA'ILAHA ILLAHUWA) :- Allah ba abin bautawa da gaskiya sai shi ) ,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Imani  kashi saba'in da dori ne ko sittin da dori  mafi girmanta shi ne fadin LA'ILAHA'ILLALLAH ;  )    shi ne mai gaskiya tsarki ya tabbata a gare shi , fadin sa kuma shi ne gaskiya alkawarin shi ma gaskiya ne  addinin shi ma  shi ne na gaskiya , kuma littafin shi ma gaskiya  kuma duk abin da ya bada labari gaskiya , kuma duk abin da ya yi umarni da shi gaskiya ne  a zatin sa da sifofinsa  mai cikakken sifofi , shi ne wanda bai gushe ba kuma ba zai gushe ba ya siffantu  da daukaka da kyau da kamala   haka nan kuma  bai gushe ba kuma ba zai gushe ba  wanda aka san shi da ihsani .
        ( ALHAYYUL –KAYYUM) :-Rayayye tsayayye  shi dinnan shi ne rayayye wanda baya mutuwa ko ya halaka ; yana da rayuwa na dindindin da wanzuwa  wanda  bayi da farko ko karshe   da za a iya iyakance shi  kuma (ALKAYYAUM)   ya kunshi  kamalar wadatuwar sa da kamalar kudurar sa  domin shi tsayyayye ne a kan kansa  sannan kuma  yake  dawainiya da wasu  ,  wanin sa ba zai iya tsayuwa ba sai da tsayuwar sa  wadan nan sunayen biyu sai suka kintsu  wajen tabbatar da kamalar sa  to, sai ya kasance shi ne abin neman agaji  da wadannan sunaye biyun  kuma ana neman agaji da dukkan suna daga cikin sunayen Ubangiji  madaukaki da kuma dukkan siffa daga cikin siffofin shi  , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance maiyana yawan adu'a da wadannan sunaye biyun ,   idan wani abin bakin ciki ya same shi sai ya ce :-  (YA HAYYU-YA KAYYUM  BI RAHMATIKA ASTAGIS)   Rayayye tsayayye  da rahamarka nake neman agaji . Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce  duk wanda ya ce Astagfirulllahal lazi la'ilaha illahuwal  hayyul kayyum wa atubu ilaik)    ina neman gafaran Allah wanda ba abin bautawa da  gaskiya sai shi rayyayye tsayayye  kuma ina tuba zuwa gare shi ,  to,   za a gafarta mi shi zunuban shi ko da ya gudu daga fagen yaki ne .
    Idan Musulmi ya lura  ya san cewa Ubangijin shi dinnan rayayye ne tsayayye  ( sai  zuciyan shi ya samu natsuwa  da kwanciyan hankali  ;    hakika an  isar mishi  daga bakin cikin duk wani shiri , kuma an bashi kariya daga dukkan wasu sharrace-sharrace da laifuka .
  ( LATA'AKUZUHU –SINATUN WALA NAUM)    Gyangyadi ko bacci bai daukan shi  to shi mabuwayi mai daukaka ya tsarkaka daga dukkan wata nakasa  ko gajiyawa ko aibi  irin wanda ke tattare ga bayin sa : -  Yanda duniya  ke gudana cikin tsari  shaida ne akan haka ,  haka nan yanda rayuwa  ke tafiya , da kuma yanda halittu ke rayuwa   ( LATA'AKUZUHU –SINATUN WALA NAUM) Gyangyadi ko bacci bai daukan shi, in ba don haka ba kuwa da wannan duniyan ta rikirkice ,  tafiyar sa ya baci ,   tsarin sa  ya rikirkice ,,(Bai dace ga rana ba ta riski wata  ko kuma dare ya sha gaban yini ) da  kuma ruwan koguna sun rinka ambaliya  da koramai .
      A lokacin da  idanuwa suka yi bacci   taurari     suka bayyana to lallai wasu mutane cikin muminai hakarkarin  su na yin nesa daga makwanci :-  suna ganawa da wanda gyangyadi ko bacci bai kama shi ,  sai ya amsa musu  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce :- (Ubangiji mu  mabuwayi da daukaka na sauka  a dukkan dare  zuwa ga saman duniya  daidai sulusin karshe na dare  sai ya ce :- wa zai roke ni na amsa mishi  kuma wa zai tambaye ni na bashi kuma wa zai nemi gafara ta na gafarta mishi).
      Abin da ke cikin sammai da kassai duka na shi ne  dukkan komai da ke cikin su  yana karkashin mulkin sa ne da kudurar sa  da kuma kaddarawan sa da  falalan sa   da fifikon sa da hukuncin sa  da hikimar sa   falakoki da duniyoyi masu girma : shi ne mahaliccin su,Mai mallakansu abin bautansu,ba abin bauta da gaskiya koma bayanSa  basu da wani Ubangiji koma bayanSa,                     
(wanene zai yi ceto gaba gare shi in ba da izininSa ba)? Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Wanda ya fi samun ceto na ranar Alkiyama shi ne wanda ya ce La'ilaha illallah yana mai ikhlasi daga zuciyarsa).
(yasan abin da ke gaban su da abin da ke bayansu, ba su iyakance wani abu na iliminsa sai abin da ya so) Shi ne wanda tsarki ya tabbata a gare shi Mai ji Mai gani Masani kuma Gwani,   yana ganin  tafiyan bakar tururuwa  akan sandararren dutse  a cikin dare mai duhu  yana ganin abin da ke damfare da jijiyoyin ta da gudun abinci a cikin  gabbanta  .
  ( Yana da mabudan gaibi ba wanda ya san su sai shi   kuma ya san abin da ke tudu da kogi , ba wani abu da ke faduwa na ganyen itaciya face ya sani ko kwaya a cikin duhun kasa  , ko danyen abu ko busasshe face yana  rubuce a littafi bayyananne )  ba abin da ya kewaye ilimin sa Mala'ika ne na kusa  ko wani Annabi manzo , to, ta yaya  masu duba da bokaye da 'yan tsubbu  za su iyakance ilimin shi ,  wadanda  suke da'awan sanin abin da zai faru nan gaba  Allah madaukakin sarki ya ce :-  (Ba wanda ya san gaibi cikin wanda suke sammai da kasa   face Allah ) .
     (wasi'a kursiyyuhussamawati wal ardi )  kujerarSa ta fi fadin sammai da kasa   abin mamaki da girman Allah  abin bauta maigirma madaukaki  kudurarSa ta bayyana tsarki ya tabbata a gare shi  , idan wannan shi ne girman kujerarSa  na cewa ya fi fadin sammai da kasa  duk da girman sunnan  da girman wanda ke cikin su  to ina ga girman mahaliccin su   da kuma wanda ya kirkire su   , to shi ne;   tsarki ya tabbata a gare shi mai yalwa a iliminSa , kuma mai yalwa a wadatarSa  kuma mai yalwa a falalar sa  da ni'imtarwanSa  da kyautarSa  shi ne kuma mai yalwa a karfinSa da kasaitarSa   kuma shi ne mai yalwa a  ikon sa,   kuma mai yalwa a hikimarSa kuma mai yalwa a gafararSa da rahamarSa .
  To Musulmi  yana bautawa Ubangiji wanda kyautarSa na da yalwa a dukkan komai  ,  falalarSa kuma ta ketare dukkan abin da ake fata  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi umarni   game da rokon mai adu'a ga UbangijinSa   ba tare da ya ga  cewa ya yawaita mishi ba sai ya ce , (idan  dayan ku ya zo roko to ya yawaita domin Ubangijinsa fa ya ke roko).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Idan za ku roki Allah to ku roke shi Aljannar firdausi don ita ce tsaka –tsakin Aljanna kuma mafi daukakanta, kuma samanta Al'arshin Mai rahama yake daga nan ne koramun Aljanna ke bubbugowa).
(Kiyaye su ba zai nauyayi Allah ba) Dukkan wani abu da ke duniya na cikin kiyayewa na Allah ne, shine Alhaafiz kuma Alhafeez) shi ne mai kiyaye ayyukan Mukallafi, kuma shi ne mai kiyaye sharri da cuta da bala'i ga wanda ya so.
Na daga ciki aduar da Annabi ya koyar da mu ita (Ya Allah ka kiyaye ni ta gaba na da ta baya na da ta dama na da ta hagu na, kuma da ta sama na, ina neman tsarinka da kasaitarka da a mini kisan gilla ta kasa ta.)
Allah- Mai tsarki -shi kadan shi ne mai kiyaye mutum in ya kiyaye dokokin Allah ya nesaci abin da ya haramta.
Allah Madaukakin sarki ya ce :(To managartan mata masu bi ne  ga mazajensu masu kiyayewa ne a fakuwa, sabo da Allah ya kiyaye su da yiwa maza wasiyya dasu )
Ayatul kursi : ganima ce ga musulmai kuma ni'ima ce daga cikin  ni'imomin Allah  mafi girma, tana daga cikin zikiri mafi karfi na safiya da maraice , wanda da ita ake samun kiyayewa mai karfi na Allah, game da ita ne manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Duk wanda ya karanta ayatul kursi karshen kowace  sallah ba abin da zai hana shi shiga Aljanna sai mutuwa) kuma idan ka karanta yayin da ka zo barci (Bai zai gushe ba kana samun kariyan Allah kuma  ba wani shaidan da zai kusance ka har ka wayi gari)
HUDUBA TA BIYU
Alokacin da magana ta yawaita kuma tashoshin watsa labarai suka cika da naji ance(kila da kala) to wajibi a kan musulmi shi ne ya auna abin da yake gani da abin da ya ke ji da abin da yake fada bisa mizani na sharia da hankali,idan ka samu kalma da zata kashe fitina ta sanya fata na gari ta kawo zaman lafiya ta karfafi kwanciyan hankali, ta kuma binne balbali ta rufe kofar fitina kuma ta rinjayar da maslahar kasa kuma zata taimaka guri dunkulewar Al'uma ta kuma kiyaye wa jagororin Addini hakkokinsu, to wannan ita ce kalma mai kyau.
To idan kalma na kara wutan fitina ne, ta na gusar da zaman lafiya kuma tana tada balbalin bala'i  tana girgiza aminta da jagororin Addini, tana taba mutuncin malamai tana kawo rarrabuwar al'uma kuma tana cin karo da maslahar kasa, to wannan ita ce kazantacciyar kalma, to binne ta tun tana karama ya fi dacewa, kuma kaurace mata shine tafarki mafi daukaka.
Kasar saudiya tana da gini mai karfi wanda ta kafu a zuciya, taba darajarta kaskanci ne, duk wanda ya yi gaba da ita zai fadi ya kaskanta, yin kokarin kawo mata zaman lafiya da amincin masallatayya biyu masu alfarma,kuma tare Masun da aka nufe ta da su, da karfafa dunkulewarta abu ne na wajibi a sharia, kuma abu ne da ya dace duk wani maihankali ya nema, (To su bautawa Ubangijin wannan daki. Wanda ya ciyar da su daga yunwa, ya amintar da su daga tsoro.)  

الاثنين، 15 أكتوبر 2018

Tsarkake Rai


HUDUBAR MASALLACIN ANNABI  25-1-1440 NA SHAIKH  ABDULLAHI BIN ABDURRAHMAN AL-BUAIJAN
HUDUBAR  FARKO
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga wanda ya halicci zukata ya daidaita su, ya  kimsa fajircewarsu da takawar su, kuma ya wajabta  rabauta ga tsarkake ta, hasara ta tabbata ga wanda ya  biye wa son ransa.
Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunan mu da munanan ayyukanmu, wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, wanda ya batar da shi ba bu mai shiryar da shi,
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, dahir kuma tabbas, kuma na shaida cewa Annabi Muhammad bawan sa ne kuma Manzonsa ne,tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, aminci tabbatacce mai yawa,
Bayan haka, mafi alherin zance shi ne maganar Allah,kuma mafi kyan shiryarwa shi ne koyarwar Annabi Muhammad, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, mafi sharrin al'amura sune fararrunta, kuma dukkan fararrun abubuwa bidi'a ne, kuma dukkan bidi'a bata ce.
Ya ku bayin Allah !
 ina muku wasiyya da ku ji tsoron Allah, da ku yi wa kan ku hisabi, ( ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah kuma rai ya yi dubi ga abin da ya kaddamar don gobe, ku ji tsoron Allah. Lalle Allah masani ne ga  abin da ku ke aikatawa ,)   ALHASHR 18
Ya taron musulmi !
Lalle Allah ya hallici mutum ya sanar da shi fasaha, ya bashi kyautan hankali da harshe, ya nusar da shi hanyoyi  biyu, ya bayyana mishi hanya ko ya gode ko ya butulce.
Ya jarraba shi da kiyayyar rayi da shaidan ya rubuta masa dace  ko tabewa, ya sanya makomansa wuta ko aljanna.
Ya shar'anta  sharia sabo da shi, ya saukar da littatafai ya turo manzanni  suna masu albishir masu gargadi, cikin mutane akwai wanda ya amsa kira ya tsarkaku, duk wanda ya tsarkaka to don kansa, daga cikin su akwai wanda ya juya baya ya ki ya warware, wanda ya warware to don kansa.
Ya jama'ar musulmi!
 Ku sani rai abokin gaba ne kuma mai umarni da mummuna ne,mai yanke tsakani zukata da Ubangiji  masanin gaibi.
Rai a dabi'arsa mai kwadayi ne ga abin  sha'awe sha'awe  da son jin dadi, mai nawa ne gurin da'a  da ayyukan alheri, rai abin hawan shaidan, ne motarsa ne, kuma wasilarsa ne , kuma kayan alatonsa ne, ta hanyarsu ne ake masa biyayya, kuma hujjarsa ne kuma katangarsa ne. (sai iblis ya fada yayin da aka hukunta Al'amari Lalle Allah ya muku alkawari alkawarin  gaskiya ni kuma na yi muku alkawari na karya na saba muku, kuma ba ni da wani karfi  akan ku, sai dai na kira ku ne ku ka amsa min, kada ku zarge ni ku zargi kawunanku) Ibrahim 22
Rai na yawan umarni da mummuna, mai yawan karkata ga son rai  (Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa gaban UbangijinSa ya hana kansa ga barin   soye-soyen rai , to, lallai aljanna ita ce makoma)  kuma ya ce :-(Ase baka ga wanda ya riki abin bautar sa son ransa ba kuma Allah ya batar da shi bisa ilimi ya toshe jinsa da zuciyan sa  ya sanya rufi a ganin sa  to wa zai shiryar da shi bayan Allah ).
    Rai  matattara ce ta alheri da sharri  Allah madaukakin sarki ya ce :-(  Wanda a ka kiyashe shi kwadayin kan sa wadancannin ka su ne hakikanin marabauta)  al hashir aya 8 ,  kuma ya ce:- ( Lallai rayi  mai yawan umarni ne da mummuna ) .
 Ya ku bayin Allah ;
 Lallai Allah yana yiwa zuciya ilhami na alheri da na sharri , kamar yanda Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Da rayukan dan adam da wanda ya daidaita su . kuma ya kimtsa mata fajircin ta da tsoron Allah ) surah asshams aya 7-8 .
 Kamar yanda Allah ya bawa mutum kyautan ji na zahiri , to, haka kuma ya bashi kyautar rayi  wanda ita ce ta tattari basira na ciki  Allah madaukakin sarki ya ce :-(  Bari !  shi mutum malami ne a bisa kansa  ko da zai zo da hanzare-hanzaren sa )
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni zuwa ga haka  sai ya ce:- (Shi laifi shi ne abin da ya sosa a zuciyan ka ka sani mutane su gane shi )
YA KU BAYIN ALLAH:
Lallai rayi na da bukatan kulawa  da sa ido  da tarbiyantarwa  da kuma tsarkakewa da bibiya    sabo da haka ne annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da husaini dan munzir : - (Ka ce ya  Allah ka  kimtsa mini shiriya ta  ka kare ni daga sharrin rayi na )  ya zo a cikin khudubatul haja (  Muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunan mu ).
YA JAMA'AR MUSULMI:
Lallai hanyar kubuta daga sharrin rayi shi ne a tsarkake ta  a bata kulawa  a kuma bibkiye ta ,  kuma hakika Allah ya yi rantsuwa a cikin littafin shi a wurare goma sha daya a jere  bisa ga rabautan  wanda  ya tsarkake  ta  , kuma da hasaran wanda ya turbude ta  sai  ya ce :- (Allah ya yi rantsuwa da rana da hasken walahan ta .    Da wata  idan ya bi ta .     Da wuni idan ya bayyana rana   .     Da dare idan ya lullube ta.    Da sama da  wanda ya gina ta.    da kasa da wanda ya shimfida ta .  Da rayukan dan adam da wanda ya daifdaita ta  kuma ya kintsa mata fajircinta da tsoron Allah.   Hakika wanda ya tsarkake ta ya rabauta.   Hakika wanda ya turbude ta ya tabe.
      Allah ya yiwa muminai baiwa da ni'ima mafi girma sai ya ce : -( Hakika Allah ya yi baiwa  bisa muminai  da ya aiko Manzo a cikin su daga kawunan su  yana karanta ayoyin sa a gare su  yana tsarkake su yana sanar da su alkur'ani da hikima , hakika  su sun kasance gabanin aiko shi  lallai suna cikin bata mabayyani ).
          Allah   ya bada labari kan cewa tsarkake rayi wasila ce  na samun babban rabo da rabauta da aljanna  sai ya ce  : -( Hakika  wanda ya tsarkaka ya rabauta , ya ambaci Ubangijin sa  ya yi  salla ).
      Kuma ya ce :- (Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa gaban UbangijinSa ya hana kansa ga barin   soye-soyen rai , to, lallai aljanna ita ce makoma)  
YA KU BAYIN ALLAH :
 Lallai tsarkake rayuka  bai samuwa  sai da matsayi na  ihsani :-  Kan ka bautawa  Allah kamar kana ganin shi , in kai baka ganin shi to shi yana ganin ka .
 Baya samuwa sai da sabawa son rai  da lazimtar tsoron Allah  kuma bai samuwa sai da sabawa rayi mai umarni da  mummuna , da kyale abubuwa na jin dadin rai da sha'awe-sha'awenta.
To duk mai ciyar da rayi abin da take sha'awa
Tamkar mai ciyar da wuta ne busasshen kirare

To duk wanda  aka datar ya fi karfin zuciyar shi to ya cinma manufa kuma ya habaka rayin sa.    Wanda ya sake mata linzami  sai ta wurga shi  cikin hanyoyi na  halaka.
Duk  wanda ya kauracewa jin dadi zai cinma manufa
Wanda ya dukufa akan ababan jin dadi zai yi nadama
Daukakan rai na cikin tunkude sha'awarta
Cikin  samun abin da yake sha'awa   akwai kaskanci na har abada
Kar ka shagalta sai da abin da zai kawo ma daukaka
Kar ka yarda da halaka ga rai mai tsada
                                                                                                                                                                                                                               
YA KU JAMA'AR MUSULMAI :
Jihadi shi ne kololuwan tozo na musulunci  farilla ne   mafi  girma daga cikin farillai  mafi girman jihadi shi ne jihadin rai  , ku sa mata linzami game da abubuwan jin dadin ta , ku yaye ta daga sha'awe-sha'awen ta , daukakan ta na daga cikin fin karfinta game da sha'awe-sha'awen ta,  kaskancinta da walakantar ta na cikin bata dama game da sha'awanta
 Rayi kamar jariri yake wurin shan nono  in an kyale shi sai ya girma
a kan haka  in an yaye shi sai ya yayu
Ka yaki ranka da shaidan ka saba musu
Idan sun maka  nasiha to ka tuhume su
 Kar ka yi biyayya gare su  suna abokan jayayya ko hukunci
Domin kai dinnan kasan kaidi irin na abokin jayayya  da kuma mai hukunci

Gaba irin na rayi kwatankwacin gaba irin na shaidan ne  kuma hakika Allah ya gargade mu game da musu da'a a cikin alkur'ani ((Amma wanda ya ji tsoron tsayuwa gaban UbangijinSa ya hana kansa ga barin   soye-soyen rai , to, lallai aljanna ita ce makoma).
Allah ya sa muku albarka ni da ku  a cikin alkur'ani.
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya halicci  mutum ya daidaita shi ya girmama shi ya fifita shi , ya kuma kalifantar da shi ya ba shi aminci ,  kuma ya ba shi kiwo  ya daga  darajar shi kuma ya azurta shi  kuma ya masa baiwa ya mar kyauta   .
Tsira da amincin Allah su tabbata ga wanda Allah ya zaba  Annabin mu Muhammad dan Abdullahi   da iyalan sa da sahabban sa da duk wanda ya bi tafarkin sa kuma ya bi shiriyar sa .
 YA JAMA'AR MUSULMI:
Rayi mai yawan umarni ne da mummuna   ita dinnan ta hada yawan zalunci da kuma yawan jahilci, tana yin jiji da kai da kuma nuna girman kai  da kuma hasada da riya   da fushi da kuma  kwadayi ,  da handama da babakere,  da rowa da  kankamo   da tsoron talauci da kuma   da sauran su na daga cututtuka.
    Tsarkake ta  shi ne  a cire mata wadan nan  sifofin  .
   Tsarkake rayi shi ne siffantuwa da kyawawan dabi'u  da kuma kyawawan halaye da laduba irin na shari'a   kamar  kauna  da ikhlasi da hakuri da gaskiya  da kuma kankan da kai  da tsoro da fata  da karamci da kyauta da tuba da istigfari ,  da kuma tuna mutuwa da karewa  da juya baya ga duniya  da fiskantar Allah madaukaki.
  Tsarkake rayi  yana tabbatuwa ta hanyar sabawa son arai da rashin amsa bukatun ta , da kuma yaye ta daga sha'awe-sha'awen ta   da jin dadin ta  da kuma yi mata inkari  da zarginta  Allah madaukakin sarki ya ce: - (Duk wanda  ya tsarkaka ya rabauta  . Ya kuma ambaci sunan Ubangijin shi.  Ya tsarkake  sunan Ubangijin shi mafi daukaka  )
  YA KU BAYIN ALLAH :
Ku yi kokari wurin tsarkake rayuka   kafin mutuwar gaggawa ta zo mu ku  da kuma yin da na sani ,(Ranar da ko wace rai take samun abin da ta aikata  na alheri  abin halartarwa da abin da ta aikata mummuna   tana burin da hakika akwai fage mai nisa ).
     Ku yi kokari wurin tsarkake rayuka  kafin  rayi ya zo ya ce ya hasara na bisa ga sakaci da na yi a sha'anin Allah  ko da kuwa na kasance cikin masu yin isgilanci  ko kuma ta ce  ina  ma da Allah ya shiryar da ni  da na kasance cikin masu tsoron Allah  , ko kuma ta ce ya yin da ta ga azaba  ina ma da  ina da kome sai in kasance cikin masu kyautatawa.
  Ku yi kokari  wurin tsarkake rayuka  kafin a toshe baki ba zai iya yin furuci ba , shaidu za su tsaya abokan jayayya  sune gabbai  kamar yanda Allah ya ce :- ( A yau ne muke yumkewa  bakunan su , hannayen su za su yi mana zance , kafafuwan su za su yi mana magana   za su shaida  bisa ga abin da suka kasance suna aikatawa)
(Ranar da muke tara makiya Allah to su ana kora su  (zuwa wuta). Har yayin da suka zo mana  sai kunnuwan su da idanuwan su da fatun su suka shaida a gare su da abin da suka kasance suna aikatawa ,  za su fada ga fatun su don me kuka yi shaida a kanmu , sai suka ce Allah ne ya furtar da mu  wanda ya furtar da ko wani abu  shi ne ya halicce ku  marrar farko izuwa gare shi ake komawa da ku.   Ba ku kasance kuna buya ga miyagun al'amura  don kunnuwan ku da idanuwan ku   da fatun ku su yi muku mummunar shaida ba, kai dai kun yi zato ne ya yin buyan ku cewa  hakika Allah bai san yawanci daga abin da kuke aikatawa ba , abin da kuke boyewa ba  .  Wancannin ku zaton ku wanda kuka zata ga Ubangijin ku shi ne ya halakar da ku  ku ka zamanto daga cikin tababbu .
   In sun  yi hakuri  to wuta ne makomar su , in suka nemi a yarda da su to su basa daga cikin ababen yarda . )
         Ku yi kokari wajen tsarkake  rayi  kafun  ranan da zai zame a cikin shi ( Ranar da mutum zai gujewa dan uwan shi.    Da uwar sa da Uban sa .   Da matar sa da diyar sa . Ko wani mutum a cikin  su a wannan ranar yana da sha'ani da zai shagalar da shi .
  YA KU BAYIN ALLAH:
Mai wayo shi ne wanda  ya yiwa kan sa hisabi ya yi aiki domin abin da zai zo bayan mutuwa , shi kuma gajiyayye shi ne wanda ranshi ya bi abin da yake so , ya yi ta gurace-gurace a wurin Allah  .
   Ku yiwa kan ku hisabi kafin a yi muku hisabi  ku auna kafin a auna ku  , lallai hakan ya fi saukin hisabi a gobe   idan kuka yiwa kan ku hisabi a yau   kuka yi ado  domin halartowa a wuri mafi girma , a wannan ranar ne za a kawo ku  babu wani mai tsoro a cikin ku .
  Wata rana Umar dan khaddab Allah  ya yarda da shi ya  shiga wani kango sai ya kebanta da ranshi yana mata hisabi  Anas dan Malik Allah ya yarda da shi yana sa mishi ido daga nesa ta inda  baya ganin shi  , sai ya ji umar shugaban muminai  yana cewa  sannu, sannu  na rantse  da Allah ya kai dan Khaddab  ko dai ka ji tsoron Allah ko Allah ya azabtar da kai .
  Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah , ku sani fa zaku hadu da shi
Ya Allah zukatan mu ka bata tsoron Allah
Ya Allah ka daukaka musulunci ga musulmai .