الجمعة، 20 أبريل 2018

sha'aban wata ne na kimtsawa don ramadan


Hudubar juma'a  na Masallacin Annabi tare da sheikh Abdullah Bin Abdurrahman Albu'aijan 4-8-1439AH
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, wanda ya sanya jinjirin – wata  lokuta ne ga mutane da kuma sanin kidayan  zamani, shekaru da watanni , ya sanya dare da wuni  mayau ga wanda ya ke  nufin ya wa'azantu ko ya ke nufin  godiyar    ni'imar  Ubangiji  , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya , ya sanya rana ya zama mai tsananin haske da wata kuma mai haske   na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne  , ya turo shi da shiriya da addini na gaskiya , yana mai albishir da gargadi kuma mai kira  zuwa ga Allah da izinin shi da fitila mai haskakawa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi da aminci tabbatacce mai yawa .
            Bayan haka :
 Lallai zance mafi gaskiya shi ne littafin Allah , mafi kyan koyarwa shi ne koyarwar Annabi  mafi sharrin al'amura shi ne fararrun ta , kuma dukkan fararrun abu bidi'a ne  kuma dukkan bidi'a bata ne  kuma dukkan bata na wuta .
        Bayin Allah :
Ina muku wasiyya da ni kai na da tsoron Allah  mabuwayi da daukaka, domin ita ce wasiyyar mutanen farko  da na karshe  ( Hakika mun yi wasiyya ga wadan da aka bawa littafi  kafin ku da ma ku kanku da ku ji tsoron Allah ).
YA JAMA'AR MUSULMI:
Lallai  Allah na da  wasu yanki na  rahama  to ,  ku yi kokari ku same su  da wasu zamuna na alheri  to ku yi kokari ku same su  da kuma lokuta masu falala ku yi kwadayin riskan su, ga su sun  fiskanto  ku,  to ku fiskance su  ga su sun sauka gare ku to ku ribace su  domin su dinnan wasu lokuta ne kadan  da za su zo su wuce kamar kyabtawan ido,  kaito ga sarayar da rayuwa ga mutumin da  ya sarayar da ita, madalla  kuma da  wanda ya ribace ta  ya yi nasara da ita (Shi ne wanda ya sanya dare da rana mayau ga wanda  yake nufin  ya wa'azantu ko yake nufin godiyar ni'imar Ubangiji ).
                     Rajabu ya shude  to me  ka kaddamar a cikin shi  *** Ga kuma watan   sha'abanu mai albrka   
Ya kaiton wanda ya sarayar da lokuta bisa jahilci *** da alfarmar ta  ka farka  ka kuma kiyaye  albarkoki 
To da sannu  za ka rabu da jin dadi  cikin karfi *** mutuwa kuma  zai sanya ka a kana ki   ka bar gidan ka
Ka yi kokari  ka tuba daga kusakurai ***tuba irin na mai iklasi kuma ka sanya  abun riska
Bisa neman kubuta daga wutar jahima *** mafi alkairi ga ma'abota laifuka shi ne wanda ya yi kokari ya gyara.
YA KU BAYIN ALLAH
Hakika watan sha'abana ya sauka a gare ku, kuma yana cikin lokuta na da'a  da kuma lokuta masu falala,  ana neman alheri a cikin shi  ana daga ayyuka a cikin shi  da ayuka na kusanci , an karbo da Usama Dan Zaid Allah ya kara yarda a gare su da baban shi  ya ce : '' na ce ya  Manzon Allah  ban gan ka kana azumtar wani  wata daga cikin watanni ba kamar yanda  kake azumtar sha'aban''. Sai Manzon Allah ya ce  (Wannan wata ne da mutane ke gafala daga gare shi,  wanda ke tsakanin rajab da ramadana  shi ne watan da ake daga ayyuka a cikin shi  zuwa ga Ubangijin talikai , ina so  kuma a daga ayyuka na  ina mai azumi , an karbo daga Aisha Allah ya kara yarda a gare ta  ce : Manzon Allah ya kasance yana azumi har mu ce ba zai sha ruwa ba , kuma yana shan ruwa har mu ce ba zai yi azumi ba  ban ga Annabi ya cika azumin wani wata ba  sai ramadana  ban ganshi kuma yana yawaita azumi ba kamar yanda yake yawaitawa a sha'aban .
YA KU BAYIN ALLAH
Lalle watan sha'aban fage ne na kimtsawa da shiryawa don fiskantar ramadan, to shi rai na bukatar maimaci da a bi da shi mataki bayan mataki, da shimfida har ya saba da shi, haurawa zuwa sama na bukatar matakala da tsani, rayi kan kwace, jiki kan gaji  kuma mutum ya kosa daga ibada   sabo da ba abi da shi mataki -mataki ba sai ya rasa jin dadin ta  kuma ya rinka haduwa da tsananin ta , ta iya yiwuwa ma ya yanke daga  gare ta  ya kasa cigaba da ita  sai alheri mai yawa ya tsere mishi .
               Ya yin da sha'aban ya kasance  mukaddima  ne ga  ramadan  to ya dace ga musulmi ya dage a cikin ta  irin kokarin da zai yi a ramadan , matsayin azumin sha'abana ga ramadan kamar matsayin sunnonin farilla ne  ga  sallan farilla , azumtar shi na daga cikin shiri ne da kwadayi bisa ga  ramadana daya daga cikin rukunnan musulunci   kuma azumi  na  daga cikin ibadoji  da ake  neman kusanci da shi  da kuma  da'a  da ibada mafi girma,  an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : '' Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ''Allah madaukakin sarki ya ce : ( Dukkan aikin dan adam na shi ne sai azumi  lallai shi nawa ne kuma ni zan sakanya game da shi ).
          (Kuma azumi garkuwa ne  idan dayan ku na azumi  kada ya yi fasikanci   kada ya yi batsa  kada ya yi hayaniya   in wani ya zage shi  ko ya yi fada da shi ya ce ni mutum ne mai azumi .( Na  rantse da wanda ran muhammadu ke hanunsa   warin bakin mai azumi ya fi kamshi a wurin Allah a kan turaren almiski),  ( mai azumi na da farin ciki biyu ; farin ciki yayin shan ruwarsa da kuma  farin ciki yayin  haduwa da Ubangijinsa) .
   YA JAMA'AR  MUSULMI:
Kofofin alheri a bude suke, kuma Allah baya sarayar da ladan wanda ya kyautata aiki  ,ga aiyuka na da'a da suke saki waiwai  ba a kayyade su da zamani ko wuri ba,  nau'ukan ayyukan da'a   suna da yawa  kuma suna fin junan su  gwargwadon lokaci  sai dai  ba wasu ibadoji na da'a da aka kebance  su da watan  sha'aban  sai dai wata ne da ake daukaka ayukan shekara a cikin ta  kamar yanda ake daukaka ayukan mako     a litinin da alhamis  ya dace mutum ya yi kwadayin  ya cika ta , sabo da haka ne Manzon Allah yake  son  azumtar shi , kamar yanda ya ke son azumtar litinin da alhamis .
    Ya jama'ar Musulmi :
Lallai gafala wata cuta ce mai wuyan magani  kuma  abu ne na laifi wanda yake mai zunubi  yana  yanke sila tsakanin bawa da Ubangijin shi ba zai rinka jin wani laifin shi  ba   ko ya yanke daga  alhakin shi ba ,  ba zai tuba daga zunubin shi  ba  ba zai yi wani ma'arufi ba ko ya yi hani ga wani munkari ba   lokutan alheri na ta wuce shi da lokutan falala  alhali yana cikin bacci na gafala  baya farkawa  yana gani baya lura ana mishi wa'azi baya wa'azantuwa ana fadakar da shi baya fadakuwa  hakika Manzon Allah ya kwadaitar game da  azumin sha'aban sabo da gafalan da yawa daga cikin mutane game da shi  sai ya ce  : (  Wancan wani wata ne da mutane suke gafala game da shi  yana tsakanin rajab da ramadana ).
         Ya mai yiwa kan shi nasiha ka gajarta buri  kuma ka farka daga gafalan ka  ka yi shiri don hisabi  kafin zuwan ajali .
      Ina neman tsarin Allah daga shaidan  abin jefewa 
(Ka tsare kanka tare da wadan da suke bautawa Ubangijin su  safiya da maraice suna nufin  fuskan Allah da ibada  ta su  kada ka juyar da idanunka da barin abokantaka ta su , kana nufin kawar duniya   kada ka bi wadan da muka rafkanar da zuciyar sa da barin ambatonmu  ya bi son zuciyar sa  a cikin shirka  al'amarin sa ya kasance faifayi )
Allah ya sa mini albarka ni da ku  a cikin alku'ani
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah , yabon da ya dace da daukakar sa  tsira da amincin Allah su tabbata  bisa ga  zababbe cikin Manzannin sa da Annabawan sa  da iyalan sa da sahabban sa  da mabiyan sa da masoyan sa   .
YA KU BAYIN ALLAH :
 Lallai Allah  bai halicci mutum ba  ya kara mishi a tsawon rayuwa face don ya yi kokari wajen yi mishi da'a kuma ya nesanci saba mishi Allah madaukakin sarki ya ce :(Ban halicci mutum da aljani ba sai don su bauta mini)  Hakika Allah ya fifita wasu sashi na lokuta ya kwaranya musu sauki  da albarkatu da alheri mai busowa, ya shar'anta wasu hukunce-hukunce da ayyuka da kuma da'a, kuma ya yi wa bayin sa izini da su nemi  alheri a cikinta, to ku nemi alheri a dukkan zamaninku,kuma ku kutsa don karbar rahamar Allah, lalle Allah Mabuwayi da daukaka,na da wani yanki na rahamarsa da ke samun wanda ya so da ita daga cikin bayinsa.
Ya Al'uma masu kadaita Allah!
Ku kiyaye akidarku   ku rike ta da  hakwaran cin tuwo   domin ita ce tushen tsiran ku,  ku yi riko da addinin ku da littafin ku da shiryarwan Annabin ku
 YA JAMA'AR MUSULMI :
 Lallai Shaidan makiyi ne a gare ku to,  ku rike shi makiyi  domin shi dinnan yana iya kokarin shi a lokutan alheri da falala don ya batar da mutane daga shiriya ya yi shamaki tsakanin su da yanki na rahama da gafara ya katange su daga da'an Ubangijin su kuma ya sanya alheri mai yawa ya tsere musu  , sai ya batar da wasu sashi na daga  mutane ta hanyar shubuhohi  kamar yanda yake batar da wasu sashi na su ta hanyar   sha'awe –sha'awe  , sai ya fitini wasu mutane ta hanyar bidi'o'i da fararrun abubuwa   ya sarayar musu  da dama na lokutan alheri  ta hanyar bidi'o'i da sha'awe-sha'awe.
 TO YA JAMA'AR MUSULMAI :
(Hakika kuna da abin koyi mai kyau daga Manzon Allah   ga wanda ya kasance yana fatan Allah da ranar lahira )
(kuma duk wanda ya yi wani aiki wanda ba umarnin mu a ciki to an maida mishi )
To ku yi riko da sunna to fa dukkan fararren abu bidi'a ne dukkan bidi'a bata ne kuma   dukkan bata na wuta.
YA KU BAYIN ALLAH :
Duk wanda yake da ramuwa na ramadana a kansa to ya gaggauta azumtar shi  kafin shigowar ramadana  domin lokacin ya matse,  to, wajibi ne ga dukkan musulmi ya gaggauta biya  , ku yi tsere wurin ayukan alheri  ku gaggauta wurin da'a ku yi gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijin ku  da aljanna fadint ya kai kasa da sammai .
                YA KU BAYIN ALLAH
Hakika lallai Allah ya saukar a gare ku mafi daraja cikin littatafai ya kuma aiko muku da mafi daraja cikin manzanni ya cika muku addini kuma ya yarda da shi a gare ku  ya bayyana shi akan dukkan addinai , ya cika ni'ima  sai ya ce :  (A yau na cika muku addininku kuma na cika muku ni'imata a gare ku , na yarda a gare da musulunci a matsayin  addini)
 Hakika mun yarda da Allah shi ne Ubangiji da musulunci shi ne addini  kuma Muhammadu shi ne Annabi kuma Manzo ,
 muna rokon Allah da ya tabbatar da mu da tabbataccen zance  a rayuwan duniya  da kuma lahira , kuma ya  nisantar da fitina daga gare mu na bayyane da na boye ,  kuma ya azurta mu da riko da sunna  kuma ya tunkude mana gafala da tabewa kuma ya datar da mu  a sha'abana kuma ya riskar da mu da ramadana.
 ya  Allah ka daukaka musulunci ga musulmai  

       
      


الجمعة، 6 أبريل 2018

NI'IMAR ALJANNA


Hudubar juma'a na Masallacin Annabi  tare da sheikh Salah bin Muhammad Albudair 20-7-1439 AH.
Hudubar farko:
Ya ku Musulmai ! Ajali na kusantowa, Burace –burace na karewa, duk wani tsani ya yanke, lokacin tafiya da kaura ya zo, ya raba mutum da iyalai da sadawa da su,
Ba na ganin akwai abin da zai sha gaqban mutuwa ya tsallake ta, *
                                                                              Mutuwa ta katse jin dadi ga mawadaci da talaka.
Ka yi dubi ga duniya da idon mai ban kwana, *
                                                                      Domin hakika tafiyar ta kusa lokacin ban kwana ya yi.
Lallai Masoyi abin fizgewa ne daga masoyansa, *
                                                                                          Mai gadi ko mai tsaro bai hana  mutuwa.
Ta yaya zai yi farin ciki da duniya da jin dadin cikinta?*
                                                            mutumin da ana kidanya masa lafuzansa da numfashinsa.
Dukkan wata gida –wata rana-abar rushewa ce *
                                                         Komin dadewarta bisa ginshikinta.

Ya ku musulmai!
Yayin da duniya ta kasance gida ce ta fitintinu da jarabawa to mutum zai dandani wahalar neman abin rayuwa ,da gwagwarmaya da bala'i da cututtuka da nau'uka na musibu, da cin karo da abubuwa masu hanun riga, da kawatarwa irin na shaidan, da ma'abota barna.
Mai kyauta da karamci Mai jinkai,Mai girma ya yi kira ga bayinsa muminai zuwa ga Aljannarsa  gidan karamcinsa  gidan aminci da ni'ima, kubutacciya daga bakin ciki da bacin rai, wanda babu matsaltsalu da tashin hankali da bala'I,(kuma Allah na kira zuwa gidan aminci)
Idan duniya ta ma kunci gabadayanta *** ka zama baka da wani masauki sananne.
To ka yi gaggauto zuwa ga Jannatu Adnin  domin ita dinnan *** Masaukan mu ne na farko kuma cikinta akwai shemomi
sai dai fursunonin yaki ne na Magauda (Makiya) abin mamaki ya jama'a *** shin ko za mu koma gidajenmu mu samu aminci?
Gida ce da ni'imarta bai karewa , bai  halakewa,gidan da akwai dukkan alheri cikinta har da kari, an tanade ta an kusanto da ita an kawata ta domin karramawa ga masu tsoron Allah, ba su jin tsoron wani abu a ciki na bakin ciki ko hayaniya da gajiya,ba su tsoron talauci ko bashi a cikinta,ko fitarwa ko katsewa ko karewa ba. (Ba zaa fitar da su daga cikinta ba).
Duk wanda ya shiga Aljanna ba zai samu wata damuwa ba, tufafinsa ba zai ridddige ya tsufa ba,haka samartansa ba zai tsufa ba, mai yekuwa zai kira su : (lalle za ku samu  lafiya a cikinta ba za ku yi rashin lafiya ba har abada, kuma ku rayu ba za ku mutu ba har abada, kuma ku zama matasa ba za ku tsufa ba har abada, lalle kuma za ku samu ni'ima ba za ku samu wata damuwa ba har abada, sai a ce : Ya ku 'yan Aljanna ku dawwama ba mutuwa har abada, ya ku 'yan wuta ! ku dawwama ba mutuwa,  a cikin Aljanna akwai abin da ido bai taba gani ba, kunne bai taba ji ba,zuciyar dan Adam bai taba hararo shi ba,).
(Mala'iku na shiga musu ta kowace kofa, Amincin Allah ya tabbata a gare ku sabo da hakurin da ku ka yi, madalla da gida mai kyakkyawan karshe).
Allah Mai girma!! Mala'iku na shigo musu,!! Mala'iku su zo musu,Mala'iku  su gaishe su, Mala'iku na taya su murna!!
(To amincin Allah ya tabbata a gare ku, kun ji dadi, ku shige ta kuna masu dawwama.)
Abin mamaki da girman wannan kusancin da girmamawa a gidan aminci.
Lalle Allah Madaukakin sarki zai ce ga 'yan Aljanna,  :( ya ku 'yan Aljanna ! sai su ce : Mun amsa kirarka kuma mun rusuna, sai yace : ko kun gamsu? Sai su ce :  ta yaya ba za mu gamsu ba bayan ka bamu abin da baka baiwa wani ba daga cikin halittunka,sai yace : zan baku abin da ya fi haka.sai su ce Ya Ubangiji me ne ne ya fi hakan?, Sai yace : zan sanya yarda ta a gare ku bayan haka ba zan yi fushi da ku ba har abada).
(Kuma yardar Allah ya fi girma)
Ya fi girma bisa Aljannar da koramanta ya fi girma akan benayenta da tufafinta da guzurinta.
Amma ganin Allah a Aljanna shi ne abin da masu jan damara su ke jan damara akan shi, masu yin munafasa da rige –rige ke tsere a kan shi, ya hana shi ga wadanda aka musu shamaki da Ubangijinsu, kuma aka kore su daga kofarsa, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Wasu fiskoki a wannan rana suna mani'imta ne. masu dubi zuwa  ga Ubangijinsu) Al  kiyama 21-22
An karbo daga Abu Musa Allah kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Gonakai guda biyu na azurfa kwanukansu da abin da ke cikin su,da gonakai biyu na zinari  kwanukansu da abin da ke cikinsu, ba wani abu da yake tsanin mutanen da su ga Ubangijinsu  mai tsarki da daukaka face  rigar girmame –girmame a fiskarsa cikin Aljannar Adni) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
An karbo daga Suhaibu daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :: Idan 'yan Aljanna sun shiga Aljanna Allah Madaukakin sarki zai ce : Ko kuna son wani abu na kara muku? Sai su ce : Allah ba ka haskaka fusakanmu ba ka shigar da mu Aljanna ba kuma ka tseratar da mu daga wuta? Yace sai ya yaye hijabin  sai su ji dadin da  ba a taba basu wani abu da ya fi soyuwa a gare su ba kamar ganin Ubangijinsu  ba Mabuwayi da Daukaka).Muslim ne ya rawaito.
Ibnul Kayyim Allah ya mishi rahama ya ce :  To wannan kenan in ka tambayi ranar kari daga Mabuwayi  Abin godiya, da ganin fiskarsa tsarkakakka daga misali ko kamanci, kamar yadda kake ganin rana lokacin azahar, da kuma wata a daren sha hudu, kamar yadda aka karbo daga mai gaskiya abin gaskatawa,ta hanyoyi  masu dumbin yawa, hakan na nan cikin sahihai da sunann da musnadai, na daga riwayar Jarir da Suhaibu da Anas da Abu Huraira da Abu Musa da Abu Sa'id , Ka saurari ranar da mai kira zai yi kira ? Ya 'yan Aljanna Ubangijinku  zai nemi ziyartarku,, to ku zo , don ziyartarshi,  sai su ce : mun ji mun bi,sai su taso zuwa ga ziyara suna gaggautowa  har lokacin da suka isa kwarinmai fadi  wanda aka sanya musu magama, suka hadu a can ba wani guda da mai kiran ya bari, Ubangiji Allah sai ya yi umarni da a kafa masa kujerar sarautarsa, sai aka kafa, su kuma aka kafa musu  minbarai na haske, da minbarai na lu'ulu'u, da minbarai na zubarjadi, da minbarai na zinari da minbarai na azurfa, mafi karancin daraja a  cikinsu ya zauna,-  duk da ba wani makaskanci cikinsu- bisa wata turbaya na almiski, kuma basu ganin nan kan kujera sun fi su samu kyauta,
Har zuwa lokacin da kowa ya natsu a mazauninsa hankali ya kwanta, sai mai kira ya yi kira,: ya 'yan Aljanna  lalle kuna da wani alkawari a gurin Allah da yake so ya cika muku! Sai su ce : Mene ne shi? Ase ba an haskaka fisakanmu ba,a ka nauyaya mizaninmu ba, aka shigar da mu Aljanna ba, aka nesatar da mu daga wuta ba? Suna cikin haka sai wani haske ya bayyana  wanda Aljanna ta haskaka da shi, sai suka daga kawunansu, sai ga Aljabbaru (kasaitacce) Girmansa ta kasaita, sunayensa sun tsarkaka, ya fuskanto su daga ta samansu,yace : (ya 'yan Aljanna amincin Allah ya tabbata a gare ku) Ba a amsa wannan gaisuwar da sama da fadin cewa : ya Allah kai ne aminci, daga gun ka aminci ya ke, albarka ta tabbata a gare ka,ya Ma'abocin girma da karamci,sai Ubangiji ya yi tajalli a gare su(Ya bayyana) Albarka da daukaka sun tabbata a gare shi, ya musu dariya yace :  Ya 'yan Aljanna ! sai ya zama farkon abin da zasu ji daga gare shi shine : Ina bayi na da suka yi min biyayya a fake bisa halin ba su ganni ba? To wannan ne ranar kari , sai su yi tarayya a kalma guda: Mun yarda to  ka yarda da mu, sai ya ce ya 'yan Aljanna in da ban yarda da ku ba da ba zan saukar da ku a Aljanna  ta ba. Sai yace : wannan ne ranar kari ku roke ni! Sai duk su yi tarayya a kan kalma guda: ka nuna mana fuskar ka mu yi dubi zuwa gare shi, sai Ubangiji  Allah Madaukakin sarki ya yaye shamaki, Daukaka ya tabbata a gare shi, sai ya yi tajalli a gare su, sai ya lullube su da haskensa, sai su manta da duk wata ni'ima da su ka taba gani, badon Allah ya hukunta ba za su kone ba da sun kone, ba wani da zai rage a wannan majlisar har sai ubangiji ya mar lacca kai tsaye, har ma ya ce ya wane ko kana tuna ranar kaza ka aikata kaza da kaza,? Yana tunatar da shi wasu sashi na ha'ince –ha'incen da ya yi a duniya, sai ya ce ya Ubangiji ba ka yafe mini ba? Sai yace ai da gafara tawa ce ka kai wannan matsayin taka da ka ke kai.
Allah Mai girma! Abin mamaki  da girman irin wannan ni'imar, abin mamaki da irin wannan karramawar, zasu ga Ubangijinsu a Aljanna,  za su ga Allah Ma'abocin girma da kyau da kamala, za su ga abin bautan da sun dade suna bauta masa, suna mishi tasbihi,da halala da kabbarori, suka yi mishi  sujada kuma suka girmama shi.
Wani irin dadi ne da jin dadi, wace irin ni'ima ce, wani irin rayuwa ce wani irin walwala ce,wani irin zabi ne, zasu ga Allah wanda duniya  bata yi dadi ba sai da ambatonsa,lahira ma bata yi dadi ba sai da yafiyarsa, haka ma Aljanna ma bata yi dadi ba sai da kallo zuwa gare shi, wayyo kwadayinmu zuwa gare shi, wayyo shaukinmu zuwa ga gidan ni'ima, wacce a cikinta masu kadaita Ubangiji zasu , zai yi tajalli a gare su ya bayyana, kuma yayi dariya agare su,ya fiskanta zuwa gare su, kuma yana bayyana ga 'yan Aljanna a kowace juma'a, cikin wata turbaya na Alkafur sai su kasance kusa da shi gwargwadon gaggawar su zuwa Juma'a a duniya,ba su kara dubi zuwa ga Ubangijinsu sai hakan ya kara musu karama.
Zaka ga fiskar Ubangiji  madalla da fiska da ke cike da kauna da daukaka.
Ya ku bayin Allah!
Wannan dadin labari ina ga dadin ganin?
Ya Allah muna rokon ka dadin dubi zuwa fiskar ka, da kwadayin haduwa da kai, ba cikin wata cuta ko cutarwa ba, ko wata fitina mai cutarwa ba.
Huduba ta biyu
Ya ku musulmai !
Ku kimtsa kayanku ku gaggauta morar rayuwarku  ku ribaci lokacin ku, to me ke baya ni'ima da jin dadi da kawar rayuwa da walwalarta face mutuwa da kare wa da rididdigewa,
Mutuwa kofa ce kuma dukkan mutane zasu shige ta
Me zan ji bayan wannan kofar me ke cikin gidan?
Gidan Aljanna ne na dawwama  muddin ka yi aiki da abin da zai yardar da Allah
In ka gaarta sai wuta, sune gidaje biyu mutane basu da wasu gidan in ba su ba.
To ka duba wa kanka wanne zaka zaba.