Hudubar juma'a na Masallacin Annabi tare da sheikh Abdullah
Bin Abdurrahman Albu'aijan 4-8-1439AH
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah, wanda ya sanya jinjirin – wata lokuta ne ga mutane da kuma sanin
kidayan zamani, shekaru da watanni , ya
sanya dare da wuni mayau ga wanda ya
ke nufin ya wa'azantu ko ya ke
nufin godiyar ni'imar
Ubangiji , na shaida ba abin
bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya , ya sanya
rana ya zama mai tsananin haske da wata kuma mai haske na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma
Manzon sa ne , ya turo shi da shiriya da
addini na gaskiya , yana mai albishir da gargadi kuma mai kira zuwa ga Allah da izinin shi da fitila mai
haskakawa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da
sahabban shi da aminci tabbatacce mai yawa .
Bayan haka :
Lallai zance mafi gaskiya shi ne littafin
Allah , mafi kyan koyarwa shi ne koyarwar Annabi mafi sharrin al'amura shi ne fararrun ta ,
kuma dukkan fararrun abu bidi'a ne kuma
dukkan bidi'a bata ne kuma dukkan bata
na wuta .
Bayin Allah :
Ina muku wasiyya da ni
kai na da tsoron Allah mabuwayi da
daukaka, domin ita ce wasiyyar mutanen farko
da na karshe ( Hakika mun yi
wasiyya ga wadan da aka bawa littafi
kafin ku da ma ku kanku da ku ji tsoron Allah ).
YA JAMA'AR MUSULMI:
Lallai Allah na da
wasu yanki na rahama to ,
ku yi kokari ku same su da wasu
zamuna na alheri to ku yi kokari ku same
su da kuma lokuta masu falala ku yi
kwadayin riskan su, ga su sun
fiskanto ku, to ku fiskance su ga su sun sauka gare ku to ku ribace su domin su dinnan wasu lokuta ne kadan da za su zo su wuce kamar kyabtawan ido, kaito ga sarayar da rayuwa ga mutumin da ya sarayar da ita, madalla kuma da
wanda ya ribace ta ya yi nasara
da ita (Shi ne wanda ya sanya dare da rana mayau ga wanda yake nufin
ya wa'azantu ko yake nufin godiyar ni'imar Ubangiji ).
Rajabu ya shude to me
ka kaddamar a cikin shi *** Ga
kuma watan sha'abanu mai albrka
Ya kaiton wanda ya
sarayar da lokuta bisa jahilci *** da alfarmar ta ka farka
ka kuma kiyaye albarkoki
To da sannu za ka rabu da jin dadi cikin karfi *** mutuwa kuma zai sanya ka a kana ki ka bar gidan ka
Ka yi kokari ka tuba daga kusakurai ***tuba irin na mai
iklasi kuma ka sanya abun riska
Bisa neman kubuta
daga wutar jahima *** mafi alkairi ga ma'abota laifuka shi ne wanda ya yi
kokari ya gyara.
YA KU BAYIN ALLAH
Hakika watan sha'abana
ya sauka a gare ku, kuma yana cikin lokuta na da'a da kuma lokuta masu falala, ana neman alheri a cikin shi ana daga ayyuka a cikin shi da ayuka na kusanci , an karbo da Usama
Dan Zaid Allah ya kara yarda a gare su da baban shi ya ce : '' na ce ya Manzon Allah ban gan ka kana azumtar wani wata daga cikin watanni ba kamar yanda kake azumtar sha'aban''. Sai Manzon Allah ya
ce (Wannan wata ne da mutane ke
gafala daga gare shi, wanda ke tsakanin
rajab da ramadana shi ne watan da ake
daga ayyuka a cikin shi zuwa ga
Ubangijin talikai , ina so kuma a daga ayyuka
na ina mai azumi , an karbo daga Aisha Allah
ya kara yarda a gare ta ce : Manzon
Allah ya kasance yana azumi har mu ce ba zai sha ruwa ba , kuma yana shan ruwa
har mu ce ba zai yi azumi ba ban ga
Annabi ya cika azumin wani wata ba sai
ramadana ban ganshi kuma yana yawaita
azumi ba kamar yanda yake yawaitawa a sha'aban .
YA KU BAYIN ALLAH
Lalle watan sha'aban
fage ne na kimtsawa da shiryawa don fiskantar ramadan, to shi rai na bukatar maimaci
da a bi da shi mataki bayan mataki, da shimfida har ya saba da shi, haurawa
zuwa sama na bukatar matakala da tsani, rayi kan kwace, jiki kan gaji kuma mutum ya kosa daga ibada sabo da ba abi da shi mataki -mataki ba sai
ya rasa jin dadin ta kuma ya rinka
haduwa da tsananin ta , ta iya yiwuwa ma ya yanke daga gare ta
ya kasa cigaba da ita sai alheri
mai yawa ya tsere mishi .
Ya yin da sha'aban ya
kasance mukaddima ne ga ramadan
to ya dace ga musulmi ya dage a cikin
ta irin kokarin da zai yi a ramadan ,
matsayin azumin sha'abana ga ramadan kamar matsayin sunnonin farilla ne ga
sallan farilla , azumtar shi na daga cikin shiri ne da kwadayi bisa
ga ramadana daya daga cikin rukunnan
musulunci kuma azumi na
daga cikin ibadoji da ake neman kusanci da shi da kuma da'a da
ibada mafi girma, an karbo daga Abu
Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : '' Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi ya ce: ''Allah madaukakin sarki ya ce : ( Dukkan
aikin dan adam na shi ne sai azumi lallai shi nawa ne kuma ni zan sakanya game da
shi ).
(Kuma azumi garkuwa ne idan dayan ku na azumi kada ya yi fasikanci kada ya yi batsa kada ya yi hayaniya in wani ya zage shi ko ya yi fada da shi ya ce ni mutum ne mai
azumi .( Na rantse da wanda ran
muhammadu ke hanunsa warin bakin mai
azumi ya fi kamshi a wurin Allah a kan turaren almiski), ( mai azumi na da farin ciki biyu ; farin
ciki yayin shan ruwarsa da kuma farin
ciki yayin haduwa da Ubangijinsa) .
YA JAMA'AR MUSULMI:
Kofofin alheri a bude
suke, kuma Allah baya sarayar da ladan wanda ya kyautata aiki ,ga aiyuka na da'a da suke saki waiwai ba a kayyade su da zamani ko wuri ba, nau'ukan ayyukan da'a suna da yawa
kuma suna fin junan su gwargwadon
lokaci sai dai ba wasu ibadoji na da'a da aka kebance su da watan
sha'aban sai dai wata ne da ake
daukaka ayukan shekara a cikin ta kamar
yanda ake daukaka ayukan mako a
litinin da alhamis ya dace mutum ya yi
kwadayin ya cika ta , sabo da haka ne
Manzon Allah yake son azumtar shi , kamar yanda ya ke son azumtar
litinin da alhamis .
Ya
jama'ar Musulmi :
Lallai gafala wata cuta
ce mai wuyan magani kuma abu ne na laifi wanda yake mai zunubi yana
yanke sila tsakanin bawa da Ubangijin shi ba zai rinka jin wani laifin
shi ba
ko ya yanke daga alhakin shi ba
, ba zai tuba daga zunubin shi ba ba
zai yi wani ma'arufi ba ko ya yi hani ga wani munkari ba lokutan
alheri na ta wuce shi da lokutan falala
alhali yana cikin bacci na gafala
baya farkawa yana gani baya lura
ana mishi wa'azi baya wa'azantuwa ana fadakar da shi baya fadakuwa hakika Manzon Allah ya kwadaitar game da azumin sha'aban sabo da gafalan da yawa daga
cikin mutane game da shi sai ya ce : ( Wancan wani wata ne da mutane suke gafala game
da shi yana tsakanin rajab da ramadana
).
Ya mai yiwa kan shi nasiha ka gajarta buri kuma ka farka daga gafalan ka ka yi shiri don hisabi kafin zuwan ajali .
Ina neman tsarin Allah daga
shaidan abin jefewa
(Ka tsare kanka tare
da wadan da suke bautawa Ubangijin su
safiya da maraice suna nufin
fuskan Allah da ibada ta su kada ka juyar da idanunka da barin
abokantaka ta su , kana nufin kawar duniya kada ka bi wadan da muka rafkanar da zuciyar
sa da barin ambatonmu ya bi son zuciyar
sa a cikin shirka al'amarin sa ya kasance faifayi )
Allah ya sa mini
albarka ni da ku a cikin alku'ani
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah , yabon da ya dace da daukakar sa tsira da amincin Allah su tabbata bisa ga
zababbe cikin Manzannin sa da Annabawan sa da iyalan sa da sahabban sa da mabiyan sa da masoyan sa .
YA KU BAYIN ALLAH :
Lallai Allah
bai halicci mutum ba ya kara
mishi a tsawon rayuwa face don ya yi kokari wajen yi mishi da'a kuma ya nesanci
saba mishi Allah madaukakin sarki ya ce :(Ban halicci mutum da aljani ba sai
don su bauta mini) Hakika Allah ya
fifita wasu sashi na lokuta ya kwaranya musu sauki da albarkatu da alheri mai busowa, ya
shar'anta wasu hukunce-hukunce da ayyuka da kuma da'a, kuma ya yi wa bayin sa
izini da su nemi alheri a cikinta, to ku
nemi alheri a dukkan zamaninku,kuma ku kutsa don karbar rahamar Allah, lalle
Allah Mabuwayi da daukaka,na da wani yanki na rahamarsa da ke samun wanda ya so
da ita daga cikin bayinsa.
Ya Al'uma masu
kadaita Allah!
Ku kiyaye akidarku ku rike ta da hakwaran cin tuwo domin ita ce tushen tsiran ku, ku yi riko da addinin ku da littafin ku da
shiryarwan Annabin ku
YA JAMA'AR MUSULMI :
Lallai Shaidan makiyi ne a gare ku to, ku rike shi makiyi domin shi dinnan yana iya kokarin shi a lokutan
alheri da falala don ya batar da mutane daga shiriya ya yi shamaki tsakanin su
da yanki na rahama da gafara ya katange su daga da'an Ubangijin su kuma ya
sanya alheri mai yawa ya tsere musu ,
sai ya batar da wasu sashi na daga
mutane ta hanyar shubuhohi kamar
yanda yake batar da wasu sashi na su ta hanyar
sha'awe –sha'awe , sai ya fitini
wasu mutane ta hanyar bidi'o'i da fararrun abubuwa ya sarayar musu da dama na lokutan alheri ta hanyar bidi'o'i da sha'awe-sha'awe.
TO YA JAMA'AR MUSULMAI :
(Hakika kuna da abin
koyi mai kyau daga Manzon Allah ga
wanda ya kasance yana fatan Allah da ranar lahira )
(kuma duk wanda ya
yi wani aiki wanda ba umarnin mu a ciki to an maida mishi )
To ku yi riko da sunna
to fa dukkan fararren abu bidi'a ne dukkan bidi'a bata ne kuma dukkan bata na wuta.
YA KU BAYIN ALLAH :
Duk wanda yake da
ramuwa na ramadana a kansa to ya gaggauta azumtar shi kafin shigowar ramadana domin lokacin ya matse, to, wajibi ne ga dukkan musulmi ya gaggauta
biya , ku yi tsere wurin ayukan
alheri ku gaggauta wurin da'a ku yi
gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijin ku
da aljanna fadint ya kai kasa da sammai .
YA
KU BAYIN ALLAH
Hakika lallai Allah ya
saukar a gare ku mafi daraja cikin littatafai ya kuma aiko muku da mafi daraja
cikin manzanni ya cika muku addini kuma ya yarda da shi a gare ku ya bayyana shi akan dukkan addinai , ya cika
ni'ima sai ya ce : (A yau na cika muku addininku kuma na cika
muku ni'imata a gare ku , na yarda a gare da musulunci a matsayin addini)
Hakika mun yarda da Allah shi ne Ubangiji da
musulunci shi ne addini kuma Muhammadu
shi ne Annabi kuma Manzo ,
muna rokon Allah da ya tabbatar da mu da
tabbataccen zance a rayuwan duniya da kuma lahira , kuma ya nisantar da fitina daga gare mu na bayyane da
na boye , kuma ya azurta mu da riko da
sunna kuma ya tunkude mana gafala da
tabewa kuma ya datar da mu a sha'abana
kuma ya riskar da mu da ramadana.
ya
Allah ka daukaka musulunci ga musulmai