الجمعة، 23 مارس 2018

KABARI MASAUKIN FARKO NE NA LAHIRA


Hudubar juma'a  na Masllacin Annabi na Shaikh Abdulbari Subaiti 6/7/1439 AH
Hudubar Farko:
Tafiyan Mutum a wannan rayuwa   masaukanta na sabunta , marhalolinta na jujjuyawa , yana rayuwa ne na wasu matakai a cikin mahaifiyar sa  sannan da wasu matakai a doron kasa , da wasu matakan kuma a cikin kasa har zuwa a tashe shi.
          Wannan tafiyan tana da tsawo a zahirinta  sai dai tana da saurin gushewa ,  kuma  tana da saurin karewa da tafiya,  to ita duniya ba gidan zama ba ne ga rayayye, mai hankali zai tuna irin jujjuyawa da take da shi  da saurin karewan shekaru,  sai ya ratsa jikin   zuciyan shi ta  tausasa .
           Masaukin da baya  yiwuwa ga ko wani matafiyi sai ya sauka gare shi  wata rana shi ne kabari   , kuma lallai  ya isa abin wa'azi a  gare shi , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya  ce : (Lallai kabari na da wata matsa  wanda da a ce dayan mu zai kubuta daga gareta  da  Sa'ad Dan Ma'azu ya kubuta daga gare ta ).
      An karbo  daga Amirul muminina  Usman Dan Affan  Allah ya kara yarda a gare shi ya kasance idan ya tsaya a wurin kabari  sai ya yi ta kuka har gemun shi ya jika da hawaye , sai a ka ce da shi  kana tuna aljanna da wuta amma ba ka kuka amma in ka tsaya a wurin kabari sai ka yi kuka    , sai ya ce na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa  : ( Kabari shi ne farkon masaukan lahira  idan mutum ya tsira daga gare shi to abin da zai biyo baya ya fi sauki  a gare shi, idan kuma bai tsira ba to abin da zai biyo baya ya fi tsanani a gare shi ).
                  Yana daga cikin rukunnan imani da ranar lahira akwai kudurtawa da hakikanin imani da kabari , imani da ni'iman kabari ga ma'abota da'a da kuma   azabar kabari ga  wadan da suka cancanta ma'abota sabo  da fajirci,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Badon kada ku ki binne mamatan ku ba da na roki Allah ya jiyar da ku daga azabar kabari na daga abin da na ke ji ).
Ziyaran kabari don daukan izina da wa'azantuwa sunna ce kuma kusanci ne, wanda ya ziyarci kabari zai tuna wadannan matattu wadanda kakaninsa ne da iyayensa, sai ya sakankance cewa zai mutu a binne shi kamarsu, kuma zaa tambaye shi a kabarinsa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( ku ziyarci makabarta zai tunatar da ku lahira).
                      Idan an binne mutum a kabarin shi  iyalan shi da dukiyan shi suka bada baya farkon maziyartan shi su ne mala'iku guda  biyu su mishi jarabawa,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (  Lallai idan an sanya mamaci a kabarinsa zai ji sautin takalman su lokacin da suke bada baya   idan ya kasance mumini ne sai salla ta kasance ta kansa azumi ta kasance ta damansa , zakka kuma ta hagunsa,  zai  kasance ayukan  da yake aikatawa na alheri  na daga sadaka da salla da ma'arufi da kyautatawa mutane a ta kafan sa , sai a zo ta kansa sai salla ta ce tanan ba gun shiga zai a je  ta daman sa sai azumi ya ce ta guna ba mashiga  sai a zo ta hagun sa sai zakka ta ce  ba wani mashiga ta guna  sai a zo ta bangaren kafafuwan sa  sai ayukan alkairi   na daga sadaka da  ihsani da kyautatawa mutane  su ce ba mashiga ta guna  sai  a ce da shi zauuna , sai ya zauna  sai a suranta mishi rana tana kusan faduwa  sai a ce da shi ko ka ga wannan  da ke fiskantar ku me za kace  game da shi  me za ka shaida kuma game da shi ? sai ya ce ku barni na yi salla , sai a ce da shi, ai za ka yi amma bamu labarin a bin da muka tambaye ka game da shi ,  ka ga mutumin nan da ke ta fiskar ka me za ka ce game da shi kuma wacce shaida za ka masa? Sai yace : Muhammad, ne, kuma na shaida shi           Manzon Allah ne, kuma yazo da gaskiya daga Allah  ,  sai a ce da shi : akan haka ka rayu, kuma a kan haka ka mutu , kuma a kan haka za a tashe ka in Allah ya yarda , sai a bude mishi kofofi n Aljanna  sai a ce da shi  nan ne masaukin ka a cikinta da abinda Allah ya tattala maka a ciki  sai ya kara jin kaimi da farin ciki  , sa'annan sai a bude mishi kofofin wuta  sai a ce da shi ka ga wannan  shi ne masaukin ka da abin da Allah ya tattala maka a ciki da ka saba mishi , sai ya kara kaimi da farin ciki  sannan sai a buda mishi a kabarin shi   zira'i  saba'in  a haskaka mishi ciki  a maida jikin shi kamar yanda aka fare shi , sai a sanya ruhinsa a cikin wani iska mai dadi  wato wani tsuntsu ne ke shawagi akan itaciyar aljanna  wannan shi ne fadin Allah madaukakin sarki  ( Allah yana tabbatar da   wadan da suka yi imani da magana tabbatacciya  a cikin rayuwar duniya   da cikin lahira kuma Allah yana batar da azzalumai ).      Lallai kafuri  in anzo ta fiskan shi ba za a samu komai ba , in anzo ta daman shi ba za a samu komai ba in anzo ta hagun shi ba za a samu komai ba sai a zo ta kafafuwan shi ba za a samu komai ba  sai a ce da shi zauna sai   ya  zauna  cikin tsoro  da firgici, sai a ce da shi  ba ka  ga wancan mutumin da ya kasance a cikin ku ba me za ka ce game da shi kuma wacce shaida za ka  yi akansa , sai ya ce wani mutumi?  Ba zai ma gane sunan shi ba  sai a ce da shi Muhammad      sai ya ce ban sani ba  na ji dai mutane suna cewa wani magana sai ni ma na fada  kamar yanda suka  ce, sai a ce da shi  a haka ka rayu kuma ahaka ka mutu kuma akan haka za a tada  in sha Allahu, sai a bude mishi kofa daga   cikin kofofin wuta sai a ce da shi wannan ne masaukin ka na daga wuta  da abin da Allah ya tanada maka na daga cikinta ,   sai ya kara bakin ciki da hasara  , sannan a bude mishi kofa daga cikin kofofin Aljanna   ace da shi, wannan masaukin ka ne a cikin ta da abin da Allah ya tattala maka  da ka mishi biyayya,  sai ya kara bakin ciki da hasara  sai kabarin shi  ya kuntata a gare shi  har  kasusuwan hakarkarin shi su shiga junan su.
               Wannan ita ce rayuwa ta kunci wanda Allah ya ambata ( To lallai ne rayuwa mai kunci ta tabbata  a gare shi ,  kuma muna tayar da shi a ranar kiyama yana makaho ) Dabarani ne ya rawaito da Ibn Hibban a sahihin sa .
       Mai hankali  zai shirya ne kafin mutuwa ya kimtsa wa kabarinsa don kansa,  ya raya ta, ta hanyar ayuka na kwarai  da imani  don ya kasance yana da dausayi daga cikin dausayin Aljanna Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Yana daga cikin abin da zai riski mumini   bayan mutuwan na daga aikin shi da kyawawan aikin sa ,    ilimi da ya ilmantar kuma  ya  yada shi   ,  da Da na kwarai da ya barshi , da Alkur'ani da ya gadar da shi ko masallaci da ya gina ,  ko kuma gida da ya gina na 'yan tafarki , ko korama  da ya buda ya gudana , ko sadaka da ya fitar daga dukiyar shi ,  a halin yana mai lafiya yana raye  zai riske shi  bayan mutuwar sa .'
     Wanda ke yawan  tuna mutuwa  zai raya kabarin sa da kyawawan ayuka, domin ya sani bisa yakini , lallai shi ya sani idan ya wayi gari ba zai yi yammaci ba  , idan kuma ya yi yammaci  ba zai jira wayan gari ba  sai ya yi gaggawa zuwa ga ibada kafin a yi shamaki tsakanin shi da ita , ga Amr  dan As  yana ganin mamaci an binne shi sai yayi sauri ya tafi masallaci ya yi salla raka'a biyu, sai aka ce da shi me ya sa ka yi haka ?,  sai ya ce makabarta ta tuna min fadin Allah ( Sai aka yi   shamaki  tsakanin su da abin da suke sha'awa  ).
     Sai na sha'awi salla kafin a yi shamaki tsakani na da ita , wanda yake son aboki a kabari wanda zai debe mishi kewa, ya haskaka mishi kabarin shi  ya tafiyar mishi da kadaici to ya riki Alkur'ani .
     Yana daga cikin sabuba na tsira   daga fitinan kabari da azabar sa, dauwama akan karanta suratul mulk, da aiki da abin da ta hukunta .  An  karbo daga Dan Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce :  (Za a zo wa mutum a cikin kabarinsa sai a zo  ga kafansa sai kafofin sa  su ce :   ba ku da wata dama ko kofa ta fuskar mu ya kasance yana tsayuwa da mu  ya karanta suratul mulk sannan sai a zo ta kirjin sa ko ta cikin sa ,  sai ya ce  ba ku da wata dama ta bangare  na a kan shi ya kasance da ni yake karanta suratul mulk  sannan a zo ta kasan sa sai ya ce  baku da wata kofa  akan shi game da ni ya kasance da ni yake karanta suratul mulk  ,  sai ya ce : ita ce  mai hani, tana hani  daga azaban kabari  tana cikin attaura suratul mulk   wanda ya karanta ta a dare to hakika ya yawaita kuma  tsawaita )  Hakim ne ya rawaito shi a mustadrak ya ce ingantacce ne amma(Bukhari da Muslim) basu fitar da shi ba  Albani  ya  inganta shi  
                 Istigfari ga muminai da musu adu'a zai tabbatar da al'amarin ka a kabari yayin tambaya  , Manzon Allah tsira  da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance in ya binne mamaci  sai ya tsaya gaba gare shi sai ya ce ku nemawa dan uwan ku gafara  kuma ku roka mishi tabbatuwa domin   yanzu za a tambaye shi  , mutanen kwarai na raya  kaburburan su ne ta hanyar lazimtar adu'o'i a ko wace salla, suna  neman tsari  daga fitinan  kabari , Annabi ya kasance yana adu'a Ya Allah ina neman tsarin ka daga azaban kabari da azabar wuta ,  da fitinar rayuwa da ta mutuwa,  da fitinan  masihuddajjal).

      HUDUBA NA BIYU
Musulmi mai hankali yana kiyaye wa daga guraren fitina da halaka,wanda ke lalata al'umarsa kuma ya fitine shi a kabarinsa, na daga ciki akwai yada karerayi da sadar da su, ya zo a hadisin Isra'i da Mi'iraji mai tsawo Jibrilu ya ce da Manzon Allah ( amma shi  mutumin da ka zo mi shi ana keta mukamukin sa  zuwa keyan sa ,  da hancin sa zuwa keyan sa da idanuwan sa  zuwa keyan sa , to lallai mutum ne yana wayan gari daga gidansa sai ya yi karyan da za ta bazu a duniya  ,  yana daga ciki kuma akwai cin riba da halatta shi    ya zo a hadisin isra'i da mi'i raji , amma mutumin da ka zo mi shi  yana iyo a korama yana hadiye duwatsu to  lallai shi maciyin riba  ne )  .
    Yana daga ciki mutumin da yake bacci ya bar sallan farilla da me kauracewa kur'ani , to a cikin hadisin isra'i da mi'iraji ( Amma mutumin da ka zo mishi yana dandaka kansa da dutse shi ne mutumin da yake daukan kur'ani ya yi watsi da shi , ya yi bacci kuma daga sallan farilla).
Yana daga cikin sabuba na azaban kabari yawo a tsakanin mutane da annamimanci da yin sake wurin tsarki , manzon Allah ya wuce wasu kaburbura  guda biyu sai ya ce :( Lallai su dinnan ana azabtar da su ne kuma ba akan wani abu mai girma ba ake azabtar da su, amma dayan su ya kasance ba ya tsarkaka daga fitsari, shi kuma dayan yana yawo da annamimanci).Sahihul Jami'i:  Albani.      
   

السبت، 17 مارس 2018

GARGADI A KAN ZUNUBAI DA SABON ALLAH


Hudubar Juma'a na Masallacin Annabi na shaikh Abdullah Dan Abdurrahman Al-Buaijan 21-6-1439 AH.

HUDUBAR FARKO :
  Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin sarki,  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa ,  kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne, Allah ya turo shi don rahama ga  talikai, sai ya buda zukata, ya haskaka hankula da shi, ya buda makantattun idanuwa da shi, da kuraman kunnuwa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa  da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa har zuwa ranar sakayya .
Bayan haka :
Lalle da'a ita ce bin Allah sau da kafa  da biyayya ga Manzo, sabo kuma shi ne sabawa Allah da kirkiran bidio'i, mafi sharrin al'amura ita ce bidi'a da fararrun al'amura, da laifuka da abin da aka ki, mafi muninsu shine  sha'awe –sha'awe da shubuhohi.
Ku bi Allah cikin umarninsa , ku hanu game da abin da ya hane ku ya tsawatar,(ya ku wadanda suka yi imani ku bi Allah da takawa, a kan hakkin binsa da takawa, kuma kada ku mutu face kuna musulmai)
Ya ku bayin Allah!
Lalle Allah ya halicci mutum ya ba shi kyautan hankali da harshe,ya bashi sharia ya sanar da shi bayani, ya turo manzanni da hujjoji ya saukar da littafi da mizani, ya kaddara mutuwa da rayuwa, don ya gwada ku ya ga wanda ya fi kyan aiki .
Ya halicci mutum don ya mishi biyayya da zai haifar da yardarsa, ya hane shi ga  saba mishi da zai haifar da fushinsa, (To wanda ya aikata wani aiki gwargwadon nauyin zarra na alheri zai gan shi. kuma wanda aikatagwargwadon nauyin zarra na sharri zai gan shi ).
Ya sanya duniya gida na aiki da jarrabawa, ya rubuta mata karewa, gidan lahira kuma gidan hisabi da sakayya,ya rubuta mata dauwama da wanzuwa,(To wanda ya yi aiki na kwarai don kansa,wanda ya munana don kansa)
Ya tattalawa masu takawa  gidajen Aljanna, koramai na gudana daga karkashinsu,suna madauwama a cikinta har abada. Cikinta akwai abin da ido bai taba gani ba, kunne bai taba ji ba, bai kuma taba fadowa ga zuciyan wani dan 'adam ba, ya tanada, ya tanadawa kafurai wutan jahannama, ba ta ragewa kuma ba ta bari, mai nacewa ga jiki ce da kuna, suna masu zama a cikinta na wasu zamuna, ba su dandanar wani sani sanyi ko abin sha, face tafasasshen ruwa da rubabben jini, sakamako mai dacewa.
Kowani rai mai dandanar mutuwa ne, kuma ana cika muku ladanku ne a ranar Alkiyama, to wanda aka nesantar daga barin wuta kuma aka shigar da shi Aljanna to lalle ne ya tsira, kuma rayuwar duniya bata zama ba face jin dadin rudi.) Ali – Imran 185
Ya ku bayin Allah !
Lalle dan'adam ana jarraba shi da sha'awa da shubuhohi, yana tunkuduwa cikin jin dadi da hutu, ana jarabta shi da zunubai, da munanan laifuka, hakika makiyansa sun yi hayan masa da abokan fadansa, shaidan abokin tafiyansa ne kuma makiyinsa ne, makiyyinsa ne mai tsananin jayayya, ga rai mai yawan umarni da mummuna, kuma tana cikin jiki, ga gabbai masu musu ne kuma shaidu.
Hakika shaidan ya yi rantsuwa  ( sai ya ce :To ina rantsuwa  da buwayarka sai na batar da su gaba daya. Face bayinka tsarkakku daga gare su )Sad 82
Ya kuma bamu labari game da rai sai ya ce :    (Lalle rai mai yawan umarni ne da mummuna)Yusuf  52
Game da gabbai sai yace : ( A ranar da harsunansu zasu yi shaida akansu da hannayensu da kafafuwansu da abin da suka kasance suna aikatawa) Annur :24
(kuma suka cewa fatunsu don me kuka yi shaida akanmu? Suka ce Allah wanda ke sanya ko wani abu yayi furuci shi ne ya sanya mu mu yi furuci kuma shi ne ya halitta ku can da farko kuma zuwa gare shi za ake mayar da ku. Baku kasance kuna sani ba a boye cewa jin ku zai yi shaida a kan ku kuma ganinku zai yi,kuma fatunku zasu yi, kuma amma kun yi zaton Allah bai san abubuwa masu yawa daga abin da ku ke aikatawa ba,)
To shaidan na ingizawa zuwa ga sabo da laifuka masu halakarwa, rayi na umarni da munana da abin da aka ki, gabbai shaidu ne masu tabbatarwa, mai wayo shi ne wanda  ya yi wa kansa hisabi ya mata linzami don kar ya auka ga zunubai.
Ya ku musulmi!
Lalle aikata zunubai  da laifuka akwai cutuwa da kuma barna a ciki da ke haifar da fushin Allah da ukubarsa, da azabarsa, kuma yana janyo  saukar azabarsa da bala'insa. (kuma da yawa daga alkarya wadda ta yi tsaurin kai daga barin umarnin Ubangijinta da Manzanninsa, sai muka yi mata hisabi,hisabi mai tsanani, kuma muka azabtar da ita, azaba abar kyama. Sa'annan ta dandana masifar al'amarinta , kuma karshen al'amarinta ya kasance hasara. Allah ya musu tattalin wata azaba mai tsanani, sabo da haka ku bi Allah da takawa ya ma'abota hankula ).Dalak 8 -9.
To abin da ke faruwa ga musulmai na fitintunu da musibu  masu radadi da jarabawa da tsadan kaya da mulka irin na makiya, da fari da fako,da cututtuka da yunwa da bala'i  ba wani abu ya haifar da shi ba face sabon Allah da laifuka da zunubai, da abin ki.
Hakika Allah ya buga misali ga mai lura ya koro ayoyi ko akwai mai wa'azantuwa, ya bayyana  cewa zunubai da laifuka na daga mafi girman sabuba na gushewar ni'ima da saukar azaba, sai Allah ya ce :(kuma Allah ya buga misali, wata Alkariya ta kasance amintacciya natsatsiya  arzikinta yana je mata a wadace daga kowane wuri,sai ta kafurta da ni'imomin Allah sabo da haka Allah ya dandana mata tufafin yunwa da tsoro, sabo da abin da suka kasance suna sana'antawa, ). Annahl 112
To Abin mamaki ga  walakancin halitta a gun Allah Mabuwayi idan an saba umarninsa.
Ya ku bayin Allah!
Lalle hadarin sabo na girmama kuma ukubanta na kasaita da musibanta  idan aka wayi gari mutane sun saba da ita suna bayyana ta a fili jama'a na fito na fito da Allah, kuma dukkan al'uma na samun kubuta daga sabo banda masu bayyanawa, mutane ba za su halaka ba sai an basu hanzari akansu.
Ya ku bayin Allah!
Lalle bayyana sabo wani nau'i ne na watsi da hakkin Allah da bushewar  ido gare shi, da ja da mumunai da kara yawan masu sabo,da  kuma isar shi gurbin   sabon ne zuwa  ga wani,
Kuma da zamewa sababi na janyo su gare shi da kwadaitar da su, da kuma kasancewa  sababin sanya zunubai ga wanda bai yi inkari ba(hani ba). Duk wanda aka jarabce shi da wasu sabo to ya boye da boyewar da Allah ya mishi, kuma ya tuba zuwa ga Allah tuba na gaskiya.
Ya ku Musulmai!
 Lalle dogewa a kan zunubai  da sake jiki cikin aikin sabo, da dulmuya cikin laifuka da murna da su,da bushewan ido cikinta, da aminta daga makarkashiyar  Allah,da rena laifuka, abu ne da ke shelanta gafala da janyo fushin Allah, kuma sababi ne na tabewa da halaka, An karbo daga  Abdullahi dan Mas'ud Allah kara yarda a gare shi, yace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : ku kiyayi rena kananan laifuka, domin su ne ke taruwa  akan mutum har su halaka shi, lalle Annabi ya buga misali game da su yace kamar mutane ne suka sauka jeji sai lokacin dafa abincin su ya yi, sai mutum ya je ya kawo kirya, wani mutum ma ya dauko kirya,har suka hada taru mai yawa, sai suka hura wuta suka dafa abinda suka jefa a  ciki). Ahmad ne.
Musiba na girmama  ga mai laifin idan ya ga kananan zunubai abin renawa an kididdige su,sun habaka ,sai ya firgita ya  ce :(Kaitonmu mene ga wannan littafi ba ya barin karama kuma ba ya barin babba face ya kididdige ta,to kuma suka sami abin da suka aikata halarce, kuma ubangijinka ba ya zaluntar kowa.)
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya  sun tabbata ga Allah da yake gafarta zunubai, ya suturce aibi, ya yaye bakin- ciki, yana shinfida hannayensa da dare ga masu laifin wuni don su su tuba,kuma yana shimfida hannayensa da rana ga masu laifin dare don su tuba su koma.
Ya ku bayin Allah! Ku ji tsoron Allah kada ku aikata zunubai kada ku rena shaninsu,  ku kankantar da su, ba abin da ya fi a gare ku, ku hadu da Allah da shi kamar karancin laifuka.
Ya jama'ar musulmi!
Lalle hadarin zunubai na kanzaga kuma yana tada hankali,bala'inta da musibanta  na girmama na tsoratarwa, idan ta zama abu sananne mutane suka  tabbatar da ita, baa umarni da kyakkyawa ko hani ga mummuna,  Allah Madaukakin sarki ya ce : An la'ani wadanda suka kafirta daga  banu Isra'ila, akan harshen Dauda da Isa da maryam, wannan kuwa sabo da sabawar da suka yi ne, kuma sun kasance suna ta'adi.sun kasance ba su hana juna daga abin ki, wanda suka aikata,hakika abin da suka kasance suna aikatawa ya munana.)
An karbo daga Abi bakra Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ;Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle mutane idan sun ga munkari basu canja ba to suna kusa da Allah ya game su da azaba daga gare shi.).
Umarni da kyakkyawa da hani ga mummuna na daga cikin dabia ta al'umar Muhammadu, kuma aminci ne daga saukar bala'i, kuma katanguwa daga  kaidin makiya da wawaye ,Allah Madaukakin sarki ya ce: Ku kasance, Allah ya yi umarni da shi ya kwadaitai a inda ya ce.(A cikinku a samu wata al'uma suna kira zuwa ga Alheri suna umarni da kyakkawa , suna hani da mummu ,  to lalle wadannan sune masu rabauta)
Ya Al'umar Muhammada ku yi umarni da kyakkya wa , ku hana munkari, Duk wanda , ya ga abinki to ya canza shi da hanunsa, idan ba zai iya ba to ya sanja shi da hannunsa,in ba zai iya ba da harshensa, idan bai iya ba da zuciyarsa, idan bai iya ba da zuciyarsa, wannan shine mafi raunin imani)
Ya ku bayin Allah!
Lalle ku din nan abin tambaya  ne  game da gidajenku da abin da aka ba ku kiwo,to ku ji tsoron Allah cikin 'ya'yanku da matayenku, ku sanar da su shariar Allah, kuma ku hana su fadawa ga abin da Allah ya haramta, ku tarbiyantar da su bisa halaye masu kyau da kyakkyawan dabiu, domin lalle zaa tambaye ku game da su gobe gaba ga Allah, kuma zasu zama shaidu akan ku, kuma zaa rubuta shaidar su kuma zaa tambaye su, a ranar da mai laifi zai yi fatan a fanshe shi daga azabar wannan rana da 'ya'yanan sa, da matarsa da dan'uwansa,  da danginsa da suke tattara shi,da wanda ke cikin duniya duka gaba daya sa'annan fansar ta sirar da shi.
Ku kula da abin da aka baku kiwo, kuma  (kada ku yaudari Allah, da Manzonsa, kuma ku yaudari amanoninku, alhali kuwa kuna sane. Kuma ku sani cew abin sani kawai dukiyoyinku da 'ya'yanku wata fitina ce, kuma lalle ne Allah a wurinsa akwai lada mai girma).
Ba wani mutum da Allah zai bashi kiwon wani abin kiwo,  ya zama ya zambace su, face Allah ya haramta Aljanna a gare shi.
Wanda ya yi kokari wurin gyaran mutanen gidansa, ya tsaida shariar Allah  a cikin abin da aka bashi kiwo,ya dasa musu imani a cikin zukatansu, zai kasance yana da lada kwatankwacin aikin da suka yi, ba tare da an tawaye wani abu na daga ladansu ba.
Ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce : (Idan dan'adam ya rasu ayyukansa zasu katse sai guda uku daga ciki akwai :Da na kwarai da  ya ke mishi adu'a ).
Ya jama'ar musulmai!
Lalle koyi da yammaci ya fadada, ya kutsa gidaje, da na'urori da hanyoyin sadarwa, sun rusa kyawawan halaye sun bata dabiu na kwarai , an wayi gari abin ki (MUNKARI) a jiya ya zama  shine  abin so (MA"ARUFI), abin da ya ke ma'arufi ne a jiya an wayi gari ana sifanta shi da ci-baya da rashi wayewa da fandarewa.
Abu Mas'ud Al'ansari ya shiga wa Huzaifa sai ya ce : ka mana wasiyya ya Baban Abdullahi, sai Huzaifa ya ce : Ase yakini bai zo ma ba? Sai yace : E ya zo, da buwayar Ubangiji na, sai yace : ka sani Bata hakikanin bata shine ka zama abin da ka ke ganinsa  a jiya mara kyau ya zama abu mai kyau, haka kuma abu da jiya ka ke gani mai kyau  to yau ya zama mara kyau , to na hore ka da juyawa,  addinin Allah daya ne.)           
  To ya ku bayin Allah ku riki sunna, Ina muku gargadi da fararrun abubuwa , domin dukkan fararren abu bidi'a ne, kuma dukkan bidi'a bata ne, kuma dukkan bata na wuta.
Ya Allah ka nuna mana gaskiya gaskiya ce ka bamu ikon bin ta, ka nuna mana karya karya ce ka ba mu ikon guje mata.
Ya Allah ka sanya mana son imani , ka kawata shi a zukatanmu, ka sa mu tsani kafurci da fasikanci da sabo,ka sanya mu cikin shiryayyu.
Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai,ka taimaki bayinka masu kadaita ka,
Allah ka sanya wannan gari cikin aminci da natsuwa, da sauran garuruwan musulmai,
Ya Allah ka kasance tare da masu rauni a garin suriya mai ruwa da itatuwa, ya Allah ka kare jininsu, ka suturce al'aurarsu, ka amintar da su daga tsoro.  Ya Allah ka musanya musu tsoron su da aminci, bayan rauninsu Allah ka basu nasara.
Ya Allah an zalunce su ka taimake su, ya Allah ka taimake su akan wanda ya zalunce su,
Ya Mai karfi  ya Mabuwayi.