Hudubar juma'a na Masllacin Annabi na Shaikh Abdulbari
Subaiti 6/7/1439 AH
Hudubar Farko:
Tafiyan Mutum a wannan
rayuwa masaukanta na sabunta ,
marhalolinta na jujjuyawa , yana rayuwa ne na wasu matakai a cikin mahaifiyar
sa sannan da wasu matakai a doron kasa ,
da wasu matakan kuma a cikin kasa har zuwa a tashe shi.
Wannan tafiyan tana da tsawo a
zahirinta sai dai tana da saurin gushewa
, kuma
tana da saurin karewa da tafiya,
to ita duniya ba gidan zama ba ne ga rayayye, mai hankali zai tuna irin
jujjuyawa da take da shi da saurin karewan
shekaru, sai ya ratsa jikin zuciyan shi ta
tausasa .
Masaukin da baya yiwuwa ga ko wani matafiyi sai ya sauka gare
shi wata rana shi ne kabari , kuma lallai ya isa abin wa'azi a gare shi , Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce : (Lallai kabari na da wata matsa wanda da a ce dayan mu zai kubuta daga
gareta da Sa'ad Dan Ma'azu ya kubuta daga gare ta ).
An karbo
daga Amirul muminina Usman Dan
Affan Allah ya kara yarda a gare shi ya
kasance idan ya tsaya a wurin kabari sai
ya yi ta kuka har gemun shi ya jika da hawaye , sai a ka ce da shi kana tuna aljanna da wuta amma ba ka kuka
amma in ka tsaya a wurin kabari sai ka yi kuka , sai
ya ce na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana
cewa : ( Kabari shi ne farkon masaukan
lahira idan mutum ya tsira daga gare shi
to abin da zai biyo baya ya fi sauki a
gare shi, idan kuma bai tsira ba to abin da zai biyo baya ya fi tsanani a gare
shi ).
Yana daga cikin rukunnan
imani da ranar lahira akwai kudurtawa da hakikanin imani da kabari , imani da
ni'iman kabari ga ma'abota da'a da kuma
azabar kabari ga wadan da suka
cancanta ma'abota sabo da fajirci, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi ya ce: (Badon kada ku ki binne mamatan ku ba da na roki Allah ya
jiyar da ku daga azabar kabari na daga abin da na ke ji ).
Ziyaran kabari don
daukan izina da wa'azantuwa sunna ce kuma kusanci ne, wanda ya ziyarci kabari
zai tuna wadannan matattu wadanda kakaninsa ne da iyayensa, sai ya sakankance
cewa zai mutu a binne shi kamarsu, kuma zaa tambaye shi a kabarinsa, Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :( ku ziyarci
makabarta zai tunatar da ku lahira).
Idan an binne mutum a
kabarin shi iyalan shi da dukiyan shi
suka bada baya farkon maziyartan shi su ne mala'iku guda biyu su mishi jarabawa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce : ( Lallai
idan an sanya mamaci a kabarinsa zai ji sautin takalman su lokacin da suke bada
baya idan ya kasance mumini ne sai
salla ta kasance ta kansa azumi ta kasance ta damansa , zakka kuma ta hagunsa, zai
kasance ayukan da yake aikatawa
na alheri na daga sadaka da salla da
ma'arufi da kyautatawa mutane a ta kafan sa , sai a zo ta kansa sai salla ta ce
tanan ba gun shiga zai a je ta daman sa
sai azumi ya ce ta guna ba mashiga sai a
zo ta hagun sa sai zakka ta ce ba wani
mashiga ta guna sai a zo ta bangaren
kafafuwan sa sai ayukan alkairi na daga sadaka da ihsani da kyautatawa mutane su ce ba mashiga ta guna sai a
ce da shi zauuna , sai ya zauna sai a
suranta mishi rana tana kusan faduwa sai
a ce da shi ko ka ga wannan da ke
fiskantar ku me za kace game da shi me za ka shaida kuma game da shi ? sai ya ce
ku barni na yi salla , sai a ce da shi, ai za ka yi amma bamu labarin a bin da
muka tambaye ka game da shi , ka ga
mutumin nan da ke ta fiskar ka me za ka ce game da shi kuma wacce shaida za ka
masa? Sai yace : Muhammad, ne, kuma na shaida shi Manzon Allah ne, kuma yazo da gaskiya daga Allah , sai
a ce da shi : akan haka ka rayu, kuma a kan haka ka mutu , kuma a kan haka za a
tashe ka in Allah ya yarda , sai a bude mishi kofofi n Aljanna sai a ce da shi nan ne masaukin ka a cikinta da abinda Allah
ya tattala maka a ciki sai ya kara jin
kaimi da farin ciki , sa'annan sai a
bude mishi kofofin wuta sai a ce da shi
ka ga wannan shi ne masaukin ka da abin da
Allah ya tattala maka a ciki da ka saba mishi , sai ya kara kaimi da farin
ciki sannan sai a buda mishi a kabarin
shi zira'i saba'in
a haskaka mishi ciki a maida
jikin shi kamar yanda aka fare shi , sai a sanya ruhinsa a cikin wani iska mai
dadi wato wani tsuntsu ne ke shawagi
akan itaciyar aljanna wannan shi ne fadin
Allah madaukakin sarki ( Allah yana
tabbatar da wadan da suka yi imani da
magana tabbatacciya a cikin rayuwar
duniya da cikin lahira kuma Allah yana
batar da azzalumai ). Lallai kafuri in anzo ta fiskan shi ba za a samu komai ba ,
in anzo ta daman shi ba za a samu komai ba in anzo ta hagun shi ba za a samu
komai ba sai a zo ta kafafuwan shi ba za a samu komai ba sai a ce da shi zauna sai ya
zauna cikin tsoro da firgici, sai a ce da shi ba ka
ga wancan mutumin da ya kasance a cikin ku ba me za ka ce game da shi kuma
wacce shaida za ka yi akansa , sai ya ce
wani mutumi? Ba zai ma gane sunan shi ba
sai a ce da shi Muhammad sai ya ce ban sani ba na ji dai mutane suna cewa wani magana sai ni
ma na fada kamar yanda suka ce, sai a ce da shi a haka ka rayu kuma ahaka ka mutu kuma akan
haka za a tada in sha Allahu, sai a bude
mishi kofa daga cikin kofofin wuta sai
a ce da shi wannan ne masaukin ka na daga wuta
da abin da Allah ya tanada maka na daga cikinta , sai
ya kara bakin ciki da hasara , sannan a
bude mishi kofa daga cikin kofofin Aljanna
ace da shi, wannan masaukin ka ne a cikin ta da abin da Allah ya tattala
maka da ka mishi biyayya, sai ya kara bakin ciki da hasara sai kabarin shi ya kuntata a gare shi har
kasusuwan hakarkarin shi su shiga junan su.
Wannan ita ce rayuwa ta kunci
wanda Allah ya ambata ( To lallai ne rayuwa mai kunci ta tabbata a gare shi ,
kuma muna tayar da shi a ranar kiyama yana makaho ) Dabarani ne ya
rawaito da Ibn Hibban a sahihin sa .
Mai hankali zai shirya ne kafin mutuwa ya kimtsa wa
kabarinsa don kansa, ya raya ta, ta
hanyar ayuka na kwarai da imani don ya kasance yana da dausayi daga cikin
dausayin Aljanna Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
ce : ( Yana daga cikin abin da zai riski mumini bayan mutuwan
na daga aikin shi da kyawawan aikin sa ,
ilimi da ya ilmantar kuma ya yada shi , da Da na kwarai da ya barshi , da
Alkur'ani da ya gadar da shi ko masallaci da ya gina , ko kuma gida da ya gina na 'yan tafarki , ko
korama da ya buda ya gudana , ko sadaka
da ya fitar daga dukiyar shi , a halin
yana mai lafiya yana raye zai riske
shi bayan mutuwar sa .'
Wanda ke yawan tuna mutuwa zai raya kabarin sa da kyawawan ayuka, domin
ya sani bisa yakini , lallai shi ya sani idan ya wayi gari ba zai yi yammaci
ba , idan kuma ya yi yammaci ba zai jira wayan gari ba sai ya yi gaggawa zuwa ga ibada kafin a yi
shamaki tsakanin shi da ita , ga Amr dan
As yana ganin mamaci an binne shi sai
yayi sauri ya tafi masallaci ya yi salla raka'a biyu, sai aka ce da shi me ya
sa ka yi haka ?, sai ya ce makabarta ta
tuna min fadin Allah ( Sai aka yi
shamaki tsakanin su da abin da
suke sha'awa ).
Sai na sha'awi salla kafin a yi shamaki tsakani
na da ita , wanda yake son aboki a kabari wanda zai debe mishi kewa, ya haskaka
mishi kabarin shi ya tafiyar mishi da
kadaici to ya riki Alkur'ani .
Yana daga cikin sabuba na tsira daga
fitinan kabari da azabar sa, dauwama akan karanta suratul mulk, da aiki da abin
da ta hukunta . An karbo daga Dan Mas'ud Allah ya yarda da shi
ya ce : (Za a zo wa mutum a cikin
kabarinsa sai a zo ga kafansa sai kafofin
sa su ce : ba
ku da wata dama ko kofa ta fuskar mu ya kasance yana tsayuwa da mu ya karanta suratul mulk sannan sai a zo ta
kirjin sa ko ta cikin sa , sai ya
ce ba ku da wata dama ta bangare na a kan shi ya kasance da ni yake karanta
suratul mulk sannan a zo ta kasan sa sai
ya ce baku da wata kofa akan shi game da ni ya kasance da ni yake
karanta suratul mulk , sai ya ce : ita ce mai hani, tana hani daga azaban kabari tana cikin attaura suratul mulk wanda ya karanta ta a dare to hakika ya
yawaita kuma tsawaita ) Hakim ne ya rawaito shi a mustadrak ya ce
ingantacce ne amma(Bukhari da Muslim) basu fitar da shi ba Albani ya
inganta shi
Istigfari ga muminai da musu adu'a zai
tabbatar da al'amarin ka a kabari yayin tambaya , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya
kasance in ya binne mamaci sai ya tsaya
gaba gare shi sai ya ce ku nemawa dan uwan ku gafara kuma ku roka mishi tabbatuwa domin yanzu za a tambaye shi , mutanen kwarai na raya kaburburan su ne ta hanyar lazimtar adu'o'i a
ko wace salla, suna neman tsari daga fitinan kabari , Annabi ya kasance yana adu'a Ya Allah
ina neman tsarin ka daga azaban kabari da azabar wuta , da fitinar rayuwa da ta mutuwa, da fitinan masihuddajjal).
HUDUBA NA BIYU
Musulmi mai hankali
yana kiyaye wa daga guraren fitina da halaka,wanda ke lalata al'umarsa kuma ya
fitine shi a kabarinsa, na daga ciki akwai yada karerayi da sadar da su, ya zo
a hadisin Isra'i da Mi'iraji mai tsawo Jibrilu ya ce da Manzon Allah ( amma
shi mutumin da ka zo mi shi ana keta
mukamukin sa zuwa keyan sa , da hancin sa zuwa keyan sa da idanuwan
sa zuwa keyan sa , to lallai mutum ne
yana wayan gari daga gidansa sai ya yi karyan da za ta bazu a duniya , yana
daga ciki kuma akwai cin riba da halatta shi ya zo
a hadisin isra'i da mi'i raji , amma mutumin da ka zo mi shi yana iyo a korama yana hadiye duwatsu to lallai shi maciyin riba ne )
.
Yana daga ciki mutumin da yake bacci ya bar
sallan farilla da me kauracewa kur'ani , to a cikin hadisin isra'i da mi'iraji
( Amma mutumin da ka zo mishi yana dandaka kansa da dutse shi ne mutumin da
yake daukan kur'ani ya yi watsi da shi , ya yi bacci kuma daga sallan farilla).
Yana daga cikin sabuba
na azaban kabari yawo a tsakanin mutane da annamimanci da yin sake wurin tsarki
, manzon Allah ya wuce wasu kaburbura
guda biyu sai ya ce :( Lallai su dinnan ana azabtar da su ne kuma ba
akan wani abu mai girma ba ake azabtar da su, amma dayan su ya kasance ba ya
tsarkaka daga fitsari, shi kuma dayan yana yawo da annamimanci).Sahihul Jami'i: Albani.