الجمعة، 12 يناير 2018

MUTUWA GA MUTUM

  HUDUBAR  JUMA'A  NA MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI  NA SHAIKH SALAH AL-BUDAIR  NA  25-4-1439 H
HUDUBAR FARKO
Yaku musulmai babu dauwama a  duniya  da za a yi fata  ko  wanzuwa  da za a bida
  mutane ba wani abu ba ne face mai tafiya da kuma dan mai tafiya ***zamani kuma ba wani abu ba ne sai shudewan yini da dare.
Mutuwa kuma ba wani abu ba ne sai abu ne  mai sauka kuma makusanci *** rayi kuma ba wani abu ba ne  fa ce  abin da ake nesa da haihuwar sa kuma mutuwa ke kusantowa ga zukata sai ta fita.

Kaito ya mutuwa  ba ta da dauke kafa idan muddar da  aka  diba ma rayi  ta  kai makurar sa*** sa'oi  za su mika ka ga wani  sashi na daga  lokaci   zuwa wani lokaci wanda babu wani  lokaci bayan shi .

   Abin mamaki  ga saurin ranaku cikin tafiyar su  za ta zo ta wuce mu kuma ta zo ta tafi da mu,  a ko wani rana   akwai buri wanda yana yin nesa,  manufansa daga lokaci da ya kusanto  .
      Ina wanda  suka  kasance  kafin mu ina  su ke *** Ina mutanen da  suka  kasance  kyawawa kuma masu  yin kawa .
Lalle  zamani ya biyo ta kansu  ya  karar da wani  adadi daga  cikin su ***Sa'annan muma yana zuwa kanmu .
Sau da yawa muna ganin mutum mamaci   bayan da ya kasance a raye***  ba da jimawa ba za a gane mana abin da muka ganewa wasu   .
Me ya same mu ne muke amin ta da mutuwa*** kai ka ce  ba za mu ganta  ta  zo  zuwa gare mu ba .
     Ya gafalalle ya wanda ya sha'afa  ko kun manta cewa mu 'yan adam ne  kaddara na kewaye da mu kuma mu dinnan muna cikin tafiya ne,  wanda za mu tafi zuwa kaburbura  , mutuwa  za ta hada da mu , tashin alkiyama zai tattaro da mu ,    to har zuwa yaushe ne za mu wa'azantu mu daina , to har sai zuwa yaushe ne kunnen ka zai kiyaye fadakarwan mai fadakarwa  ,  ga  zuciyar ka kuma baya tausasa sabo  da  mai zargi .
     Ase lokaci bai yi ba da zuciya za ta ji tsoro ***  To kuma ina kokarin ? a cikin gyangyadi muke ne ko kuma zuciyar ta sandare?  To ka farka   dan uwa na kuma  ka kiyaye  kar ka kwanta .
 Kwanciya za ka yi ya rudadde  bayan ga wuta ana kara kunna  ta *** zafin ta ba a kahse shi haka nan kuma gaushinta baya mutuwa.
Annabi ya kasance  amma bai dauwama ba ga al'umar sa *** Da Allah ya dauwamar da wani halitta kafin shi  , to , da shi ya dauwama .
Mutuwa  acikin mu tana da wasu masu wanda ba sa kuskurewa *** wan da kifiya ta tsere mishi a yau to fa gobe  ba  zata   tsere mishi ba  .
Allah madaukakin sarki ya ce : ( Kuma ba mu sanya dawwama   ga wani mutum ba a gabanin ka  . Shin to idan ka mutu to su ne madauwama ?  ,  ko wani rai mai dandanan mutuwa ne kuma muna jarraba ku da sharri da alheri domin fitina , kuma  zuwa gare mu ake mayar da ku  ) AYA 34-35 Al-Anbiya
     Ina wadanda muka yi mu'amala da su na tsawon lokaci muka saba da  su, ina wadanda mu ka karkata zuwa gare su da kauna da tausayawa ,?   Sau da yawa mun rintse idanuwan mu( mun yi kuka )   sabo da masoyanmu,  mutum nawa ne masu izza  mu ka binne  muka tafi kuma muka bar su   sau da yawa muna binne makusanci mu kwantar da shi  a cikin kabari ba za mu tsaya ba ?  shin ko mutuwa na tausayawa mara lafiya daga cikin mu sabo da raunin halin shi? Shin  ta bar wani  mai nema   (dan kasuwa)  sabo da 'ya'yan shi?  Shin ta saurarawa   ma'aboci iyalai sabo da iyalan shi ? .
    Ya bawan Allah  a ko wani rana akwai abun lura bayan abun lura *** Acikin mutuwa kuma akwai abu mai hani  da ka kasance  cikin wan da suke  hanuwa .
                                                                                                         Tohar zuwa yaushe? To har zuwa yaushe ? * wai kai yaushe ne za ka ji gargadi  kuma  ka ji tsoro.
                                                                                                Zuwa yaushe ne  za ka  dena cigaba da dogewa da ruduwa da gafala *** Sau da yawa  haka  ne  bacci  to yaushe ne ranar   farkawa.
                                                                                          Rayuwa ta saraya a wani lokaci  da za ka iya sayan cikin kasa da sama *** wani irin  bata abu mai karewa za ka saye shi  cikin  wauta   
                                                                                       Ka saida  fushi da yarda  *** sannan ka saida  aljanna  kuma da  wuta .
                                                     Yanzu kai masoyi ne ga rayin ka ko kuma makiyi ne gare shi *** to lalle kai kana jefa ta ga dukkan musibu .
                                                                     Hakika ka saida ta  cikin araha –ina mai ma bakin ciki***  wanda ta kasance ba abu ne da yake na tabbas ba a gare ta.
                                                                 A yau kana aikata abin da ka keso kuma da  abin da  ka ke sha'awa *** a gobe kuma  za ka mutu kuma a dauke alkaluma .
                                                             Mai laifi na zama fasiki ta hanyar aikata babban laifi *** haka nan kuma idan ya doge a kan kananan laifuka.
                                                                 Mutum ba zai fita daga imani ba*** sabo da ya aikata                      manyan laifuka na sabo   .
                          Kuma ya wajaba  a gare shi da ya tuba*** daga dukkan abin da zai  janyo mishi   zunubai .
  Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma ku tuba zuwa ga Allah guda daya , ya ku muminai ko za ku samu babban rabo).
   (Lalle Allah na shimfida hanun shi da da dare don masu laifin wuni su tuba , kuma yana shimfida  hanun shi da wuni don masu laifin  dare su tuba har rana ta bulla daga yammacinta ).
 Ina neman gafarar Allah daga  zunubi na  da barna ta ***  lalle ni ko da na kasance ana boye min laifuka na to fa mai yawan laifi ne
                                                                 Ba wani sabo da  raina za ta janyo mi ni*** face na samu kai  na a tsakanin haske da duhu .
                                                             Hakika ina mamaki   bisa gafala ta  da kuma shammata ta***  a halin mutuwa zai kira ni gobe na amsa  
                                       Hakika na yi mamaki  na tsawon aminta daga mutuwa ta *** kuma gata zuwa gare  ni za ta sadado ta fisge ni.
                                                            Na sabawa Allah a wuni na da dare na *** cikin sabo na  saki jiki bone ya tabbata  a gare ni idan har aka haramta mi n Aljanna Adin .
                                                               Kuma bone  a gare ni muddin na shiga wuta kuma bone ya tabbata a gare ni.
 Allah madaukakin sarki ya ce : (  Ka ce ya bayi na wadan da suka yi barna a kan rayukan su !  kada ku yanke kauna daga rahamar Allah , lalle Allah na gafar ta zunubai  gaba daya  lalle shi mai gafara ne mai jin kai )
 HUDUBA NA BIYU
Ya ku musulmai Addini shi ne uwar kudin ku  kuma shi ne daukakan hali da makoma.
  duk wata  karaya addini na gyara ta*** amma karayan addini ba abin da zai gyara ta.
                           Dukkan wasu musibu idan sun bayyana suna da  sauki ko sun ko sun  girmama*** sabanin musiban da zai sami mutum a addinin shi.
Ga ruwan fitintinu na ambaliya  yana dukan juna, ga kasa cike da hanyoyi na macizai da kunamu da abubuwa masu cutarwa a cikin duwatsu na sanda.
 Duniya cike take da fitina da bala'i to ku shirya hakuri don bala'i,
An karbo daga Huzaifa Allah kara yarda a gare shi yace : Ya Manzon Allah lalle mun kasance muna cikin sharri sai Allah ya tafiyar da shi ya kawo mana alheri ta hanunka, to shin bayan wannan alherin ko akwai wani sharri? Sai ya ce : E,sai ya ce to menene shi? Yace wasu fitina kamar yankin duhun dare, sashi na bin sashe, zasu zo a rikice kamar fiskar shanu,baku fayyace wannan daga wancan.) Ahmad ne ya rawaito.
(Allah kara yarda a gare shi yace : fitina ba ta cutar da kai muddin ka san addininka  lallai ita fitina  idan gaskiya da bata suka rikirkice maka ka kasa sanin wadda zaka bi to   wannan ita ce fitina ) Ibn Abi Shaiba ne ya fitar da shi
    Allah ya kara yarda a gare shi ya ce '' Idan dayan ku ya so ya san  cewa fitina ta same shi ko bata same shi ba to ya yi dubi :  to in ya kasance abin da ya ke ganin shi a da haram ya koma yanan ganin shi halal , to, fitina ta same shi,  ko kuma abin da a da yake ganin shi halal ya koma yana ganin shi haram to, nan ma fitina ta same shi '' Hakim ne ya fito da shi
  Ma'ana ra'ayin mutum ya sanja  zuwa son rai da sha'awa .
   Malik Dan Anas yana cewa: "  duk lokacin da wani mutum ya zo mana mafi jayayya yana so mu maida abin da Jibrilu ya zo mana da shi  zuwa ga manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi"  .
       Yanzu zan zauna a bayan kasusuwa na  sun girgiza *** Ahalin mutuwa ta kasance ta fi kusa zuwa gare ni.
                                     Ina jayayya ga dukkan wani  mai cin karo mai yawan musu ***  na sanya addinin shi ya zamana abin da zai taba mini addini na .
                                   Na bar abin da na sani sabo da ra'ayin wani   na   a   hali  kuma  ilimi  na  yakini   ba daidai  yake da ra'ayin wani ba.
                                 Ni ban zame mai shiga cikin husuma ba *** wacce  za ta tunkude daga hagu zuwa dama.
                                      Kuma hakika an  sunnan ta mana wasu sunnoni   tsayayyu*** Wanda  zai sanya lahani ga dukkan wani  kofa  ko  kuma   wani  lokaci.
                 Gaskiya  ta kasance  bata boyuwa  *** tana bayyana  a  goshi kamar    yanda   safiya   ke   bayyana .
                                   Tafarkin jahamu bai kasance ya zamana  madadi a gare mu ba***  bisa  tafarkin  Dan Aminata  amintacce    .
       An karbo daga Abdullahi dan Dailami ya ce : (    Lallai farkon tafiyan addini shi ne barin sunna  ,   addini zai tafi sunna bayan sunna  ,  kamar yan da  igiya  ke tafiya gaba  bayan  gaba .
    Abubakar Siddik Allah ya yarda da shi ya ce : '' Ban kasance mai barin wani abu da Annabi ya kasance yana aikatawa ba  face sai na yi aiki da shi  , kuma lallai ni ina tsoron  na bar wani  abu daga umarnin sa ya zama na karkace ''.
       Ku  tabbata ya ku bayin Allah  akan  littafi  da sunna  da shari'a  da addini  da kuma dabi'u da halaye kyawawa  ku kiyaye masu batarwa,   masu tada fitina ,  ku kiyaye su kar su  fitine ku daga  wani sashi na daga abin da Allah ya saukar  a gare ka .
Ya  Allah muna rokon ka tabbatuwa  akan al'amari da kuma  azama bisa shiriya.



     

ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق