الجمعة، 26 يناير 2018

NEMAN ILIMI DA LADUBARSA

Hudubar Juma'a na Masallacin Annabi na shaikh Abdullah Dan Abdurrahman Al-Buaijan 9-5-1439 AH.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, wanda ya ilmantar da alkalami, ya sanar da mutum abin da bai sani ba,ina kyautata yabo a gare shi  bisa ni'imominsa,ina kuma  gode mishi bisa abin da ya mana na falaloli da karamci.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bai da abokin tarayya, na shaida Annabi Muhammad shine cikamakin Annabawansa da Manzanninsa, Allah ya zabe shi a kan sauran al'umu, ya turo shi don tausayawa ga talikai zuwa ga larabawa da ajamawa, ya isar da sako, ya sauke amana ya yi jahadi a tafarkin Allah hakkin jahadi har mutuwa ta zo mishi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,da iyalan shi da sahabbansa da duk wanda ya bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakayya.
Bayan haka, Lalle Alkur'ani shine zance mafi kyau, Addini a wurin Allah shine Musulunci,mafi alherin shiryarwa shine shiryarwar Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ( Ya ku mutane ! ku bautawa Allah Ubangijin ku da takawa ,  kuma ku ji tsoron wani yini, ranar da wani mahaifi baya sakawa dansa  da komai ko wani da ya sakawa mahaifin sa da komai  lallai wa'adin Allah gaskiya ne  , sabo da haka kada rayuwar duniya ta rude ku  kuma kada marudin nan ya rude ku  game da Allah ) .
    YA KU BAYIN ALLAH !
Hakika Allah ya zabi dan adam  domin ya sanya shi kalifa a doron kasa  ya bashi ilimi  wanda yana ta'alluki ne da aiki da kuma daukaka  , ya kuma bashi hankali  wanda ya ta'allaka ne da takalifi  Allah Madaukakin sarki  ya ce : (  kuma a lokacin da Ubangijinka ya ce ga mala'iku  lallai ne ni mai sanya wani halifa ne a cikin kasa:  suka ce,  ashe za ka sanya a cikin ta wanda zai yi barna  kuma ya zubar da jini  alhali kuwa mu muna yi maka tasbihi game da gode maka , kuma muna tsarkakewa  gare ka  ya ce : lallai ne ni  na san abin da ba ku sani ba )
      Sannan ya bayyana cewa ilimin nan yana ta'allake ne da falala da daukaka sai ya ce :
 ( Kuma ya sanar da Adam sunaye dukkan su sa'annan kuma ya gitta su a kan mala'iku sa'annan ya ce :  to ku gaya mini sunayen wadannan idan kun kasance masu gaskiya)
 suka ce  tsarki ya tabbata a gare ka ! ba bu sani a gare mu face abin da ka sanar da mu , lallai ne kai, kai ne masani mai hikima .  Ya ce : ya Adam ! ka gaya musu sunayen su  : '' to alokacin da ya gaya musu sunayen su , (Allah) ya ce :  ashe ban ce muku  ba lallai ni ina sane da gaibin sammai da kasa ( kuma ina sane da abin da kuke bayyanawa da abin da kuka kasance kuna aikatawa)
        Sai Allah ya fifita mutum bisa da yawa daga cikin halittun sa  a dalilin ni'ima ta ilimi da hankali ,  ya kuma dora taklifi a kan haka .
        YA JAMA'AR MUSULMI!
Dalibai maza da mata za su fiskanci sabon fasali na karatu a wannan  ranaku,  to madalla da wanda ya dage ya yi kokari  ya ja damara cikin aikin alheri to zai samu sa'ada , to lallai  ilimi shi ne ginshikin addini  kuma da shi ne mutum zai san addinin shi  kuma da shi ne  mutum zai iya sanin yadda zai yiwa Ubangijin shi da'a ,  kuma farkon  umarnin da mala'ika jibrilu ya zo da shi  daga wurin Allah zuwa  ga Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  shi ne ;  umarni da neman ilimi  , kuma farkon ayan da ta sauka a Alkur'ani shi ne;  ( yi karatu).
    An karbo daga Aisha  , Allah ya kara yarda a gare ta  ta ce : (  Farkon abin da   aka   fara wahayi wa Manzon Allah shi ne mafarki  na gaskiya  a cikin bacci , ya kasance baya ganin wani abu a cikin bacci  face abin ya bayyana kamar hasken  safiya  sannan sai aka kwadaitar a gare shi yin khalwa , ya kasance yakan tafi kogon hira ya kebanta yana ta bauta a ciki na wasu dararraki  masu adadi  kafin ya dawo zuwa ga iyalan shi ya sake samun guzuri  , har zuwa lokacin da gaskiya ta  zo mishi , mala'ika Jibrilu ya sauka a gare shi a halin yana kogon hira sai mala'ika ya zo mishi sai ya ce :  yi karatu , ya ce : ( ni ba mai karatu ba ne ) sai ya ce : sai ya kama ni ya matse ni  har na ji wahala sannan ya  sake ni  sai ya ce yi karatu :  sai na ce: ( ni ba mai karatu ba ne )  sai ya sake kama ni ya matse ni a karo na biyu har na ji ba dadi sannan ya sake ni , sai ya ce yi karatu : sai na ce : ( ni ba mai karatu ba ne) sai ya kama ni ya matse ni a karo na uku har na ji jiki , sannan ya sake ni sai ya ce : yi karatu da sunan Ubangijin ka  wanda ya yi halitta, ya halitta mutum daga  gudan jini,  ka yi karatu  kuma Ubangijinka shi ne mafi karamci ,  wanda ya sanar da (mutum ) game da alkalami  ya sanar da mutum abin da bai sani ba ).
       Ya ku bayin Allah hakika  Alkur'ani ya kwadaitar bisa ga neman ilimi, Allah bai umarci  Annabin shi ba da ya roke shi karin wani abu ba sai  ilimi , ( kuma ka ce ya Ubangiji ka kara min ilimi )
       Kuma ya koda matsayi irin na malamai  sai ya ce :  ( Malamai kawai ke tsoron Allah a cikin bayin sa).
        Kuma Allah ya hada su da kansa da mala'ikunsa cikin shaidawa  da  kadaitakarsa,  Allah madaukakin sarki ya ce : ( Allah ya shaida cewa : Lalle ne babu abin bautawa face  shi , kuma mala'iku  da ma'abuta ilmi sun shaida ,  Yana tsaye  da adalci , babu abin bautawa  face shi , mabuwayi , mai hikima ).
Kuma Allah ya yi nuni bisa kimansu sai ya ce: ( Ka  ce  ashe , wadanda suka sani , suna daidaita  da wadanda ba su sani ba ?).       
Kuma ya yi umarni da komawa gare su yace :(To ku tambayi ma'abota ilimi in kun kasance baku sani ba).
Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya kwadaitar game da shi ya bayyana cewa alama ne na alheri (Wanda Allah ya nufe shi da  alheri zai fahimtar da shi addini).
  Yace : (Wanda ya kama hanya ta neman ilimi Allah zai saukake mishi hanya ta shiga Aljanna)
To ku bawa ilimi wani kaso na daga lokutanku,kuma ku kwadaitar da yaranku bisa kokari da jajarcewa wajen nemansa.domin shi ne hanya mafi dacewa ta tarbiya, kuma mafi tabbatuwar  yakini  wurin tsarkake zuciya.kuma ya fi kawo amintuwa daga fitintinu, kuma yake kawo tabbatuwa  da tsayuwa yayin  jarabawa, yafi kawo hakuri yayin musiba,kuma yana cikin kyawawa mafi daraja da aikin lada mafi girma na neman kusanci ga Allah, da samun daraja mafi daukaka.
Ya ku Musulmai!
Duk wanda Allah ya nufe shi da alheri zai sanar da shi addini, mafi alheri cikinku a lokacin jahiliyya sune mafi alherinku a lokacin musulunci in sun yi ilimi,kuma malamai sune magada Annabawa.
Shagaltuwa da ilimi na cikin Bakiyatussalihat da sadaka mai gudana bayan mutuwa,  da  samun lada mai dorewa bayan wafati,
An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Idan mutum ya rasu ayyukansa zasu katse sai guda uku: Sadaka mai gudana, ko ilimi da ake amfana da shi, ko da na kwarai da yake mishi adu'a)
Sai dai fa ilimi na bukatar hakuri da lokaci da kokari da juriya, da bada kai,  gwargwadon wahalar  da aka sha gwargwadon yadda zaa  cinma manufa,da biyan bukata.
Neman ilimi na bukatar ikhlasi a niyya da azama ta gaskiya, da tsarkake zuciya,  da tsiraituwa daga duk  abin da zai kawo cikas ko kashe jiki,  to lalle duk wanda ya riki filo aboki ba shi ba riskan matsayi (Yaro bata dare ka yi suna).
(kuma Ba ya kasancewa ga muminai su fita zuwa yaki gaba daya. Saboda haka don mene ne wata jama'a daga kowane bangare daga gare su ba ta fita (zuwa neman ilimi ba) domin su nemi ilimi ga fahimtar addini kuma domin su yi gargadi ga mutanensu idan sun koma zuwa gare su, tsammaninsu, suna yin sauna? ).
Mai neman ilimi na bukatar laduba na shari'a a cikin nemansa  har ya zama abin koyi abin buga misali mai kyau, kuma ya zama ahali na karbar wannan sako, kuma cikin adilai na wannan Al'uma.
 Ya inganta daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, (wadanda zasu karbi wannan ilimi cikin mamaya sune adilan cikinsu, suna kore karkatarwar masu ketare iyaka da da'awar mabarnata da tawilin jahilai).
Bayan haka ya ku bayin Allah! dukkan ilmuka masu amfani an shar'anta nemansu, sawa'un tushensu Alkur'ani ne da sunna: kamar ilimin addini, na akida da tafsiri da hadisi da fikihu da wasunsu, ko tushensu ya samu asali ne daga sanin yau da kullum (Gogewa da gwaji) da dubi ga duniya da rayuwa kamar ilimin likitanci ko ilimin da ke nazari kan haske da sauti ko (kimiyya da fasaha), da waninsu.
, to duk wanda ya kyautata niyyarsa wajen nemansu ina fatan fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi : (Wanda ya kama hanya ta neman ilimi Allah zai saukake mishi hanya ta shiga Aljanna) ya game da shi.
Ina neman tsarin Allah daga sharrin shaidan abin jefewa
Shine wanda ya aika a cikin mabiya  al'adu wani Manzo daga gare  su yana karanta ayoyinsa a gare su kuma yana tsarkake su, kuma yana sanar da su littafin da hikimar sa ko da yake sun  kasance daga gabaninsa suna cikin bata bayyananna . Da wadansu mutane daga  gare su, basu ida riskuwa da su ba.alhali kuwa shine Mabuwayi Maihikima.
 
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, godiyar da ta dace da daukakarsa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai yake bai da abokin tarayya, cikin girmansa da kamalarsa, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,da iyalan shi da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa, har zuwa ranar sakayya.
Ya ku bayin Allah!
Lalle ilimi na da jakunkuna da ke adana shi, da masu tsaro da ke bada kariya a gare shi, da mazaje da ke daukanshi da shehunai da ke mishi hidima, ta hanyarsu ne yake tafiya ya yadu a duniya da kokarinsu.
Ya ku al'uma!
Lalle malami yana wakiltar Annabawa ne a ayyukansu na tarbiyantarwa da ilmantarwa, ya ke tashi da hidima don samar da al'uma masu tasowa nan gaba,kuma ya dasawa yara masu tasowa na wannan al'uma iri na kyakkyawan rayuwa da walwala na duniya da lahira,to lalle ya dace da a girmama shi a kimanta shi kuma ya dace da a mutunta shi, haka kuma a dauke kai game da kananan laifukansu a yafe masa kurakuransa.
Ya ku Malamai da masu bada tarbiya maza da mata.
Ku kasance abin koyi mai kyau ku siffantu da ilimi da ladubansa, to ku manya ne a idon dalibanku, daliban na sha'awan kwaikwayon ku da koyi da ku, to ku zama abin koyi nagari don Allah ku zame abin koyi nakwarai, idan kun bayyana musu kyan gaskiya to ku kasance cikin masu gaskiya, idan kun umarce su da hakuri to ku  zama cikin masu hakuri,
Fara da kanka ka hanu daga zalunci irin na rai   ***
idan ka hanu to kai ne mai hikima
To a nan ne zaa karbi abin da ka ke fadi a yi koyi * **
da ilimi daga gare ka, ilmantarwan ya yi amfani
Kar ka yi hani ga wani hali kuma ka aikata irin shi***
Babban laifi ne a gare ka in ka yi haka.
Ya ku Malamai!
Nauyin da ke kanku na da girma, amanar da ke wuyanku babba ce. 'ya'yan wannan al'uma amana ne a kan ku, kuma an bada ajiyar wannan al'uma a hannunku, abin da ake hanga na gabanta ya taallaka ne da nauyin da ke kanku. Ku ji tsoron Allah game da kiwon da aka baku, ku ji tsoron Allah game da kiwon da aka baku! (Dukkan ku masu kiwo ne kuma abin tambaya ne bisa kiwon da aka baku,).
To in kun kyautata to kun kyautatawa kanku ne, kuma haka ake zata muku,to kuwa kuna da falala mai girma a gurin Allah, in kun muzguna to kun muzgunawa kanku da al'umarku ne.
Ya ku dalibai zababbu 'ya'ya ga malamai masu biyayya!
Ku kasa kunnuwanku  ku saurara, wannan zance ne da ya kebance ku, daga mai tausaya muku kuma masoyinku:
Lalle girmama malami da kimanta shi ladabi ne na sharia kuma halaye ne na wajibi, kuma nasara ne na ilimi da na tarbiyya. A tafiyar Annabin Allah Musa da khidr Amincin Allah ya tabbata a gare su a kwai abin lura da wa'azi  da tunatarwa,
(yace shin ba zan bi ka ba don ka sanar da ni daga abin da aka sanar da kai na shiriya?). sai malamin ya maida mishi amsa da : (Lalle ne kai ba za ka iya yin hakuri tare da ni ba, kuma ya ya za ka yi hakuri da abin da baka kewaye sani da shi ba ga jarrabawa ).sai musa ya zanta mishi cewa ya san hakkin malami da wahala irin na neman ilimi,  (yace : zaka same ni in Allah ya so mai hakuri, kuma ba zan saba maka ba ga wani umarni).
Lalle falalar malami na da girma, kokarinsa da kyautarsa hakki ne da ba zaa saka masa ba sai da alheri, to na hore ku da ku kiyaye kar ku musu rashin ladabi, domin alama ce ta lalacewar tarbiya, da fandarewan dabiu, da hali mara fasali,  ba mai yarda da shi sai dan iska.
Kuna da abin koyi  mai kyau daga magabata, ga Rabi'u almajirin imamusshafi'I Allah ya jikansu da rahama, yana cewa : Ban iya bushewan ido ba na sha ruwa a gaban Imamusshafi'i yana kallo na sabo da kwarjininsa.
Ku girmama malamanku, kowa ku san matsayin shi, ku bawa kowani mai hakki hakkinsa, Allah ya datar da ku, ya azurta ku da ilimi mai amfani, da aiki na gari.
Ya Allah ka daukaka musulunci da musulmai.             


            

الجمعة، 12 يناير 2018

MUTUWA GA MUTUM

  HUDUBAR  JUMA'A  NA MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI  NA SHAIKH SALAH AL-BUDAIR  NA  25-4-1439 H
HUDUBAR FARKO
Yaku musulmai babu dauwama a  duniya  da za a yi fata  ko  wanzuwa  da za a bida
  mutane ba wani abu ba ne face mai tafiya da kuma dan mai tafiya ***zamani kuma ba wani abu ba ne sai shudewan yini da dare.
Mutuwa kuma ba wani abu ba ne sai abu ne  mai sauka kuma makusanci *** rayi kuma ba wani abu ba ne  fa ce  abin da ake nesa da haihuwar sa kuma mutuwa ke kusantowa ga zukata sai ta fita.

Kaito ya mutuwa  ba ta da dauke kafa idan muddar da  aka  diba ma rayi  ta  kai makurar sa*** sa'oi  za su mika ka ga wani  sashi na daga  lokaci   zuwa wani lokaci wanda babu wani  lokaci bayan shi .

   Abin mamaki  ga saurin ranaku cikin tafiyar su  za ta zo ta wuce mu kuma ta zo ta tafi da mu,  a ko wani rana   akwai buri wanda yana yin nesa,  manufansa daga lokaci da ya kusanto  .
      Ina wanda  suka  kasance  kafin mu ina  su ke *** Ina mutanen da  suka  kasance  kyawawa kuma masu  yin kawa .
Lalle  zamani ya biyo ta kansu  ya  karar da wani  adadi daga  cikin su ***Sa'annan muma yana zuwa kanmu .
Sau da yawa muna ganin mutum mamaci   bayan da ya kasance a raye***  ba da jimawa ba za a gane mana abin da muka ganewa wasu   .
Me ya same mu ne muke amin ta da mutuwa*** kai ka ce  ba za mu ganta  ta  zo  zuwa gare mu ba .
     Ya gafalalle ya wanda ya sha'afa  ko kun manta cewa mu 'yan adam ne  kaddara na kewaye da mu kuma mu dinnan muna cikin tafiya ne,  wanda za mu tafi zuwa kaburbura  , mutuwa  za ta hada da mu , tashin alkiyama zai tattaro da mu ,    to har zuwa yaushe ne za mu wa'azantu mu daina , to har sai zuwa yaushe ne kunnen ka zai kiyaye fadakarwan mai fadakarwa  ,  ga  zuciyar ka kuma baya tausasa sabo  da  mai zargi .
     Ase lokaci bai yi ba da zuciya za ta ji tsoro ***  To kuma ina kokarin ? a cikin gyangyadi muke ne ko kuma zuciyar ta sandare?  To ka farka   dan uwa na kuma  ka kiyaye  kar ka kwanta .
 Kwanciya za ka yi ya rudadde  bayan ga wuta ana kara kunna  ta *** zafin ta ba a kahse shi haka nan kuma gaushinta baya mutuwa.
Annabi ya kasance  amma bai dauwama ba ga al'umar sa *** Da Allah ya dauwamar da wani halitta kafin shi  , to , da shi ya dauwama .
Mutuwa  acikin mu tana da wasu masu wanda ba sa kuskurewa *** wan da kifiya ta tsere mishi a yau to fa gobe  ba  zata   tsere mishi ba  .
Allah madaukakin sarki ya ce : ( Kuma ba mu sanya dawwama   ga wani mutum ba a gabanin ka  . Shin to idan ka mutu to su ne madauwama ?  ,  ko wani rai mai dandanan mutuwa ne kuma muna jarraba ku da sharri da alheri domin fitina , kuma  zuwa gare mu ake mayar da ku  ) AYA 34-35 Al-Anbiya
     Ina wadanda muka yi mu'amala da su na tsawon lokaci muka saba da  su, ina wadanda mu ka karkata zuwa gare su da kauna da tausayawa ,?   Sau da yawa mun rintse idanuwan mu( mun yi kuka )   sabo da masoyanmu,  mutum nawa ne masu izza  mu ka binne  muka tafi kuma muka bar su   sau da yawa muna binne makusanci mu kwantar da shi  a cikin kabari ba za mu tsaya ba ?  shin ko mutuwa na tausayawa mara lafiya daga cikin mu sabo da raunin halin shi? Shin  ta bar wani  mai nema   (dan kasuwa)  sabo da 'ya'yan shi?  Shin ta saurarawa   ma'aboci iyalai sabo da iyalan shi ? .
    Ya bawan Allah  a ko wani rana akwai abun lura bayan abun lura *** Acikin mutuwa kuma akwai abu mai hani  da ka kasance  cikin wan da suke  hanuwa .
                                                                                                         Tohar zuwa yaushe? To har zuwa yaushe ? * wai kai yaushe ne za ka ji gargadi  kuma  ka ji tsoro.
                                                                                                Zuwa yaushe ne  za ka  dena cigaba da dogewa da ruduwa da gafala *** Sau da yawa  haka  ne  bacci  to yaushe ne ranar   farkawa.
                                                                                          Rayuwa ta saraya a wani lokaci  da za ka iya sayan cikin kasa da sama *** wani irin  bata abu mai karewa za ka saye shi  cikin  wauta   
                                                                                       Ka saida  fushi da yarda  *** sannan ka saida  aljanna  kuma da  wuta .
                                                     Yanzu kai masoyi ne ga rayin ka ko kuma makiyi ne gare shi *** to lalle kai kana jefa ta ga dukkan musibu .
                                                                     Hakika ka saida ta  cikin araha –ina mai ma bakin ciki***  wanda ta kasance ba abu ne da yake na tabbas ba a gare ta.
                                                                 A yau kana aikata abin da ka keso kuma da  abin da  ka ke sha'awa *** a gobe kuma  za ka mutu kuma a dauke alkaluma .
                                                             Mai laifi na zama fasiki ta hanyar aikata babban laifi *** haka nan kuma idan ya doge a kan kananan laifuka.
                                                                 Mutum ba zai fita daga imani ba*** sabo da ya aikata                      manyan laifuka na sabo   .
                          Kuma ya wajaba  a gare shi da ya tuba*** daga dukkan abin da zai  janyo mishi   zunubai .
  Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma ku tuba zuwa ga Allah guda daya , ya ku muminai ko za ku samu babban rabo).
   (Lalle Allah na shimfida hanun shi da da dare don masu laifin wuni su tuba , kuma yana shimfida  hanun shi da wuni don masu laifin  dare su tuba har rana ta bulla daga yammacinta ).
 Ina neman gafarar Allah daga  zunubi na  da barna ta ***  lalle ni ko da na kasance ana boye min laifuka na to fa mai yawan laifi ne
                                                                 Ba wani sabo da  raina za ta janyo mi ni*** face na samu kai  na a tsakanin haske da duhu .
                                                             Hakika ina mamaki   bisa gafala ta  da kuma shammata ta***  a halin mutuwa zai kira ni gobe na amsa  
                                       Hakika na yi mamaki  na tsawon aminta daga mutuwa ta *** kuma gata zuwa gare  ni za ta sadado ta fisge ni.
                                                            Na sabawa Allah a wuni na da dare na *** cikin sabo na  saki jiki bone ya tabbata  a gare ni idan har aka haramta mi n Aljanna Adin .
                                                               Kuma bone  a gare ni muddin na shiga wuta kuma bone ya tabbata a gare ni.
 Allah madaukakin sarki ya ce : (  Ka ce ya bayi na wadan da suka yi barna a kan rayukan su !  kada ku yanke kauna daga rahamar Allah , lalle Allah na gafar ta zunubai  gaba daya  lalle shi mai gafara ne mai jin kai )
 HUDUBA NA BIYU
Ya ku musulmai Addini shi ne uwar kudin ku  kuma shi ne daukakan hali da makoma.
  duk wata  karaya addini na gyara ta*** amma karayan addini ba abin da zai gyara ta.
                           Dukkan wasu musibu idan sun bayyana suna da  sauki ko sun ko sun  girmama*** sabanin musiban da zai sami mutum a addinin shi.
Ga ruwan fitintinu na ambaliya  yana dukan juna, ga kasa cike da hanyoyi na macizai da kunamu da abubuwa masu cutarwa a cikin duwatsu na sanda.
 Duniya cike take da fitina da bala'i to ku shirya hakuri don bala'i,
An karbo daga Huzaifa Allah kara yarda a gare shi yace : Ya Manzon Allah lalle mun kasance muna cikin sharri sai Allah ya tafiyar da shi ya kawo mana alheri ta hanunka, to shin bayan wannan alherin ko akwai wani sharri? Sai ya ce : E,sai ya ce to menene shi? Yace wasu fitina kamar yankin duhun dare, sashi na bin sashe, zasu zo a rikice kamar fiskar shanu,baku fayyace wannan daga wancan.) Ahmad ne ya rawaito.
(Allah kara yarda a gare shi yace : fitina ba ta cutar da kai muddin ka san addininka  lallai ita fitina  idan gaskiya da bata suka rikirkice maka ka kasa sanin wadda zaka bi to   wannan ita ce fitina ) Ibn Abi Shaiba ne ya fitar da shi
    Allah ya kara yarda a gare shi ya ce '' Idan dayan ku ya so ya san  cewa fitina ta same shi ko bata same shi ba to ya yi dubi :  to in ya kasance abin da ya ke ganin shi a da haram ya koma yanan ganin shi halal , to, fitina ta same shi,  ko kuma abin da a da yake ganin shi halal ya koma yana ganin shi haram to, nan ma fitina ta same shi '' Hakim ne ya fito da shi
  Ma'ana ra'ayin mutum ya sanja  zuwa son rai da sha'awa .
   Malik Dan Anas yana cewa: "  duk lokacin da wani mutum ya zo mana mafi jayayya yana so mu maida abin da Jibrilu ya zo mana da shi  zuwa ga manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi"  .
       Yanzu zan zauna a bayan kasusuwa na  sun girgiza *** Ahalin mutuwa ta kasance ta fi kusa zuwa gare ni.
                                     Ina jayayya ga dukkan wani  mai cin karo mai yawan musu ***  na sanya addinin shi ya zamana abin da zai taba mini addini na .
                                   Na bar abin da na sani sabo da ra'ayin wani   na   a   hali  kuma  ilimi  na  yakini   ba daidai  yake da ra'ayin wani ba.
                                 Ni ban zame mai shiga cikin husuma ba *** wacce  za ta tunkude daga hagu zuwa dama.
                                      Kuma hakika an  sunnan ta mana wasu sunnoni   tsayayyu*** Wanda  zai sanya lahani ga dukkan wani  kofa  ko  kuma   wani  lokaci.
                 Gaskiya  ta kasance  bata boyuwa  *** tana bayyana  a  goshi kamar    yanda   safiya   ke   bayyana .
                                   Tafarkin jahamu bai kasance ya zamana  madadi a gare mu ba***  bisa  tafarkin  Dan Aminata  amintacce    .
       An karbo daga Abdullahi dan Dailami ya ce : (    Lallai farkon tafiyan addini shi ne barin sunna  ,   addini zai tafi sunna bayan sunna  ,  kamar yan da  igiya  ke tafiya gaba  bayan  gaba .
    Abubakar Siddik Allah ya yarda da shi ya ce : '' Ban kasance mai barin wani abu da Annabi ya kasance yana aikatawa ba  face sai na yi aiki da shi  , kuma lallai ni ina tsoron  na bar wani  abu daga umarnin sa ya zama na karkace ''.
       Ku  tabbata ya ku bayin Allah  akan  littafi  da sunna  da shari'a  da addini  da kuma dabi'u da halaye kyawawa  ku kiyaye masu batarwa,   masu tada fitina ,  ku kiyaye su kar su  fitine ku daga  wani sashi na daga abin da Allah ya saukar  a gare ka .
Ya  Allah muna rokon ka tabbatuwa  akan al'amari da kuma  azama bisa shiriya.