الجمعة، 20 أكتوبر 2017

SON KASA A MUSULUNCI

HUDUBAR JUMA'A  A  MASALLACIN ANNABI  NA SHAIK HUSAINI AL-ASSHAIKH  30-1-1439 AH
HUDUBAR  FARKO
     Na daga cikin abu mafi tsada a gun masu hankali akwai son garin da aka haife su cikinta suka rayu suka ci daga albarkatun da Allah ya sanya cikinta.
Lalle wannan wani abu ne da shariar musulunci ta tabbatar da ita, kuma ta iyakance ta da kulawa da wasu hakkoki da wajibabbu  don kulawa da maslahar addini da duniya gaba daya.
Hakika son kasa da rai abu ne da ke hade kamar yadda kur'ani ya siffanta su, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Kuma da dai lalle mu mun wajabta musu cewa "Ku kashe kanku ko ku fita daga gidajenku" da ba za su aikata shi ba sai kadan daga gare su)
Kuma Allah Madaukakin sarki yace : (Allah ba ya hana ku daga wadan da basu yake ku ba sabo da addini  basu fitar da ku daga gidajen ku ba ga ku kyautata musu ku yi musu adalci.)
 Ibnul Arabi ya na magana kan kissar Musa Amincin Allah ya tabbata a gare shi da komowa  ga iyalansa sai yace : " A dawo wa ga kasa  akwai  wabcewa daga gumurzu da tsallake rijiya da baya da samun kwanciyan hankali.
Batun son kasa da kaunar gida ya sa Annabi ke cewa Makka  yayin kaurarsa  a halin bakin ciki da nuna tsananin kauna :(Abin mamaki da dadin ka (garin Makka) da soyuwarka  gare ni! ba don mutanen garin sun kore ni ba da ba zan zauna a waninka ba.) Tirmizi ne ya rawaito.
Haka kuma yayin da Allah ya nufe shi da kauratowa , ya wayi gari Madina ya zama garinsa wurin rayuwar sa sakonsa ya haskaka garin  sai ya ce : (Ya Allah ka sanya mana kaunar Madina kamar yadda ka sanya kaunar Makka a gare mu ko fiye da haka.)Bukhari ne ya rawaito.
A cikin siffanta zababbun halittu bayan Manzanni  Allah Madaukakin Sarki ya bayyana halin sahabbai da suka yi hijira daga garin Makka zuwa Madina sai ya ce : ( Ku yi mamaki ) Ga matalauta masu hijira wadanda aka fitar daga gidajensu da dukiyoyinsu, suna neman falala daga Allah da yardarsa, kuma suna taimakon Allah da Manzonsa, wadannan su ne masu gaskiya.)
Ya ku Musulmi!
     Na daga cikin ni'ima mafi girma ga bawa samun zaman lafiya a garinsa cikin aminci tare da iyalansa, yana mai bautawa Ubangijinsa, ya na biyayya ga Mahaliccinsa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ("Wanda ya wayi-gari a cikinku da aminci ga ransa, ko a cikin jama'arsa da iyalansa da dukiyarsa, ya wayi-gari da lafiya a cikin jikinsa, ya wayi-gari a wurinsa akwai abincin yininsa, to kamar an hada masa duniya ne gabadayanta".
Ya ku Musulmai ! Lalle son kasa a musulunci na nufin kiyaye mutuncin kasar da kyawawan dabiu da tsarkakan ginshikanta, wato yana nufin taimakekeniya gurin janyo dukkan alheri da gyaran kasa da mutanenta, da tunkude dukkan wata barna da wahala ga kasar da mazaunanta, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ku ma ku taimaki juna a kan aikin kwarai da takawa).
Lalle son kasa na nufin ko wani daidaiku ya rayu da 'yan uwansa cikin kauna da soyayya da tausayi da jinkai, don amsa kiran Allah madaukaki  (Lalle muminai 'yan uwan juna ne) da kuma fadin Allah mai tsarki (kuma mumunai maza da mumunai mata sashensu majibincin sashe ne , suna umurni  da alheri  kuma suna hani daga abin da ba a so kuma suna tsayar da salla kuma suna bayar da zakka kuma suna da'a ga Allah da manzonsa wadannan Allah zai yi musu rahama .) kuma manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi  ya ce :( Misalin Muminai cikin kaunar juna, da tausayin juna da tausasawa juna, kamar Misalin jiki daya ne. Idan wani sashin jiki babu lafiya sai sauran jikin su kama zazzabi da kasa barci).
Lalle kauna ne da ke sanya wasiya da biyayya da tsoron Allah  da yin nasiha da juna  cikin abin da akwai alheri ga kasa da raya ta. Allah Madaukakin sarki ya ce : ( Lalle mutum na cikin hasara. Sai wadanda suka yi imani kuma suka yi aiki na kwarai kuma suka yi suka yi wa juna wasiyya da bin gaskiya, kuma suka yi wasiya wa juna da yin hakuri)
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Addini nasiha ce, ya fade ta har sau uku, sai muka ce: ga wa nene ya Manzon Allah? Sai yace : Nasiha ga Allah da Manzonsa da littafinsa da jagorin musulmai da sauran jamaa)
Lalle shanin son kasa abu ne da ke sanya bada kariya ga kasar da abubuwan cikinta masu kima, kowa gwargwadon karfinsa da yadda zai iya kuma gwargwadon nauyin da ke kansa.    Zuwa ga wannan ne alkur'ani  ke nu ni a fadin sa Allah mabuwayi da daukaka: ( Sai suka ce mai zai hana mu yi yaki a tafarkin Allah a halin an fitar da mu da 'yayanmu daga gidajenmu ?)
Kuma zuwa gare shi ne fadin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi     na cewa : ( Duk  wanda aka kashe shi yana kokarin kare dukiyar shi to, shi shahidi ne)
 Wannan shi ne son kasa wanda ke lizimtawa daidaikun al'uman da su shirya  su tari duk wani shirin da zai taba  dukiyar kasa da maslahohinta na addini da na duniya ,  ya kuma sosa amincinta da zaman lafiyanta , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Duk wanda ya ga abin ki , to, ya canza shi da hanunsa , to, idan ba zai iya ba to,  da harshen sa , to, idan bai iya ba  da zuciyar sa ).
 Ba makawa  yana daga cikin abubuwa da aka ki  akwai shirya makirci don taba akidar kasar  da amincin ta  da zaman lafiyanta  ko kuma a taba dukiyanta da albarkatunta ,
son da Musulmi ya ke yiwa kasan sa yana sanya shi ya lizimci kiyaye dukkan wani kadarorin kasar sa da albarkatu kuma ya yi kokari domin samun aminci cikin abubuwan da yake samu kamar yanda ya ke son abubuwa da yake na maslahar kansa, da amfanin sa na karan kansa , :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce  :( Imanin dayanku ba zai cika ba har sai ya so wa dan uwan sa abinda ya so wa kansa )
YA 'YAN UWA MUSULMAI :
Yana daga cikin abinda yake  nuna kauna ga kasa a musulunci  ko wani daidaiku a cikin mutanen ta su kame daga cutar da ita ,  da kuma mazaunanta , ya zo a cikin sunna ingancecciya na daga cikin hakkokin hanya   a  gusar  da  kazanta  daga gare ta, ya zo a hadisai ingantattu daga Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi game da sanya kazanta  a farfajiyan mutane ko kan hanya ko wurin harkokin su,  to Musulmi a na bukatar  da  ya kasance  a cikin garin sa da iyalan sa  kamar yanda Annabi ya yi nusar a fadin sa  :(  Musulmi shi ne wanda musulmai suka kubuta daga sharrin harshen sa  da na hanunsa)
 YA KU MUSULMAI:
      Na daga cikin hakkoki na kasa da mutanen ta  a kan daidaiku,  da su kiyaye daga ha'intar kasan da kuma 'ya'yanta , da kuma ita al'umar kanta , lallai na daga  cikin mafi munin sifa na ha'inci  a kwai ribatar dama da ma'aikata su ke yi da masu matsayi don maslahan kan su , su fifita maslahar kan su akan maslahar al'uma , na daga cikin mafi munin barna akwai barnatar da dukiya , wanda shari'a ta zo da hani mai karfi akan hakan
 Allah madaukakin sarki ya ce :( Duk wanda ya ci gululi zai  je da abinda ya ci na gululin  a ranar kiyama )
 Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lalle wasu mutane  suna kutsawa a cikin dukiyar Allah ba tare da hakki ba , to, su na da wuta  a ranar alkiyama )
  YA KU MUSULMAI:
 Daga cikin hakkokin kasa a kanmu akwai taimakekeniya tare da  jagorori da Allah ya basu rikon wannan kasa , tare da gudanar da ita kasar,  a  yi gaskiya a gare su a bayyane da boye ,  kuma mu san cewa yi musu biyayya a abin da ba sabon Allah ba wajibi ne daga wajibabbu na shari'a. Kuma mu yi kwadayin hada kayin al'umarta da dunkulewar ta , ko wanne ya zama a shirye yake don kare kasar sa daga dukkan  wani makirci da ake shiryawa kasa , da kuma dukkan hanyoyi  da za su  iya taba amincin ta da kuma amanarta .


HUDUBA TA BIYU
      Tunda  ya tabbata  cewa  son kasa abu ne na dabi'a wacce shari'a ta tabbatar da shi to ta yaya kuma kasar da ta tattaro masallatai biyu masu alfarma a cikin ta da  kuma dakuna masu daraja  lalle wannan shi ne kasa mai tsarki wanda a ka gina ta akan musulunci, a manhajanta da  kuma kundin tsarin mulkin ta bisa  akida na tauhidi ciki da waje , alkalan ta na hukunci na shari'a , kotunan ta  na hukunci da shari'a mai tsarki , gari ne da ma'abotanta sun  rayu a kan sunna da girmamata , da kuma kore bidi'a da 'yan kanzaginta  .
To ya wajaba ga mutanen ta a hali suna samun irin wadannan ni'ima mai yawa da su yi taimakekeniya  bisa ga aminci da zaman lafiya , kuma su yi kwanton  dukkan wani   mai son rusa kasa , ko kuma son mai da dabi'unta irin na yammacin turai musamman a irin wannan  mawuyacin  yanayi , wanda  wata guguwa ke girgiza duniya gaba daya .
Ku kiyaye Allah ya kula ku bisa tabbatuwa cikin aminci, ya kuma bawa garin ku kariya  , daga wadannan fitintinu masu yawa.
 Ku kiyaye dukkan wasu kiraye –kiraye na sharri da barna  da kuma  hanyoyin da zai kawo rarrabuwar kai da raba tsakani .
      Ku kiyaye ya  matasa na wannan gari bisa abin da wannan gari ta saba, na tafiya a kan manhaji na sunna bayyananne tacecce, tsarkakekken da baya ketare iyaka ko wuce gona da iri ,  ba a san shi da wani manhaji ba na bidi'a , ko wani fandararren tunani , na daga cikin abin da zai sabawa  abin da aka gina wannan gari a kai  na kyawawan dabi'u na Musulunci , da halaye na shari'a , da kuma manhaja da mutane suka rayu a kai tsintsiya madaurin ki daya ,kuna masu  taimakekeniya akan dukkan wani alheri , masu haduwa akan  abu mai amfani  ga maslaha ga kasa da kuma bayi , irin taimakekeniya na gaskiya tare da iklasi ga  jagororin ta . Don cimma kyawawan manufofi da ake fata , kuma a tunkude duk barna da ake hasashe, kar ku canza abinda Allah ya ni'imta ku da shi har Allah ya canza muku yanayin ku , kamar yanda Allah madaukakin sarki ya ce  : (  Kuma Allah ya buga misali wata Alkarya ta kasance amintacciya  natsatssiya arzikinta yana je mata a wadace daga ko wani wuri sai ta kafurta da ni'imomin Allah , sabo da haka Allah ya dandana mata tufafin yunwa da tsoro sabo da abin da suka kasance suna sana'antawa ).  
      
                 




الجمعة، 6 أكتوبر 2017

FARAUTAR MATA DA KAI MUSU FARMAKI

HUDUBAR JUMA'A NA MASALLACIN ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI NA  16-1-1439 NA SHAIKH ABDULBARI AL-SUBAITI
HUDUBAR FARKO:
DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI
Bayan haka:
Musulunci ya karrama dan Adam  da  cikakken rayuwa ta natsuwa  da aminci da zaman lafiya da duk abin da ya kumsa,  shari'ar Musulunci ta siffantu da siffa ta kamala da gamewa na hukunce –hukuncenta ,  ta kuma kewaye al'umma da dukkan wata katanga da kyawawan halaye da dabi'u wanda zai kare ta daga dukkan bangarorin ta  ya janyo ta  zuwa ga kyawawan dabi'u  da ayyuka  nagari ,  wanda zai kauda ta ta yi nesa daga  munanan halaye da siffofi marasa kyau,  Allah madaukakin sarki ya ce : (( A yau na kammala muku addininku kuma na cika ni'ima ta a kan ku , kuma na yarda da Musulunci ya zamo addini a gare ku ))
   Koyarwar Musulunci  ya iyakance dukkan wasu laifuka ,   ta hanyar toshe sabubanta ,  da kuma hana abubuwan da za su janyo ta   , ya gama da ita tun tana karamarta ,  domin kariya da amincin al'umma ,  domin  kulawa  da hakkin daidaiku,  kamar yanda Musulunci   ya toshe kofofin bullan laifuffuka  ta hanyar bada tarbiya ga al'umma  bisa ga kyawawan dabi'u da halaye na gari  da kuma gina  kariya na fadawa ga tabarbarewan halaye ,  shari'a ta wajabta dokoki da kisasi  ,  da kuma   hukunci na horo don amincin al'umma gaba daya  Allah madaukakin sarki ya ce ((kuma kuna da rayuwa a cikin kisasi,ya ma'abuta hankula;   tsammaninku, za ku yi takawa)).
Na daga cikin manyan laifuka   da al'umma ke dandanan azabanta,  dukkan masu hankali sun yi tarayya bisa ga muhimmancin yaki da ita ko hana faruwanta  akwai  laifin  farautar mutunci 'yan mata da firgita su wanda zai kai   zuwa ga abin da aka haramta  ta hanyar batarwa ko cutarwa da yaudara ;  shi din wani banzan dabi'a ne   kuma barna ne  abin kyama ,  ana  amfani da shi wurin tafiyar da zuciya da tada sha'awa , wannan laifin na da illoli da suka kai makura ;  cutarwan ta mafi girma ya boyu ne cikin fadawa ga abin da Allah ya haramta , da kuma tada hankulan al'umma da kuma cututtuka irin na zuci  ga wanda abu ya shafa , wanda hakan yakan kai  zuwa ga fadawa   ga kololuwan sharri,   yakan zamar da mutum ya gangara da shi zuwa ga sharri mafi zurfi  ,  ko ma ya kai ga kashe kan shi .
 Tsawatarwa masu farautar mata da kai hari da farmaki  don keta mutuncinsu, masu isgilanci masu wasa , abu ne  da  ya ke na wajibi a shari'a  ,  kuma abu ne  da yake na tilas a zamantakewa . Allah Madaukakin sarki ya ce: (( Kuma wadan da suke cutar muminai maza da muminai mata, ba da wani abu da suka aikata ba , to lalle sun dauki  kiren  karya da zunubi bayyananne)).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Lalle mafi sharrin mutane matsayi  a ranar alkiyama a wurin Allah  shi ne wanda mutane suka kyale shi ko suka guje shi  don tsoron alfashan shi )).
Rikan farautar mata da kai musu  farmaki a matsayin laifi , da kuma yakansa  aiki ne mai daraja , kuma akwai tsaida hukunci na Allah  ta hanyar tsoratar  da duk wanda ya ke so ya kawo barna a doron kasa  ,  da kuma kunna wutar fitina , da kawo tashin tashina  ga aminci  ya kuma doge cikin bata ,  hukuncin Allah na kiyayewa mutane mutuncin su  da sum'ar su da kuma karamar su ; Nasa'I da Ibn Maja sun rawaito daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi  , cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce : (( Haddi da za a tsaida a doron kasa ya fi alheri ga mutanen bisa a musu ruwa na kwana arba'in))
  Ga kira na Alkur'ani mai girma ga muminai , da su yi nesa da bin hanyoyin shaidan  Allah madaukakin sarki ya ce (( Kuma kada ku kusanci abubuwan alfasha  abin da ya bayyana daga gare ta  da  abin da ya boyu))
 (( ya ku wadanda suka yi imani kada ku bi hanyoyin shaidan ,    Kuma wanda ke bin hanyoyin shaidan ,  to, lalle ne shi  yana umurni da yin alfahasha da abin da  aka ki )).
Dukkan wannan domin a toshe kofofin sharri ne  da kuma wanda  da ya ke kokarin yada alfahasha   a cikin wadan da suka yi imani .
 Kai farauta da farmaki ga mata  mummunar sifa  ce  da a ke samun su daga wadanda suke masu raunin hankali kuma wawaye , marasa lafiyan zukata ,  masu illa a dabi'u  kuma marasa mutunci , wadan da suke aikata ayyukan assha.
Laifi irin na kai farauta da farmaki ga mata   yana da salo daban-daban masu yawa , da hanyoyi  iri-iri  wanda ana fara shi ne da lafuza na batsa , da maganganu na fitsara , wanda masu aikata shi  ke yin shi,  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Ina muku gargadi da ku nisanci batsa  domin lalle Allah baya son masu batsa, da kuma masu neman ayi alfasha))  kuma ya ce:  (( Mumini bai zama mai yawan zagi ba ko yawan tsinuwa ko alfasha ko kuma batsa ba )).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ((  Ga ko wani dan Adam akwai wani kaso na daga zina ,  idanuwa biyu suna yin zina ;  zinan su kuma shi ne kallo,  hannaye biyu suma suna zina; zinan su kuma shi ne damka , kafafuwa biyu suma suna zina ; zinan su kuma shi ne tafiya , baki ma yana zina ; zinan shi kuma shi ne sumba, zuciya kuma na dimauta cikin fatan hakan, farji kuma sai ya gaskata ko kuma ya karyata shi )). Ahmad ne ya rawaito da isnadi ingantacce bisa sharadin Muslim
Idan mutum ya sakarwa  harshen sa linzami , da ya yi wasa  to, zai kai kansa ne bisa ga saraya a duniya    da kuma tsiyacewa  a lahira, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Ba ya lafazi da wata magana face a like da shi akwai mai tsaro halartacce)
Kuma ya ce : (ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah  ku fadi magana madaidaiciya).
Kai farauta da harin taba mutuncin mata ; wani ciwo ne mai game dukkan guri, ya ke kwankwasa dukkan kofa, kuma yana kara bazuwa a sararin samaniya, ba iyaka na wuri ko zamani,  da wasu  irin dabaru da ba a saba  da su ba, da makircin da ba a sansu ba  sai ya  ratsa cikin zuciya yana barna ya kuma gurbata hankali , ya bata kyakkyawan tunani .
 Daga cikin nau'uka na kai hari akwai amfani da  wasu hotunan bidiyo  na batsa ,  a kafafen sada zumunta  na yanar gizo, wanda a ciki akwai yada sharri  da  alfasha,  da kwadaitarwa mai ban tsoro zuwa gare ta  da cutarwa mai tsanani wanda ba za a iya siffanta shi ba , ((Lalle ne wadan da ke son alfasha ta watsu  ga wadan da suka yi imani , suna da azaba mai radadi a cikin duniya da lahira . kuma Allah shi ne ya sani , alhali kuwa ku ba ku sani ba  )).
  Masu yada wadan nan hotunan bidiyo kuma  suna masu tashi da  tallata  ta , makomar su ba kyau  , kuma karshen su abin bakin ciki ne  mai radadi : Allah ya kare mu da ku daga mummunan karshe ,   Allah madaukakin sarki ya ce: (( Domin su dauki zunuban su cikakku aranar kiyama , kuma daga zunuban wadan da suke bautarwa ba da wani ilimi ba .  to, abin da suke dauka na zunubi ya munana )).
Allah madaukakin sarki ya ce : (( Kuma lalle suna daukan kayan nauyin su ,  da wadan su nauyayan kaya , tare da kayan nauyin su , kuma lalle za a tambaye su a ranar kiyama ,  game da abin da suka kasance suna kirkirawa  na  karya   )).
Hakika cutan kai hari ga mutuncin mata da farautarsu ya yadu ne sakamakon bayyana sabo da sakaci da alfahari da kawata mummunan  abu,   kamar yanda  rashin kwanciyar hankali a gida ya ke saka 'yan mata  da yara  da mata  su zama abin farauta , mafi sauki a gun  masu kai farmaki da hari ga mutuncin mata .
Ma'abota shari'a da tunani da ra'ayi mai kyau sun san cewa lalle mafificin hanya na  kariya daga wannan mugunyar cutan, shi ne a dasa  kariya na addini  da kuma karfafan imani  da kuma bin koyarwar kur'ani , da lazimtar tsoron Allah a fadi da kuma  dabi'a da kuma runtse ido da sanya tufafi mai suturcewa , da tsarkake rayi  ta hanyar kamewa da kuma tsoron Allah. Baya boyuwa  cewa matasa suna da wani karfi  da fisgan kai na samartaka , to, amma idan ya samu saiti da nusarwa  da jan ragama , sai ya dawo kan hanyar da ya dace , tunanin shi da natsuwan shi sai su daidaita, sai ya zama cikin masu kawo gyara da gini ga al'umma , wannan kuma yana taimakawa wurin bada kariya ga al'uma daga aikin  kai farmaki ga mutuncin mata .
 Kamar yanda aure da  wuri yana kosar da bukatu, ya kan hana zaman banza kuma yana bada kariya daga munanan halaye , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (( Ya ku taron matasa  wanda yake da ikon yin aure  a cikin ku , to, ya yi aure , domin shi din ya fi bada kariya ga runtsa ido da katange farji )).
Gina alaka mai karfi da amincewa tsakanin iyaye da yara ,  yana gina mutum akan halin da yake kai nakwarai  ya kuma ba shi karfin gwuiwa  akan kyawawan dabi'un sa , kuma ya  gina mishi mazantakan shi ya cire mishi irin  dabi'un  mata , yana tarbiyantar da 'yan mata bisa ga kamun kai da suturcewa  da hijabi , amma iyalan gidan da ba su damu da  dulmuya acikin matsalolin zamani da  cin karon al'adu  da rarrabuwa kawuna ba , to   kamar wani sarari ne na shanya da masu farautar mata da kai farmakin suka samu  don kai farmakin  



    HUDUBA NA BIYU:
 Yana daga cikin abin da ya dace   a yi tsokaci a kai  kula da ba da muhimmanci kan tarbiyan yara  da kuma  rashin sakaci da su , musamman  lokacin da a ka hangi wasu munanan halaye da ake shakku a kansu.
  lalle yaki da farauta  ko farmaki ga mata da dukkan laifuka nauyi ne da ya rataya a kan kowa ,  a cikin al'uma ,  duk wanda bai ji tsawatarwan kur'ani ba da kira na imani ba to fa dole ne a wannan lokaci  ayi anfani da bulala ta hukuma.
 Hakika ya zo daga Usmanu Allah ya kara yarda a gare shi, ya ce : Lalle Allah na tsawatarwa da karfin mulki irin tsawatarwan da baya yi da kur'ani

        
    

.