الخميس، 21 سبتمبر 2017

RIBATAR DAMA A RAYUWA TA HANYAR BIYAYYA GA ALLAH

Hudubar Masallacin Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi 2/1/1439 H
Na Sheikh Abdullah Bin Abdurrahman Albuaijan
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda sammai da kasa na shi ne, gare shi al'amura ke komawa, godiya da yabo da kyakkyawan ambato da wanzuwa nashi ne, kuma gare shi zaa koma, tsarki ya tabbata gare shi ya horar da rana da wata suna karbar juna ya kuma hore muku dare da wuni kome gare shi a kaddare ya ke.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya mulki da godiya na shi ne, yana rayawa kuma yana kashe wa kuma shi rayayye ne ba ya mutuwa, alheri na hanunsa kuma mai iko ne ga dukkan komai.
Na shaida Annabi Muhammadu cikamaki ne na Annabawansa  da Manzanninsa, an turo shi a lokacin da ba Manzanni  sai ya isar da sako ya kuma bada amana ya yi nasiha ga al'umma, ya yi jahadi don Allah hakkin jahadi har mutuwa ta zo mishi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da iyalansa da sahabbansa  wadanda suka yi hijira daga gidajen su da dukiyoyinsu suna neman falala na Allah da yarda.
 Da Ansar da da suka mallaki gida da imani suna son wadanda suka yi hijira zuwa gare su, basu jin wani bukata daga ransu cikin abin da su bada ko sun kasace mabukata.
Da kuma wadanda suka bi sawunsu su ka bi su da kyautatawa,da aminci tabbatacce mai yawa har zuwa ranar alkiyama.
Bayan haka! Lalle mafi gaskiyan zance shi ne littafin Allah mafi karfin abin riko shi ne kalmar takawa, mafi alherin addini shi ne addinin Ibrahim, mafi kyan kissoshi shine Alkur'ani, kuma mafi kyan shiryarwa shine shiryarwar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, mafi al'amura shi ne fararrunta, dukkan bidiah bata ne.
Ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah hakkin tsoronsa, kar ku mutu face kuna musulmai)
Ya ku bayin Allah!
Duniya gidan jarabawa ne da karewa  ita kuma lahira gida ce na sakayya da wanzuwa, duniya jindadi ne na rudi, wasu sa'oi ne da kwanaki da watanni da shekaru  da zama shekaru na karewa  wasu zamuna n su zo su riska, ranaku su shude, watanni su zo su wuce, Allah na juya dare da wuni, a hakan akwai abin lura ga masu basira.
Zamani na karewa  gurace gurace na karewa , kuma ajali na cika ( kuma duk wanda ke kan ta na kare wa, fiskan Ubangijinka ne zai wanzu ma'aboci daraja da daukaka ).
*Wallahi duniya ba gidan wanzuwa ba ne* A'a ko da mutane sun gina benayenta
*Shekaru na shan banban sai dai * suna mai tsawon kwana da gajere na  daidaita  a yayin mutuwa.
Nesa ba kusa ba gidan duniya ba gidan da ake  fatan wanzuwa ba ne , farin- cikinta bai cika, mutuwa abin buri ne ga dukkan rayuka * ga mai hankali ba banbanci tsakanin benayenta da kaburanta
Yaku Musulmi!
Shekara ta kare, kuma shekarun duniya na raguwa, ga ajali na kusantowa , an rufe ayyukanta,  an nade takardunta, Madalla da barka ga wanda ya ribaci damanta, ya ribaci lokacinsa. Ya gyara ayyukansa.
Ku saurara ga mu mun shigo  farkon sabuwar shekara , wanda zai  tattara mu zuwa kabari  ya tunkuda mu zuwa ga ranar tadawa da tattarowa.
To ya dace ga duk mai zuciya da wanda ya kasa kunnen shi, ya ribaci dama ta rayuwarsa kafin nadama da da na sani, da zubar da hawaye ya riske shi, (Kada wani rai ya ce ya nadama ta akan abin da na yi sakaci a cikin  sashen Allah, kuma lalle na kasance hakika daga masu isgili,ko kuma (kada) ya ce ; da Allah ya shiryar da ni da na kasance daga masu takawa, ko kuma (kada) ya ce, a lokacin da ya ke ganin azaba da lalle ace ina da wata komawa zuwa duniya.) domin in kasance daga masu kyautatawa).
 Ya ku bayin Allah!
Lalle lokaci na shudewa rayuwa na ta tafiya, kuma rayuwar lokaci ne kankani, ga wajibabbu sun taru, ga hakkoki sun cunkushe mutum abin tambaya ne game da rayuwarsa  yadda ya tafiyar da ita da samartarsa yadda ya gudanar da ita. Kuma zaa yi mar bincike game da yadda ya sarayar da rayuwarsa, da zamanin da ya daidaitar, duk yadda shekuru ya  tsawaita to lokaci ne kankani,  ( Ya ce nawa ku ka zauna acikin kasa na kidayar shekaru? Suka ce , mun zauna a yini daya ko rabin yini sai ka tambayi masu kidanyawa. Ya ce ba ku zauna ba face kadan da dai kun kasance kuna sani, shin to kun yi zaton cewa mun halitta ku ne da wasa  kuma lalle ku zuwa gare mu ba za ku koma ).
Ya ku bayin Allah !
Lalle Allah bai halicce ku don wasa ba , kuma bai bar ku haka kawai ba, hakika ya halicci mutuwa da rayuwa domin ya jarraba ku. Ya nuna waye daga cikinku ya fi kyawun aiki.
Ku saurara! Lalle  mafi girman musiba , kuma mafi tsananin wahala  da kuma abu mafi tada hankali da bakin ciki mafi firgitawa  , shi ne ; hasara bisa sarayar da lokaci  ,  da kwacewan ajali   da cudewan sa'o'I na zamani ba tare da aiki ba ,  hasararta na farawa ne da nadamar tata  tun daga lokacin halartowar magagin mutuwa , (   Har idan mutuwa ta je wa dayan su sai ya ce : '' Ya Ubangijina ku mayar da ni ( duniya). Tsammani na  in aikata aiki na kwarai cikin abin da na bari , kayya , lalle ne! ita kalma ce shi ne  mafadinta alhali kuwa a baya gare su akwai shamaki har ranar da za a tayar da su''.
''Ya     ku wadanda suka yi imani kada dukiyoyin ku da 'ya'yan ku su shagaltar da ku daga ambaton Allah , kuma wanda ya yi haka , to wadannan  shu ne masu hasara , kuma ku ciyar daga abin da muka azurta ku daga gabanin mutuwa  ta je wa dayan ku har ya ce ya Ubangijina  don me ba ka yi min jinkiri ba zuwa wani ajali makusanci, domin in gaskata kuma in kasance daga salihai !    kuma Allah ba zai jinkirtawa wani rai ba idan ajalin sa  ya zo kuma Allah masani ne bisa abin da kuke aikatawa ''.
     To lokacin rayuwa -bayin Allah- wata dama ce na aiki  kuma  ni'ima ce da take wajabta yin godiya   ( Idan za ku kidaya  ni'imomin Allah ba za ku iya lissafa ta ba)     
Mafi alherin cikin ku shi ne wanda shekarun shi  ya tsawaita kuma ayyukansa suka kyautata, Mafi sharrin ku shi ne wanda ya yi tsawon rayuwa kuma ayyukansa  ya munana.
Ku saurara ! lalle na daga cikin godiya ga ni'ima ribatan ni'ima na lokuta , da rayuwa cikin da'a wa Allah  mabuwayi da daukaka daidai  yanda ya shasr'anta wa Annabin sa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.
 A daya bangaren kuma yana daga cikin kafurcewa ni'ima ,  da sababi na bala'I da  azaba  da  hasara da kuma nadama   akwai tafiyar da lokaci da ruwa cikin sabawa Allah , ko kuma cikin abin da Allah bai shar'anta ba , (  To wanda ya aikata (wani aiki) gorgodon nauyin zarra   na alheri zai gan shi .  kuma wanda ya aikata    gorgodon nauyin zarra zai ganshi .
 Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin alkur'ani mai girma.
    HUDUBA  TA  BIYU
Dukkan yabo da godiya  sun tabbata ga Allah  Ubangijin talikai ya kammala mana addini  kuma ya cika mana ni'imomi ,  kuma ya yardar mana da Musulunci a matsayin addini , na shaida ba  abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya , wanda ya hada Allah da wani hakika ya bata ,   bata mabayyani.
 Na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne , tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi da aminci tabbatacce mai yawa.
 YA KU MUSULMAI
Lalle farkon wata na hijira na shekara shi ne watan Almuharram kuma wata ne mai alfarma  Allah madaukakin sarki  ya ce:  ( lalle   ne kidayan watanni a wurin Allah wata goma sha biyu ne a cikin littafin Allah ,  a ranar  da ya halicci sammai da kasa , daga cikin su  akwa hudu masu alfarma , wannanne addini madaidaici    sabo da haka  kada ku zalunci kawunan ku a cikin su )
 An karbo daga Abu bakrata Allah ya kara yarda a gare shi  daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ''  Lalle zamani ya juyo kamar siffan shi a ranar da Allah ya halicci sammai da kasa  shekara watanni goma sha biyu , cikin su akwai guda hudu masu alfarma  uku a jere su ke :- Zulkada, Zulhijja da Almuharram,  da Rajab  na MUDAR  wanda ke tsakanin Jimada da sha'aban) Bukhari da Muslim ne su ka rawaito.
Ya ku Bayin Allah!
Na daga cikin koyarwar Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma na daga cikin masu kankare  zunubai da kuma  godiya ga Allah , da kuma girmama shi , akwai azumtar ranar ashura  , shi ne goma  ga watan Almuharram .
 An karbo daga  Dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su, ya ce: '' Ya yin da  Annabi ya  zo garin madina ya sami yahudawa  suna azumin ashura sai ya tambaye su game da hakan sai suka ce ; wannan rana ne da Allah ya bawa  Annabi musa nasara da Banu Isra'ila a kan Fir'auna , kuma mu muna azumtar shi don girmamawa gare shi   sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi  ya ce: '' mu muka fi dacewa da musa akan ku , sai  Manzon Allah ya yi umarni da azumtar shi ''. Buhari da Muslim ne su ka rawaito shi
 Kuma daga gare shi ya ce :'' ban taba ganin Annabi  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana kirdadan azumin watarana ba ,  wanda ya fifita shi akan wanin shi ba face wannan ranan    na ashura da wannan wata  yana nufin watan ramadan ''.  Buhari ne ya rawaito
 Ya zo a cikin sahihu Muslim Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : '' azumin   ranar Arfa ina fata Allah ya kankare  zunuban shekaran kafin shi ,  da kuma shekaran da take bayan shi, da azumin Ashura ina fatan Allah ya kankare shekaran da take kafin shi''.
 Ya yin da  labari ya sami  Annabi   a  karshen rayuwan shi  , kan cewa yahudawa na rikan ashura a matsayin idi  , sai ya nufi  ya azumci  tara da  goma a shekara  mai zagayowa ,  sai mutuwa ta shiga tsakani , 
An karbo daga Abdullahi dan Abbas  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: a yayin da Annabi ya yi azumin ashura   ya yi  umarni da azumtar shi sai suka ce  :'' ya Manzon Allah Yahudu da Nasara su na girmama shi  ,  sai Manzon Allah tsira da  amincin Allah su tabbat a gare shi ya ce  : idan Allah ya kai mu badi za mu azumci tara ''. yana nufin tare da goma   .  ya ce : shekaran bata kewayo ba har Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya rasu.''   Muslim ne  ya rawaito
 Abin da ya fi falala shi ne a yi azumi  guda kafin shi, sabanin na yahudawa  in hakan  bai samu ba to a yi azumin ranar goma.
Ya Ku Musulmai !
Bidia fitina ce, fitina kuma jarabawa ce,  mafi sharrin al'amura su ne fararrunta , dukkan bidi'a bata ce    dukkan bata na wuta , to ku yi riko da igiya mai karfi da tafarki mikakke,  kada ku bi hanyoyi ,  sai su kawar da ku daga tafarkin 
ku yi riko da littafin ku da shiryarwar Annabin ku , to hakika an isar mu ku,.
 (Sabo da haka ka yi riko ga abin da aka yi  wahayi da shi zuwa gare ka, lalle ne kai kana kan hanya madaidaiciya. Kuma shi (Abin wahayin ) ambato ( na daukaka ) ne a gare ka da kuma ga mutanenka, kuma za a tambaye ku.)
Ya ku Musulmai !
 Lalle abin nan da mabarnata  suke shiryawa, mujirimai ke tsarawa, makirai da mahassada ke gudanarwa, na daga makiyanmu da makiya addinin mu da garuruwanmu  wasu tawaga ne na 'yan jarida da farfaganda irin na shaidan, da kai wa mummunan hari , da wani kazamin makirci suna yi ne don karanbawul ga zaman lafiyanmu, da wargaza hadin kanmu, da kunna fitina a garuruwanmu, a tsakanin sahun mu, da keta alfarmar watanni  masu  alfarma, da warware alkawari,da janye mubaya'a da fita daga da'a da barna a doron kasa, mun gani da idanuwarmu  yadda kasashe makwabta suka koma,  na daga rugujewa, to  ku yi lura ya masu basira!
Ya Allah ka kiyaye wannan gari ya zama cikin aminci da zaman lafiya, ya Allah ka kiyaye garin daga fitintinu, ya Allah ka kiyaye shi daga makircin masu makirci, da sharrin mabarnata, da  sharrin makiya da mahassada,
Ya Allah ka kiyaye garin da sauran garuruwan musulmai, ya Ubangijin talikai,
Ya Allah ka taimaki musulmai a Borma ka kare jinin su kuma ka suturce al'auran su , ka basu aminci a abin da suke tsoro  ka yi gaggawan yaye musu bakin ciki .
 Allah ka datar da jagoran al'amarin mu mai hidima ga masallatayya biyu masu alfarma   da datarwarka , ka karfafe shi da karfafanka.
Ya  Allah ka datar da shi da mataimakin shi , da abin da a cikin shi akwai gyaran garuruwa da bayi  da abin da  a cikin shi akwai alheri ga musulunci da Musulmai , ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka kiyaye mana iyakan mu , ka bawa sojojin mu  nasara  ya Ubangijin talikai.
Ya Allah ka warkar da marasa lafiyan su , ka karbi matattun su, ka kiyaye su da kiyayewarka, ka kare su da kariyarka .
BAYIN ALLAH  ( Llle Allah  na yin  umurni da kyautatawa,  da  bai wa ma'abucin  zumunta , kuma yana hani da alfasha  da abin da aka ki , da rarrabe jama'a . Ya na yi muku gargadi,  dammaninku,  kuna tunawa.
(Kuma ku cika da alkawarin  Allah idan kun yi alkawari,  kuma kada ku warware rantsuwoyin ku a bayan karfafa su,  alhali kuma hakika kun sanya  Allah mai lamuncewa a kanku .  Kuma lalle Allah ne  ya ke sanin abin da kuke  aikatawa) .  


  

الخميس، 7 سبتمبر 2017

TUSHEN KARBAR AIKI IKHLASI

Hudubar Jumaa a Masallacin Annabi  na Sheikh Abdul Muhsin Alkasim 17 ga zulhijja 1438 AH
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da kuma munanan ayyukanmu, Duk wanda Allah ya shiryar babu mai batar da shi, wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzonsa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatace mai yawa.
Bayan haka!
Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah hakkin tsoronsa,ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.
Kadaita Allah da bauta shine manufa na halittawa da umarni, Allah Mai tsarki da daukaka ya ce :(Ban halicci Aljani da mutane ba face su bauta min) Da hakan ne za a raya kasa, kuma dan Adam ya samu walwala, Allah Madaukakin sarki ya ce :  (wanda ya yi aiki na kawarai na daga na miji ko mace  yana mumini to zamu raya shi rayuwa na jin dadi  kuma mu sakanya mishi da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa )
Yana yarda da aiki na kwarai ya amince da shi, Allah Mai tsarki ne bai karba sai mai tsarki,
Tushen karbar aiki shi ne Imani da Allah da yin aiki don neman yardarsa, Allah Mabuwayi da daukaka ya ce : (kuma wanda ya nufi lahira kuma ya yi aiki sabo da ita irin aikinta alhali kuwa yana mumini, to wadannan aikin su ya kasance godadde.)
 Aikin kafiri a lahira abin mayarwa ne ko da wani irin aiki ya yi, Allah Madaukakin sarki ya ce :(kuma muka gabata zuwa ga abin da suka aikata daga aiki sai muka sanya shi kura watsattsiya )
A duniya zaa ciyar da shi da kyakkyawan ayyuka da ya aikata, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :(Amma shi kafiri zaa ciyar da shi da kyakkyawan abin da ya aikata don Allah a nan duniya, har idan ya koma lahira sai ya zama bai da wani aikin lada guda da zaa saka mishi.) Muslim ne ya rawaito.
Aisha Allah kara yarda a gare ta ta ce :Ya Manzon Allah! Dan Jud'an ya kasance a lokacin Jahiliyya ya na  sada zumunci kuma yana ciyar da miskinai ko wannan zai amfane shi? Sai ya ce : Ba zai amfane shi ba,sabo da bai taba cewa :" ya Allah ka gafarta min kusakurai na a ranar sakayya"  ba ko da rana daya )  Muslim ne ya rawaito.
Wanda ya bayyana Musulunci ya boye sabanin haka a zuciyarsa ba zai amfana ba da abin da ya bayyana ba kuma zaa maida masa da aikinsa ba zaa karba ba. Allah Madaukakin Sarki ya ce game da halin munafukai : (Ku ciyar bisa kuna so ko akan tilas ba za a karba daga gare ku ba lalle ne ku kun kasance ne mutane fasikai. Kuma ba bu abin da ya hana a karbi ciyarwarsu daga gare su face domin su sun kafirta da Allah da Manzon sa.)
Kaiwa da komowar ibada ya dogara ne a kan niyya da aiki, kuma sharadin karbarta ita ce tsarkake niyya da kyautata aiki, da Ikhlasi ne manufa ke yin kyau  da bin sunna ne ayyuka ke daidaituwa, Allah Madaukakin sarki ya ce : (sabo da haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da Ubangijinsa to sai ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bautawa Ubangijinsa).
Kuma addinin Musulunci an gina shi a kan tushe ne guda biyu, : da a bauta wa Allah shi kadai ba shi da abokin taryya, kuma mu bauta masa da abinda ya shar'anta, shi ne abin da Manzon Allah ya zo da shi, tsira da amincin Allah sau tabbata a gare shi. Kuma wannan shine hakikanin shahada biyu, kuma sune rukunai biyu na karbabbun aiki.
Jarabawa a duniya ya doru ne bisa tabbatar ikhlasi da bin sunna, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Allah wanda gudanar da Mulki ya ke ga hannunsa, ya tsarkaka kuma shi mai iko ne akan kome. Shi ne wanda ya halitta mutuwa da rayuwa domin ya jarraba ku, ya nuna waye  daga cikin ku yafi kyawun aiki) wato wanda ya fi ikhlasi da yi daidai, Fudail dan Iyad Allah ya mishi rahama : " Lalle aiki idan ya kasanceAllah kadai aka nufa amma ba a kawo shi daida da koyarwar sharia ba to ba zaa karba ba, haka kuma idan an yi shi daidai amma ba ikhlasi to ba za a karba ba, ba za karba ba har sai ya hada ikhlasi da bin sunna, Taceccen aiki shi ne wanda aka yi don Allah, shi kuma daidai: shi ne idan an yi shi bisa koyarwar Annabi.
Hakikanin ikhlasi shi ne bawa ya nufi yardar  Allah a biyayyarsa, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Ka bauta wa Allah kana mai tsarkake addini a gare shi)
To duk abin da musulmi  ya ke yi na da'a  an umarce shi  ne da ya aikata shi tare da tsarkake shi ga Allah Ubangijin talikai,ba zai nemi sakayya ko godiya daga wani halitta ba, Gyaruwan zuciya shi ne tushe gurin karbar aiki, aiki na gyaruwa ne idan niyya ta yi kyau, niyya ce uwa uba na wadannan aiki ita ce niyya , kuma mutum niyyarsa na kai shi inda aikin shi ba zai kai shi ba, ta iya yiwuwa aiki karami amma niyya sai ta maida shi babba, ko kuma aiki babba amma niyya ta mai da shi karami.
Yahya Bin Abi kasir Allah ya mishi rahama ya ce : (ku koyi niyya don tafi tasiri bisa aiki)
Dukkan ibadar da baa yi ikhlasi ba da kyakkyawar badini ba to ba a karbar ta, ikhlasi bai haduwa a zuciya tare da kaunar yabo da kyakkyawan ambato, da kwadayin abin da ke hanun mutane, bin Annabi sharadi ne a gun karbar aiki, in an rasa shi to aikin abin maidawa ne ga mai shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Duk wanda ya aikata aiki ba umarnin mu a ciki to an maida mishi da kayansa).Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Sa'id Bin Jubair Allah ya mishi rahama  ya ce : (Ba a karbar fadi sai da aiki, ba za a karbi aiki ba sai da fadi, ba za a karbi fadi da aiki da niyya ba sai da bin sunna )
Sanya tsoron Allah a cikin ayyuka na daga sababi na karbar ayyuka Allah Madaukakin sarki ya ce : (Allah na karba ne daga masu takawa) 
Musulmi na da tsananin tsoro ga kan sa,kada ya zama bai cikin su,ba za a karbi aikinsa ba,wannan shi ne halin magabata, Abu Darda Allah ya kara yadda a gare shi ya ce : (Da na samu yakinin Allah ya karba sallah ta guda   yafi min duniya da abin da ke cikinta sabo da Allah na cewa : " Allah na karba ne daga masu takawa".
Wanda  ya ji tsoron Allah da ikhlasin aikinsa  da kuma bin sunna, to ya dace Ubangiji  mai karamci ya karbe shi.)  Sheikhul Islam Allah ya mishi rahama ya ce : (A gun Ahlussunna waljama'a ana karbar aiki daga wanda ya ji tsoron Allah a cikinsa  ya yi da ikhlasi don Allah yana bin daidai da umarnin Allah,duk wanda ya ji tsoronsa a wani aiki to zai amsa masa ko  da yana sabo a waninsa, wanda bai ji tsoron shi ba a cikinsa ba zai karba masa ba ko da yana mishi biyayya a waninsa.)
Yin da'a bayan da'a alama ce ta karbarta, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Kuma wadannan da suka nemi shiryuwa (Allah) ya kara musu shiryuwarsu kuma ya basu (sakamakon takawarsu).
Alhasan AlBasri Allah ya mishi rahama ya ce : (Na daga sakayyar kyakkyawa a bi ta da kyakkyawa, na daga ukuba ta mummuna a bi ta da mummuna,  abin mamaki da kyakkyawa  ta biyo mummuna don za ta goge ta, tir da aikata mummuna bayan kyakkyawa don zata lalata ta, ta debe albarkarta. Wanda bai kasance cikin kari na da'a ba to kuwa yana cikin ragi
Saukin ibada ga ma'abocin shi  da kaunan aikin alheri albishir ne na duniya,Allah Madaukakin sarki ya ce: (To amma wanda ya yi kyauta kuma ya yi takawa, kuma ya gaskata kalma mai kyau, to za mu saukake masa har ya kai ga sauki)
Tsayuwa a kan aiki da tabbatuwa akan da'a dalili ne na alheri da dace,Ibnu kasir Allah ya yi mishi rahama: ( Allah na tafiyar da al'adarsa cikin karamcinsa bisa wanda  ya rayu a kan abu zai mutu a kai,in har ya mutu a kan wani abu to  za a tashe shi a kai ranar Alkiyama.)
Na daga koyarwar Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai  dawwama a kan aikin alheri  ya kasance yana cewa : (Mafi soyuwar aiki a gun Allah shi ne wanda aka dawwama akai ko dan kadan ne.)Bukhari da Muslim ne suka rawaito
Gyaruwar gabbai da daidaituwarta na daga cikin fa'ida na karbuwar aikin daa , da kaunar ma'abocinta, Allah Madaukakin sarki ya ce  a hadisin Alkudsi : (Ba abin da bawa na  zai kusance ni da shi da ya fi soyuwa a gare ni kamar abin da na  farlanta mishi bawa na ba zai gushe yana kusanta na da nafila har na so shi,idan na so shi sai na zama jin shi da ya ke ji da shi da ganin shi da ya ke gani da shi da hanun shi da yake damka da shi da kafarsa da ya ke tafiya da ita kuma idan ya roke ni zan ba shi, in ya nemi tsari na zan bashi tsari )Bukhari ne ya rawaito.
Shanin mumini kokari cikin ibada da ganin aikin shi kankani, idan ya kammala wani biyayya sai ya sadar da wata ibada,bai nunawa ga Ubangijin shi yawan aikin sabo da in an kwatanta da abin da ya yi mar na ni'ima ya bashi kadan ne,) Allah ya ce : (kada ka yi kyauta kana neman kari) Duk wanda ya shaida hakikanin rububiya da hakikanin Ubudiyya, ya san Allah Ubangijinsa zai bayyana a gare shi, shi ,ba kome ba ba ne, ba wanin mu da shiga Aljanna a cikin mu don aikin shi sai dai da falalar Allah da karamcin sa da rahamarsa. Ibnu Abu Mulaika Allah ya mi shi rahamayace : " na riski  talatin daga cikin sahabbai kowannen su na tsoron munafunci a kansa, ba wani daga cikinsu da ke cewa yana da imani irin na Jibrilu da Mika'il "
Istigfari bayan da'a da bayyana gajartawa hali ne na bayin Allah masu ikhlasi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Sun kasance a lokaci na dare kadan su ke yin barci,kuma alokacin asuba suna ta yin istigfari)
Ibnul kayyim Allah ya mishi rahama ya ce : (Alamar karbar aikin ka shi ne ka rena aikin naka ka kankantar da shi, ka kalle shi karami a zuciyarka har ya kai wanda ya san Allah zai rika neman gafara a karshen aikin sa na daa).
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya kasance  idan ya sallame daga sallah yana neman gafarar Allah sau uku"
Kuma Allah ya umarci bayin sa bayan aikin hajji da neman gafara, ya kuma ya yabe su sabo da neman gafara a karshen tsayuwan dare, Manzon Allah ya shar'anta a karshen Alola tuba da istigfari, duk wanda ya shaida wajibin Ubangijinsa da gwargwadon aikinsa,da laifin kansa to dole ne  ya nemi  gafarar Ubangijinsa daga gare shi ya kuma rena kansa da aikinsa ya dauke su ba komai ba  ya rena kansa.
,    Allah ya yabi bayinsa da fadinsa  :( Da wadanda ke bayar da abin da suka bayar alhali kuwa zukatarsu  suna tsorace domin suna komawa  zuwa ga Ubangijinsu  )
Aisha ta ce ya Manzon Allah ! shin su ne su ke shan shan giya suna sata, sai yace a'a ya 'yar siddik sai dai su ne wadanda suke azumi suna sallah suna sadaka amma suna tsoron kar baa karba musu ba (Wadancan suna gaggawar tsere a cikin ayyukan alheri  alhali kuwa suna masu tserewa zuwa gare su(Ayyukan alheri)Tirmizi ne ya rawaito
Shi Mumini yana hada Ihsani da tsoro, Abdul'Aziz Dan Abi Rawad (Na riske su su na kokari cikin ayyukan kwarai idan su aikata shi sai su shiga damuwa na shin ko za'a karba musu ko a'a,)
Na daga cikin abu mafi girma na sababin karbar aiki da samun biyan bukata akwai rokon Allah hakan, to Ibrahim daIsma'il Amincin Allah ya tabbata a gare su a halin suna daga tubalin dakin ka'aba kuma suna rokon Allah, (Ya Ubangijin Mu ka karba daga gare mu lalle ne kai kai ne Mai ji Mai sani,)
To 'yar Imrana ta yi bakancen abin da ke cikin ta don hidima ga Masallacin Aksa, ta kasance tana adu'a  tana cewa : ( ya Ubangiji na lalle ne ni na yi bakancen abin da ke cikin ciki na gare ka ya zama 'yantacce, sai ka karba daga gare ni.lalle ne kai kai ne mai ji , masani ).
Annabi ya yi laiha sai ya ce : Ya  Allah ka karba daga Muhammad da Iyalan Muhammad    da kuma daga Al'umar Muhammad) Muslim ne ya rawaito.

 Godiya tafarki ne na karbar aiki, kuma kofa ne na kari Allah ya ce : (kuma alokacin da Ubangijinku ya sanar Lalle ne idan kun gode ina kara muku)
Kuma bayin Allah na cewa  :( Ya Ubangiji na ka kange ni domin in godewa ni'imar wadda ka ni'imta a kai na da kuma a kan Mahaifa na biyu, kuma domin in aikata aikin kwarai, wanda ka ke yarda da shi, kuma ka kyautata mini a cikin zuriya ta, lalle ni na tuba zuwa gare ka kuma lalle ni ina daga masu sallamawa  (ga umarninka)
Sai Allah ya musu alkawari da fadinsa  ( Wadancan ne wadanda muke karba daga gare su, mafi kyawun abin da suka aikata kuma muke gafarta mafi munanan ayyukansu,(suna ) a cikin 'yan Aljanna akan wa'adin gaskiya wanda suka kasance ana yi musu alkawari (da shi).
 Musulmi na kodayin a karba masa aikinsa kuma ya na kokari don  tabbatar da haka kuma yana taka tsantsa don tsananin  tsoron lalacewan aikin da rushewansa,  ba wai ya tsaya a aiki kadai ba a'a amma al'amarin ya hada da kiyaye aikin  bayan gama shi daga abin da zai bata shi ya rusa shi, mafi girman shi shi ne hada Allah da wani, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Da sun yi shirki da hakika abin da su ka kasance suna aikatawa ya lalace )
Mutuwa cikin ridda na rusa aiki, Allah Mabuwayi da daukak :(Kuma wanda ya yi ridda daga gare ku ga barin Addinin sa,har ya mutu alhali kuwa yana kafiri to wadannan ayyukansu sun baci a cikin duniya da lahira)
Kuma kin addini na rusa aikin mai shi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (wannan sabo da lalle su sun ki abin da Allah ya saukar domin haka ya bata ayyukansu).
Kafirci da Allah da haduwa da shi na sanya laacewar aiki Allah Madaukaki ya ce : (kuma wadanda suka karyata game da ayoyin mu da gamuwa da lahira ayyukansu sun baci )
Duk wanda ya bi abin da zai fusata Allah ya ki neman yardarsa Allah zai saka masa da ga irin aikin sa sai ya rusa aikinsa Allah Madaukakin sarki ya ce : (wannan domin lalle su sun bi abin da ya fusatar da Allah kuma sun ki yardarsa sabo da haka ya bata ayyukansu)
Kuma munafunci aiki ne mai mummunan karshe da sharri, Allah ya ce : (wadannan basu yi imani ba sabo da haka Allah ya bata ayyukansu ).
A cikin sabawa Manzo Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ta hanyan saba umarninsa akwai bata aiki da rusa shi Allah Madaukakin sarki  ya ce : ( Lalle ne wadanda suka kafirta kuma suka kange daga tafarkin Allah kuma suka sabawa Manzonsa abayan shiriyar ta bayyana a gare su ba za su cuci Allah da kome ba kuma zai baita ayyukansu.)
Kuma daga sauti a gaban Annabi na bata ayyuka. (yaku wadanda suka yi imani kada ku daukaka saututtukanku bisa sautin Annabi kuma kada ku bayyana sauti gare shi a magana kamar bayyanawar sashin ku ga sashe, domin kada ayyukanku su bacialhali kuwa ku baku sani ba)
Alfahari da aiki da shisshigi  ga Allah,  yana suka ne ga bangare rububiya Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace ga da wanda yace da wani Wallahi Allah ba zai gafarta ma wane  ba, sai Allah ya ce   : wane ne ya ke yi min shisshigi  kan cewa ba zan gafarta wa wane ba to ni lalle na gafarta masa kai kuma na rusa aikin ka).Muslim ne ya rawaito
Riya na lalata aiki Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisi kudsi: (Ni na wadatu daga abokan tarayya duk wanda ya yi wani aiki ya hada ni da wani na a ciki to na bar shi da shirkarsa)Muslim ne ya rawaito.
Duk wanda ya zo gurin boka  ya tambaye shi wani abu to ba za a karba mishi sallan kwana arba'in ba) Muslim ne ya rawaito.
(Duk wanda ya bar sallar la'asar to aikin ka ya rushe) Bukhari ne ya rawaito
(Zalunci duhu ne ranar alkiyama).
Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,ya ce : ( Tsiyatacce wanda aka yi wa wasoso shi ne wanda zai zo ranar Alkiyama da sallah da azumi da zakka kuma ya zo yazagi wannan ya yi kazafi ga wane ya ci dukiyan wane, ya zubar da jinin wane ya duki wane, sai a bawa wannan dag kyawawan shi wancan ma daga kyawawan shi, idan kyawawan shi sun kare kafin a biya bashin da ke kansa, sai a dauki kusakuransu sai a dora mishi sannan a jefa shi a wuta.) Muslim ne ya rawaito.
Zunuban  boye na goge kyawawa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Na san wasu mutane magana cikin al'umata za su zo ranar alkiya ma da kyawawa  sun kai girman dutsen tihama   da hasken sa sai Allah ya maida shi Turbaya tarwatstse
Sauban Allah ya yarda da shi ya ce : ya Manzon Allah siffanta su gare ka fayyace mana su ka mu kasance cikinsu ahalin ba mu sani ba, sai ya ce : ( Ai su 'yan uwanku ne masu irin fatar jikin ku, suna rikan kamar yadda ku ke yi na daga dare, sai dai su mutane ne da idan sun kebanta da abin da aka haramta sai su keta alfurmarta) Ibnu Maja ne ya rawaito.
(Wanda ya riki kare inba na kare dabbobi ba ko farauta ko kare shuka ba za a rage a kowani rana ladan sa da ya kai kiradi.)Bukhari ne ya rawaito.
(Duk wanda ya sha giya to Allah ba zai karba masa salla ba na safiya na arba'in ) Ahmad ne ya rawaito.
Makurar hasara shi ne mutum ya zaci yana kan aiki mai kyau a halin yana kan sabanin hakan. Allah Madaukakin sarki ya ce : (kace ko mu gaya muku game da mafifita hasara ga ayyuka?(wadanda aikinsu ya baci a cikin rayuwar duniya ,alhali kuwa suna zaton lalle ne su suna kyautata (abin da suke gani)aikin kwarai?)
Bayan haka ya ku musulmai :
To Ita ibada da  kiyaye ta abin nema ne a musulunci, dawwama akanta har zuwa mutuwa tushe ne a sharia, Allah Madaukaki ya ce : ( Kuma ka bautawa Ubangijinka har mutuwa ta zo ma)
Ya wajaba akan musulmi kada ya guji duk wani aikin alheri,ko da dan kadan ne, ya kuma nesanci dukkan munana ko da karama ce don bai san wace kyakyawan ce Allah zai jikan shi a dalilinta.bai kuma san wace mummunar ce Allah zai yi fushi da shi akan ta ba, ya wajaba ga Musulmi da ya tafi cikin ibadar sa yana mai tsakanin fata da tsoro, yana raya zuciyar sa da kaunar Allah da kyautata masa zato,
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa.
(Ka ce lalle ne salla ta da yanka na da rayuwa ta da mutuwa ta na Allah ne Ubangijin talikai, babu abokin tarayya a gare shi, kuma da wancan aka umarce ni, kuma ni ne farkon masu sallamawa)
Allah ya sanya min albari ka ni da ku a cikin Alkurni Mai girma,
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah bisa kyautatawarsa.godiya ta tabbata bisa datarwarsa da baiwarsa, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya muna girmama shaninsa, kuma na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma Manzon sa ne, tsira da amincin Allah ya tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacce mai yawa,
Ya ku Musulmai!
Ku kasance kun fi kula da karbar aikin akan shi kan shi aikin, ku kiyaye abin da zai tafiyar muku da da'a  daga abin da zai lalata shi ko ya rage shi, duk wanda yayi aiki mai kyau to ya godewa Allah da ya datar da shi zuwa ga aikata  wannan aiki, kuma ya roke shi tabbatuwa da dogewa a kai,kuma kiyaye da'a ya fi aikata ta. Kuma bin lura shine na karshe, shi wanda ya san Allah yana kuma bauta masa zai sanya a cikin biyayyar sa wani abu da zai rika tsarkake mishi rayinsa ta hanyar lazimtar ibada,
Da gaskiya da kubutaciya kuma  da kankan da kai lafiyayyar zuciya,da kyawawan dabiu zai so alheri ga waninsa kamar yadda ya ke so wa kansa, kada ya aminta daga Makru na Allah kuma kada ya yanke kauna daga rahamar Allah.

Sannan ku sani Allah ya  umarce ku da salati ga Annabinsa.