الخميس، 24 أغسطس 2017

Gyaran zahiri da badini (Ciki da Waje

Hudubar  Juma'a na Masallacin Annabi na sheikh Abdulbari Bin  Awad  Assubaiti 3/12/1438 AH

Hudubar farko
Allah ya halicci mutum a cikin mafi kyawun tsayuwa, ya mar ni'ima da sura ta bayyane mai kyau, da na ciki daidaitacce mai daraja.
Allah Madaukaki ya ce : (Ya kai mutum me ya rude ka game da ubangijinka Mai karimci ? wanda ya halitta ka sa'annan ya daidaita ka ya kuma tsakaita ka. A cikin kowace irin sura ya so gina ka a kanta)
Cikan kyan dan Adam na daga gyaruwan badinin shi, wanda ke bayyana kyan wajen shi. Tsabtatuwan ciki na bayyana  amfanin  tsarkin waje.
Ko da ya ke mutane sun fi damuwa da abu na bayyane don shi ne makurar sanin su, amma shi Allah ya fi la'akari da na badini game da dan adam, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle Allah bai dubi ga surorin ku ko dukiyarku, sai dai yana dubi  ne ga zukatanku da ayyukanku)
A duk lokacin da aka fi kyautata  badini wurin karfin  alaka  da Ubangiji sai a samu kauna da karbuwa, ba wani bawa da ya kyautata cikinsa da son Allah Madaukaki face ya samu karbuwa  ta zuci a sama da kasa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Lalle idan Allah ya so bawa sai ya kira Jibrilu yace : Lalle ina son wane ta ka so shi! Sai Jibrilu ya so shi, sannan ya yi yekuwa a sama, ya ce : Allah na son wane to ku so shi! Sai na cikin sama su so shi, sai a sanya mishi karbuwa a doron kasa.)
A ranar Alkiyama ; za a kwalkwale hisabi ciki da waje na bayi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (kuma kada ka bi abin da ba ka da ilimi game da shi, lalle ne ji da gani da zuciya dukkan wadancan (Mutum) ya kasance daga gare shi wanda ake tambaya,)
Wannan fahimta mai zurfi zai sanya musulmi ya gyara badinin shi, wanda ya ginu a kan tsarkaki niyya ga wanda ake bautawa, don niyya ne sirrin bauta , kuma ginshikin bautawa Allah na zahiri yana ga kyautatuwan bin Manzo da koyi da shi, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ka ce idan kun kasance kuna son Allah to ku bi ni Allah ya so ku, kuma ya gafarta muku)
 Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Dukkan al'uma ta zasu shiga aljanna sai wanda ya ki, sai suka ce ya Manzon Allah wa zai ki? Sai ya ce : Wanda ya bi ni zai shiga aljanna wanda ya saba mini to hakika ya ki.)
Ibada na tarbiyantar da  musulmi a zahiri da badini, wanda ya lura da koyarwar Annabi zai ga akwai kulawa da ciki da waje, na daga cikin haka akwai tsayuwar musulmai gaba ga Ubangijinsa da daidaita sahu da la'akari da ita na da ga cikin tsaida sallah, hakika ya tabbata daga gare shi ya kasance ya na umartan mutane da daidaita sahu  ya na cewa ya ku bayin Allah ko dai ku daidaita sahun ku ko Allah ya rarraba fiskoki.
Muna gani cikin ayyukan hajji kulawa da tsarkake zahiri da tsaftace badini, to fitan musulmi yana nufan yin hajji ya dumfari dakin Allah mai alfarma yana nuna mana mafi girman sura na amsa kiran Allah ciki da waje, tufafi da niyya da talbiya da ambaton Allah na dada tabbatar mana da hakan.
 Allah Madaukakin sarki ya ce : (Hajji watanni ne sanannu cikinsu to babu jima'I kuma babu fasikanci  kuma babu jayayya a cikin hajji kuma abin da kuka aikata daga alheri Allah  ya san shi kuma ku yi guzuri to mafi alherin guzuri yin takawa kuma ku bi ni da takawa ya ma'abuta hankula  سورة البقرة 197
 Kamar yadda Manzon Allah Almusdafa  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fito da hakan a fili a hudubarsa ta hajjin ban kwana inda ya bayyana mana matsayin abubuwa na badini a musulunci, kuma shine abin da Allah ke sa ido akai, yana cewa : (Ya ku mutane ! ku saurara  lalle Ubangijinku guda ne kuma mahaifinku daya ne, ku sani ba fifiko tsakanin balarabe da ba'ajame  haka farin fata bai fi bakar fata ba haka jar fata bai fi bakin fata ba kuma bakin fata bai fi jar fata ba sai da tsoron Allah)
Musulmi an umarce shi da ya nesaci sabo na bayyane da na boye Allah Madaukakin sarki ya ce : (  Ka ce abin sani kawai Ubangijina ya hana abubuwan al-fasha abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya boyu ) سورة الاعراف 33
Lalle tsaftar zahiri da tsarkake badini na kai wa ne ga tsaftace matattarar al'umar musulmi da kuma sifantuwa da kyawawan halaye da kyautata dabi'u, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Kuma Allah ne ya fitar da ku daga cikunan iyayenku ba da kuna sanin kome ba kuma ya  sanya muku ji da gannai da zukata tsammaninku za ku gode  سورة النحل 78
     Duk wanda ya gyara zahirinsa ya tsaftace badininsa  to zai yi kokari kar ya saba abin da yake kira a kansa na shiriya da halaye na mutunci da alheri, Allah Madaukakin sarki ya ce :( Shin kuna umurnin mutane da alheri kuma ku manta da kanku alhali kuwa kuna karatun littafi ? shin ba za ku hankalta ba)  سورة البقرة 44
Cikin alakar musulmi da dan uwansa musulmi a zahiri da badini akwai ya fiskance shi da fara'a da runguma sa'annan ya ya yi mishi adua na alheri a boye cikin tsarkin zuciya, ya so wa 'yan uwansa alheri  ya kuma bayyana kauna tare tsarkake zuciya game da shi, Manzon  Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Ba wani bawa musulmi da zai yi adu'a ga dan uwan shi musulmi a boye face Mala'ika ya ce : Kai ma kana da kwatankwacin hakan)
Musulmi shi ne wanda musulmai suka kubuta daga sharrin harshensa da hanunsa a bayyane kuma  suka aminta daga hasadarsa da  kullinsa a zuci, Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(kar ku yi hasada kar ku yi munajasha (cinikin ingiza mai kantu ruwa) kar ku yi gaba da juna, kar ku yanke wa juna, kada wanin ku ya yi ciniki a kan cinikin wani, ku zama bayin Allah 'yan uwan juna, Musulmi dan uwan musulmi ne ba zai cuce shi ba, ba zai tabar da shi ba, ba zai yi mishi karya ba, ba zai rena shi ba)
'Yan Uwantaka  na hukunta taimakawa musulmi ga dan Uwansa  Musulmi da harshe da rubutu a bayyane, a boye kuma a zuciya da tunani.
Ya wajaba ga dukkan musulmi ya taimaka game da al'amuran musulmi da dukiya da matsayi da shawari da adua,  (Kuma lalle Mun aika zuwa ga al'ummai daga  gabaninka sai muka kama su da tsanani da cuta tsammaninsu za su kankan da kai) سورة الانعام 42
 Idan musulmi zai zartar da wani hukunci bai dace a gare shi ya yi ta bibiyan sirrin mutane ba ko ya dora wa kansa nauyin haka ba ko farauto abin da ya boyu daga gare su ba, to Allah shi ne mafi sanin abin da ya boyu, kuma hisabin su na kan wanda ba abin da ke boyuwa a gare shi,   Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( An umarce ni da na yaki mutane har sai sun shaida ba abin bauta da gaskiya sai Allah kuma Muhammadu Manzo ne na Allah su kuma tsaida sallah su bada zakkah, to idan sun yi hakan to kare jininsu daga gare ni, sai da hakki na musulunci, kuma hisabin su na kan  Allah Madaukai).
Neman kutsawa cikin badinin musulmai da hukunci game da abin da ke zukatansu  keta alfarmansu ne, wanda hakan zai kai ga sakaci game da mutunci musulmi da halasta jinin su, Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Gushewar duniya wallahi ya fi sauki gurin Allah a kan kashe mutum musulmi,)
Hakika Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance yana muamalantar munafukai  da ke bayyana musulunci irin muamalar musulmai kuma yana gudanar musu da hukunci  na musulunci a zahiri duk da cewa ya san wasun su a boye munafukai ne.
Alamu na imani na bayyana a lokacin jarrabawa: ta hanyar  hakuri a zahiri da neman lada a badini, gabbansa ba za su wuce gona da iri ba ko ya yi rashin ladabi ga Ubangijinsa kuma Majibincinsa. Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lalle idanu na zubar da hawaye kuma zuciya na bakin ciki amma ba za mu fadi wani abu ba sai abin da Ubangiji ya yarda da shi, kuma lalle ya kai Ibrahim muna bakin cikin rabuwa da kai)
A wurin tsere zuwa ga aljanna ba a yin nasara sai an gyara ciki tare da muhimmancin waje, to da gyaruwan badini ne masu cin nasara suka yi fintinkau, masu isa suka haye suka kai gaci, Allah Madaukakin Sarki ya ce :  (Lalle wadannan da suka ce Ubangijinmu shi ne Allah sa'an nan suka daidaitu mala'iku na sassauka a kansu (a lokacin saukar ajalinsu suna ce musa ) kada ku ji tsoro kuma kada ku yi bakin ciki kuma ku yi  bushara da Aljanna wadda kun kasance ana yi muku wa'di da ita   سورة فصلت 30

Huduba ta biyu
Bayan haka ! na daga cikin yelwar rahamar Allah ya hore wa mutum  tasha ta karin imani da zai yi guzuri da abin da zai tsarkake badininsa ya kuma habaka zahirinsa, na daga ciki akwai wadannan ranaku masu girma masu albarka wanda lada ke ribanyuwa a ciki wato ranaku goma na zulhijja wanda ke da nunanun fa'idoji ga daidaiku da al'uma, ya zo a falalansu fadin Allah Madaukakin sarki  (Ina rantsuwa da Alfijri  da daruruwa goma) da fadin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ( Ba aikin da ya fi kamar na wadannan ranaku goma ) sai aka ce har jihadi? Sai yace ( ko jihadi ne sai dai mutumin da ya fita da ransa da dukiyarsa bai dawo da komai ba)Buhari ne ya rawaito
Kamar yadda kabar bari na saki waiwai sunna ne a goman zulhajji da sauran ranakun Sallah (Tashrik) tun daga shigar watan zulhajji  har zuwa  ranar karshe na Attashrik, shi kuma kabarbari kayyadaddu na fara wa ne tun daga asubahin ranar arafa har zuwa faduwar rana  na ranar karshe na ranaku Attashrik.
Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu akbar La'ilaha illallahu Allahu akbar wa lillahil Hamd
Na daga cikin ayyuka da a ke kusantar  Allah da  shi akwai yanka dabbar  laiha, hakika Imam Attirmizi da Ibnu Majah daga A'isha tana mai jingina shi ga Annabi (Ba wani aiki da dan adam zai yi a ranar babbar sallah da ya fi soyuwa ga Allah da ya  kai zubar da jini( wato yanka dabba ) don zai taho a ranar alkiyama da kahonsa da abin alamarsa da kofotonsa, kuma jinin na zuba a gurin Allah a wani wuri kafin ya zuba a kasa, to ku tsarkake kawunanku da shi) Hakim ya inganta shi a Almustadrak.

Ya tike.

الجمعة، 11 أغسطس 2017

KUNYA A MUSULUNCI

Hudubar Juma'a  a Masallacin Annabi  19-11-1438AH sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albuaijan
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya raba halaye a tsakaninku kamar yadda ya kasa arziki a tsakaninku ya sanya kyakyawan hali shine ma'uni na fifiko a tsakaninku                                                             na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke bashi da abokin tarayya yana da kyawawan sunaye da kuma siffofi madaukaka.
Na shaida Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi bawansa ne kuma Manzonsa ne, ya isar da sako, kuma ya sauke amana, ya yi nasiha wa alumma, ya yi jahadi don Allah yadda ya dace a yi jahadi har lokacin da mutuwa ta zo mishi .
Ya Allah ka yi dadin tsira da aminci a gare shi da iyalansa da sahabbansa da wanda  ya bi shiryarwarsa  ya kuma yi riko da sunnarsa har zuwa ranar sakayya.
Ya ku bayin Allah ku ji tsoron Allah, Mabuwayi da daukaka,domin takawa daukaka ne a nan duniya kuma guzuri ne a lahira.
(ya ku wadanda suka yi imani! In kun ji tsoron Allah zai sanya muku mararraba kuma ya kankare kananan zunubanku kuma ya gafarta muku. Kuma Allah ne Ma'abucin falala Mai girma)
Lalle duk da sabawan harshen su da launin su ko da kuwa sun kasance daga  Uba guda,to su kamar ma'adinai ne (da ake tonowa a kasa) wani na da fifiko kan wani haka wani nau'in ya dara wani, sabo da dabiu ne maauni na kyawawan halaye, kuma shi ne mizani na al'umu, kuma tsani zuwa ga daukaka, da kaiwa kololuwa, Manzon Allah ya yi gaskiya da ya ce :(Lalle zababbun ku su ne mafi kyan halaye a cikinku) Bukhari ne ya rawaito.
Ya ku bayin Allah ! Lalle addinin da muke dangantuwa gare shi addini ne na kyawawan dabiu. Kuma AnnabinMu Muhammad an turo shi ne don ya cika kyawawan dabiu, kuma biyu bisa ukun farfajiya na duniyan musulmai sun karbi musulunci ne ta hanyar kyawawan dabiu.
      kunya ne sarkin halaye nagari kuma, ba sabani kan  kunya ne abu mafi kyau da ado  a cikin kyawawan dabiu,                                                                                                                                                                                                             ya ku bayin Allah  kunya ita ce tushen kyawawan dabiu'kuma ita ce mabubbugan kyawawan halaye dukk wata falala ta boyu a cikin kunya wanda ya siffantu da ita  musuluncinsa ya yi kyau, haka nan kuma dabiu'.
Ita  za ta daukaka mutum ta sa ya  yi nesa daga sabo domin jin kunyan ubangijin shi dabia' ce mai daraja wanda ke haifar da aikata dukkan wani aiki mai kyaw ya hana mutun aikata aiki dukkan mara kyaw yasa mutun ya yi nesa daga dukk wani  aiki na kunya muna na da kuma ya yi nesa da abubuwa na minkari lalle shi din nan dalili ne da ke nuna girman hali da tsarkakan zuciya ga mutun kunya na tunkude mutun daga  aikata aikin ashshakuma kuma ya kare mai mutuncin shi ya dasa mishi kame kai a zuciyan shi shi kama wani ma'dini ne  mai tsada wanda ba mai siffantuwa da shi sai zukatanda suke na ayaba kuma kaman wani ado ne na annabawa an karbo daga abu masu'd Allah ya kara mishi yarda  ya ce: manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ce''Na daga cikin abinda mutane suka riska na maganganun Annabawan farko  akawai " in baka ji kunya ba to ka aikata abin da ka so ) Bukhari ne ya rawaito   
 kunya  alami ne na musulunci ko wani addini yanada wasu dabiu'                                       
Na daga cikin dabi'u na musulunci  akwai kunya,Ibnu maja ya rawaito kuma Albani ya inganta shi a cikin sahihuhu aljami 
Imani  yanki saba'in da dori ne kuma kunya  daya daga cikin yanki  ne na imani muslim ne ya rawaito
 Manzon Allah ya wuce wani mutumi yana zargin dan uwan shi sabo da yawan   kunya sai ya ke cewa lalle kai din nan kana jin kunya sai yana cewa har kaman hakan ya maka illa sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yake cewa kyale shi domin lalle kunya na daga cikin imani kuma babu imani ga wanda ba yi da kunya Bukhari ne ya rawaito
Kuma na daga cikin sirri ya ku bayin Allah da ke sanya kunya ta zama  a cikin imani saboda dukkan imani da kunya sun kasance suna kira ne zuwa ga alheri kuma suna kusantarwa zuwa gare shi kuma suna tunkudarwa daga sharri kuma suna  nesatarwa daga gareshi  kunya kofa ne daga cikin kofofin alheri.
An karbo daga Imran dan Husain Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Annabi tsira da amicin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Ita kunya bata kawo wani abu sai alheri ) kuma ya ce (kunya alherine dukkaninta ) muslim ne ya rawaito
Ya ku bayin Allah hakika manzon Allah ya tattaro dukkan siffofi  na mutanen farko da na karshe ya siffantu da dukkan sifa mafi daukaka da daraja har Allah ma ya ke ce da shi (lalle kai din nan kana kan dabiu' masu girma).
Manzon Allah ya  kasance mafi jin kunya a kan budurwa da ta ke cikin kafunta idan yaga wani abu da ya ki sai  a ga kin a fuskar shi ta hanyan kunya  ya lullubeshi
 ya ku musulmai lalle kunya daya daga cikin surori ne da darajoji mafi kololuwa a wurin Allah ta inda za ka ji kunyan a ganka wurinda ya haneka hakika kuma shi ya halicceka kuma ya daidaita ka kana jin kunyan ka yi amfani da ni'marsa da ya baka wurin saba mishi , Manzon Allah ya kwadaitar bisa ga kunya kuma cewa kunya daga Allah ne sai ya ce (ku ji kunya ya ku bayin Allah yanda ya dace a ji kunya sai suka ce ya manzon Allah dukkan mu muna jin kunya Ahamdu llillahi sai ya ce ba shi a ke nufi ba ana nufin jin kunya daga Allah yanda ya dace da  cancancin jin kunyarsa) wato kayi ya kiyaye abunda ya tattara ciki ya kiyaye abinda ya kumsa kuma a tuna mutuwa da karewa duk wanda ya nufi lahira zai bar kawan rayuwan duniya wanda ya yi haka to hakika ya ji kunyan Allah bisa cancancin kunyarsa  ) Hakim ne a mustadrak ya rawaito kuma ya inganta shi zahabi ya mar muwafaka kunya daga malayiku masu daraja da kuma masu kiyayewa masu rubutu da su shaida a gareka wato daga dama da hagu suna zaune ba abin da zai ambata  ko ya furta na fadi face  akwai mai kulawa tare da shi kunya na mutane shi ne ka keta dokan Allah da ya suturta a gare ka ka bayyana sabo a gabansu Annabi ya ce dukkan alummana ana basu lafiya suna kubuta sai wadanda su ke masu bayyana sabo kunya daga rayi daga gabbai domin su din nan sune zasu zama shaida a gareka sun yi musu da kai ranar alkiyama Allah ya ce ( ranarda harsunansu  za su shaida musu da hannayensu da kafafuwansu da abinda suka kasance suna aikatawa a wannan ranar ne Allah zai cika musu addininsu na gaskiya kuma su san cewa lalle Allah shi ne gaskiya kuma bayyananne )




 HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah mai kunya kuma mai suturcewa ya sanya daga cikin dabiu' masu daraja da kuma ya cika kyawawan dabiu' ta hanyan turo mai albishir kuma mai gargadi wato fitila mai haskakawa annabin mu muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi da aminci tabbatacce mai yawa ya ku musulmai lalle muna rayuwa acikin wata marhala na halaye wanda suke na kunci muna karshen zamani wanda wadan nan munanan dabiun sun yi rinjaye kuma sun yawaita shubuhohi dabin soye soyen rayuka sun yadu abunda da ya kasance  a jiya sanennen abune a yau ya zama shi ne  abin ki abunda kuma ya kasance abin ki a jiya ya zama shi ne abin so abinda aka saba da shi munanan dabi' sun sulale su shigo cikin gidaje ta hanyoyin nau'urorin  sadarwa  na zamani a wannan yanayi gashi ana fiskantanmu to ya wajaba mu  tarbiyyantar da masu tasowa kuma mu katangesu da akida na musulunci kyawawan dabiu' daga Allah ne kuma su din nan katanga ne daga cikin katanga wanda suke masu bada kariya kuma da aminci ga tarbiyya da tsarkake zukata da kuma murakaban Allah .
Ya ke musulma ya ke yar uwata mai daraja lalle kunya ko da ya kasance abu ne da ake nema a hakkin maza sai de kuma ya fi wajabta a kan hakkin mata a bangarenta yafi karfi domin lalle matanda ta ke bautawa  Allah da kyawawan dabiu'nta tana neman lada kuma tana jin tsoron ukubarsa  lalle kunya na daga cikin kyawawan dabiu' na addini kuma da ake tada mutane a kansu wanda ke lullube mace a cikin kafunta da shi tana ci tana sha kuma tana tufata shi kuma ta ke kai komo fita ta tafi tare da shi lalle kunya ga mace musulma shine hanun jarinta kuma kuma shi ne daukakanta kuma shi ke kiyaye karamarta kunya na janyo wa ya mace aminci da kuma daukaka da kuma kawa dalili ne kuma na nuna cewa ita kamemmiya ce haka nan kuma wani katanga ne mai katangewa mai karfi ya ke musulma Allah ya yi nuni a cikin littafinsa da kunya mace a kissan musa alaihi assalam ayayinda ya zo diba daga ruwan madyana  ta inda wata mace daya daga cikin diyar shua'ibu ta zana mana mana siffa daga cikin siffofi na kunya na daga ciki abinda annabi musa ya yi la'kari da shi na irin kame kanta da kunyanta da rashin cakudedeniyansu da mutane sai ya shayar da su Allah madaukakin sarki ya ce game da annabi musa  (kuma a lokacin da ya isa mashayar madyana ya sami wata jam'ar mutane suna shayarwa kuma a bayansu ya sami wadansu mata biyu suna korar (tumakinsu ).ya ce menene sha'ninku ? su ka ce ba za mu iya shayarwa ba sai makiyaya sun fitakuma uban mu tsoho ne mai daraja ) (sai ya shayar da su )
Shi kunya da kame wana daga cikin abubuwa ne na kunya kuma alamane na musulma kuma  dalili ne na kyakyawan tarbiyya ayan nan mai girma ta nuna mana misali daga cikin kyawawan dabiu shi wato kunya da kuma nitsuwa a dukkan kai komo  da zance Allah ya yabi daya daga cikinsu  , lokacin da ta dawo gare shi , sabo da abin da ta siffantu da shi na kunya, ba ta yi wani rangaji ko kwarkwasa ba , ba ta bayyana kwalliyanta ba kuma bata  rausaya murya ba, (  sai dayansu ta je masa  tana tafiya akan jin kunya ta ce: Ubana yana kiran ka domin ya sakanya  maka  ladan abin da ka shayar )

 YA KE MUSULMA :
Ga mahaifiyarki kuma abin koyin ki Aisha uwar muminai tana buga misali mafi kaye game da kunya , don ta kasance tana jin kunya har ma ta suturce daga rayayye da matacce ,  tana cewa :- na kasance na kan shiga dakin da aka binne Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata agare shi tare da Abubakar a cikin shi, ba tare da tufafi ba ,  sai nake cewa wannan  miji na  ne wannan kuma mahaifi na  ,   to a yayin da aka binne Umar wallahi ban shiga dakin ba face da tufafi na a daure a kai na sabo da kunya da nake ji na Umar .
 Kuma ta kasance idan ta zo daura da mahaya  a halin tana ihrami sai ta  sake jalbabinta a kan fiskanta .
Kuma ta kasance tana dawafi a dakin ka'aba  kamar  yanda ya zo a cikin littafi mai inganci  ba ta cakudaidainiya da su , a yayin da wata 'yar gidan ta take cewa da ita , na yi dawafi bakwai a dakin ka'aba kuma      na taba rukuni sau biyu ko uku sai Aisha ta ce, kar Allah ya baki lada , kina tuttunkude maza, ase ba za ki yi kabbara ba kawai ki wuce .
 YA KE MUSULMA :
Hijabin mace da kamun kanta na cikin addininta kuma yana cikin kyawawan  halayen ta , to, idan har fidiranta ya juya , ta shakala yin addinin ta sai ta yada kwarjallenta , ta yi wurgi da mayafinta , ta bayyana adonta  wuraren da za ta sa a fitinu da ita , tofa ta yi hasarar addinin ta kuma ta sarayar da amananta , an karbo daga Abu Huraira ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (nau'I biyu na mutane suna cikin 'yan wuta ban gansu ,   sai ya ambata daga cikin su , Matayen da suke sanya sutura amma suna cikin tsiraici , suna kuma jan hankalin mutane , masu karkatarwa ne kuma karkatattu, kayukan su kamar tozon rakumi , wanda suka karkace ,  ba za su shiga Aljanna ba ba za ma su ji kamshin ta ba , kuma a hali kamshinta a na jin shi tun daga tafiyan kaza da kaza ).

YA KU MUSULMAI :
(Dukkan ku masu kiwo ne , kuma dukkan ku abun tambaya ne bisa ga kiwonsu ,  na miji me kiwo ne akan iyalan gidan shi  kuma  abin tambaya ne game da  su ,  haka ma mace mai kiwo ne a kan gidan mijinta da kuma 'ya'yan shi ,   kuma ita abin tambaya ne game da su ,  ku saurara ! dukkan ku masu kiwo ne kuma dukkanin ku abin tambaya ne bisa ga kiwon da aka ba ku) Muslim ne ya rawaito
 Ya  Allah ina rokonka kunya da zai tsare ni daga saba maka ,
Ya Allah ka shiryar da mu bisa ga mafi kyan halaye ba mai shiryarwa  zuwa gare su sai kai , ka tunkude mana munanansu daga  gare mu , domin  ba mai tunkude munanan daga gare mu sai kai.
 Ya Allah muna rokon ka shiriya da takawa da kame kai da wadata .
 Ya Allah ka daukaka Musulunci ga musulmai ka kaskantar da shirka da mushrikai, ka taimaki bayinka masu Tauhidi ,