الخميس، 9 فبراير 2017

HUDUBAR JUMA'A A MASALLACIN ANNABI  13/05/1438AH, NA SHAIKH SALAH BIN MUHAMMAD AL-BUDAIR.
HUDUBAR FARKO:
Ya ku Musulmai:
Hakkoki tsakanin ma'aurata biyu ya ta'allaka ne da Kulla aure, wanda kuma ke lazimta kyakkyawar muamala  da juna, kada  ya jinkirta bashi hakkin shi ko ya ki  bada abin da ke kan shi. Kyautata muamalarsa ga abokin zamansa da tausaya masa da juriya bisa ga cutarwarsa sabo da fadin Allah (su matayen suna da hakki akan maza irin wanda mazan suke da shi akansu, da abin sani.)
Ita kyakkyawar mu'amala da kyakkyawan zama ya fi kawo sanyin ido, da kwanciyan hankali da daddadan rayuwa, Allah madaukakin sarki ya ce :- ( ku yi mu'amala da su da kyakkyawa)  ma'ana ku yi cakudedeniya da abota da su, da bishara da kuma sakin fiska , da bada hakkoki da aka farlanta, kamar na daga sadaki da ciyarwa da raba kwana, da barin cutar da ita da kakkausar magana , da bijire mata,  da karkata zuwa ga watanta,  da rashin hada mata fiska, da turmuke mata ba tare da wani laifi ba , sa'annan Allah na ladabtar da bayinsa da fadin sa (  sa'annan kuma idan kun ki su , to, akwai tsammanin ku ki wani abu, alhali kuwa  Allah ya sanya wani alheri a cikinsa mai yawa)  a cikin ayan kwai kwadaitarwa bisa rike su da kyautata zamantakewa da su, ko da mijin ya tsani wani abu daga cikin halayen su, domin rai ya ki abu ba ya nuni da kore alheri da wannan abu, ta iya yuwuwa  abinda rai taki ya zama shi ya fi maslaha a addini, kuma ya fi zamewa abun godiya a karshe , so da yawa abin ki kan komawa abin yabo, kuma abin yabo kan koma wa abin zargi,  miji kan tsani mata  sabo da wata sifa daga cikin sifofinta, amma kuma a rike ta din akwai wani alheri da yawa da bai sani ba,   kuma ba zai gane hakan ba, Abdullahi dan Abbas  Allah ya yarda da shi da mahaifin shi ya ce: ta iya yiwuwa Allah  zai azurta shi da Da daga gare ta , sai Allah ya sanya alheri mai yawa acikinsa .
Ya ku musulmai:
Lallai mutum yana da wahala ya samu wanda ya ke kauna  wanda bai da wani abu da ya ki tare da shi  ,  to yayi hakuri da abin  da ya ki sabo da abin da ya ke so,  yana da wahala ka samu mutane biyu  suna mu'amala ko wannensu ya yarda da dukkan dabi'un junansu, ba wasu mutane biyu da za su yi mu'amala  da junan su fa ce daya na kawaici dan uwansa an karbo daga Abu huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:-  ( Kada mumini ya tsani mumina, idan yaki wani hali na ta idan ya ki wani hali na ta to zai so wani hali nata Muslim ne ya rawaito) .
Wato kada  mutum ya ki matar sa ki na gaba daya wanda zai sanya shi ya rabu da ita ya sake ta ya warware kullin aure, to idan ya tsani wani hali nata mara kyau to kuwa zai samu wani hali nata abin yarda.
To  ya ku mazaje  ku riki matayenku kar ku yi gaggawan kosawa da sa'insa kar ku yi gaggawan rabuwa   kada ku yi gaggawa zuwa ga cika , kar ku kambama abu wurin nuna tsana da kiyayya  so dewa mutum rauni na hankali  yaka yi galaba a kanshi  fushi ya rinjaye shi  sai ya yi aiki na wauta ya yi gaggawa  ya yi cika sannan daga baya kuma ya dawo yana nadama a halin kuma wato kome ya tsere mishi  ya wuyata a gare shi,  ta koma gare ta daga cikin wadanda suka saki matan su  sannan rayin kuma tabi ta shiga damuwa akwai Qais Dan zarih in da yayi waka yana mai nuna hasara  cewa:-
Wayyo zuciyata da ta saki ginina  £ Rabuwa da abin ginina kamar wani yaudara ne
Masu kai komo a tsakani su suka kewaye ni su suka ruda ni £ kaito da mutanen da za su yiwa masu shiga tsakani biyayya  £  ga shi na wayi gari  cikin zargin zuciya ta ga wani al'amarin da ba ni da kuma yanda zan yi ba yanda na iya £
Kamar mutumin da  abu ya boyu a gare shi yana cizon yatsa  £ kamar mutumin da ya yi faduwa yayi asara yana ciza yaza £ sa annan kuma sai bayan ya  riga ya saida abinne sai ya gane ase faduwa yayi.
Ya ke mata mumina , kar ki zama cikin masu ci don tarawa, kuma ki zama kina yawaita zargi, mai yawan hayaniya da saurin fushi, wacce bata bin umarnin mijinta , kuma in ya yi rantsuwa bata biye mishi  , ki kyautatawa mijinki , ki kasance kusa da kaunarsa, mai taimaka masa yayin bukatarsa  mai amsa kiransa,  mai sauka zuwa ga bukatarsa  mai tuna falalarsa da   kyautatawansa, kar ki zama mai munana mishi mu'amala  , kar ki yi musu da shi yayin fushin shi da fusatan shi,  kar ki tsauwala mishi  yayin da ya cije ko ya harzuka , Mu'awiya Allah ya kara mishi yarda ya ce da Sa'asa'atu dan sauhan cikin mata wacce tafi soyuwa a gareka ? sai ya ce :- mai biyewa  abinda kake so, waccece kuma ka fi ki acikinsu ? wacce tafi nesa da abinda kake so , sai Mu'awiya ya ce :- wannan cin gyara na duniya kenan, sai Sa'a'sa'atu  ya ce:-Da  ma'auni na  adalci .
 An karbo daga abu Uzaina Assadafi    Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- (  masu tsananin kauna masu  yawan haihuwa , mai aikta  (abinda ka ke so) , muddin suka ji tsoron Allah , mafi sharrin matayen ku kuma sune masu bayyana tsiraici , masu alfahari sune munafukai, ba wanda zai shiga aljanna a cikin su, face kamar bakin hankaka.  Nasa'I ne ya fito da shi
 An karbo daga Abdullahi Dan  Mihsan daga wata gogon  shi cewa ta shiga wurin Manzon Allah sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  agare shi  sai ya tashi don wata bukata ,  sai ya biya mata bukatar tata , sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce mata ko ke  kina  da miji ? sai  ta  ce e,  sai ya ce   yaya kike da shi sai ta ce bana gajartawa ( a hakkinsa) sai abinda ya gagareni  sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- to,  ki duba matsayinki a gunshi domin shi ne aljannan ki kuma wutanki)  . Nasa'I ne ya rawaito shi
Idan rayuwa ta kasance ana rayatacike  da  kyawawan halaye ba kiyayya ba gaba, to ya haramta akan mace ta nemi cika , ko kuma ta nemi kul'i a daya daga cikin zantuttuka mafi inganci a magan ganun malamai an karbo daga saubana Allah ya kara mishi yarda ya ce:- Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi  ya ce  ( Dukkan matan da ta tambayi mijinta saki ba tare da wani laifi ba to, kamshin aljanna ya haramta a gare ta ) Ahmad ne ya rawaito.
An karbo daga Ukubata dan Amir Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :-( Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:-  lallai mataye wadanda suke wofantattu ,  masu  yin khil'I masu warware auren su sune muna fukai ) Dabarani ne ya rawaito shi    Ibnu kudama ya ce :- wannan yana nuni cewa haramunne  yin khul'I ba tare da bukata ba sabo da akwai cutarwa ga ita da kuma mijin nata ,  da kuma  gusar da maslahohin aure ba tare da bukata ba  , sabo da haka aka haramta.
Mustahabbi ne  a sulhu tsakanin ma'aurata  biyu wanda suke rikici da junansu an karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah ya kara yarda a gare su shi da mahaifinshi  cewa mijin  barira ya kasance bawa ana ce da shi  Mugithu kai kai  ka ce ina kallo zuwa gare shi ina dubi yanda yake shawagi a bayanta yana kuka  hawaye na zuba  a gemun sa  sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce ga Abbas :-  (  Ya Abbas baka mamaki irin kaunar da mugithu yake yiwa barira da kuma irin kin da barira take yiwa shi Mugith sai ya ce da ita da kin koma mishi sai ta ce ya Manzon Allah umarni ne ka ke min  sai ya ce a'a  sai dai kawai ina nema mishi shawara sai ta ce bani da bukata  zuwa gare shi  ).Buhari ne ya fito da shi. …       

Yana nuni cewa idan mace ta ki miji bai kasancewa ga waliyinta da ya tilasta mata kan zama da shi. Idan ta so shi kuma bai kasance wa ga waliyinta da ya raba su, Allah ya amfanar da mu da Alkur'ani da sunna da abin da ke cikin su na daga ayoyi da shiriya bayyanannu da wazi da hikima .
Ina neman gafaran Allah ku nemi gafararsa shi Ubangiji na mai gafara ne Mai kauna.
 HUDUBA TA BIYU
Ya ku Musulmai ! Allah ya sanya shika da warware igiyar da aka kulla tsakanin ma'aurata biyu a hanun miji, sai dai  ya haramta ya munana amfani da hakkin nasa cikin sakin da rikon sa wata hanya don ribatar ita matar da firgita ta, ya sanya shi kamar wata bulala ce a fiskar ta don ya bautar da ita da tsorata ta, da walakanta ta, Allah madaukakin sarki ya ce : ( To ku rike su da kyautata wa ko ku sake su da kyautata wa.) An karbo daga ASSUDI  kan fadinsa  (ko a sake su da kyautata wa) Da ya bata cikakken hakkinta kada ya cutar da ita, ko ya zage ta, wanda ya katange matarsa bai sake ba bai kuma barta ta yi aure ba idan iddarta ya kare, ya cutar da ita da duka, da kuntata mata, ko ya hana ta hakkokinta na daga ciyarwa da kason kwana, da makamancinsau don ta fanshi kanta daga gare ta sai ta yi to khulin ya baci kuma zaa maida mata abin da ta bada don fansan.    
(ba ya halatta a gare ku ku gaji mata a kan tilas kuma kada ku hanasu aure domin ku tafi da sashen  abin  da kuka basu ).
Idan ta zo da alfahasha sai ya hana ta aure don ta fanshi kanta daga gare shi sai ta yi hakan to khul'in ya inganta. Sabo da fadin Allah Madaukaki: (kuma kada ku hana su aure domin ku tafi da sashin abin da ku ka ba su, face idan suka zo da wata alfahasha bayyananniya.)
Ba ya dace wa rike wacce ba ta kamun kai, sabo da tawaya ne ga mijin a addinin shi da dabiunsa da bata sunansa da zubar da mutuncinsa, bai da amincin kada ta bata mishi shimfidinsa da jingina mishi wani da da ba nashi ba, kuma mace mai sakaci da hakkokin Allah na wajibi kamar sallah da makamancinta, wacce ba ta jin nasiha  Mustahabbi ne a sake ta.
Kuma rantsuwar shika na cikin rantsuwa na fasikai, wadanda ke rikan ayoyin Allah da izgilanci, Ibnul Arabi yace a cikin Ahkamul Kur'an : (Na daga cikin rikan ayoyin Allah da izgilanci abin da aka rawaito daga Abdullahi dan Abbas kan cewa an tambaye shi game da mutumin da yace da matarsa : Ke sakakkiya ce sau dari, sai yace : Ukun ya isan maka a gare ta, sauran casain da bakwai ka riki ayoyin Allah da su bisa izgili ).
Daga cikin mazaje akwai wanda  ya sanya furta shika da yawaita shi abin ambato a bakinsa kuma abin sabon shi da al'adan shi,da abu mafi soyuwa a gare shi a abu mai kima da mara kima da babba da karami da mai girma da abin da bai taka kara ya karya ba,sai yace : In kiyi magana da wane to mata ta ta saku,ko saku ya tabbata a gare ni idan na ci abincin wane. Ko shika ya tabbata  a gare ni muddin kika tafiya da wane, ko shika ta tabbata a gare ni muddin mata ta ta shiga gidan wane, ko yace wa bako: Shika ta tabbata a gare ni muddin baka ci abincin rana a gu na ba, wannan dare , ko kuma in gobe baka ci abincin dare a guna ba, amma ba shikan yake nufi ba, ko rabuwa ba, sai dai ya yi hakan ne kamar rantsuwa, don yana nufin kwadaitarwa ko hanawa,ko tilastawa, wadannan lafuza ne haramtattu da ayyuka ne na laifi, da walakanta rayuwan zamantakewa da rena hakkokin mace da yara da wasa da shika  da hukunce – hukuncenta.
Ya wajaba ga miji ya kiyaye harshensa daga yawaita furucin shika, da tsoratarwa da ita da jirwaye da kamar ruwa game da  aukar da shi.
Ku ji tsoron Allah ya ku Musulmai kada ku riki ayoyin Allah abin izgili kar ku ketare iyakokin Allah madaukaki duk wanda ke ketare dokokin Allah to ya zalunci kansa, kuma dun wanda ke katare dokokin Allah to wannan yana cikin azzalumai.
Ya kare.



ليست هناك تعليقات:

إرسال تعليق